mu zai iya haifar mana da matsala." Та
sunkuyar da kai.
Ya vi ajiyar zuciya. Shi bai ga, wata manufa ta
gudu ba tunda idan sun gudu ba a mstaayin ma'aurata ba ya
ya za su yi?
"Gaskiya Asama'u mu hakura zuwa wayewar gari
ni na san yadda zan yi za mu samu nasara in Allah ya so."
Ta girgiza kai. Abin da ta tuna shi ne idan Aminu
ya iva da ivayensa ya zai yi da nata iyayen? Ba zai iya
hana su aiwatar da abin da suke shirin yi ba.
"Gaskiya Aminu babu dabara ga zaman mu, amma
idan ka ce haka ba komai ni zan tafi..."
"Ina za ki?" Y'a katseta.
"Duk inda ta kama." Ta share hawayen dake
idanunta "Na gode Amin ne san yanzu ka nuna min
46
kauna." Shisshikar kukan da ke barazana a gareta ta katse
ta.
ita.
Ya san ba'a ta yi masa don haka sai ya je kusa da
"Asama'u.....na rantse da Allah ina matukar
kaunarki, kar ki ga na ki amincewa da wannan gudu namu
ki yi tsammanin ba na sonki ne, sam ba haka bane na dai yi
ne kawai domin na tseratar da mu daga cikin fushin
Ubangiji da kuma gujewa ga afkawa ga fushin iyayenmu."
Ya yi shiru "Asama'u mu yi hakuri mu zauna, ni na ce
miki na san abin da zan yi."
Ta girgiza kanta "Ba hali." Ta ce a zuciyarta.
Amma da ta yi wani tunani sai ta ce dashi.
"Ba komai Aminu na amince zan koma gida."
Ba wani abu ta tuna ba da ya wuce cewa idan ta bari suka ci gaba da jayayya da Aminu gari sai ya waye mata. Ita fa ta yi damara kuma ta yi azamar barin gida
kuma babu gudu babu ja da baya.
ce.
Suka fito da nufin ya rakata har kofar gida,sai ta
"Aminu nan ma ya isa, ka san watakila yanzu baba
ya tashi saboda zuwa masallaci sallar Asuba kar ya ganmu
tare."
Ya gyada kai cikin gamsuwa.
"To sai da safen." Ya koma ciki.
Ta yi ajiyar zuciya cikin murnar ganin ta yi nasarar
kubcewa tarnakin rashin gudun da Aminu ke kokarin saka
mata.
Alhaji Masa'ud ya saki baki cikin mamaki sa'ar da
ya fito falo ya ga kofar falon a bude. Ya riga ya san babu
mai budewa in dai ba shi ba. To waye ya bude.
Ya isa ga kofar ya leka kamar me tunanin zai ga
wanda ya bude kofar amma babu abin da kwayar idanunsa
ta dauko masa sai irin duhun da ke cikė da barandar gidan.
A hankali cikin dimbin mamaki ya jawo kofar ya
rufe ya nufi saman benen dakin matarsa Hadiza.
Yana hawa ya iske kofar dakin Asama'u a bude,
bai tsaya yin wata-wataba ya kutsa kai cikin dakin, ba
kowa a ciki.
"Asama'u! Asama'u!! Asama'u!!!" Shiru ba amsa.
Ya fito da sauri ya isa dakin Hadiza, ga mamakinsa
sai ya tarar a kulle. Ya bubbuga kofar, sai da ya buga
kamar sau uku sannan ta bude. Alamun barci tattare a
fuskarta.
Ta murtsuke idnaunta "Alhaji lafiya?"
"Ina Asama'u?" Ya amsa mata da tambaya.
"Asama'u?" Ta nanata. "Ba ta nan ne?"
Ya gyada kai "Ban gànta a daki ba kuma bata nan,
kofar falon ma a bude take."
Hadiza ta dafe kirji "To tana ina.....kuma wa ya
bude?"
"Ban sani ba." Ya amsa a tsorace.
Ta yiwo waje da sauri, ya bi ta a baya kamar jela
suka koma dakin Asama'u. Trbbas bata nan.
"To ina ta yi?" Hadiza ta bukata sa'ar da ta isa ga
gadon ta daga kayan na Asama'u wanda ta sauya.
Ta dubi Alhaji Masa'ud.
"Alhaji waman kayan dake jikinta ne jlya." Ta kai
dubanta ga sif din ajiyar kaya na Asama'u ganinsabude.
Da sauri ta isa ga sif din,kamar an yi kiran sunanta ta baya ta waigo ta dubi maigidanta ta ce.
bude "Sauya kayanta ta yi Alhaji kuma ina ganin ita ta gidan nan ta fita."
Alhaji ya yi ajiyar zuciya. Ya gyada kai "Ba shakka."
"To ina ta je?" Hadiza ta bukata. Ya wara hannu alamar bai sani ba.
Hadiza ta kuma ficewa daga dakin, bai yi kasa a
gwiwa ba ya bi ta har bakin kofar falon. Ta ja ta tsaya.
"Bana jin ta bar gidan nan."
"Saboda me kika ce haka, kuma tana ina? Nuna
min ita." Ya ce a harzuke.
Ta girgiza kai "To ina maigadi?"
Lallai tana da gaskiya sai yanzu ma shima ya tuna
da maigadin. Taбbas idan zata fita sai maigadi ya sani.
Wannan tunani yasa kai tsaye ya nufi babbar kofar gidan,
matarsa Hadiza ta dafa masa baya.
Har yanzu maigadin barci yake ta shararawa.
Alhaji Masa'ud ya mari kafarsa da tafin hannu.
Firgigit! Maigadi Uba ya tashi. Cikin magagin
barci yan soma 'ya soshe-soshe.
"Kai! Uba ina Asama'u" Alhaji Masa'ud ya bukata
cikin tsawa.
Uba maigadi ya wartsake saboda fahimtar cewa
Alhaji ne a kansa. Da sauri ya mikc.
"Asama'u.....ban ganta ba." Ya ce a tsorace.
"To tana ina?" A wannan karon Hadiza ce ta
tambaya.
"Wallahi Hajiya ban ganta ba..."
"To kai kana ina?" Ta kuma bukata.
U
"Ina nan."
Cikin fushi Alhaji ya daka masa tsawa ya ce.
"Kana nan kana ta faman barci ko?"
Ya sosa habarsa "Ba haka bane Alhaji..."
"To menene? Yanzu wannan kofar a rufe take?"
Alhaji Masa'ud ya nuna babbar kofar ganin ta a bude.
Uba ya kai dubansa kofar. Babu shakka a bude
takc.
Ya tafi da sauri ya dafa kofar sai ta wangamc.
Lallai ta tabbata Asama'u ta gudu.
Alhaji Masa'ud ya ji kansa ya dau zafi.
"Yanzu ina zai samu Asama'u kuma ya ya zai yi da
mutanen da ya gayyato daurin aure yau?"
Ya ji zuciyarsa ta kuma kunci da ya tuno da
Aminu. Amsar a ina 'yar sa take yanzu ya samu. Kawai
tana wajen Aminu.
*
Aminu ya fito daga wanka, tawul daukc a
kafadarsa.
A gurguje ya sanya kayansa kana ya yi waje kansa
ko hula babu. Dakin mahaifinsa ya nufa.
Da sallama ya shiga.
Mahaifinsa da ke tsaye a tsakiyar falon ya amsa.
"Aminu lafiya kuwa?" Ya bukata da gaggawa
saboda karantar abu biyu da ya yi. Na farko dai ya san dan
nasa bai saba zuwa gaida shi da sassafc haka bha. Na biyu
kuma ya ga ransa a bace.
zauna.
Ya samu wajc ya zauna, shima Alhaji Gambo ya
"Aminu ya ya dai?" Ya kuma bukata.
Ya daga kai ya dubi mahaifinsa muryaa tausashe
56
ya ce.
"Baba na zo neman wata alfarma ne." "Alfarma?" Ya nanata "Ta me fa?"
"Baba na dai dawo ne ina neman alfarmar ka amince da aurena da Asama'u."
Ya murtuke fuska.
"Kai Aminu wai me yasa kake son mayar dani
karamin yaro ne? Na fada maka tsakaninka da mutanen
nan babu ko ga maciji amma kai...." Ya yi shiru cikin cije lebe.
Aminu kuma marairaicewa ya yi.
"Na san da haka baba amma ni dai yau alfarma
nake nema, ka ceto rayuwata Baba idan ba haka ba zan
halaka. Yau ake so a daura mata aure da wani wanda bata
Kauna." Ya yi shiru.
Alhaji Gambo ya yi matukar farin cikin jin cewa za
a daura auren Asama'u da wani yau.
Ya girgiza kai.
"Ba zan iya taimakonka ba, a cikin irin wannan
yanayin. domin da ka san abinda ke tsakanina da mahaifin
wannan yarinya da kai ma baka neme ta ba."
"Ko menene a tsakaninku zan iya nemanta baba."
Ya cè a cikin zuciyarsa, amma a fili ya ce.
"Ni dai yau alfarma na ke nema gareka baba ka je
ka roki Alhaji ya aura min ita."
Ya daka masa tsawa "Na ce ma ba zai yiwu ba ka
hakura kawai."
Aminu ya sunkuyar da kansa da ya tuna damar da
suka samu jiya amma ya ki yarda su gudu. Yanzu ya yi
mata Bakiyar da ba ruwa kenan?
"Nan da nan sai ya shiga tunanin hanyar da zai bi
51
don sanin irin wannan gaba dake tsakanin mahaifinsa da
mahaifin Asama'u.
Ya dubi mahaifinsa da zummar tuntufarsa akan
sanin makasudin wannan gaba, sai Alhaji ya mike.
"Ka gama...? Idan ka gama to ka tashi ka tafi kana
batamin lokači, ka ji ko?".
Ba zai iya musu ba, don haka sai ya mike ya nufi
waje zuciyarsa na saka masa ya tafi gidansu Asama'u.
Ya durfafi kofar idan su Asama'u, kai tsaye ya
wuce in da maigadi yake.
"Sannu Malam Uba."
"Yauwa sannunka dai......" Uba va amsa cike da
mamakin ganin Aminu, mutumin da aka ce ya dauke
Asama'u. Cikin mamaki ya kara da cewa.
ya ce.
"Aminu ina Asama'u?"
Ya dubeshi a fusace. "Ina na zo nema, tana ciki?"
Maigadi Uba ya kalli Aminu sama da kasa a raine
"Ban gane abin da kake nufi ba. Ina Asama....?"
"Na ce ma ita na zo nema."
"To ai kai zamu tambaya inda take domin ta fice da
daddare an ce kuma ana tsammanin tana wajenka."
Gabansa ne ya fara faduwa kafin fuskarsa ta sauya,
tabbas yanzu ya san Asama'u guduwa ta vi. To amma ina
labbaci?
Fuska a yakune ya dubi maigadi.
"Ban gane abinda kake nufi ba, kana nufin yanzu
Asama'un ba a ganta ba?"
"Ka fini sani." Uba ya ce masa cikin gadara, domin
a tunaninsa Aminu na kokarin raina masa wayo ne bavan
an ce Asamalu tana wajensa. Kume dole ne ya yi hakan
52
tunda an ce sakacinsa ne ya ba Asama'u damar guduwa.
Aminu ya dukar da kai cikin tsananin damuwa.
"Gaskiya Aminu babu dabara ga zaman mu, amma
idan ka ce haka ba komai ni zan tafi."
"Ina za ki?"
"Duk inda ta kama." Ya tuno abin da ya faru
tsakaninsa da Asama'u a daren yau.
Yanzu ya yarda a irin furucin da ya fita daga bakin
Asama'u ba shakka za ta iya guduwa.
"To amma ina zata?" Shi ne abinda yanzu
zuciyarsa ke son sani.
Lallai yana matukar son Asama'u domin yanzu da
yake a tsaye zazzabine ke yunkurin lullubeshi.
Bai damu da hakan ba, yanzu tunaninsa. Ina zai
samu Asama'u?
"Duk inda take sai na nemota, don ba zan iya
rayuwa babu ita ba..." Zuciyarsa ta ambata.
Cikin fushi ya juya ya nufi gida ya bar maigadi
Uba anan.
Jikinsa a sanyaye ya shiga dakinsa kai tsaye ya
nufi gadonsa ba tarc da ya tube takalmansa ba. Ya fada a
kai rub da ciki. Cikin kunar zuciya va ke furta.
"Asama'u ina kika tafi ne? Ya ya kika yi min haka?
Me ya sa ba ki jirani ba? Kina sona kuw...." Tunaninsa va
katse sa'ar da ya tuna lokacin da Asama'u'tá zo ta nemi su
tafi ya ce bai yarda ba.
"Ba laifinki ba ne...ba laifinki ba ne....Asama'n" Ya
shiga furtawa cikin sassanyar murvar nadamaa
53
A hankali ya birkice daga rub da cikin da ya yi
zuwa riginginc. Ya zuba wa silin ido ko kiftawa ba ya yi.
Sannu a hankali sai wani tunani ya darsu a zuciyarsa
tunanin daya fatattaki zargin da ya ke yiwa kan sa da
wanda yake yiwa masoyiyarsa. Tunanin kafiyar
mahaifansu, ba shakka ita ce ta kawo faruwar wannan
guduwa ta Asama'u kuma ba shakka ita ce ke yunkurin
ingiza keyarsa shima ga barin garin.
Ya yi nannauyar ajiyar zuciya, a lokaci guda
fwalla mai dumin gaske, ta soma gangarowa daga cikin
idanunsa tana bi ta kumatunsa izuwa matashin kan da ya
dora kansa a kai.
Lallai yana da bukatar sanin wannan mummunar
gaba ta iyayensu da makasudinta, wadda har take
barazanar kawar da rayuka biyu daga doron kasa.
"Baba me ya hada ka da mahaifin Asama'u." Ya
shiga ambata a fili kamar wanda ke magana da mahaifin
nasa.
Bai samu amsa ba, ba ya kuma tunanin samu,
kuma koda zai samu ma baya bukatar yanzu. Babban abin
da yake bukata a yanzu wanda ya fi damunsa shi ne sanin
inda masoyiyarsa ta tafi.
"Oh! Yanzu ko a wannc hali Asama'u ta ke, dadi
ko wuya, oho?" Zuciyarsa ce ta saka masa. Ta ke sai ya ji
kamar an tsikara masa allura.
Ya yi zumbur ya tashi zaune, kai tsaye ya mike
tsaye, cikin kuzari kamar ba abin da ke damunsa ya nufi
babbar jakarsa da ke dauke da kayansa, ya bude. Ya soma
birkice kayan da yake ciki. Ba wani abu yake nema ba
kudi vake nema.
Ya daukosu sababbi fil da su Ya mayar da jakar ya
54
rufe, sannan ya tashi ya nufi teburin littattafansa ya dauki
makullin motar sa da gaggawa ya yi waje, har ya nufi
dakin mahaifinsa sai ya kuma komawa ya dauki hoton
Asama'u da ke ajiye cikin dubban hotunan dake cikin
album, ya kuma ficewa.
A daidai lokacin ne motar 'yan sanda cike da su ta
ja ta tsaya agaban kofar gidansu Aminu, baro-baro rubuce
a jikin motar,ANTI CRIME.
'Yan sandan suka fara diddirowa hannunsu rike da
bindigogi kamar sa ci babu.
Alhaji Masa'ud dake bin su cikin tashi motar shima
ya bude ya fito.
"Nan ne gidan." Ya ce cikin fushi.
Daya daga cikin 'yan sandan ya isa kofar gidan ya
tsaya, kamar an wurgoshi ya fito.
"Yauwa! shi ne wannan!" Alhaji Masa'ud ya ce a
harzuke yana nuna Aminu da ya fito cikin sauri.
Kamar kura taga kare 'yan sandan suka nufi Aminu
kowanne na gyara zaman bindigar a hannunsa.
dashi.
"Malam you are under arest." Wani sajen ya ce
"Menene ya faru?" Aminu ya bukata a rikice ganin
wani dan baki kakkauran kurtun fan sanda na kokarin
dadumarsa.
"Za ka ci ubanka ne...sai an je can kasan abinda ka
yi munafuki...6arawon mata." Alhaji Masa'ud ya cс а
fusace.
A daidai lokacin ne Alhaji Gambo mahaifin Aminu
ya fito. Dumu-dumu ya ga dansa Aminu a hannun yan
sanda suna jan sa,Alhaji Masa'ud babban makiyinsa na ta
kwarara masa zagi...!
55
Zan ci gaba a na biyu
Ya ya za a yi tsakanin Alhaji Gambo da Alhaji
Masa'ud babban makiyinsa,Alhaji Gambo zai bari a tafi da
dansa kuwa?
A ina Asama'u take,wacce rayuwa ta kasance a ciki
bayan barin ta gida?
Za ta dawo kuwa? Ko za a nemo ta ne? Idan ta
samu waye zai aureta tsakanin masoyinta na hakika Aminu
da dan uwanta Yusif?
Ku biyo 'yar uwarku
Zainab Lawal Brigade
08029460293
Don samun amsar wadannan tambayoyi....
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels