sakewa su huta.
Tun lokacin da Abbah da Anty Amarya da Hajiya Barau suka saka ta gaba suna mata nasiha kan aure, ta fara kuka, sai duk ta ji wani yanayi na daban, kamar lokacin da za ayi aurenta na farin, banbanci wannan ba irin wacan auren ba ne.
Yasa an kawo musu komai daga hotel kama daga abinci har abun sha. Misalin ƙarfe uku Yarima ya kira wata ƙanwar Abbah wacce gwaggo ce gurin Namra ya faɗa mata zai aiko da motocin da zasu shiga ita da Namra da wasu mutun uku aje faɗar Mai Martaba.
Namra na zaune a ɗayan bedroom ɗin tare da Maryam da wasu Cousins ɗinta da Aysha da suka zo tare, gwaggo Ramatu ta shigo tana faɗin.
“Ki shirya angon zai aiko da mota a ɗauke mu muje faɗar mai martaba”
Maryam ta daka tsalle.
“Yeeee kaga daɗin abun malam, mu shiga cikin masarauta muna tinƙaho kowa yayi mana iskanci musa a tsire shi a gari”
Sai duk suka sa dariya, har Namra dake leƙa duniyar gizo. Gwaggo Ramatu ta juya ta fice tana jinjina kai.
Maryam ta nufi babban akwatin Namra da aka zo da shi ta buɗe tana duba irin tufafin da Namra zata saka. Wani tsadadden lace ta ɗauko red color da mayafi ta aje saman gado.
“Raihanatu duba min wannan lace ɗin yayi”
Wacce aka kira da Raihanatu ta miƙe tsaye tana duba lace ɗin.
“Kai wannan ai sai ace matar president ce gaba ɗaya”
“Gaskiya kam wannan lace ɗin yayi kyau sosai”
A gajiye Namra ta miƙe ta shiga wanka ta shirya cikin lace ɗin sai suka gyara mata fuskarta, ana cikin ɗara mata ɗankwali wayar Namra ta yi ringing.
Tana ganin Number Abdool ta yi dariya.
“Ango ango”
“Maryam ya gajiyar biki? Ina Amaryata? Na kira wayarta ta ƙi ta ɗaga ki ce ina gaidata kuma ki ɗaukar min pictures ɗinta”
“An gama ranka ya daɗe”
Ya sauke wayar tana dariya tare da amsa sallamar Gwaggo Ramatu.
“Ku fito ga motoci can an zo da su, Maryam ke kaɗai kin isa ni da Talatu zamu je sai a samu wasu cikin ƙannen Anty Amarya su biyu kuma suje tun da ance mutum biyar sun isa”
Raihanatu ta mike tsaye tana kare ɗankwali.
“Haba Baba Ramatu wane irin Maryam kuma ita da take da aure, ai ƙara dai ki ce ni ko zan samu ɗan saurayi da zai ɗauke cikin ƙannen Yarima”
Sai duk suka bushe da dariya Gwaggo Ramatu ta ce
“To shirya har ke aje da ke”
Motocin dake waje guda biyu sun kusan awa ɗaya sannan Namra ta fito tare da Gwaggo Ramatu da su Maryam da Raihanatu suka shiga motocin.
A tunaninsu za a wace ne gidan sarkin kai tsaye sai suka ga ya kai su gidan Ummi. Kunya sosai Namra ta samu kanta da ji lokacin da motar ta faka a bakin ƙofar shiga falon Ummi. Meesha da Fauza suka fito da wayoyinsu a hannu suka ɗaukarta video, Amal kuma ta zo da gudu ta rumgume ta.
Sam Amal bata gane wace Namra ba, sai dai ita Namra ta gane ta tun a wayar Abdool da take kallon hotunan family ɗin ƴan gidansu. Cike suka tarar da gidan da mutane tana saka ƙafarta cikin falon aka ɗauki guɗa. Ɗakin Ummi aka wuce da ita yayinda su Maryam da Gwaggo suka tsaya a waje a falo suna gaisawa da jama'ah dan basa iya tantance Ummi balle ma bata falon. Namra na shiga Ummi ta shigo sai ta yi saurin yin ƙasa tana gaishe da Ummi. Domin sarai ta san ita mahaifiyar Abdool ga kamanin Abdool nan xube a fuskarta kuma tana ganin ƴadda yake koɗa mahaifiyar ta shi a instagram. Da Murmushi Ummi ta zauna saman gado tana dafa Namra.
“Tashi Tashi Ƴata Allah yayi miki albarka”
Sai Namra ta ɗago sai dai bata yarda ta koma saman gadon ba sai ta zauna ƙasa fuskarka rufe da mayafinta.
Amal ce ta turo ƙofar ɗakin ta shigo cike da zumuɗin ita ƙanwar ango.
“Ummi kin ga fuskarta? Mu bata buɗe mana ba”
“Ai zata buɗe muku har sai kun gaji da ganinta”
“Ni dai ba zan iya haƙuri ba”
Ta faɗa a shagwaɓe. Ummi ta miƙe.tsaye tana gyaɗa kai ta nufi wata dorowa ta buɗe ta ɗauko wasu robobi guda huɗu ta dawo ta zauna.
“Ungo wannan shanye duka”
Hannu biyu Namra tasa ta karɓa ta kafa kai ta shanye abunda yake ciki tas sannan ta sake amsar na biyu ta shanye a na ukun ma shanyewa ta yi sai a huɗu ne Ummi tace karta shanye ta raga. A nan Amal ta samu damar ganin fuskarta har ta yi mata hoto da wayar Ummi.
Bayan Namra ta gama sha Ummi tasa Amal ta ɗauke robobin ta fitar, sai mai Makeup ta shigo da kit ɗinta ta yi zaman dishin a gaban Ummi tana miƙa mata gaisuwa.
Meesha ce ta shigo ɗakin ɗauke da wani koren lace ta aje saman gado.
“Ummi ga shi”
Ummi ta kalli Namra tana nuna mata wani ƙaramin ɗaki dake gefen bathroom ta ce
“Ƴata shiga can ki shirya da wannan kayan”
Meesha ce ta riƙa ta sai suka nufi gurin tare Amal na gaba tana cigaba da leƙen fuskarta.
“Ummi hancinta dogo ne.. Kuma tana da manyan ido.. Fuskarta ma mai D ce”
Ummi ta riƙe baki tana kallon ikon Allah, gulmar mutun a gaban idonshi, wannan ƙulalaici ma Amal har ina!
Bayan ta saka lace ɗin ta fito sai duka suka fita suka barta da mai makeup ɗin, ta zauna saman kujera Mai Makeup ta fara mata fentin fuska amman mai ma'ana, bayan ta gama ta ɗaura mata ɗankwali. Ita kanta wacce ta yi mata kwaliyar sai da ta ɗauke ta a hoto saboda kyau da tayi. Three later Ummi da Fauza da Meesha da Amal suka dawo ɗakin
“Wowwwwwwwwwww”
Shine abunda duk suka faɗa ban da Ummi da ke murmushi. Ɗaukarta suka shiga yi hoto suna selfie. Farar Alkyaba Ummi ta ɗauko miƙawa mai Makeup ɗin ta saka mata. Sannan ta ɗauko fararen takalmi ta aje mata, sannan ta ɗauko akwatin turarenta ta buɗe sisters ɗin Abdool suka shiga fesa mata. Ummi da kanta ta kamo hannunta ta saka mata awarwaro, a ɗayan hannun kuma ta saka mata agogo.
Sannan ta miƙe tsaye, yayinda Namra take ƙasa risine ta saka mata sarka, sai ta miƙawa mai makeup ɗin ta manna mata ƴan kunne.
“To ku fita ku bamu guri”
Kamar umarni suke jira duk suka fita daga ɗakin aka bar Ummi daga ita sai Namra. Ummi ta kama hannayen Namra biyu ta riƙe.
“Ƴata ke tauraruwace, yanzu kin shigo cikin wani sabon shafi, ki haƙuri da duk abunda zaki ji, ba kowa ne zai faɗa miki magana ki mayar masa ba wanna ba tarbiya ba, ki zama mai riƙe sirrin mijinki da iyalansa, idan yayi miki ba dai-dai ba ki fara kawo ƙararsa a guna kamin ki kai ko ina.
Sannan yanzu zaku je gidan Mai Martaba ne wato mahaifin Abdallah, zaki gaishe da shi da iyalinsa, idan kin shiga a tsakiyar falon zaki zauna, karki raɓi kujera, idan kuma kika fito Amal zata ɗauki takalmin ta juyo miki da su ki saka, karki yarda idonki ya haɗu da na matan mai martaba balle ma mai martaba da kansa, karki yarda ki ci abunda za a baki za a miki kallon rashin kunya ko marar tarbiya.
Da misalin ƙarfe tara zaku fita gurin walimar cin abinci da Mai martaba ya shirya muku, Sai dai kamin kuje gurin walimar uwargidan Mai Martaba nasan zata nemi canja miki tufafi, zata aiko barorinta su canja miki kaya, karki yarda su canja miki komai, zan bawa Meesha da Fauza kayan da zaki canja anjima kuma kai makeup zata iso ƙarfe bakwai ta gyara miki fuska. Sai dai karki yarda lokacin Sallah yayi baki yi ba, Allah ya miki albarka”
“Na gode Mama na gode”
Ummi taɓshafa kanta tana murmushi sai ta miƙe tsaye ta fita. Bayan few minutes gwaggo da Maryam suka shigo suka riƙa Namra suka fita tare.
Mashallah shine abunda duk wanda ya kalli fuskar Namra da tufafinta yake faɗa.
Motar da Namra ta shiga daban ita kaɗai ake driving su kuma suka shiga wasu motocin.
Suna isa Faɗar Mai Martaba, aka ɗauki busa ana zuba musu kirari, sai barori suka sheƙo da gudu suna guda aka shimfiɗawa Namra carpet mai sunan Masarautar, sai wani ƙaton mutum cikin kayan dogarai yazo ya buɗewa Namra mota.
Hasbunallahu Namra ta karanta a zuciyarta sannan ta saka ƙafarta ta sauko daga cikin motar. Sai barorin suka rufa mata baya, wasu kuma suka wuce gurin tawagar da suka zo tare da Namra aka musu iso zuwa cikin gida.
Cike da hankali da natsuwa Namra take takawa barori suna take mata baya har suka isa gaban wata ƙatuwar ƙofa. Bakin ƙofar barorin suka tsaya sai Dogarai suka wangale mata ƙofar suka bakin ƙofar suna zuba mata kirari.
“shiga da ƙafar dama yar gidan girma, ƴar da tafi ko wace mace sa'ah a duniya, an gaishe ki gimbiya matar yarima, Allah ya ƙara miki lafiya da nisan kwana”
Kunna kai ta yi cikin faɗar, tana wuce carpet na farko ta cire takalminta saboda ta ga jerin takalmi a gurin. Wani irin maryaba da girma ta ji ya kamata musamman ta ta risina gaban mai martaba tana gaishe shi.
“Sarki ya amsa kuma ya gaishe ki”
Shine abunda mafadawan suke faɗi, sannan mai martaba yayi musu hannu suka tashi suka bar shi da Namra. Nasiha sosai yayi mata akan rayuwa da kuma zaman aure sai kuma kan haƙuri da iya kula da mutane.
Sai da Mai Martaba ya tabbatar Nasihar ta shiga jikinta sannan ya sallame dan ta shiga cikin gida ta gaishe da matansa.
ASIM POV.
Tun bayan da ya saka ƙarin aure a gabansa be waiwayi kowa ba, duk da da irin kuka da magiyar da Mardiya ta riƙa masa akan karka ya ƙara auren. Sai dai be ji ba sai da ya auro ƴar manyan mutane wato Balkisu.
An kashe dukiya sosai gurin auren daga duka ɓangarorin guda biyu, domin ko gidan da ya sakata mai tsada ne sosai.
Gida ne mai part biyu a ɗayan part ɗin ya saka Mardiya ta ƴar tabarmarta ta shinfiɗa saboda bata katifa kuma malamin da suka je gurinsa ya faɗa musu karta yarda ta saka katifa ko gado a gidan, abun shinfiɗa kawai zata je da shi sai kayan abinci.
Haka ta riƙa zama har tsawon wata tara duk wanda ya leƙa part ɗinta sai ya sha mamakin ganin babu komai a ciki, part ɗin Balkisu kam Aljannar duniya. Wannan matsalar ta damu Mardiya sosai har ta kai bata da wani sukuni a rayuwarta, ga mafarkin wutar da take bata daina ba, sau da dama zata zauna ta yi da kuka, wani lokaci kuma ko da tana cikin mutane zaka ganta ta koma wata iri kamar wacce aka ɗauki tunanin duniya aka ɗora mata. Ita da tayi aure dan jindaɗi abu ya zame mata ɗan zane, ta san matsalar daga gareta ne saboda yawan mafarkin wutar da take kuma gashi ita Balkisu wutar ba kama ta ko da sau ɗaya.
Ba ko wace ranar girkinta ba ne Asim yake kwana part ɗinta saboda bata da katifa balle kuma gado, sai a lokacin da yaji yana buƙatarta. Yau ma part ɗin Balkisu ya kwana, bayan yayi wanka ya shirya ya leƙo part ɗinta suka gaisa, duk ta yi wani zurun-zurun gwanin tausayi kamar marar lafiya, bayan sun gaisa ya dawo part ɗin Balkisu da yi mata sallama, sai ya samu tana tsaye jikin ƙofa tana jiranshi.
“Sai ina?”
Ta faɗa ta wani langaɓar da wuya tana kaɗa jiki, kamar wata tsohuwar karuwa.
“Gari zan shiga, amman zan dawo ajima saboda zamu je wani biki da za'ayi a faɗar Mai Martaba, kuma an gayyace mu kinsa ɗansa abokina ne”
Ya faɗa irin yana alfahari ɗin nan.
“Okay to a dawo lafiya, kar dai aje ayi gane-gane”
“Ni wa zan gani, ga ni da ke cikin gida”
Matsowa ta yi ta masa kiss, sannan ya juya ya tafi tana ɗaga masa hannu.
WHAT DO YOU EXPECT NEXT...?
[7/28, 10:15 PM] Khadeeja Candy♥: *91*
Kamar yadda Ummi tace mata a duk ɗakin da ta shiga ta kan zauna a tsakiyar ne har ta gama gaisuwar ta tashi, bata yarda ta haɗa ido da matan mai martaba. Sai dai a yadda take tararda ko wanne falo tana auna yawan family da mai martaba yake da su a gidan, wata ƙila kuma saboda tana amarya ne suke zuwa ganinta.
Bayan ta gaishesu aka kaita ɗakin Hajiya Shafa, sai aka kawo musu abinci da drinks. Bata ci komai ba duk kuwa da irin matsa mata da suka riƙa yi. Ana yin sallah magariba duk suka shiga shiryawa, wasu motocin Abdool ya aiko aka ɗauki su Maryam aka mayarda masaukinsu domin suma su shirya. Bayan sun wuce wata cikin ƴaƴan Hajiya Shafa ta shigo tana faɗin.
“Hajiya tace Mai Makeup zata zo ta gyara miki fuskarki, kuma za a kawo miki kaya ki canja”
Namra ta amsa da to. Har Amal ta buɗe baki ta gatsawa yarinyar magana sai Meesha ta riga ta.
“Ai ko har Ummi ta yi magana da mai Makeup zata zo yanzu ta mata”
“Auoak”
Yarinyar ta faɗa sai ta juya tana tafiya cike da isa ta fice. Amal taja tsaki tana binta da harara.
“Wai yarinyar nan tun ɗazu nake ganin tana ta wani shauƙi”
Meesha ta zaro ido.
“Ina ruwanki? Amal me yake cikin kan ki?”
“Aljanuna akai na”
“Ƴar gadon baƙar magana duk abunda kika yi sai na faɗawa Ummi”
Ta tsuƙe baki ta juyarda fuska. Around eight o'clock mai Makeup ɗin ta iso. Namra bata yarda an mata makeup ɗin ba sai da ta yi sallah isha'i.
Ƙarfe tara dai-dai Abdool ya aika aka kwaso ƴan'uwan Namra aka kaisu tsohuwar faɗar Mai Martaba inda aka shirya taron.
Sai tara da kwata Amarya ta iso barori na take mata baya, farin lace ne mai shegen kyau da farar Alkyaba, fararen takalmi da farar sarƙa, mai video na biye da iya ita yana ɗauka har aka ta kai zamanin da aka tanadar mata dan ta zauna. Bayan kamar minti biyar da zamanta Abdool ya shigo shi da abokaninshi, farar shadda ce jikinshi da fararen takalma sai farin rawani da farar alkyaɓa, kallonsa take kamar yadda kowa yake kallonsa, ita kanta ta san ta yi sa'ar miji, yadda yayi mata kwarjini da haiba ga fuskarsa sai annuri take, ɗaya bayan ɗaya yake tafiya ana masa kirari ana koɗashi. A kujerar da Namra take zaune ya zauna sai masu busar suka koma gefe suka cigaba da busar. Ko ina ka duba masu kaki kake gani sun cika gurin wato gayyar Abdool ne kawai sai kuma na ƴan'uwansa. Saboda Mai Martaba be gayyaci kowa ba walima ce da ya shirya a cikin gidanshi domin addu'ah kawai da kuma son tara family ɗinsa guri ɗaya, wannan walimar ta al'ada ce da ya saba shiryawa a duk lokacin da ya aurar, ko da kuwa mace ce zai gayyato mijinta azo gidan ayi walima.
Yara da rabi Mai Martaba ya iso, daman matanshi sun daɗe da isa gurin tun kamin amarya da ango su isa. Karatun alqur'ane aka buɗe filin da shi sannan Hajiya Shafa ta miƙe tsaye ta karɓi microphone tana yi ma kowa barka da zuwa.
ASIM POV.
Tsaki yake ja lokaci zuwa lokaci kamin ya kalli wanda ya shigo motar yanzu ya ce.
“Kaga Mubarak bana son jira, na tsani jira wallahi, ni da nasan haka zaka ɓata min lokaci ba zan je ba wallahi”
Mutumen ya kalleta yana murmushi.
“Sorry Man ai gani na zo yanzu”
Asim ne yake driving har suka isa Kan wurin sarki, ba a basu damar shiga ba duk da guest pass ɗin da suka nuna, sojoji ne jibge a gurin babu abunda suke sai kai da kawo suna ta ƙoƙarin ganin su bada tsaro agurin. Har Asim yaja motarsa su koma sai Abokinshi ya hana shi.
“Bari na kira shi”
Wayarsa ya fiddo ya kira wayar ƙanen Abdool wanda suke uba ɗaya wato Zayyan.
Bayan ya faɗa masa abunda ya faru sai ya miƙawa Sojan wayar suka yi waya, sannan aka buɗe musu page ɗin suka shiga. A gate na buyu aka nuna musu inda zasu faka motarsu, sannan suka fito sojoji suka tantance su sannan aka buɗe musu gate ɗin suka taka da ƙafa suka shiga harabar gidan.
Ba Zayyan ne kawai a gurin ba, domin yasam abokansa da yawa sun je bikin dan haka ya kira wani abokinsa yayi directions ɗinsu inda ake bikin saboda gidan ya kasu kashi kashi. Fitowa yayi ya shiga da su saboda yasan duk yadda zai faɗa musu ba ganewa zasu yi ba.
Wani kalar baƙauye Asim da abokinshi suka zama tun a bakin ƙofar shiga, a takw ya manta da a katsina yake, saboda gurin ya koma kamar sabuwar Abuja, daman tun farkon shigowarsa gidan ya gane shi ɗin ba kowa ba ne a cikin masu kuɗi, dan ya fahimci ko akaifar Mai Martaba be kamo ba indai akan dukiya ne. A bakin ƙofar faɗar ma sai da aka tantance su sannan aka basu guri suka sshiga. Ko da suka shiga Malama Hauwa na tsaye tana gabatarda ƙasida akan haƙoƙin mijin aka mata. Har Asim ya zauna be gane Namra ba ce saboda ta canja gaba ɗaya ta koma kamar ba ita ba, sai da ya gama gaisawa da waɗanda ya sani a gurin sannan ya zauna ya natsu tare ta tattara hankalinta gaba ɗaya ya mayar gurin mai wa'azin. Kama da Namra yake gani a fuskar Amaryar sai dai wannan kamar ta fi Namra kyau da haske, baya iya ganin angon saboda rawanin da ya rufe masa fuska.
“Kamar Namra wallahi”
Ya faɗa a fili yana kallon abokin na shi, fuskarsa with so much confused.
“Wacece Namra?”
“Matata mana”
Har abokin yasa dariya sai yayi saurin rufe bakinsa tunawa da inda suke.
“Haba Asim kamar wanda ya sha wani abu, matarka ɗan sarki zai aura? Look at you”
Ya ciro wayarsa ya kira yaron daya saba bashi labarin halin da Namra take ciki sai aka yi rashin sa'ah be ɗauka ba. Sai kawai ya kira wani abokinsa da ke sokoto dan gaba ɗaya natsuwarshi ta bar jikinshi. Miƙewa yayi tsaye da zimmar fita daga gurin saboda ƙarar loudspeaker ba zata bar shi yayi magana yadda yake so ba, miƙewarshi ke da wuya ya hango Maryam ta je tana magana da Namra a kunne.
“Wallahi wannan Matatace, Namra ce Wallahi”
Abokin yayi saurin riƙo shi ya zaunar domin shi kaɗai yake jin abunda Asim ke faɗa, hankalin kowa yana can gurin amarya da ango.
“Matata ce wannan wallahi”
“Na ji matar ka ce muje gida”
Ya faɗa dan yana ganin kamar Asim baya cikin hankalin kansa.
Asim ya fisge hannunshi zuciyarsa na mugun bugawa da ingizashi yayi duk abunda zai yi.
“Baka yarda da ni ba?”
Biyu daga cikin mutanen da suke gurin ne hankalinsu ya dawo gurin Asim, har ɗayan ta tambaya ganin yadda Asim ke hucin hanci.
“Wai miya faru ne?”
“Wannan matar yake cewa Matarshi ce”
“Asim ko ka sha wani abu?”
Ɗayan ya faɗa yana kallonshi.
“Babu abunda na sha gaskiya na ke faɗa wallahi, matatace wannan”
“Ka rufa mana asiri mu fita gurin nan lafiya, wane irin matarka wai? Matarka zata fita daga gidan ka ta auri wani?”
“Tana gidansu ai tana gidansu, ita ce matata ta farko da na fara aure”
“Ka sake ta ko? Shi kuma ya aura ai daman na ji ance bazawara ce ya aura”
“What...? Wallahi wannan Namra ce”
Zayyan ne ya juyo yana kallon Asim dake kumfar baki, yana sauraren abunda yake faɗa, sai ya baro mazauminsa ya dawo kusa da Asim ya zauna yana faɗin.
“Ina fatar dai lafiya”
Da lafiya ƙalau duk suka amsa mashi suna murmushi, sai Asim ya girgiza kai ya ce.
“Ba lafiya ba, wannan matar matatace wallahi”
Wani wawan kallo Zayyan ya aika masa.
“Baka da hankali Asim wallahi, ƙa fara shaye-shaye ban gayyace ka a nan dan ka ɓata min rai ba, tashi ka bar gurin nan”
“Kana tunanin bana da hankali ko?”
Asim ya nuna kanshi yana ƙoƙarin tashi tsaye..
[7/30, 7:12 PM] Khadeeja Candy♥: *92*
Zayyan yayi saurin riƙe shi
“No karka ja kanka wahala a gurin taron nan, muje waje na saurareka wata ƙila kana da hujja”
Yana faɗar haka, ya miƙe tsaye suka fita daga faɗar suka nufi wani ɓangare na masarautar sai ga wasu abokansa sun biyo bayanshi.
“Faɗa min taya wannan matar ta zama matarka?”
Asim ya natsu sosai yana tsara irin ƙaryar da hankali zai ɗauka.
“Wannan yarinyar sunanta Khadija amman Namra muke kiranta, sunan mahaifinta Manjo Usman Zamau a sokoto yake da zama, ni kuma ai kasan ɗan sokoto ne ko? A can muka haɗu da ita a makaranta iyayenta basa so na a haka muka yi aure daga baya itama ta fara tsanata sanadin hakan ta gudu da cikina kuma ba gidansu ta koma ba sai taje wani gurin daban domin na aika nemanta a gidansu aka ce bata zo ba, daga lokacin ban sake sakata a ido ba, sanadin hakan nayi aure na auri Mardiya yanzu kuma ga wannan amaryar da na yi, kuma ta inda na tabbatar da wannan itace tana da ƙanwa Maryam wacce ta yi magana da ita a yanzu”
Zayyan yayi shiru yana nazari, tabbas ɗan'uwansa bazarawa ya aura kuma ƴar sokoto idan be manta ba kamar Mai Martaba ya taɓa faɗa masa ƴar tsohon soja ce bayan haka kuma sunanta Namra.
“Amman kai baka sake ta ba?”
Abokinshi ya tambaya.
“Idan na saketa mi zai sa na zo yanzu na ce matatace”
“Lallai akwai jan aiki, ta yaudari Abdallah kenan”
Zayyan ya faɗa yana zuba hannayensa a aljihu.
“Ka min wani lamani mana Asim, ka haƙura har a gama walimar nan sai na samu Mai Martaba na faɗa masa”
“Na aminta”
Ya faɗa zuciyarsa na mugun bugawa. Daga Zayyan ɗin har Friends ɗinsa ruɗani suka shiga da tunanin yadda haka zai faru da kuma halin da ko wannensu zai shiga idan ya samu labarin abunda Asim yace.
Ko da suka koma ciki wani malami ne yake wa'azi akan haƙoƙin mace akan mijinta. Zaunawa suka yi kowa da abunda yake saƙawa a zuciyarsa, ta ɓangaren Asim kuma yana jin zai yi ganganci idan har ya kuskura cewa Namra matarsa ce tun da yasan har ga Allah ya sake ta, sai dai what yasan tana da cikinsa ta bar gidan, and yana ganin kamar wayo ne Zayyan zai masa a zasu iya taushe maganar idan babu wanda ya sani amman idan aka ji dole a tsaya a bincike.
Wani irin abu ne ya fisgi zuciyarsa sai kawai ya miƙe tsaye ya ɗaga kujera da yake zaune ya jefar dan kawai hankalin kowa ya dawo gurinsa. A take kowa ya juyo yana kallonsa kasancewar yana can baya ne, sojoji kuma suka yo kansa da gudu, sai ya kware baki yana ihun.
“Wannan matar ta yi aure kan aure ne, matatace Namra matatace”
Ba kowa ba ne yake jin abunda yake faɗa sai waɗanda ke kusa da shi, sai dai kowa zai iya fahimtar faɗa ne yake, kamin sojaji su buga masa bindiga a ƙwari (knees) ya faɗi a gurin sai wani ya aika masa wani mugun shuri a ciki kamin su miƙar da shi tsaye su banƙareshi su fita da shi, babu wanda yace uffan har Zayyan da yake abokinsa.
Bayan an fita da Asim, Zayyan ya miƙe tsaye ya ƙarasa gaban Mai Martaba ya kai bakinsa dai-dai kunnensa yayi masa raɗa.
NAMRA POV.
Kaganin komai take kamar a mafarki, a kujerar da take zaune kawai a abar kallo ce, yau itace ake yi ma walimar aure da ɗan sarki, kuma sarkin yana zaune yana kallonsu. Wasu hawaye ta ji sun zubo mata masu sanyi, kamin hankalinta da dubanta ya karkata kan hayaniyar da take hangowa.
Wani irin mugun faɗuwa gabanta yayi, tasan yana nesa da ita amman idonta ba zai mata gizo ba, tabbas Asim take hangowa, sai dai bata iya jin abunda yake faɗa.
‘Miya kawo shi a nan?’
Itace tambayar da ta fara zuwa mata a zuciya. Sai kawai ta ji hannun Abdool cikin nata yana ƙoƙarin luma yatsunsa cikin nata, matse mata hannu yayi gam kamar za a ƙwace masa ita, be wayancin Asim sosai ba kasancewar gani ɗaya yayi masa lokacin da zai bata kyautar gida, gashi kuma yana nesa da su balle ya iya tantancewa, sam be kawo
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 65 Chapter of 71