gaisuwar Siddiqah da wani kyakkyawan (maternal feeling) akan fuskarta. Kafin su zauna su bude babin hirar Saudiyyah tsakanin Hajiyar Lagos da kawarta Hajiya Zainab irinta wadanda suka aminta da juna, tabbas kawancensu hadin Allah ne kawai, domin ajin rayuwarsu ko kusa ba daya bane. Allah shi yake hada mutum da mutum su kaunaci juna saboda Allah.
Nenne tace da Haj. Zainab ta nema mata iznin Baban Aisha tana so ta tafi da ita Lagos taga likitansu Firdausi, kwararre ne sosai akan lalurar huhu da numfashi, wanda shi yake duba Princess Firdausi (itama asthmatic ce), daga nan tana so Aisha ta karasa hutun wannan zangon a hannun ta.
Hajiya Zainab tayi dan jimmm! Kafin tace “Babanta yana wajen aikinsa amma na san ba zai ki baki Petel ba, don ba tun yau yake da labarinki ba, zan masa bayani idan ya dawo kafin ki gama abinda ya kawo ki Gombe, kwarai nice dai zanyi kewarta, don bama raba gari tun haihuwarta sai da ta fara makaranta a Billiri.
Akwai yaron da ke rikon neman aurenta Ishaqa dan makwabtanmu, yana jami’a a Ibadan, yanada da hakki shima a sanar dashi kafin ku tafi din”.
Nenne tace cikin jin faduwar gaban ta sameta a take “an yi musu baiko ne?” Kafin Haj. Zainab ta bata amsa Nenne ta kira sunan Allah sau ba adadi tana neman daukinsa akan Allah yasa Aisha rabon su ce. Wani ikon Allah sai Haj. Zaina tace “A’ah tukunna, Ishaqa dalibi ne a jami’a, mahaifinsa yace sai ya kammala ya fara aiki koda zai masa aure, suna dai matukar kaunar juna shi da Petel kowa ya sani, sabida shi Aisha bata sauraron kowa.
Gida biyu ne a tsakanin mu dasu, tare suka taso tun suna kanana soyayyar ba ta yau bace, kuma dai Ishaq yana da hankali da nasaba mai kyau, ya dade yana hidima da ita don haka dukkanmu mun yi na’am da shi tuntuni sai fatan Allah ya nuna mana lokacin”.
Aisha na jin su, kunya kamar tayi yaya! Sai ‘yan mutsu-mutsu take kamar tace kasar ta tsage ta shige.
A karshe Haj. Zainab da Haj. Sappa sunyi sallama kan sai jibi zata zo ta gana da Baban Aisha, in ya amince ta wuce da ita Lagos ganin kwararren likitan numfashi da huhu. Da Nenne zata tafi ne ta matsa gaban gadon Siddiqah.
Tana murmushi tasa hannu ta shafa gashin kanta cike da damuwar ganin yadda take ta kokawa da inhaler ita kadai, tace “get well soon my dear, Allah ya baki lafiya kinji ko Siddiqah? Sai na dawo”.
Har bakin mota Haj. Zainab ta raka Nenne. Suka sake kafa sabuwar hira kafin suyi sallama da kyar.
Nenne Sappa ta samu dan uwanta Uban kasar Gombe da iyalinsa lafiya, suka sha hirar zumunci irin wadda suka dade basu sha ba. Kafin ya gaya mata maqasudin abinda yasa shi kiran da yayi mata, wanda dama ta tsammace shi tun ma kafin ta ji shi. Maganar dai guda day ace. Gabadaya danginta da iyayenta da dangin mahaifinsa da nasa mahaifin basu da damuwa yanzu sai ta auren Prince.
“Ki turo AbdulRasheed ya zo ya ga ‘yar uwarsa Naziha, malaman fada sun gayamin idan har ba auren muka yi masa da kanmu ba, a haka zai kare rayuwarsa bazai taba kawo mace yace yana so ba don sunce aljana ta aure shi.
Sannan ance dani akwai aguminsu na maketan Yarbawa makiya Kakansa, akwai kuma sihiri irinna magauta gidansu duk a jikin sa, bazai taba ganin mace yace yana so ya aura ba”.
Nenne tayi ajiyar zuciya cikin damuwa, bata son irin wannan false beliefs din ita sam, gasgata malaman tsubbu da Yayanta Uban kasa ke yi a rayuwarsa yana damunta, ita tafi yarda da cewa auren Abdulrasheed LOKACI ne bai yi ba, kuma koda yayi din, duk da za’a kira shi ‘LATE MARRIAGE’ tofa ba zai wanke masa tarihin cewa ya jima bai yi aure ba, don haka ba kowacce mace zata yarda ya aura ba musamman cikin ‘ya’yan ‘yan uwa don kada abata zumunci in ya jingine musu ‘ya’ya saboda Polo.
Ta rasa abinda zata ce da Uban kasa, a karshe ta samu bakinta yana bashi hakuri, tana fadin ta yi wa AbdulRasheed mata, kuma anan Gombe, sannan cikakkar bafullatana diyar dattijai. In sha Allahu data koma Lagos zata gabatar da maganar ga mahaifinsa.
Uban kasa bai ce a’a ba, duk da yafi matukar son Abdulrasheed yayi aure a cikin gidansa, saidai ya nemi jin su waye iyayen yarinyar data ke ikirarin ta samar masa ta kuma fada masa, yace zai yi bincike akan Malam Yunus din da sana’arsa da gaggawa.
Ba’a kwana ba, ba’a yini ba saida komai na Malam Yunus ma’aikacin hukumar Alhazai tsohon malamin federal government na jihar Gombe ya zo kunnen Uban kasa har asalinsa, duk wata shaidar arziki da kyakkyawar nasaba malam Yunus Hamza da maidakinsa Haj. Zainab Hamza sun gama samun ta a unguwarsu Jeka da fari.
Sunyi waya da Haj. Zainab a ranar da zata wuce Lagos bayan an sallamesu daga FMC cewa tana tafe a hanya zuwa gidan Malam Yunus.
Yau ko fita Abba bai yi ba, yana jiran zuwan Haj. Zainab. Bakuwar da matarsa take ambata da alkhairi kamar tafi kowa kirki da darajta dan adam a duniya.
Nenne ta iso wajejen karfe goma na safe don taredasu ma ta karya kumallo da kunun gyada da kosai mai zafi a falon Haj. Zainab.
Aisha na daki tana ta kumburi, Ummah tace wai zata bi kawarta Lagos tayi hutu kuma taga likita.
Tunda Aisha take a duniya bata taba barin garin Gombe ba, kai ko Azare bata taba shiga ba banda Billiri makaranta, balle akai ga kwana da wani wuri da ba makaranta ko dakin ta ko na Ummanta ba.
Aisha akwai makon UWA, irin yaran nan ne da gasu dai sun girma, amma kamar yaran goye suke agaban iyayensu mata, ko kusa bata son gusawa daga jikin Ummanta.
Amma yanzu maganar zata je tayi sati biyu a Lagos ake yi. Tun jiya da taki hada kayanta Umma da kanta ta hada mata. Tana ta lallashin ta da cewa Haj. Zainab bazata roki alfarma ta kasa yi mata ba. Kuma dai lafiyarta ake son ingantawa.
Budar bakin Aisha sai cewa tayi (cikin alamu na karyewar zuciya da damuwar cewa yau Umma tace zata tafi wani gari ta kwana ba tare da ita ba).
“Amma dai Umma kinsan ba yau na fara ciwona ba ko, wane irin likita ne ban gani ba? Kuma Umma kin dai san Asthma bata da wani magani bayan inhaler ta da wadanda nake sha yanzu ko?”
Umma ta girgiza kai itama ranta a dame da damuwar Aisha tace “babu ciwon da bashi da magani sai tsufa sai mutuwa kinji ko Petel, shi magani dace ne, shin Siddiqah in baki koyi shiga mutane yanzu ba sai yaushe ne?
Ko wajen yan uwana ko na Abban ki ba kya yarda ki je ki kwana, kada ki manta watarana aure ne zai raba mu gabadaya”.
Ai kuwa Aisha ta balle da kuka tana fadin “Umma in kika sake cewa zamu rabu in nayi aure to bazan yi auren ba har abada”.
Umma na dariya tace “to ai Ishaq din bazai yarda ya daukemu mu biyu ba, mun yi yawa a gidan Ishaqa”.
Aisha ta hau rantsuwa, kan cewa sun dade suna kulla alkawari itada Ishaq cewa in yayi kudi ya tashi ginin gida zai ginawa Umma daki a gidan sa, in ba haka ba bazata yi auren ba”.
Umma abin ya bata dariya sosai, da yake lallabata take don ta yarda ta bi Hajiya Sappa sai tace toh ya isa haka ta ji, ta kuma amince ita din itace ‘yar zaman dakin Petel (Siddiqah)”.
Suna daki suna dambarwa ita da Aishah Haj. Zainab na can gaban Malam Yunus a falonsa tana gabatar masa da uzurinta na nemawa tilon dan ta wanda a cewarta ya manyanta auren Aisha-Siddiqah daga mahaifin ta Malam Yunusa Hamza.
Tace masa in ya amince da ta koma Lagos zata sanar da mahaifin Abdulrasheed, cewa tayi masa matar aure a Gombe, ba jimawa iyayen Abdulrasheed maza zasu zo da komai na dukiyar aure, basa bukatar komai, amarya kawai za’a basu su dauka.
Malam Yunus ya hau zufa nan take, sabida kwarjinin da Nenne Sappa tayi masa sai ya kasa cewa kai tsaye bazai bayar ba, yasa habar taguwarsa yana share zufa daga goshin sa daya tuno irin soyayya da shaquwar dake tsakanin Ishaq da Aisha, ya kauda idonsa daga kwarjinin Nenne yana fadin “akwai wanda ke neman aurenta tun tana kankanuwa, amma ban tari hanzarin ki ba inna tambayi cewa shi Abdulrasheed dinne ya ga Aisha yace yana so?
Ko kuwa shi Abdulrasheed ne yace a nemo masa matar aure? Ke kuma hakannan kika ga dacewar zaba masa Aisha-Siddiqarmu?
Nenne Sappa ta saka habar mayafinta tana share hawayen da suka kawo mata a idon ta, ta kwashe labarin su kaf ta baiwa Malam Yunus, da yawan shekarun AbdulRasheed a duniya amma bai taba aure ba.
A karshe ta gaya masa halin tsangwamar da take fuskanta daga dangin mijinta akan rashin auren Prince, kowa ya bude baki laifinta yake gani, sabida mijinta baya son laifinta, da yadda take raba dare bata barci saboda damuwa da addu’ar Allah ya yanke masa, in yana da rabon aure a rayuwarsa Allah ya nuna mata, don ita bata yarda da wai aljana ta aure shi ba, tafi yarda in za’a ce yawan sabgogin Polo da ya saka a gabansa ne suka cire masa tunani da sha’awar aure kwatakwata.
Har mafarkin fuskar Petel data sha yi sai da ta gaya masa a duk ranar data yi istikhara, Malam Yunus ya tausaya ma damuwar da Nenne ke ciki akan dan nata, ya kuma dan tsorata duk da bai gaya mata ba, shima fa yanata mafarkin mutum akan doki a ‘yan kwanakinnan, gashi tace dan nata mai hawa Doki ne.
Nenne Sappa ta katse masa tunani da cewa, “na yarda Ubangiji ya aiko ni Gombe ne wannan karon don lokacin da nake ta addu’ar zuwan sa ya zo ga AbdulRasheed, kada ka juyawa wannan alkhairin da nake nufin mu kulla nida ku baya.
Ka yiwa Allah malam Yunus mu taru mu taimaki juna ta hanyar kulla aure mai albarka tsakanin ‘ya’yanmu. Wanda zai mikar da zumunci na daku har illa ma sha Allahu.
Na amince daku dari bisa dari ba tun yau ba, haka na amince da Siddiqah ce kadai zata zama surukata a cikin duk matan dake garinnan, da wadanda ke garinsu mijina (Ilorin) dama kasar Najeriya gabadaya Siddiqah nake fata da addu’ar ta zame min suruka.
Malam Yunus ya nisa, duk da yayi na’am da komai da Haj. Sappa ke furtawa amma yace tayi hakuri, ba zai yi gaggawar amsawa ba sai yayi shawara da na gaba da shi, kuma sai ya san hakikanin abinda ya hana Abdulrasheed yin aure har zuwa wannan lokacin sannan zai yarda ya bashi Aisha, shima kuma sai idan Ishaq bai tashi aure yanzu ba.
Yace ya gaji da yawan maneman auren Aisha, kullum masu zuwa yau daban dana gobe, yace gara ya aurar da ita haka ya huta, kowa ya huta, dama bai mata alkawarin samun ilmin gaba da sakandire ba. Amma shi baya ra’ayin karatun boko mai zurfi sam a gareta.
Burinsa shine tayi aure da wuri ta haifa masa jikokin da zai kalla a matsayin ‘ya’yan da shi Allah bai yi nasa sun zauna a raye ba, don mahaifiyarta ma iyakacin ta firamare ya aure ta.
A karshe yace ya ji bukatar ta na son tafiya da Aisha taga likitan Asthma, sai kuma yace bai yarda ta zauna a Lagos har sai hutu ya kare ba, saboda tana zuwa Tahfiz yin haddar Al’qur’ani a kowanne hutu anan kusa dasu a unguwar Dawaki, da ta gama ganin likitan don Allah a dawo da ita gida ta karasa hutunta tare da su don suma sun jima basa tare da ita tun tafiyarsu aikin Hajji.
Nenne Sappa tayi ta mamakin wannan soyayya ta iyayen Aisha ga diyarsu Aisha, ta dauka Haj. Zainab ce kawai ke mummuken Siddiqah ahe har baban nata, ta amince da yadda Malam Yunus ya zaba cewa Aisha zata yi sati daya a Lagos ta dawo musu da ita gida.
Malam Yunus ya bukaci sanin waye mahaifin AbdulRasheed da kuma asalin ita Nenne anan Gombe. Nenne ta bashi damar yayi duk wani bincike da addini ya bashi dama akan Prince AbdulRasheed dasu iyayensa.
Sun rabu akan cewa zai yi bincike zai kuma yi shawara da maidakinsa da Yayansa, sannan zai sa Zainaba ta sanar da ita abinda suka hadu suka yanke.
An samu shawo kan Aisha da kyar da sudin ludayi ta yarda zata bi Hajiya Sappa Lagos bayan ta ci kuka ta koshi ta gode Allah a toilet don kada Hajiya Sappa ta ga kukanta, wai sati guda! Sati guda babu Umma yaya rayuwa zata yi dadi ga PETEL?! Sati gudan da a cikinsa dukkkan kundin kaddarar rayuwar Aisha take, tareda dan kabilar Yarbawa.
Nenne da Aisha suka kama hanyar Lagos ta jirgin sama, domin daga Gombe kai tsaye suka tashi a jirgin Azman mai zuwa Ikko.
**** ***** ****
MURFIN LITTAFI NA DAYA
Ga dai Aisha-Siddiqah a hanyar zuwa Lagos gidansu Prince ABDULRASHEED IDRIS (KEHINDE) AKANNI, gidan da ga dukkan alamu zai zame mata fadar rayuwar aure da surukuntaka, ga dai Aisha da Prince (Fullatana da Bayarabe) na shirin zama mata da miji kamar yadda manyan alamu suka nuna, alhalin Aisha ga hasashenta da alkiblarta da take-takenta akan kabilar Yarbawa.
Mu biyo Siddiqah Petel ‘yar Ummanta, don jin cikakken labarinta, yadda zata kaya tsakanin ta da Polo Legend na Africa da turai, wato Yariman Ilorin PRINCE ABDULRASHEED (KEHINDE) IDREES AKANNI, mijin da kaddara ta zabar mata su fafata har su baiwa hammata iska a fagen soyayya, wanda ya kasance dan asalin kabilar Yarbawa.
Yanzu ne zamu shiga cikin gundarin labarin Aisha da Prince. Har yanzu a himfidar labarin muke.
Abinda zamu so sani a gaba shine; Shin ko Aisha-Siddiqah zata barranta kanta daga matan da Prince Abdulrasheed ya riga yayiwa kudin goron maha’inta, mayaudara, masu saka khairan da sharran, sannan (gold-diggers&insatiable)?
A cewarsa dai “duk mata marassa godiya ne, da yawansu mazinata ne, marassa tsoron Allah ne, sannan basa yin soyayya ta fisabilillah!
Ta yaya Aisha zata goge wannan perception din daya ya riga ya ginu tun kuruciya daga kwanya da zuciyar Prince Abdulrasheed Kehinde?
Shin ko Prince zai samu irin soyayyar da yake fata, yake kwadayi, yake mafarki, yake kuma burin samu shekara da shekaru daga Aisha? Mun ji dai sanda yace “He’s a hopeless romantic, in search of true LOVE! Wanda ya riga ya amince babu shi a duniya”.
Shin ko Aisha-Siddiqah zata so kabilar Yarbawa tunda ga dukkan alamu kaddarar rayuwarta na cikinsu?
Mu karasa a littafi na biyu wanda tare suke da dan uwansa.
Taku har abada
SUMAYYAH ABDULKADIR
(TAKORIN TAKORITES)
07030137870
WHATSAPP ONLY.
10/4/2024
(PAID BOOK)
(INA TALLATA MUKU AISHA LAME ORIGINAL ORIFLAME AMBASSADOR)
Kina neman jakadiyar oriflame ta kwarai? Kinason mayuka da zasu dace da launin fatarki a wannan lokacin na zafi kona sanyi? Kinason kamshi na alfarma? Kinason supplements ingantattu na wellness and meal replacement ga masu bukatar weight loss and weight control? Kayan kwalliya na kerewa sa’a? Kina bukatar zama Dawisu sarkin ado? Kawai tuntubi AISHA LAME a lambar waya 07036662633 zaki samu duka wadannan cikin farashi mai inganci da kyakkyawar mu’amala. Aisha lame karshe ce wajen baiwa fata hakkinta ku tuntubi Aisha ku zo ku bani labari.
-Takorinku
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels