sanye cikin malum-malum ta danyen farin boyal.
Ta yi murmushi gami da ajiyar zuciya
"Har ka sani cikin damuwa a tunanina ka manta
da ni yau."
Ya yi dariya bayan ya rufe kofar motar.
"Haba wane ni na manta da uwargida, ashe zan
iya manta wa da sunana?"
"Har ma na zama uwargidan taka?"
Ya gyada kai "Kwarai kuwa. Ni kuma me gidan Asama'u ba."
Suka yi dariya, Sannan suka nufi inda suka saba
zama suka zauna.
"Asama'u kinga na yi amarya ko?n
Ta dubeshi da sauri "Amarya, tana ina?"
Ya nuna mata motar "Gata nan."
Ta yi ajiyar zuciya "Har ka sa gabana ya fadi."
23
Suka kuma yin dariya.
zamani."
"Kai zarkadi amma Aminu ka more da motar
Ya girgiza kai "Haba Asama'u ai babu batun
morewa domin akwai abin morewar da nake son
mallaka fiye da wannan a rayuwata."
Ta yi masa wani irin kallo, tare da alamar
tambaya a fuskaayarsa.
"Alhaji mene ne ya faru?"
Washegari Asama'u ta tąshi bata jin dadi, kusan
ko ina a jikinta ciwo yake yi sakamakon dukan da ta ci
wajen babanta a jiya, amma duk ba wannan ne ya dame
ta ba, yadda za su hadu da masoyinta yau shi ne abinda
ya fi damunta.
A wannan rana haka ta wuni sir babu cin abinci,
babu kuma mai rarrashin ta akan hakan sai Dela.
Da lokacin haduwar su ya yi sai ta ji ranta ya yi
mugun faci, ta ji kamar ta yi bindiga ta fashe da ta tuna
cewa yanzu fa Aminu na can cikin jiranta "Allah sarki
masoyina." Ta ambata a ranta.
"Sa'o'i biyu da wucewar lokacin da suka saba
haduwa, tana kwance a daki Dela na rarrashinta sai ta ji
na'urar sadarwarta wadda ke amfani da iska ta dau kara.
Kamar ba ta son fauka ta mika hannu ta dauka.
Sunan wanda ta ke kauna ne ya fito a kan
gilashin na'urar. Da gaggawa ta kai kunnenta.
24
"Aminu...." Ta ambata a maimakon amsawar da aka saba yi "Hello!"
Shiru ta ji, hakan ya kuma sawa ta cc. "Aminu, kana ina?"
"Ina nan ina jiranki, a wajen da kika shanya ni..." "Wayyo masoyina." Ta runtse idanunta kana ta mike da kyar ta zauna. "Bana jin dadi ne yau." Ya yi shiru na dan lokaci sannan cikin damuwa
ya cc.
"Ba ki da lafiya, me ya ke damunki?" Ya bukata muryarsa kunshe da damuwa.
Ba ta so ya san abin da ya faru a kanta sai ta сс. "Ba komai ma na warke..."
"Eh, na ji kin warke, tambayarki na ke me ya sameki?
Ta yi shiru tana tunanin abinda za ta ce masa. "Na ce ma na samu sauki."
"Ni kuma na ce me ya sameki?" Ya maimaita. Dabara ta fado mata.
"Ciwon son ka ne ya kwantar da ni." Ta hada da 'yar dariya.
Ya san ba haka abin ya ke ba kawai bata son
sanar da shi, don haka sai ya ce.
"To yanzu yaushe zamu hadu?"
Ta dubi Dela kamar ta ki fada sai ta ce.
"Zan yi kokari mu hadu gobe."
Allah ya kai mu." Ya ce a sanyaye sannan ya kashe. Har ya kashe wayar tana makale a kunnenta.
25
Se
Aminu ya hau ya motarsa koma gida jikinsa a
sanyavc. Tunda ya isa gida mahaifiyarsa ta fahimci
hakan, wannan ya sa ta nace da tambayarsa ko bashi da
lafiya ne?
"Lafiya Kalau Momi." Ya ce da ita sa'ar da ta je
har daki ta sameshi a kwance.
"Lafiyar ka kalau kuma ka zo ka kwanta tun
yanzu, da haka ka ke yi?" Ta ce cikin zargin kin fada
mata gaskiya.
Ya yi shiru bai yi magana ba, hakan ya sa ta kKara
tabbatar da zarginta kuma shi ya bata kwarin gwiwar ci
gaba da tambayarsa
"Wato kai yanzu har akwai abin da za ka iya
boye min ko? Ka girma kenan mu ba mu isa komai a
wajenka ba."
Ya girgiza kai daga kwancen.
"To me ka ke nufi da kin fada min abin da ke
damunka?"
Ba shi da amsa, mafita daya kawai ya sanar mata
abinda yake akwai ko wata kila ta iya tallafa masa.
Ya dogara hannayensa biyu ya tashi zaune. Ya
dubi mahaifiyarsa ya cе.
"Momi Baba ne ya cc ba zan auri 'yar gidan
Alhaji Masa'ud ba..." Ya yi shiru gami da dukar da kai.
Babbar magana dan sanda ya ga gawar soja. Ai
ita ma abin ya fi karfin ta. Ta jima tana dubansa duba na
tausayawa saboda ya zo da abin da ta san yiwuwarsa
26
tamkar yiwuwar fitowat kaho ne akan jaki. "Abba na." Shi ne sunan da ta ke kiransa da shi saboda sunan mahaifinta gareshi.
Ya daga kai ya dubeta gami da amsawa a
sanyaye.
Kai tsaye ta wuce da cewa "Ka zo da babbar
matsala guda daya me matukar sarkakiya, sarkakiyar da
warwararta za ta zama gagarumin aiki ja."Ta dan sarara
ta ja numfashi sannan ta ci gaba.
"Abba ka riga ka san irin dambarwar da ke
tsakanin mahaifinka da mahaifin varinyar nan anya ka yi
tunani na zabo ta a matsayin matarka ta aure kuwa?"
Bata bukatar amsa, don haka ta ci gaba "Ba ka yi tunăni
ba kuma lallai ina mai baka shawara da ka sauke
wannan nufi naka tun dare bai yi ma ba domin ba za ka
yi nasara ba. Ba don komai ba sai don sanin cewa Alhaji
Masa'ud makiyinmu ne, ba mai kaunar mu ba ne." Ta yi
shiru tana kallonsa.
Tuni idanunsa sun fara cikowa da kwalla. Ya
daga a hankali ya dubi mahaifiyar tasa duba mai cike da
ban tausayi sannan ya се.
"Momi ni fa da ke na dogara, ke daya ce na
jingina a tunani na a gareki ne kawai zan samu sa'ida"
Ya kuma dukar da kai.
Tausayin Aminu ya lullube zuciyar Hajiya
Sa'ade. A hankali ta taso daga kujerar da take zaune akai
ta tako ta zauna a gefen gadon da yake zaune.
"Abba." Ta kuma kiran sunansa a sanyaye
"Kamar yadda ka ce ni kake tunanin samun nasara ta
27
hanyata wannan haka yake kuma zan iya matuka ga duk
abinda kake so don ganin ka mallakeshi, amma ka sani
ban da wannan.
"Abin da ya sa na ce ma haka shi ne tun sa'ar da
na shigo gidan nan na iske wannan matsananciyar gaba
ta su ni kaina yanzu idan ka takura ni ban san dalilin yin
ta ba." Ta yi shiru, sannan ta ci gaba "Ka yi hakuri
Abbana ka nemi wata komai mai wuce wa nc."
"Amma ban da son Asama'u." A zuciyarsa ya
fada. Amma a zahiri bai ce komai ba.
Ta dauke kanta daga kallonsa "Idan kana son
wadda zaka aura ne ba-sai lallai Asama'u ba ga yan
matan nan barjak a gari. Ka sauya shawara ka ji?"
Bai yi wata alama da ta nuna ya yi na'am da
zancen mahaifiyar tasa ba haka kuma bai yi mata
gardama ba. A haka ta tafi ta bar shi zaune yana ta
faman tunani.
Karfe biyar na yamma kamar yadda suka saba a
can ta vi masa, inda suka saba haduwa. amma shiru har
tsawon sa'a guda babu ita babu dalilinta.
Ya mike ya kade babbar rigarsa ya nufi motarsa,
zuciyarsa cike da zulumin rashin ganin masoyiyarsa
tsawon kwana biyu.
Lokacin da ya kama murfin motar ne da zummar
budewa sai ya ji wata murya daga bayan shi.
"Assalamu alaikит."
28
4
"Wa alaiku mus salam." Ya amsa bayan ya juya
ya dubi mai yin sallamar.
Mai gadin gidan su Asama'u ne.
"Ina wuni?" Ya ce da Aminu cikin girmamawa.
"Lafiya kalau Uba ya aiki?" Aminu ya amsa gami da tambaya.
"A Alhamdu lillahi, aiki da godiya. Aminu gashi
in ji Asama'u."
"Yanzu tana ina?" Aminu ya katse shi.
"Tan gida." Uba ya amsa.
Aminu ya karbi takardar da Uba ke miko masa.
Uba ya yi 'yar dariya kana ya dan motsa kafarsa.
"Ni zan koma."
Aminu ya dubeshi.
"Ka ce tana gida ko?"
Ya gyada kai "Tana gida."
Aminu ya jinjina kai. "To na gode kwarai....godiya nake." Ya sa hannu a aljihu ya dauko
naira dari ya ba shi.
Ya sa hannu biyu har da dan durkusawa, cikin
girmamawa, ya ce "Na gode sosai Allah ya bar ku tarc."
Aminu ya san da wadda mai gadin yake nufi dona
haka sai ya ji dadi sosai.
"Nima na gode." Maigadi ya yi godiya ya tafi.
Aminu ya dubi envelop din. A jikinta 6aro-baro da manyan haruffa an rubuta:
DAGA MAI KAUNARKA. A daya bangaren kuma an rubuta ZU'WA GA WANDA ZUCIYA TAKE
BEGE. Har ya kama zai bude, sai ya yanke shawarar ya
29
bari sai ya je gida.
Nan danan ya hau motarsa sai gida. Yana zuwa
bai tsaya wata-wata ba ya zarce dakinshi.
Bayan ya zauna a bakin gado sai ya 6are
wasikar. Bata da yawa sosai. Ya shiga karantawa kamar
haka:-
Assalamu alaikuт
Bayan gaisuwa da fatan ka tashi sumul, Allah ya
sa haka amin.
Masoyina na san za ka yi mamakin rashin ganina
kwana biyu, wannan ya faru ne bisa wata gagarumar
maisalar da ta sha kaina wadda fada maka ita cikin
wannan 'yar guntuwar takardar ba zai yiwu ba. Amma
ina son don Allah ka saurare ni yau da daddare misalin
karfe takwas zan zo har gida na saneka mu tattauna. Da
fatan zan samu damar ganinta.
zuciya.
Bissalam.
Matarka in Allah ya so
Asama'u Alhaji Masa'ud
Yana gama karantawa ya linketa ya yi ajiyar
30
A
BABI NA UKU
minu ya numfasa da jin duk labarin abin da ya faru ga masoyiyarsa a dalilinsa, shekaran jiya/
Ransa ya6aci sosai, Ya dube ta.
"Asama'u ni fa tunda wannan abu ya ki ci ya ki cinyewa zan dauki wani mataki na karshe akan al'amarin."
"Wannc irin mataki za ka dauka." Ta tambayeshi
a tsorace.
Ya kuma dubanta "Zan yi sallama da gida ne kawai na yi nawa wajen."
"Ni kuma fa?" Ta bukata cikin mamaki.
Jikinsa ya yi sanyi. Shima ya san fada kawai ya
yi amma bai yi amanna da hakan ba har cikin zuciyarsa.
Ba shakka yin rayuwa a gareshi ba tare da ita ba tamkar
yin tafiya ne ba guzuri.
Ya nisa. "Ke ma idan kin shirya sai ki yi azama."
Ya ce da ita.
31
Ta girgiza kai "Ni ina ga ba haka ya dace mu yi
ba, mu dai ci gaba da yin hakuri har zuwa lokacin da
Allah zai sa mu dace da alkairi."
Ya dubeta "Ai al'amarin ne ba..."
"Kar ka ce haka." Ta katseshi "Kai dai mu ci
gaba da addu'a."
Ya gyada kai alamar gamsuwa "To amma kin
ji!" Ya cc.
Ta mika kunnen ta ya yi mata rada.
"Ko ya ki ka gani?" Yana 'yar dariya.
"Wannan ka yi daidai." Ta ba shi.Kwarin gwiwa.
Ya dubi agogon da ke hannunsa "Ya dace ki
tashi ki tafi." Ta saki baki alamar mamaki.
"Au kora ta ma ka ke?" Ta mike tsaye.
Shima ya mike "Haba-haba wane ni na kore ki
uwargida na zauna da wa?"
Ta yi dariya.
"Wannan fata naka Allah ya karba shi."
"Arnin-amin."
Suka fice daga dakin.
Kamar yadda ya same shi shekaran jiya, yau ma
shi kadai ne a falon a zaune yana kallon labarai.
Aminu ya shiga cikin ladabi da biyayya ya gaida
mahaifinsa. Alhaji Gambo ya amsa da kyar domin tun
shekaran jiva da va je masa da jawabin neman auren
Asama'u ya daina sakar masa fuska.
32
"Aminu ya ya me ya faru?" Ya bukata ganin ya
yi zaune kai a duke.
Ya cira kai ya dubi mahaifinsa.
"Baba na zo da wata magana ne."
"Ina jin ka."
Ya dan gyara murya.
"Baba na zo ne na shaida maka, ina so zan yi
kaura daga garin nan zuwa garin su Mama." Ya sa
hannu a aljihu ya dauko 'ya'yan makullai da wasu
takardu ya mika wa mahaifin nasa.
Bai karba ba ya ce "Na mene ne wadannan?"
"Baba wadannan takardu dai sun kunshi bayanin
duk harkokin kasuwancin da ka dora ni ne a kai, su
kuma wadannan mukullai na sito-siton dake jaba ne sai
kuma mukullkin motar nan." Ya yi shiru.
Alhaji Gambo ya hadiyi yawu "To na ji yanzu
me kake nufi da yin haka?"
Kai tsaye ya ce "Baba ina nufin zan bar duk
wadannan abubuwa domin tafiya wajen da na ke tunanin
zan iya samun iyayen da za su iya son abinda nake so
har su mallaka min shi."
Alhaji Gambo ya numfasa. Ya gano cewa fan sa
na barazanar kaurace masa ne saboda bai bashi goyon
bayan aurar 'yar gidan babban makiyinsa ba. Idan kuwa
haka ne to lallai yana kallon dan nasa amatsayin wanda
ya yi babban kuskure domin da ya yarda da auren
gwanda ya mutu shi kansa. To amına fa yana mugun ji
da babban dan nasa kwaya daya tal da ya mallaka. Zai hakura dashi ne ko zai yi hakuri da yarda a daura auren
33
da ya yi alkawarin sai iri sun kare. Ya dubi Aminu.
"Aminu bai kamata a matsayina na mahaifinka
ka guje min ba, saboda na hana ka auren wannan
yarinya. Ka tuna a duniya kaf ana sauya masoya amma
ba a iya sauya mahaifa, idan ka kaura ce mana ma dai ka
gudu ne ba ka tsira ba, dole wataran ka nemi inda
muke."
"Baba hakika duk abubuwa da ka ce daidai ne
kuma gaskiya ne amma nima ya dace a duba bukatuna.."
Ya yi shiru.
Alhaji Gambo ya nisa.
"To yanzu abin da nake so ka tashi ka je zan yi
shawara."
Ya mike fuska a daure ya fice.
Fitar Aminu ke da wuya sai Alhaji Garfibo ya
dau waya ya bugawa Alhaji Sabo kaninsa da Alhaji
Abdullahi wansa ya sanar da su cewa lallai su zo akwai
wata muhimmiyar magana.
Ba tare da Gata lokaci ba kuwa suka zo.
Ya kwashe kaf yadda suka yi da dan nasa ya
sanar da su.
Haba ai nan da nan suka dau zafi suka soma fada
su basu yarda a hada zuri'a da Alhaji Masa'ud ba sai dai
idan garin zai bari ga fili ga mai doki.
Aka kirawo Aminu ya zo, suka rufe shi da fada
kamar sa cinycshi danve.
Alhaji Abdullahi cewa yake yana nanatawa.
"Ka ga 'dan ka shiga ma uwa duniya, wa za a
zaga mu ko ka Kuma ka sani daga karshe dai dole nc a
34
nemi mahaifanka sai ka dawo ka ce su waye?" Sannu a hankali daga kan fada suka shiga yi
masa rarrashi akan ya janyc maganar tafiyar nan. Da kyar dai suka shawo kansa amma tare da amincewar za su duba lamarin soyayyar ta su.
Ita kuwa Asama'u sai ta zama matar kulle, daidai
da zaure ba a barinta ta fito, haka tagar da wasu lokutan
ta ke hango Aminu da su ya sa an toshe. Masoyan biyu
suka rasa inda za su sa kansu., Rana zafi inuwa kuna.
Da dai suka ga babu sarki sai Allah sai suka sake
salo suka mayar da soyayyar tasu a wasikance.
Kullum idan Asama'u ta rubuta wasika-sai ta
kaiwa direban su Tanimu ta ce ya kaiwa Aminu. Haka
shima Aminun idan ya rubuto ta sa wasikar sai ya nemi
Tanimu ya ba shi.
Abin tsautsayi ran nan Asama'u ta gama rubuta
wasikar, ta fito tana rike a hannunta da zummar kaiwa
direba Tanimu sai ta ci karo da mahaifinta.
Ya dubeta da kyau ya dubi wasikar da ke hannunta.
ita. Gabanta ya yi mugun fadfuwa sa'ar da ya ce da
"Menene wannan a hannunki?"
Ta dukar da kai"Takarda ce."
"Ta mece ce?" Ya kuma bukata.
Shiru bata bashi amsa ba.
35
"Mu ga?" Ya mika hannu.
Ba ta yi gardama ba ta mika masa hannunta na
karkarwa.
Abin da ya fara gani jikin jakar wasikar shi ya
fara sa zuciyarsa bugawa.
FROM YOUR'S ASAMA'U. Da sauri ya juya
bayan takardar sai ya ga an rubuta;
TO MY SWEETHEART.
Ya dubeta cikin fushi.
"Uban wa za a kaiwa wannan?"
Shiru ba ta yi magana ba.
"Ba da ke nake ba?"
Babu amsa.
A fusace ya zabga mata mari.
Da sauri ta dafe kuncinta. A daidai wannan
lokaci Hadiza ta kawo kai wajen.
faruwa.
Yanayin fuskarta ya sauya ganin abin da ke
Kamar yadda ta saba sai ta cc.
"Alhaji ya ya kuma?"
Ya dubeta da sauri, cikin fushi ya сс.
"Hajiya wannan yarinyar ta yi matukar raina mu,
sam bata jin maganar mu." Ya mika mata wasikar "Dubi
wannan."
budeta.
Ta karba jiki a sanyaye.
Bayan kalmomin da ta gani a jikin wasikar sai ta
Bayan sallama.
Masoyina ya gari ya al'amura ya kuma fama da gwagwarmaya akan wannan mawuyacin al'amari? Ina fatan kana nan kana ta yi mana addu'a kamar yadda nima nake yi?
Aminu a kullum ina tunanin ka fiye da sau dubu ba ni da wanda ya fika. Wallahi wadannan 'yan kwanaki
da bana saka a idanuna sam ji nake kamar ba a raye nake ba. Kaima haka kake ji kuwa? Idan haka ka ke ji lallai
ya dace acc yau mu hadu, kuma ina ya kamata mu hadu
da lokaci. Ni na san irin dabarar da zan yi a gida na taho. Bissalam, ta ka har abada.
Asama'u A. Masa'ud.
Hadiza ta nisa gami da duban maigidanta dake ta
faman huci,. Ta kuma duban wasikar sannan ta dubi 'yar
ta Asama'u.
"To uwar dabara....yau dabarar ta ki ta kare,
saura kuma me?" Ta kalli mijinta "Lallai wannan yarinya sai mun dauki matakin gaggawa a kanta idan ba haka ba tana daf da lalacewa.
Alhaji Masa'ud ya gyada kai.
"Ai dama ni tuni yanzu na gama zartar da
hukunci kuma ya dace ki kara sani nan da mako uku za
a daura auren ta da Yusif dan gidan Alhaji Abdullahi.
Saboda haka ko kin yarda ko ba ki yarda ba aikin gama
ya gama." Ya shige ya bar ta tsayc anan. Ita ma Hadiza
ta shige ciki suka bar ta tsaye cikin takaici.
37
*
A kwana a tashi ba wuya, har aka cinye
makwanni biyu a cikin makwanni ukun da Alhaji
Masa'ud ya ajiye a matsayin lokacin da za a daura auren
Asama'u da dan gidan yayansa Yusuf. Amma a tsawon
wannan lokaci Asama'u ba taga Aminu ba shima kuma
bai ganta ba kuma babu wata kafa da za su san halin da
suke ciki. Wannan ba Karamin cusa damuwa ya yi a
zukatan masoyan biyu ba.
Tana kwance a kan gadonta sai ta ji zuciyarta na
bata shawarar kawai ta tashi ta tafi ganin masyinta koma
me za a yi ayi.
Ta mike cikin kwarin jiki ta ja gyalenta dake
makale jikin raki ta yi waje.
Sannu a hankali cikin sanda ta fice daga gidan.
Zuciyarta na ta bugawa ta nufi gidansu Aminu.
Tana sa kanta cikin zauren su Aminu sai ta ji
gabanta ya yi mummunar bugawa sakamakon karo da
suka kusan yi da wanda ta je nema a yayin da shima
yake kokarin fitowa daga gidan don zuwa wajenta.
Suka yi turus! Suka dubi juna, a lokaci guda suka
vi ajiyar zuciya.
"Aminu..."
"Asama'u.."
Suka kirayi sunan juna a lokaci guda.
"Aminu dama kana nan?"
Ya nisa.
"Ke zan tambaya dama kina nan?"
Ita ma ta nisa. Ta dubeshi.
"Zai fi kyau mu sami waje don nan ba..."
Ya katse ta "Zo mu shiga daga ciki."
Ta bishi a baya har cikin dakinsa.
Bayan sun zauna sai hirar yaushe gamo ta bude
tsakaninsu.
Anan Asama'u ta kwashe labari kaf! Game da
auren da ake son yi mata nan da mako guda ta fadawa
Aminu.
Ya numfasa yayin da ta kammala, fuskarsa cike
da alamun damuwa ya ce.
ta ce.
"Yanzu Asama'u ina mafita?"
Asama'u ta dukar da kai idanunta cike da kwalla
"Aminu abin da ya fi kawai shi ne mu manta da
wannan kudiri nasu, mu ei gaba da soyayyarmu. Idan
kuwa har aka matsa min to na yi alkawarin yin tawaye
ko kuma na halaka kaina na huta...."
Ya girgiza kai "Kar ki yi haka Asama'u, kar ki
yarda akan wani al'amari ki halaka kanki, idan kika yi
hakan Allah madaukakin sarki zai tsine miki..." Ya yi shiru.
ba?"
Ta dubeshi "To kai me ye mafita idan ba wannan
Ya nisa "Eh akwai mafita amma ki bari sai na yi
tunani daga yau zuwa gobe."
"Ya yi nisa". Ta ce a sanyaye tana dubansa
"Kuma da ka ce zuwa gobe ina zamu samu ganin juna?" "Sai mu kuma haduwa anan."
"Yanzu ka san da yadda na fito?"
39
Ya girgiza kai (alamar bai sani ba).
"To ba a sani ba na fito."
Kwayoyin idanunsa suka kara girma alamar
tsoro.
"Ba a sani ba....ba a sani ba fa kika ce?"
"Sosai kuwa." Ta amsa cikin dakiyar zuciya.
Da sauri ya dubi agogon dake daure a hannunsa,
"Ya kamata to ki koma, domin dare ya şoma yi."
"Ba zan tafi yanzu ba." Ta ce dashi.
Gabansa ya fadi, ya san da gaske ne abin da ta
fada to amma shi ba wani abu yake jin tsoro ba yadda
ake wulakantata a gida ne baya so.
tafi."
Ya mike tsaye "Asama'u ki yi hąkuri ki tashi ki
Tana daga zaune ta dubeshi "Me ka ke jin
tsoro?"
"Idan an taba lafiyar. Asama'a akan Aminu har "Kar a taba lafiyarki."
wani abu ne?"
Ya yi murmushin karfin hali.
"Ba komai ba ne amma..."
Ta mike "To na ji yanzu a ina muka tsaya, ka ga
saura mako guda fa..?н
"Muna dà sauran lokaci ki bani zuwa gobe."
Ta kada kai "Allah ya kai mu."
Suka fice daga dakin ya rakata har kofar gida,
suka yi sallama, shi ya koma gida, ita kuma ta nufi cikin
gida cikin fargaba.
Tana shiga falo ta iske mahaifinta zaune rai a
40
бае.
"Daga ina kike?" Ya mike tsay,
Ta dafe kirji ta ja da baya.
Ya soma takawa zuwa gareta yana fadin.
"Da ke nake fa?"
Ta dau alkawarin ta daina 6oyewa don haka kai
tsaye sai ta ce.
"Daga gidansu Aminu nake." Sai data fada ta
gane cewa ta yi kuskure.
Idanun Alhaji Masa'ud suka yi ja ransa ya 6асі
ya rasa me yake masa dadi. Kawai sai ya tsaya cak! Kamar an soke shi da mashi. Sannu a hankali ya koma
mazauninsa ya zauna
kira.
"Hadiza.....Hadiza!" Ya shiga rafkawa matarsa
"Na'am" Ta amsa daga cikin daki, da gaggawa ta shigo falon.
"Zauna." Ya ce da ita.
Ta zauna tana duban Asama'u da ke tsaye
hannayenta dafe da kirjinta.
Ya nuna Asama'u da yatsa.
"Hadiza ina so ki sani gobe-goben nan zan daura
wa wannan yarinyar aure da Yusif don haka ki vi maza
yanzu duk wanda kika san na 6angarenki ne ki sanar
masa ta waya. Ni ma zan yi hakan."
Hadiza ta gyada kai cikin rashin sanin me ya
jawo hakan.
Asama'u kuwa da zancen ya doki dodon
kunnenta kamar a mafarkí, sai ta fara jin juwa mai
tsananin gaske ta afka mata. Ta yi luuu-luu ta zame ta
fadi kaşa sumammiya.
BABI NA HUDU
annu a hankali Asama'u dake kwance kan gado ta S
bude idanunta. Tsawon sa'o'i bakwai ta kwashe tana sharara barci tun sa'ar da ta suma.
Ta juya kanta hagun zuwa damarta cikin mamakin yadda aka yi aka kawo ta nan har aka kwantar da ita bata sani ba.
Daki-daki sai zuciyarta ta shiga tariyo mata abin da ya faru a daren jiya.
"...Ina so ki sani gobe-goben nan zan daura wa wannan yarinyar aure da Yusif, don haka..." Maganar da mahaifinta ya yi ta rika bayyana a zuciyarta.
"To na ji, yanzu a ina muka tsaya?" "Muna da sauran lokaci ki bani zuwa gobe."
Ta tuna yadda suka yi da masoyinta Aminu. Nan da nan sai ta shiga nadama tare da zargin kawukan su da kasa zartar da komai a jiyan. Da ta san abin da mahaifinta
zai yanke kenan to da bata koma gidan ba.
A hankali ta tashį zaunc. Har zuwa yanzu juwar ba
43
ta saketa ba kuma kanta yana matukar sarawa.
"Idan fa kika zauna yanzu, nan da sa'ao'i biyar kin
zama amarya." Zuciyarta ta rada mata.
Tabbas ta yarda da abinda zuciyar tata ta ambata
don ta sán babanta baya magana biyu.
To yanzu ina mafita? Ta bukata daga zuciyar tata.
"Mafita kawai ki san yadda za ki yi ki gudu..." Тa
samu amsa daga zuciyar tata, ba ta tsaya tantancewa ba ta
diro daga kan gadon. Ta yi na'am da shawarar zuciyarta.
Ta nufi teburin kayan kwalliyar ta ta dauki
agogonta ta daura, ta sa 'yan kunnenta kana ta dawo ga sif
din-da-take ajiyar kayan sawarta ta bude ta dauko wasu
kaya ta nufi kan gado. Da gaggawa ta tube wadanda ke
jikinta ta sa wadanda ta dauko.
A hanzarce ta koma ga teburin kayan kwalliyar ta
dauki wayar sadarwar ta, ta tafi da gidanka, ta lallatsa
lambobin Aminu kana ta kara a kunnenta.
Karar da ke nuna alamar wayar ta shiga ta soma
dukan dodon kunnenta, amma shiru ba a dauka ba har ta
gama karar ta ta gaji ta katse.
Ta yi tsaki ta kuma maimaitawa,ta kara a kunnenta.
cikin sa'a sai aka dauka.
"Aminu." Ta ce bayan ya amsa.
"Kana gida ko?" Ta bukata.
"Gani nan zuwa yanzu." Ta ce bayan ya tabbatar
mata yana gida. Bata yi jiran jin abin da zai ce ba ta kashe.
Da sauri ta je ta sa takalminta ta yi waje.
Cikin sanda ta nufi cikin falo, ta yi turus!
Sakamakon motsi da ta ji kamar a cikin falon. Bayan ta
tabbatar ba motsi bane sai ta sa kai ciki ta ratsa falon ta
nufi kofar fita, ta kama ta murda ga farin cikinta sai ta ji ta
44
bude, a sannu ta tura kofar ta fice.
Gadan-gadan ta nufi makckiyar kofar gidan, tun
kafin ta isa ta hangi mai gadi Uba kwance akan dogon
benci yana ta yin barci abinsa. Cikin sanda ta bude babbar
kofar ta ficc.
Kai tsaye ta nufi gidan su Aminu. Ba ta vi
mamakin ganinsa tsaye a kofar gida yana jiranta ba.
Ba su yiwa juna magana ba, ya juya kawai ta bishi
suka nufi dakinsa.
lokaci?"
Tun kafin su kai ga zama Aminu ya dubeta a rude.
"Asama'u menene ya faru, na ganki cikin wannan
Ta dubeshi a tsorace.
"Aminu baba ne ya ce idan an jima zai daura min
aure da Yusif."
Tana gama fada ya ji kirjinsa ya buga.
"Me kika ce?" Ya bukata a razanc. Ba yana nufin
ta maimaita masa bane don haka ya сe.
"Yanzu ya ya aka yi kika fito?"
"Ba wannan banc yanzu a gabanmu....Aminu mu
sam na yi?"
"Me kike nufi?" Ya bukata.
'Ina nufin mu gudu."
"Mu gudu mu je ina?" Ya kuma bukata.
Bata san inda za su ba don haka sai ta dukar da kai.
"Asama'u me yasa kike tunanin u gudu?"
"Saboda mu tsare muruncin kaunar mu.."Ta amsa
kai tsaye.
Ya yi ajiyar zuciya, abin da ta fada haka ne amma
ina za su yanzu idan sun fita.
"Aminu lokaci fa yana ja. kat
45
waye."
Bai san sa'ar da ya nufi gadonsa ba, ya fauko
hularsa ya dora.
ya tsaya.
"Mu je." Ya ce da ita.
Ta juya ya bi ta a baya. Har sun kai bakin kofar sai
Ta tsaya itama ta dubeshi.
"Ya na ga ka tsaya?"
Ya girgiza kai.
"Ban ga manufar gudun mu ba."
"Kamar ya ya?"
Ya rikc hannunta.
"Asama'u gudun mu bashi da wata fa'ida ta azo a
gani, ya kamata dai mu san abin yi. Ki gane a rayuwa...
Ta kwace hannunta.
"Aminu banga wata manufa ta zama ba. Iña so ka
sani zaman