Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 3
sanye cikin malum-malum ta danyen farin boyal. Ta yi murmushi gami da ajiyar zuciya "Har ka sani cikin damuwa a tunanina ka manta da ni yau." Ya yi dariya bayan ya rufe kofar motar. "Haba wane ni na manta da uwargida, ashe zan iya manta wa da sunana?" "Har ma na zama uwargidan taka?" Ya gyada kai "Kwarai kuwa. Ni kuma me gidan Asama'u ba." Suka yi dariya, Sannan suka nufi inda suka saba zama suka zauna. "Asama'u kinga na yi amarya ko?n Ta dubeshi da sauri "Amarya, tana ina?" Ya nuna mata motar "Gata nan." Ta yi ajiyar zuciya "Har ka sa gabana ya fadi." 23 Suka kuma yin dariya. zamani." "Kai zarkadi amma Aminu ka more da motar Ya girgiza kai "Haba Asama'u ai babu batun morewa domin akwai abin morewar da nake son mallaka fiye da wannan a rayuwata." Ta yi masa wani irin kallo, tare da alamar tambaya a fuskaayarsa. "Alhaji mene ne ya faru?" Washegari Asama'u ta tąshi bata jin dadi, kusan ko ina a jikinta ciwo yake yi sakamakon dukan da ta ci wajen babanta a jiya, amma duk ba wannan ne ya dame ta ba, yadda za su hadu da masoyinta yau shi ne abinda ya fi damunta. A wannan rana haka ta wuni sir babu cin abinci, babu kuma mai rarrashin ta akan hakan sai Dela. Da lokacin haduwar su ya yi sai ta ji ranta ya yi mugun faci, ta ji kamar ta yi bindiga ta fashe da ta tuna cewa yanzu fa Aminu na can cikin jiranta "Allah sarki masoyina." Ta ambata a ranta. "Sa'o'i biyu da wucewar lokacin da suka saba haduwa, tana kwance a daki Dela na rarrashinta sai ta ji na'urar sadarwarta wadda ke amfani da iska ta dau kara. Kamar ba ta son fauka ta mika hannu ta dauka. Sunan wanda ta ke kauna ne ya fito a kan gilashin na'urar. Da gaggawa ta kai kunnenta. 24 "Aminu...." Ta ambata a maimakon amsawar da aka saba yi "Hello!" Shiru ta ji, hakan ya kuma sawa ta cc. "Aminu, kana ina?" "Ina nan ina jiranki, a wajen da kika shanya ni..." "Wayyo masoyina." Ta runtse idanunta kana ta mike da kyar ta zauna. "Bana jin dadi ne yau." Ya yi shiru na dan lokaci sannan cikin damuwa ya cc. "Ba ki da lafiya, me ya ke damunki?" Ya bukata muryarsa kunshe da damuwa. Ba ta so ya san abin da ya faru a kanta sai ta сс. "Ba komai ma na warke..." "Eh, na ji kin warke, tambayarki na ke me ya sameki? Ta yi shiru tana tunanin abinda za ta ce masa. "Na ce ma na samu sauki." "Ni kuma na ce me ya sameki?" Ya maimaita. Dabara ta fado mata. "Ciwon son ka ne ya kwantar da ni." Ta hada da 'yar dariya. Ya san ba haka abin ya ke ba kawai bata son sanar da shi, don haka sai ya ce. "To yanzu yaushe zamu hadu?" Ta dubi Dela kamar ta ki fada sai ta ce. "Zan yi kokari mu hadu gobe." Allah ya kai mu." Ya ce a sanyaye sannan ya kashe. Har ya kashe wayar tana makale a kunnenta. 25 Se Aminu ya hau ya motarsa koma gida jikinsa a sanyavc. Tunda ya isa gida mahaifiyarsa ta fahimci hakan, wannan ya sa ta nace da tambayarsa ko bashi da lafiya ne? "Lafiya Kalau Momi." Ya ce da ita sa'ar da ta je har daki ta sameshi a kwance. "Lafiyar ka kalau kuma ka zo ka kwanta tun yanzu, da haka ka ke yi?" Ta ce cikin zargin kin fada mata gaskiya. Ya yi shiru bai yi magana ba, hakan ya sa ta kKara tabbatar da zarginta kuma shi ya bata kwarin gwiwar ci gaba da tambayarsa "Wato kai yanzu har akwai abin da za ka iya boye min ko? Ka girma kenan mu ba mu isa komai a wajenka ba." Ya girgiza kai daga kwancen. "To me ka ke nufi da kin fada min abin da ke damunka?" Ba shi da amsa, mafita daya kawai ya sanar mata abinda yake akwai ko wata kila ta iya tallafa masa. Ya dogara hannayensa biyu ya tashi zaune. Ya dubi mahaifiyarsa ya cе. "Momi Baba ne ya cc ba zan auri 'yar gidan Alhaji Masa'ud ba..." Ya yi shiru gami da dukar da kai. Babbar magana dan sanda ya ga gawar soja. Ai ita ma abin ya fi karfin ta. Ta jima tana dubansa duba na tausayawa saboda ya zo da abin da ta san yiwuwarsa 26 tamkar yiwuwar fitowat kaho ne akan jaki. "Abba na." Shi ne sunan da ta ke kiransa da shi saboda sunan mahaifinta gareshi. Ya daga kai ya dubeta gami da amsawa a sanyaye. Kai tsaye ta wuce da cewa "Ka zo da babbar matsala guda daya me matukar sarkakiya, sarkakiyar da warwararta za ta zama gagarumin aiki ja."Ta dan sarara ta ja numfashi sannan ta ci gaba. "Abba ka riga ka san irin dambarwar da ke tsakanin mahaifinka da mahaifin varinyar nan anya ka yi tunani na zabo ta a matsayin matarka ta aure kuwa?" Bata bukatar amsa, don haka ta ci gaba "Ba ka yi tunăni ba kuma lallai ina mai baka shawara da ka sauke wannan nufi naka tun dare bai yi ma ba domin ba za ka yi nasara ba. Ba don komai ba sai don sanin cewa Alhaji Masa'ud makiyinmu ne, ba mai kaunar mu ba ne." Ta yi shiru tana kallonsa. Tuni idanunsa sun fara cikowa da kwalla. Ya daga a hankali ya dubi mahaifiyar tasa duba mai cike da ban tausayi sannan ya се. "Momi ni fa da ke na dogara, ke daya ce na jingina a tunani na a gareki ne kawai zan samu sa'ida" Ya kuma dukar da kai. Tausayin Aminu ya lullube zuciyar Hajiya Sa'ade. A hankali ta taso daga kujerar da take zaune akai ta tako ta zauna a gefen gadon da yake zaune. "Abba." Ta kuma kiran sunansa a sanyaye "Kamar yadda ka ce ni kake tunanin samun nasara ta 27 hanyata wannan haka yake kuma zan iya matuka ga duk abinda kake so don ganin ka mallakeshi, amma ka sani ban da wannan. "Abin da ya sa na ce ma haka shi ne tun sa'ar da na shigo gidan nan na iske wannan matsananciyar gaba ta su ni kaina yanzu idan ka takura ni ban san dalilin yin ta ba." Ta yi shiru, sannan ta ci gaba "Ka yi hakuri Abbana ka nemi wata komai mai wuce wa nc." "Amma ban da son Asama'u." A zuciyarsa ya fada. Amma a zahiri bai ce komai ba. Ta dauke kanta daga kallonsa "Idan kana son wadda zaka aura ne ba-sai lallai Asama'u ba ga yan matan nan barjak a gari. Ka sauya shawara ka ji?" Bai yi wata alama da ta nuna ya yi na'am da zancen mahaifiyar tasa ba haka kuma bai yi mata gardama ba. A haka ta tafi ta bar shi zaune yana ta faman tunani. Karfe biyar na yamma kamar yadda suka saba a can ta vi masa, inda suka saba haduwa. amma shiru har tsawon sa'a guda babu ita babu dalilinta. Ya mike ya kade babbar rigarsa ya nufi motarsa, zuciyarsa cike da zulumin rashin ganin masoyiyarsa tsawon kwana biyu. Lokacin da ya kama murfin motar ne da zummar budewa sai ya ji wata murya daga bayan shi. "Assalamu alaikит." 28 4 "Wa alaiku mus salam." Ya amsa bayan ya juya ya dubi mai yin sallamar. Mai gadin gidan su Asama'u ne. "Ina wuni?" Ya ce da Aminu cikin girmamawa. "Lafiya kalau Uba ya aiki?" Aminu ya amsa gami da tambaya. "A Alhamdu lillahi, aiki da godiya. Aminu gashi in ji Asama'u." "Yanzu tana ina?" Aminu ya katse shi. "Tan gida." Uba ya amsa. Aminu ya karbi takardar da Uba ke miko masa. Uba ya yi 'yar dariya kana ya dan motsa kafarsa. "Ni zan koma." Aminu ya dubeshi. "Ka ce tana gida ko?" Ya gyada kai "Tana gida." Aminu ya jinjina kai. "To na gode kwarai....godiya nake." Ya sa hannu a aljihu ya dauko naira dari ya ba shi. Ya sa hannu biyu har da dan durkusawa, cikin girmamawa, ya ce "Na gode sosai Allah ya bar ku tarc." Aminu ya san da wadda mai gadin yake nufi dona haka sai ya ji dadi sosai. "Nima na gode." Maigadi ya yi godiya ya tafi. Aminu ya dubi envelop din. A jikinta 6aro-baro da manyan haruffa an rubuta: DAGA MAI KAUNARKA. A daya bangaren kuma an rubuta ZU'WA GA WANDA ZUCIYA TAKE BEGE. Har ya kama zai bude, sai ya yanke shawarar ya 29 bari sai ya je gida. Nan danan ya hau motarsa sai gida. Yana zuwa bai tsaya wata-wata ba ya zarce dakinshi. Bayan ya zauna a bakin gado sai ya 6are wasikar. Bata da yawa sosai. Ya shiga karantawa kamar haka:- Assalamu alaikuт Bayan gaisuwa da fatan ka tashi sumul, Allah ya sa haka amin. Masoyina na san za ka yi mamakin rashin ganina kwana biyu, wannan ya faru ne bisa wata gagarumar maisalar da ta sha kaina wadda fada maka ita cikin wannan 'yar guntuwar takardar ba zai yiwu ba. Amma ina son don Allah ka saurare ni yau da daddare misalin karfe takwas zan zo har gida na saneka mu tattauna. Da fatan zan samu damar ganinta. zuciya. Bissalam. Matarka in Allah ya so Asama'u Alhaji Masa'ud Yana gama karantawa ya linketa ya yi ajiyar 30 A BABI NA UKU minu ya numfasa da jin duk labarin abin da ya faru ga masoyiyarsa a dalilinsa, shekaran jiya/ Ransa ya6aci sosai, Ya dube ta. "Asama'u ni fa tunda wannan abu ya ki ci ya ki cinyewa zan dauki wani mataki na karshe akan al'amarin." "Wannc irin mataki za ka dauka." Ta tambayeshi a tsorace. Ya kuma dubanta "Zan yi sallama da gida ne kawai na yi nawa wajen." "Ni kuma fa?" Ta bukata cikin mamaki. Jikinsa ya yi sanyi. Shima ya san fada kawai ya yi amma bai yi amanna da hakan ba har cikin zuciyarsa. Ba shakka yin rayuwa a gareshi ba tare da ita ba tamkar yin tafiya ne ba guzuri. Ya nisa. "Ke ma idan kin shirya sai ki yi azama." Ya ce da ita. 31 Ta girgiza kai "Ni ina ga ba haka ya dace mu yi ba, mu dai ci gaba da yin hakuri har zuwa lokacin da Allah zai sa mu dace da alkairi." Ya dubeta "Ai al'amarin ne ba..." "Kar ka ce haka." Ta katseshi "Kai dai mu ci gaba da addu'a." Ya gyada kai alamar gamsuwa "To amma kin ji!" Ya cc. Ta mika kunnen ta ya yi mata rada. "Ko ya ki ka gani?" Yana 'yar dariya. "Wannan ka yi daidai." Ta ba shi.Kwarin gwiwa. Ya dubi agogon da ke hannunsa "Ya dace ki tashi ki tafi." Ta saki baki alamar mamaki. "Au kora ta ma ka ke?" Ta mike tsaye. Shima ya mike "Haba-haba wane ni na kore ki uwargida na zauna da wa?" Ta yi dariya. "Wannan fata naka Allah ya karba shi." "Arnin-amin." Suka fice daga dakin. Kamar yadda ya same shi shekaran jiya, yau ma shi kadai ne a falon a zaune yana kallon labarai. Aminu ya shiga cikin ladabi da biyayya ya gaida mahaifinsa. Alhaji Gambo ya amsa da kyar domin tun shekaran jiva da va je masa da jawabin neman auren Asama'u ya daina sakar masa fuska. 32 "Aminu ya ya me ya faru?" Ya bukata ganin ya yi zaune kai a duke. Ya cira kai ya dubi mahaifinsa. "Baba na zo da wata magana ne." "Ina jin ka." Ya dan gyara murya. "Baba na zo ne na shaida maka, ina so zan yi kaura daga garin nan zuwa garin su Mama." Ya sa hannu a aljihu ya dauko 'ya'yan makullai da wasu takardu ya mika wa mahaifin nasa. Bai karba ba ya ce "Na mene ne wadannan?" "Baba wadannan takardu dai sun kunshi bayanin duk harkokin kasuwancin da ka dora ni ne a kai, su kuma wadannan mukullai na sito-siton dake jaba ne sai kuma mukullkin motar nan." Ya yi shiru. Alhaji Gambo ya hadiyi yawu "To na ji yanzu me kake nufi da yin haka?" Kai tsaye ya ce "Baba ina nufin zan bar duk wadannan abubuwa domin tafiya wajen da na ke tunanin zan iya samun iyayen da za su iya son abinda nake so har su mallaka min shi." Alhaji Gambo ya numfasa. Ya gano cewa fan sa na barazanar kaurace masa ne saboda bai bashi goyon bayan aurar 'yar gidan babban makiyinsa ba. Idan kuwa haka ne to lallai yana kallon dan nasa amatsayin wanda ya yi babban kuskure domin da ya yarda da auren gwanda ya mutu shi kansa. To amına fa yana mugun ji da babban dan nasa kwaya daya tal da ya mallaka. Zai hakura dashi ne ko zai yi hakuri da yarda a daura auren 33 da ya yi alkawarin sai iri sun kare. Ya dubi Aminu. "Aminu bai kamata a matsayina na mahaifinka ka guje min ba, saboda na hana ka auren wannan yarinya. Ka tuna a duniya kaf ana sauya masoya amma ba a iya sauya mahaifa, idan ka kaura ce mana ma dai ka gudu ne ba ka tsira ba, dole wataran ka nemi inda muke." "Baba hakika duk abubuwa da ka ce daidai ne kuma gaskiya ne amma nima ya dace a duba bukatuna.." Ya yi shiru. Alhaji Gambo ya nisa. "To yanzu abin da nake so ka tashi ka je zan yi shawara." Ya mike fuska a daure ya fice. Fitar Aminu ke da wuya sai Alhaji Garfibo ya dau waya ya bugawa Alhaji Sabo kaninsa da Alhaji Abdullahi wansa ya sanar da su cewa lallai su zo akwai wata muhimmiyar magana. Ba tare da Gata lokaci ba kuwa suka zo. Ya kwashe kaf yadda suka yi da dan nasa ya sanar da su. Haba ai nan da nan suka dau zafi suka soma fada su basu yarda a hada zuri'a da Alhaji Masa'ud ba sai dai idan garin zai bari ga fili ga mai doki. Aka kirawo Aminu ya zo, suka rufe shi da fada kamar sa cinycshi danve. Alhaji Abdullahi cewa yake yana nanatawa. "Ka ga 'dan ka shiga ma uwa duniya, wa za a zaga mu ko ka Kuma ka sani daga karshe dai dole nc a 34 nemi mahaifanka sai ka dawo ka ce su waye?" Sannu a hankali daga kan fada suka shiga yi masa rarrashi akan ya janyc maganar tafiyar nan. Da kyar dai suka shawo kansa amma tare da amincewar za su duba lamarin soyayyar ta su. Ita kuwa Asama'u sai ta zama matar kulle, daidai da zaure ba a barinta ta fito, haka tagar da wasu lokutan ta ke hango Aminu da su ya sa an toshe. Masoyan biyu suka rasa inda za su sa kansu., Rana zafi inuwa kuna. Da dai suka ga babu sarki sai Allah sai suka sake salo suka mayar da soyayyar tasu a wasikance. Kullum idan Asama'u ta rubuta wasika-sai ta kaiwa direban su Tanimu ta ce ya kaiwa Aminu. Haka shima Aminun idan ya rubuto ta sa wasikar sai ya nemi Tanimu ya ba shi. Abin tsautsayi ran nan Asama'u ta gama rubuta wasikar, ta fito tana rike a hannunta da zummar kaiwa direba Tanimu sai ta ci karo da mahaifinta. Ya dubeta da kyau ya dubi wasikar da ke hannunta. ita. Gabanta ya yi mugun fadfuwa sa'ar da ya ce da "Menene wannan a hannunki?" Ta dukar da kai"Takarda ce." "Ta mece ce?" Ya kuma bukata. Shiru bata bashi amsa ba. 35 "Mu ga?" Ya mika hannu. Ba ta yi gardama ba ta mika masa hannunta na karkarwa. Abin da ya fara gani jikin jakar wasikar shi ya fara sa zuciyarsa bugawa. FROM YOUR'S ASAMA'U. Da sauri ya juya bayan takardar sai ya ga an rubuta; TO MY SWEETHEART. Ya dubeta cikin fushi. "Uban wa za a kaiwa wannan?" Shiru ba ta yi magana ba. "Ba da ke nake ba?" Babu amsa. A fusace ya zabga mata mari. Da sauri ta dafe kuncinta. A daidai wannan lokaci Hadiza ta kawo kai wajen. faruwa. Yanayin fuskarta ya sauya ganin abin da ke Kamar yadda ta saba sai ta cc. "Alhaji ya ya kuma?" Ya dubeta da sauri, cikin fushi ya сс. "Hajiya wannan yarinyar ta yi matukar raina mu, sam bata jin maganar mu." Ya mika mata wasikar "Dubi wannan." budeta. Ta karba jiki a sanyaye. Bayan kalmomin da ta gani a jikin wasikar sai ta Bayan sallama. Masoyina ya gari ya al'amura ya kuma fama da gwagwarmaya akan wannan mawuyacin al'amari? Ina fatan kana nan kana ta yi mana addu'a kamar yadda nima nake yi? Aminu a kullum ina tunanin ka fiye da sau dubu ba ni da wanda ya fika. Wallahi wadannan 'yan kwanaki da bana saka a idanuna sam ji nake kamar ba a raye nake ba. Kaima haka kake ji kuwa? Idan haka ka ke ji lallai ya dace acc yau mu hadu, kuma ina ya kamata mu hadu da lokaci. Ni na san irin dabarar da zan yi a gida na taho. Bissalam, ta ka har abada. Asama'u A. Masa'ud. Hadiza ta nisa gami da duban maigidanta dake ta faman huci,. Ta kuma duban wasikar sannan ta dubi 'yar ta Asama'u. "To uwar dabara....yau dabarar ta ki ta kare, saura kuma me?" Ta kalli mijinta "Lallai wannan yarinya sai mun dauki matakin gaggawa a kanta idan ba haka ba tana daf da lalacewa. Alhaji Masa'ud ya gyada kai. "Ai dama ni tuni yanzu na gama zartar da hukunci kuma ya dace ki kara sani nan da mako uku za a daura auren ta da Yusif dan gidan Alhaji Abdullahi. Saboda haka ko kin yarda ko ba ki yarda ba aikin gama ya gama." Ya shige ya bar ta tsayc anan. Ita ma Hadiza ta shige ciki suka bar ta tsaye cikin takaici. 37 * A kwana a tashi ba wuya, har aka cinye makwanni biyu a cikin makwanni ukun da Alhaji Masa'ud ya ajiye a matsayin lokacin da za a daura auren Asama'u da dan gidan yayansa Yusuf. Amma a tsawon wannan lokaci Asama'u ba taga Aminu ba shima kuma bai ganta ba kuma babu wata kafa da za su san halin da suke ciki. Wannan ba Karamin cusa damuwa ya yi a zukatan masoyan biyu ba. Tana kwance a kan gadonta sai ta ji zuciyarta na bata shawarar kawai ta tashi ta tafi ganin masyinta koma me za a yi ayi. Ta mike cikin kwarin jiki ta ja gyalenta dake makale jikin raki ta yi waje. Sannu a hankali cikin sanda ta fice daga gidan. Zuciyarta na ta bugawa ta nufi gidansu Aminu. Tana sa kanta cikin zauren su Aminu sai ta ji gabanta ya yi mummunar bugawa sakamakon karo da suka kusan yi da wanda ta je nema a yayin da shima yake kokarin fitowa daga gidan don zuwa wajenta. Suka yi turus! Suka dubi juna, a lokaci guda suka vi ajiyar zuciya. "Aminu..." "Asama'u.." Suka kirayi sunan juna a lokaci guda. "Aminu dama kana nan?" Ya nisa. "Ke zan tambaya dama kina nan?" Ita ma ta nisa. Ta dubeshi. "Zai fi kyau mu sami waje don nan ba..." Ya katse ta "Zo mu shiga daga ciki." Ta bishi a baya har cikin dakinsa. Bayan sun zauna sai hirar yaushe gamo ta bude tsakaninsu. Anan Asama'u ta kwashe labari kaf! Game da auren da ake son yi mata nan da mako guda ta fadawa Aminu. Ya numfasa yayin da ta kammala, fuskarsa cike da alamun damuwa ya ce. ta ce. "Yanzu Asama'u ina mafita?" Asama'u ta dukar da kai idanunta cike da kwalla "Aminu abin da ya fi kawai shi ne mu manta da wannan kudiri nasu, mu ei gaba da soyayyarmu. Idan kuwa har aka matsa min to na yi alkawarin yin tawaye ko kuma na halaka kaina na huta...." Ya girgiza kai "Kar ki yi haka Asama'u, kar ki yarda akan wani al'amari ki halaka kanki, idan kika yi hakan Allah madaukakin sarki zai tsine miki..." Ya yi shiru. ba?" Ta dubeshi "To kai me ye mafita idan ba wannan Ya nisa "Eh akwai mafita amma ki bari sai na yi tunani daga yau zuwa gobe." "Ya yi nisa". Ta ce a sanyaye tana dubansa "Kuma da ka ce zuwa gobe ina zamu samu ganin juna?" "Sai mu kuma haduwa anan." "Yanzu ka san da yadda na fito?" 39 Ya girgiza kai (alamar bai sani ba). "To ba a sani ba na fito." Kwayoyin idanunsa suka kara girma alamar tsoro. "Ba a sani ba....ba a sani ba fa kika ce?" "Sosai kuwa." Ta amsa cikin dakiyar zuciya. Da sauri ya dubi agogon dake daure a hannunsa, "Ya kamata to ki koma, domin dare ya şoma yi." "Ba zan tafi yanzu ba." Ta ce dashi. Gabansa ya fadi, ya san da gaske ne abin da ta fada to amma shi ba wani abu yake jin tsoro ba yadda ake wulakantata a gida ne baya so. tafi." Ya mike tsaye "Asama'u ki yi hąkuri ki tashi ki Tana daga zaune ta dubeshi "Me ka ke jin tsoro?" "Idan an taba lafiyar. Asama'a akan Aminu har "Kar a taba lafiyarki." wani abu ne?" Ya yi murmushin karfin hali. "Ba komai ba ne amma..." Ta mike "To na ji yanzu a ina muka tsaya, ka ga saura mako guda fa..?н "Muna dà sauran lokaci ki bani zuwa gobe." Ta kada kai "Allah ya kai mu." Suka fice daga dakin ya rakata har kofar gida, suka yi sallama, shi ya koma gida, ita kuma ta nufi cikin gida cikin fargaba. Tana shiga falo ta iske mahaifinta zaune rai a 40 бае. "Daga ina kike?" Ya mike tsay, Ta dafe kirji ta ja da baya. Ya soma takawa zuwa gareta yana fadin. "Da ke nake fa?" Ta dau alkawarin ta daina 6oyewa don haka kai tsaye sai ta ce. "Daga gidansu Aminu nake." Sai data fada ta gane cewa ta yi kuskure. Idanun Alhaji Masa'ud suka yi ja ransa ya 6асі ya rasa me yake masa dadi. Kawai sai ya tsaya cak! Kamar an soke shi da mashi. Sannu a hankali ya koma mazauninsa ya zauna kira. "Hadiza.....Hadiza!" Ya shiga rafkawa matarsa "Na'am" Ta amsa daga cikin daki, da gaggawa ta shigo falon. "Zauna." Ya ce da ita. Ta zauna tana duban Asama'u da ke tsaye hannayenta dafe da kirjinta. Ya nuna Asama'u da yatsa. "Hadiza ina so ki sani gobe-goben nan zan daura wa wannan yarinyar aure da Yusif don haka ki vi maza yanzu duk wanda kika san na 6angarenki ne ki sanar masa ta waya. Ni ma zan yi hakan." Hadiza ta gyada kai cikin rashin sanin me ya jawo hakan. Asama'u kuwa da zancen ya doki dodon kunnenta kamar a mafarkí, sai ta fara jin juwa mai tsananin gaske ta afka mata. Ta yi luuu-luu ta zame ta fadi kaşa sumammiya. BABI NA HUDU annu a hankali Asama'u dake kwance kan gado ta S bude idanunta. Tsawon sa'o'i bakwai ta kwashe tana sharara barci tun sa'ar da ta suma. Ta juya kanta hagun zuwa damarta cikin mamakin yadda aka yi aka kawo ta nan har aka kwantar da ita bata sani ba. Daki-daki sai zuciyarta ta shiga tariyo mata abin da ya faru a daren jiya. "...Ina so ki sani gobe-goben nan zan daura wa wannan yarinyar aure da Yusif, don haka..." Maganar da mahaifinta ya yi ta rika bayyana a zuciyarta. "To na ji, yanzu a ina muka tsaya?" "Muna da sauran lokaci ki bani zuwa gobe." Ta tuna yadda suka yi da masoyinta Aminu. Nan da nan sai ta shiga nadama tare da zargin kawukan su da kasa zartar da komai a jiyan. Da ta san abin da mahaifinta zai yanke kenan to da bata koma gidan ba. A hankali ta tashį zaunc. Har zuwa yanzu juwar ba 43 ta saketa ba kuma kanta yana matukar sarawa. "Idan fa kika zauna yanzu, nan da sa'ao'i biyar kin zama amarya." Zuciyarta ta rada mata. Tabbas ta yarda da abinda zuciyar tata ta ambata don ta sán babanta baya magana biyu. To yanzu ina mafita? Ta bukata daga zuciyar tata. "Mafita kawai ki san yadda za ki yi ki gudu..." Тa samu amsa daga zuciyar tata, ba ta tsaya tantancewa ba ta diro daga kan gadon. Ta yi na'am da shawarar zuciyarta. Ta nufi teburin kayan kwalliyar ta ta dauki agogonta ta daura, ta sa 'yan kunnenta kana ta dawo ga sif din-da-take ajiyar kayan sawarta ta bude ta dauko wasu kaya ta nufi kan gado. Da gaggawa ta tube wadanda ke jikinta ta sa wadanda ta dauko. A hanzarce ta koma ga teburin kayan kwalliyar ta dauki wayar sadarwar ta, ta tafi da gidanka, ta lallatsa lambobin Aminu kana ta kara a kunnenta. Karar da ke nuna alamar wayar ta shiga ta soma dukan dodon kunnenta, amma shiru ba a dauka ba har ta gama karar ta ta gaji ta katse. Ta yi tsaki ta kuma maimaitawa,ta kara a kunnenta. cikin sa'a sai aka dauka. "Aminu." Ta ce bayan ya amsa. "Kana gida ko?" Ta bukata. "Gani nan zuwa yanzu." Ta ce bayan ya tabbatar mata yana gida. Bata yi jiran jin abin da zai ce ba ta kashe. Da sauri ta je ta sa takalminta ta yi waje. Cikin sanda ta nufi cikin falo, ta yi turus! Sakamakon motsi da ta ji kamar a cikin falon. Bayan ta tabbatar ba motsi bane sai ta sa kai ciki ta ratsa falon ta nufi kofar fita, ta kama ta murda ga farin cikinta sai ta ji ta 44 bude, a sannu ta tura kofar ta fice. Gadan-gadan ta nufi makckiyar kofar gidan, tun kafin ta isa ta hangi mai gadi Uba kwance akan dogon benci yana ta yin barci abinsa. Cikin sanda ta bude babbar kofar ta ficc. Kai tsaye ta nufi gidan su Aminu. Ba ta vi mamakin ganinsa tsaye a kofar gida yana jiranta ba. Ba su yiwa juna magana ba, ya juya kawai ta bishi suka nufi dakinsa. lokaci?" Tun kafin su kai ga zama Aminu ya dubeta a rude. "Asama'u menene ya faru, na ganki cikin wannan Ta dubeshi a tsorace. "Aminu baba ne ya ce idan an jima zai daura min aure da Yusif." Tana gama fada ya ji kirjinsa ya buga. "Me kika ce?" Ya bukata a razanc. Ba yana nufin ta maimaita masa bane don haka ya сe. "Yanzu ya ya aka yi kika fito?" "Ba wannan banc yanzu a gabanmu....Aminu mu sam na yi?" "Me kike nufi?" Ya bukata. 'Ina nufin mu gudu." "Mu gudu mu je ina?" Ya kuma bukata. Bata san inda za su ba don haka sai ta dukar da kai. "Asama'u me yasa kike tunanin u gudu?" "Saboda mu tsare muruncin kaunar mu.."Ta amsa kai tsaye. Ya yi ajiyar zuciya, abin da ta fada haka ne amma ina za su yanzu idan sun fita. "Aminu lokaci fa yana ja. kat 45 waye." Bai san sa'ar da ya nufi gadonsa ba, ya fauko hularsa ya dora. ya tsaya. "Mu je." Ya ce da ita. Ta juya ya bi ta a baya. Har sun kai bakin kofar sai Ta tsaya itama ta dubeshi. "Ya na ga ka tsaya?" Ya girgiza kai. "Ban ga manufar gudun mu ba." "Kamar ya ya?" Ya rikc hannunta. "Asama'u gudun mu bashi da wata fa'ida ta azo a gani, ya kamata dai mu san abin yi. Ki gane a rayuwa... Ta kwace hannunta. "Aminu banga wata manufa ta zama ba. Iña so ka sani zaman

Chapter 2 of 3