hango wucewar wani abu cikin gidan. Bata tantance menene ba kawai sai tayi Saurin kama hannun mai gadin wanda yake kokarin juyawa wajen da idonta ya hango,hankalinsa ya bayar kanta ganin yanda ta rike mararta tareda sakin ɗan marayan nishi.
"Sannu baiwar allah,lallai kina ganin rayuwa kam,barina kawomiki ruwan koh"
Ɗaga kai kawai tayi,dan maganar ma ta gagareta.
Bace wa ganinta yayi ya nufi wani lungu na gidan,da alama anan zai samo ruwan. Zama tayi a bakin barandarsa inda ya barta tana maida numfashi.
A hankali cikin sanɗa suka samu nasarar shigewa gidan,ganin yanda wata mata ta samu nasarar ɗauke masa hankali.
A bakin kofar falon suka tsayah,inda ɗaya daga cikin su ta saka wani a bu a kofar makullin. Nan da nan kofar ta bude suka shige.
Rarrabuwa sukayi kowanne yayi wani wajen,hanyar balcony daya daga cikinsu yayi inda zai kaita dakunan dasuke wajen,kara kunnensa yayi a jikin kofar domin jin wannene na mai gidan.
Ganin sun dade amma basu ganoba yasa dayah daga cikinsu yah daga wayah tareda danna kirah
"Ogah mun kasa gane a wanne ɗaki fah yake,gashi kince karmu kuskura mu bari wani ya ganmu,tayah zamu gane ɗakin dayake toh?"
"Mtsww shiyasa fah nashiga aikinnan dan nasan sai kunyimin shirme,har yanzunku bazaku iyah gane yanda zaku fitar da kurege daga cikin raminsa ba,indai anan dabararku ta ƙare to zan san yanda zanyi daku,ƙanana ma in an basu aiki sun fiku iyawa, ku fito daga gidan kafin a ganku,zanji dashi ni,shiyasa fah nake aikina ni kadai babu ku"
"Kiyi hakuri v-lady zamuyi yanda ya dace sosai,kinsan abinne sai a hankali"
"Okay shikenan na baku minti ashirin ku fitomin dashi daga gidan,idan ba hakaba kuma zan tafi na barku ku kukasani"
Daga ta kashe wayar tana sauke ajiyar zuciya,sai a sannan na kula ashe dukkansu matane,tsabar kawai kwarewane da kuma taurin zuciya yasakasu yin abinda ba kowanne na mijinba.
Kiran sauran abokan aikin tayi tareda cewa,
Ɗayace daga cikinsu tace
"Kai ni tsiyata da itah idan wani ya ta'bota to ba sani ba sabo da ƴan uwanta,hmmm inka gane halintane zaka san ya take
Hakane kam,yanzuma tace ta bamu nan da miniti ashirin,mai kuke ganin za'ayi,hmmm gashi tace karmu yi wani abinda zai ta'ba iyalansa,da tuntuni mungama da shi fah"
Tafaɗa cikin ƙosawa,suma jugum sukayi,can sai taji ƙarar massage a wayarta,
Dubawa tayi ganin an saka v- lady,
"Yau yadawo kasar bayan wata biyu,dan haka dole idonsa biyu shida matarsa basuyi bacciba,a dakinsa zai zamo dole suke,saboda kowanne gida yawanci ɗakunan yara na kusada na matar gida.
Dole zakuji dakin yafi kama turaren Emergency,saboda shine turaren dayafi amfani dashi,ku shiga daƙin,kafin tayi wani abu ku fesamata maganin bacci,shima ku fesamasa sanann ku kawo minshi ina jiranku"
"Wow kuga yanda v-lady ta solver abinnan cikin ƙanƙanin lokaci,lallai dole mu sara mata,maza kuzo a kammala aiki"
Sakin hancinsu sukayi domin jin ta ina turaren yafi ƙarfi a gidan,dukkan su samun kamsu sukayi a bakin wata ƙofah wadda take ƙarshen wani corridor.
Dukkan su kallon kansu sukayi,tabbas hasashensu gaskiya ne,dan gashinan suna jiyo numfashinsu a ɗakin.
"Vl4 ki tsaya ta gefen dama,ke kuma Vl5 ki tsayah ta gefen hagu,bari na shiga,ina shiga kowaccenku sai tayi kokarin fesamusu kafin suyi wani ƙoƙari,clear?"
"Yesss Vl3,dukkan su suka haɗa baki.
Tana buɗewa kuwa suka feshemusu fuska da spray ɗin,faɗawa sukayi ta bayansu akan gadon,shikamma uban gayyar daga shi sai gajeren wandon daya samu damar gyarawa lokacin da yaji motsin shigowarsu.
Ɗaukar bargo sukayi suka jefawa matar tasa tareda kinkimarsa suka fita daga gidan.
Ta bakin get din suka zo suka wuce abinsu hankali kwance, Haɗa ido sukayi da matar da take zaune a wajen,ko kallonsu batayiba sai aikin nishinta take,duk kuwa da cewar akan idonta suka wuce ɗin.
Lokacin mai gadin ya kawo mata ruwan,ya tafi nemo mata magani suka wuce,shikuma sannan ya dawo.
"Sannu baiwar allah ya jikin dai,ko nayiwa hajiya magana su taimaka miki,dan naga kaman ko haihuwa zakiyi"
"Ahah baba ba haihuwa bace,kawai wahalar dana shane,watan haihuwar bai kama na tukunna,zan iyah amfani da banɗakinka idam babu laifi"
"Lahh ba komai ki shiga,barina ɗan zagaya kafinnnan"
"Toh nagode allah ya saka"
Bata daɗe da shiga sashennata ba saigata ta fito tana gyara zaninta wanda duk ya yage ,kallon mai gadin tayi wanda yake tsaye tareda cewa,
"Baba zan tafi,dan akwai tasha nan kusa,nasan yanzu wanda suke bina sun wuce,zan je da sassafe na kama hanyar ƙauyenmu,dan dama a wajen ƴar uwata nake anan"
"Da naso kiɗan zauna ganin yanda kike,amma tunda kince haka shikenan,gsshi kuma bansan sunan ki ba"
"Hhh baba kawai ka ƙirani da MABARACIYAH dan haka kowa ke ƙirana,dan nan ɗin ma barar mukeyi dana taho daga garinmu,saida nazo nagane ashe inada ciki na tsohon mijina da muka rabu"
"To shikenan allah ya bada lafiya ki kulada hanya"
Fita tayi a hankali kaman bazata iya kaiwa karshen layinba.
*____*_____*____*
Wata macece mai kaya riga da,zani na hausawa, ta fito daga wani lungu,kaɗan kaɗan ake ganin fuskarta saboda yanayi na dare sosai,a hankali take tafiya kaman mai tsoron kar wani ya ganta,saida tazo saitin wani lungun kafin ta shiga.
Wata leda ta ciro a wani kango ɗan nesa da gidan data fito.
Zanin jikinta ta cire ta jefar da kuma rigar,buɗe ledar tayi saiga baƙaƙen kaya sun bayyan irin na wanda suka dauƙi alhajin,saidai kuma nata akwai purple din macijiya (Viper)ta buɗe baki a bayan rigar ƙatuwa.
Nan da nan ta saka tareda daukar rikagar sanyi mai irin kayan itama ta sakata,sanann ta ɗau Hula da kuma baƙin glass.
Waya taciro a cikin aljihunta tareda yin magana cikin dakewa,
"Kuna ta wajen ina yanzu haka,dafatan babu wanda ya ganku ko"
"Eh V-lady babu wanda ya ganmu,muna karshen layin dakike tahowa".
Tafiya kaɗan kuwa tayi saigata ga baƙar mota,buɗe baya tayi ta shiga,motar ta tashi ta nausa kan hanya,dan dama jiran shigarta akeyi .
Sun dade suna tafiya har suka bar cikin gari suka shiga wani ƙyauye,a bakin wata bukkah suka tsayah a bayan garin.
Dukkansu fitowa sukayi yayinda ɗaya daga cikinsu ta kinkimi mutumin zuwa cikin gidan,yayinda wacce take tuƙa motar kuma ta koma da baya zuwa cikin gari.
Bukkar ƴar karamace bata wuce ace mutum ɗaya ne yake rayuwa a cikinta ba,saboda yanayin ƙanƙantarta da kuma yanda ta tsufah.
Babu komai a cikin bukkar sai fili mai rairaiyi(ƙasa).
Wani key wacce suke kira da v-lady din ta ɗauko tareda sakawa a wani dan abu dayake gefen bangon wajen kaman makunna.
Tsakiyar ɗakinne ya buɗe saiga wani rami ya buɗe,dukkansu faɗawa sukayi cikin wajen..
Boyyayar hanyace ta karkashin ƙasa,wacce zata kaisu wani waje daban,sunyi kaman minti biyar suna tafiyah a wajen kafin suka bullo a fili mai ɗauke da wani gini babba,saidai ba lallai ya ɗauki hankalin mutane ba.
Wasu matane a bakin kofar suka buɗemusu suka shiga.
Abin mamaki da al'ajabi,gidan ko kaɗan baya kama da yanda yake ta waje,saboda kofah kofah ce dashi,sannan kuma da wurare daban daban.
Wani ɗaki na karfe direct suka nufah da mutumin dayake rike a hannunnata,
"Ku dakata ,ina naga kuna nufin kaishine,a zatonku daɗewa zayyi kuke nufin kaishi kejin masu jimawa,ku ajiyeminshi anan"
Ajiyeshi sukayi suna kallon yanda yake sakin jiki saboda magananin bacci da har yanzu bai bar jikinsa ba,
Kujera taja ta zauna tareda ƙaremasa kallo,hankalinsa ma wato akwance kaman bai san inda yake ba.
Ɗaga hannunta tayi iyah ƙarfinta ta zabga masa mari.
Wata gigitacciyar zaburah yayi kafin ya bude idonsa yana ƙwarewa wajen kallo.
"Hajiya salah wayyo"
Hada ido sukayi da itah ta ɗaga masa girarta ta hagun alamar kalleni da kyau.
"Ƙaremin kallo dai doctor mai tashe,dan tsabar dama kai tantirine wato da sunan matarka zaka tashi daga bacci ko kuma inkaji wuyah koh,to ƙirata da kyau dan ba ganinta zaka sake yiba har abada,bari kaji bayani babbakeka zanyi a wajennan babu mai kwatarka,yau ma kuwa basai gobeba"
"Wayyo to wacece keɗin ranki yaɗaɗe?"
" raina ya daɗe? Ameen wanann shi ake fata,danna samuma naci karena babu babbaka ba,inason wanann addu'ar sosai.
Har yanzu yallabai baka ganeni ba,ina ɗaya daga cikin masu tsaron dasuka kaika har gidanka cikin koshin lafiya jiyah,suka kuma yimaka fatana zaman lafiyah,saikuma gashi na laluba na kwamusoka bayan na kaika gidan.
To ya kaji zancen yayi maka daɗi?"
,"mai kike buƙata,idan ƙudine zan baki number dazaki ƙira a baki,nasan kidnapping ɗina kikayi koh?"
Kaga nayimaka kama da wacce take neman kuɗi,wato ku koma da kuɗi zaku fansheshi koh,duk abinda kuka yi idan aka nufo kanku saiku bada kuɗi,saboda kun saku kaji zaku saka musu tsaba koh"
"To mai kike buƙata kika kamani,ko wanine ya aikoki daga cikin maƙiyina,sabod......."

Browse

MABARACIYAH
by SAKHNA03
 
chp 3___4
124 3 0

by SAKHNA03

*MABARACIYAH*
_hakkin mallaka_
_*sadi-sakhna*_
(Yar mutan Jama'are)
Link chapter
https://arewabooks.com/chapter?id=6273d156156f9eb3f299ade0
Free Page 3••4
_Shekarar yanzu_
Katsina____12:00pm
Layin tsitt yake baka jin komai sai kukan karashiyah wanda sukan fito da daddare domin nemo abincin su.
Daga ganin yanayin anguwar kasan masu hannu da shuni ne ke zama a cikinta.
Bisa la'akari da yanda kowanne gida ɗaɗɗaine bashida get,ruwa,da kuma wutar nepa mai kyau.
A hallayah irinta wannan anguwa akan rufe gidan kaman misalin karfe goma,hakanne ya sauƙaƙawa masu shirin shiga wani gida,wanda yafi kowanne gida a kusan wajen kyau.
Su ukune sanye da baƙaƙen kaya,da kuma junduma junduman hijabai,a yanayinsu sunyi kama da mata,saidai kuma yanayin kujarinsu akwai shakku idam matanne,koma matanne to kuwa basuyi kama da masu zama a gidaba suna rainon yaransu.
Ɗaya daga cikinsu ne ya kama katangar wajen ya hau,kaman dama danshi akayi wajen saboda tsabar ƙwarewa.
Saida ya daidaita zamansa a wajen kafin ya mikawa na kasan hannu.
Wani abu ya bashi a gwangwami yafara fesawa security ware tada zagaye gidan mai kaman spray.
Saidai daga yanda yake rike abin cikin kulawa kasan abin da alamar hatsari a tattare dashi,koma ince fiyeda haka.
Cikin abinda bai wice sakanni ba karfen wajen yafara narkewa kaman an zubawa kankara ruwan zafi.
Saida suka tabbatar yabada wajen da mutum zai iya shigewa kafin dukkkan su suka hau,tareda afkawa cikin gidan.
A yanayin yanda suka dire a tiles din gidan,yakai karar ya ankarar da hankalin mai gadin,saidai ko kadan hankalinsa ya tafi ga wata mata dayake mata magana a bakin get
wajen misalin karfe 11:30pm,a cikin magagin bacci mai gadin yaji bugun kofar gidan,tsorone ya ɗarsu a cikin zuciyarsa,dan yasan ba kowa bane sai barayi,shikuwa yanda yake gudawar nan,ko iskan suka saita masa jefarshi zatayi.
Har ya koma zai cigaba da kwanciyarsa dama ga sanyin da'ake,saikuma yaga rashin dacewar hakan,musamman da mutanen gidan suka yarda dashi suka bashi amanar kariyarsu.
Tashi yayi cikin sanyin jiki ya nufi bakin get din,duk da daga kaga tafiyar dayake kasan ƙara ƙadance zata saka ya koma daga inda ya fito.
Shuru yayi yana jiran yaji wanene,ga mamakinsa sai kuma yaji nishin mace,wacce take cikin mawuyacin hali.
"Wayyooo,maga allah daga gidannan ya taimakamin dan allah"
Saurin bude kofar yayi idonsa ya sauƙa kan wata mace,bazata wuce shekara ashirin da biyu ba,ga kuma ciki haihuwa ko yau ko gobe a jikinta.
Kayan jikin ta da kuma yanda take maida numfashi ɗaya bayan ɗaya ya isa ya tabbatarwa da mutum halin data ke ciki.
Karisawa wajenta yayi yadan bawa bakin kofar get din nisa kadan.
Durƙusawa yayi a gabanta tareda tambayarta cikim tausayawa.
"Baiwar allah lafiyah naganki a wannan wajen cikin yanayinnan da tsohon dare haka"
Hannunsa ta kama na hagun wanda yake kusada ita,tamkar dukkan rayuwarta tana jikin hannunasa,numfasawa tayi da ƙyar kafin tace,
"Bawan allah kai musulmine,kadubeni da idon rahma,a matsayina na ƴar uwarka musulma,wasune suke bina zasu kasheni,yanzu haka ƙishirwace ta kamani kaman zan mutu,shine na keso ka taimaka min da ruwan dazan sha dan allah"
"Toh amma baiwar allah bakya bukatar inda zaki zauna kuwa,bai kamata ki zauna a waje ba,idan na shiga gidan ma kinga ke kadaice a wurin"
"Ina bukatar hakan sosai,saidai kar na takuraka dayawa shiyasa kaga nace ka bani ruwan ma ya isa "
"Ahah baza'ayi haka ba,a wanann halin dakike ciki rayuwarki nacikin haɗari sosai,shigo daga cikin na kawo miki ruwan"
Har ta tashi zasu shiga sai idonta ya hango wucewar wani abu cikin gidan. Bata tantance menene ba kawai sai tayi Saurin kama hannun mai gadin wanda yake kokarin juyawa wajen da idonta ya hango,hankalinsa ya bayar kanta ganin yanda ta rike mararta tareda sakin ɗan marayan nishi.
"Sannu baiwar allah,lallai kina ganin rayuwa kam,barina kawomiki ruwan koh"
Ɗaga kai kawai tayi,dan
********************** ⬇ **************************
********** Ai Hausa Novels ****************
*************************⬆ **********************
DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.
Visit > https://www.aihausanovels.com.ng
Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.
Email > aihausabooks@gmail.com
******* FOLLOW US ******
Facebook: Ai Hausa Novels
Twitter: Ai Hausa Novels
Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels
WhatsApp Number: 08138873799
Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.
********************** ⬇ **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** ⬆ **************************
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels