biyar da ya wuce inda ta dawo kano da zama a lokacin ta bar yarta can a hannun kakanta mahaifiyar marigayi din.
Sai lalura ya kama tsohuwar zaman su yanzun ya dawo misau din gidan danta wa ga marigayin danta.
Kamar yadda kowa yasan mutan misau da karatun addini dana boko suna noma da kiyo kamar yadda yake al,adane hakan ga kasan hausa sai wani dan sana,an daba,a rasa ba.
Sai dai gidan malam sale abin yasha bambam don yaran gidan gasu da son hutu sun ki tsaya su dage ga karatun boko ko na addini wanda hakan yana cikin matsalan da hjy maimuna take hangowa yarta akan zaman gidan.
Wanan yasa da zaman su fatima yar gurin hjyn ta dawo nan karatun nata ya fara rawa aje yau gobe ba a zuwa har ma a debi lokaci ba a je ba.
Gashi ba wani kula a gidan zakaga yaro ya shigo da ledan idomie yana dafawa ya bad abincin gida bai ci ba duk da malam salen yana iya kokati shi gurin ganin ya kawo abinda za a sarafa aci a gidan wanda shine ya jawo mashi wanan bakin wahalan bayan yayi ritaya.
Ko dan makarantar da take zuwa sai da taimakon gwagon ta kanwar mahaifin ta Adda ta samu take zuwa makarantar jefi jefi don ba,a sata da zaman su ya dawo garin ba.
Da kyar yaran gidan suke kare secondary school di wanda dags nan sun kare karatu ke nan sai zaman bin gari da yawon buki.
Wanda duk wanan abubuwan yana cikin abinda ya tayar da hankalin hjy maimuna da zama ta gidan ba wanda ke kula lamatin wani kowa kansa ya sani a gidan daga manyar har kananan.
Dan abinda kakan ke samu take tallafawa rayuwan yar jikan nata dashi idan kuma bata dashi sai dai su hakkura ke nan.
Hakan baisa yarinyar ta dan canza ga tarbiyan da take dashi ba sai dai akwai inda take da dan rauni wanda zaman gidan yasa ta koyi rashin kunya sosai don hakan taga anayi a gidan itama ta koya ta iya.
Ga yawo bin makwata saboda gudun aiki da aike tula mata a gida don sun ganta da zafin nama aiki baya sha mata kai ko kadan
Kamar yadda kowa ya sani mutanen azare gauraye ne sai dai akwai fulani da yawa a cikkn su hakan zuri,an su fatima ma fulani usuline don har yanzun kakar tata bafa jin hausa a baki ta sosai sai ta hada da fulanci.
Itace komai na kakan tata da farkon zuwan su babu mai taimaka ma lalurar kaka sai da Adda tazo gidan tayiwa mata gidan yankar kauna kafin su fara dan taimakawa dattijuwar.
Yau ma zaune take a gaba kakar nata tana ci dan abincin da ka saka masu wanda wani lokaci dole kaka ke hakkura ta barwa jika nata tacinye sai dai tausayi kakar nata wani lokaci bai barin yarinyar taci abinci sai tace ai taci a gidan su kawar ta Rahama gidan da ke makwabtaka dasu inda duk yawon ta idan ka nemay ta ana zaka samay ta.
Dan kadan ta taba shinkafa da waken da take ci tace da kakar tata ta koshi don kakar ta samu itama ta taba bawai don ta koshi tace hakan ba.
Sai da yarinyar mai tausayi ta tabbatar da kakan ta koshi ta debo ruwa ta kawo mata ta wanke hannu ta kawar da kayan ta dawo ta dan zauna a dakin nasu wanda ke ta wajen gidan da aka gina aka kewaye da kwano ya shigo ta cikin gidan.
Ganin kaka nata ta dan kishingida yasa ta mikewa don tasa yanzun za a kwala mata kiran aike ko wani aiki na gidan wanda ya kamata ace yan matan gidan sunyi gasu zagada zagada dasu amma basu kawar da kara a gidan nasu.
Na fito ke nan daga dan dakin mu da aka ware muna a gidan ina sanda don kada wani a gidan ya ganni ya aike ni ko yace in mashi wani aikin.
Ta kai daidai kofan fita tajiyo muryan mama saude tana kiran ke ke ke Fatima ina ji hakan tuni ba baza da gudu na bar gidan ina jin tana fadin ai zaki dawo ko yaushe kika gama gantalin ki kika dawo wanke wanke yana nan yana jiran ki a gida nan.
Jin hakan ya falkar da kakan nata da bata san fitar yarinyar daga dakin su ba sai murya taji ana kwala mata kira daga waje kuma tasan bata dawo ba tunda taji kalamin saude din kan yarinyar.
Da kyar ta samu ta mke ta dan dogara kafan ta zuwa waje ta samun sauden a zaune tana wanki tana sauraron wankan yan wasan hausa tana bi.
Sai murya dattijuwar saude taji a kanta tana fadin haba saude yar nan ita kadaice a gidan nan ina ga yaranan birjit a gidan nan su ba yayan moriya bane sai wanan yar marainiyar Allah kwaya daya tilo a gidan nan da ba uba uwa kuma tayi mata nisa ita kadai ce ko yaushe tsaye a gidan nan.
Yarinya babu daman ta motsa kowa dai fatima fatima don Allah ku bar yar nan ta huta hakana mana, ko kwatanta a kan ku idan haka ya samay ku ko yayan ku.
Tsohuwar bata kai ga ci gaba da maganan ta ba tajiyo muryan Tj bayan ta daya daga cikin jikokin ta na gidan yana fadin dallah ji wanan tsohuwar.
Yomar idan ba a saka ta aiki ba wani moriya take dashi a gidan nan bayan dan aikin da takeyi mafarin ki lalata yarinya kawai.
Shiyasa ai yanzun bata tsoron kowa a gidan nan wata jikan nata da taji ana maganan ta fito daga daki tana daura dankwali a kanta zata fita yamma yayi zata ta zubar din da suka saba .
Take fadin kema wai manjo ina ruwanki kiyi fama da kanki mana kina wani fada kan wata fatima can kamar ita kadaine jikan ki a gidan nan.
Da anyi magana kice yeyeyeye, , , , wai yar marainiyar Allah ce ita kada a taba ta ubanta ya mutu waye waye da sauran su.
Ikon Allah yanzun ni kike kwakwayo yar nan komai abinku dai nice na haifi uban ku sai yaro farko yace yo ai shi kika haifa bamu ba sai kije ki ta haihuwar su can.
Badai zaji taba haihuwan mu ba mu tace wa ni Allah ya tsari gatari da saran dutse da in haifi irin ku ai gara in zauna ba haihu yafi mun jika ji shigan ka kamar ba dan musulmai ba ji kanwar ka a haka zata fita uwayen ku na ganin su.
Shine bakin cikin ki inji yarinyar da ke murza janbaki a bakinta ta gyaran fuskanta ko inzo in shaga mak ne dallah ban wuri gantalaliyar da bata san ciwon kanta ba .
Diba uwarki ne nan zaune take wankin kayanta da kanta baki san ki kama mata ba aini yarinyar nan Fatima tafi mun ke sau dubu wallahi a gidan nan.
Ke tafiwa ba muba inji namijin kai rufe mun baki mai sufar arnakun farko jika ji wanan shigan a haka kake bin gari kamar wullakantace.
Haba babba zagin yayi yawa hakana ai shigan zamanin nan ne haka ba wai ra,ayi bane Saude dakan ki kike fadan haka a gaban yaran nan.
May ye a ciki babba yanzun akan yar jikan ki da kike so kike wanan tada jijiyan wuyan haka yaron ya matsa kamar zai mangare yar tsohuwar.
Salati ta saka tana fadin yau naga yaron kawai Allah ya ban lafiya in bar gidan nan da kafana.
Aike ne dai da aiki fatima ba zatayi ba yau a gidan na soke wanan a gare ta caraf uwargidan malam sale ta fito daga dakin ta tana fadin.
Babba kibar wanan zancen don Allah kada yarinyar nan taji dadin kara finjiraiwa a gidan nan hinjira kan ai ga hinjirarun nan a gaban ku su da ba a iya aike ko nan da can.
Aikine daga yau idan fatima bata yi shi ba bazata kara cin ko loma a gidan nan kunji na fada maku.
Manjo dake kallon ta a ciki mamaki ta kasa magana sai cewa tayi Allah ka kawowa yar nan dauki a gidan nan ta huta ganin wanan warin a gidan wan ubanta.
Ta juya da kyar zuwa dakin ta na faman mita akan abinda akewa yarinyar a cikin gidan.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
YA ALLAH KA GAFARTA MUNA KURA KUREN MUN WANDA MUKA SANI DA WANDA BAMU SANI BA UBANGIJI KAJI KAN MU KA GAFARTA MU.
KASA MUNA YSORON KA DA IMANI A CIKIN ZUKATAN MU YA ALLAH KA BA MU IKON BAUTA MAKA BAUTA TSARKAKKE A SAURAN RAYUWAN MU AMEEN YA ALLAHU, , , , , , ,
Lokacin da nafito dan gidan baffan nawa bayan na gama jin umma saude tana kwala min kira wanda nasan kiran na dayan biyu ne ko aiki ko aike da bai kare min a gidan muddin ina cikin gidan sai idan Manjo ta hanani zuwa ko fita na ke samun sauki.
Shiyasa na kwammace zuwa gidan Atika ita kadaice kawata a garin tunda nazo tsiwa da fada bai bari muyi nisa da sauran kawayen da suke sona da kanwance a garin.
Amma ita Atika banda matsala da ita yanzun zamuyi fada mu koma mu shirya hakama mahaifiyar Atikan takan nuna min kulawan ta sosai kasancewa ta marainiya a gidan da ban samun kulawan da ya dace.
Da sallama na shiga gidan wanda doka ne hakan ko kana dan gida zaka shigo dole sai kayi sallama kafi shiga idan ba haka ba sai ka koma baya ka kara sallama zasu barka ka shiga.
Ba iri gida Baffa na ba da kirikiri kana sallama suna ji ka za, a kyale ka wasu ma suce ka damay su da sanaben yin sallama idan zaka shigo ka shigo kai tsaye.
Atika ce zaune tana tsifan kai a yar kujerar mata ina ganin hakan na bata rai don nasan za ai dayan biyu ko in taya ta ko mahaifiyar ta malle tace nima in sance nawa kan ai muna kitso a tare.
Wanda ban son hakan ko kadan naki jinin abinda zai taba min lafiyan kaina a rayuwana sai kitso yai min wata daya akai har tsagan kitso ya fara bacewa akaina ban sance shi sai wani yaji tausayina yasani sance kan dole zan kwance kan.
Atika tana ganina bayan karba min sallama da tayi tace yauwa kamar kin san yanzu malle ta gama maganan ki kizo mu kwamce kai mu tafi kitso yau.
Harara na watsa mata tare da fadin ki dai tafi kitso ni har yaushe kaina ya tsufa da zan sance kai tace lah yanzun wana kan da nayi kitso uku bayan wanan zaki fadi haka.
Fuska na bata ina zama tare da fadin kin san Allah Atika bana son abinda zai taba min lafiyan kan nan nawa ko kadan .
Tace rashin sabo da yi a koda yaushe ne yasa baki saba da taba kan ba har yanzu amma mutucin mace ai shine gyara kitso kuma na cikin gyaran mace don da zaran wani yaga kanki a haka sai yai maki kallon kazama.
Na harare ta tare da fadin kina nifin ke nan ni kazamace ko haka ma ranan ya sadi ya kirani da kazama wai na daga karyayi ball dani gurin da yake cin abinci.
Sai kuma naja tsuki tare da fadin koda yake wa yan nan ma ko may nayi haka zasu ce min don babu mai kaunar zamana a gidan don ciwon Malle kawai muke zaune a gidan nan.
Yanzun mu guduwa nayi ina jin umma saude na kwala min kira nasan wani aikin zata sani ga jaka sun samu a gidan ke nan ko ?
Atika tace ko basu son ki tunda Baffa shi yana son ki da Malle ai shike nan dama don Baffa di kuke zaune a gidan ai.
Nace matsalan ai shi Baffa baya zama agida kullun yana wurin tsaron shagon shi Malle kuma kinga ba maganan ta suke ji ba tunda sunga yanzun bata da kafa da zata mike ta daki mutum.
Mikewa nayi ina fadin kowa kibiyar in kama maki tace ke ba zaki kwance naki kan ke nan ba raina kara batawa ina fadin idan baki so na zauna.
Ta miko min kibiyan na shiga kwance mata kan muna hira wanda hiran duk zagin yan gidan mu nake muna fadin halin kowa a gidan.
Muryan Malle mukaji a kan mu tana fadin yau naga ikon Allah Fatima bana ce idan kin shigo ta fada maki ki sance wanan kan daya komar dake kamar mahaukaciya ba.
Ba dama in magana saboda nauyi da kunyan marar da nake ji a raina yasa na sakewa Atika kanta na samu guri na zauna.
Daki ta koma sai gata ta fito da wani kibiyan ta miko min nan na fara kwance kan nawa na dole ba don na so ba.
Saboda wanan kitson da muka tsayayi yasa na kai dare ban dawo gida ba abinda ya kara tunzura ran yan gidan mu ke nan fiye da yadda nayi tsamanin zasuyi min dama idan na koma gidan.
Ga laifin da nayiwa umma saude ga kuma wani na kara a samsn shi nasan kuma Manjo na can cikin damuwan rashin dawowana gida da wuri don duk dadewa na a gidan su Atika ban kai magariba ban shigo gida ba.
Ban yarda na shiga gidan ba kai tsaye sai da na dan leka ko babu kowa a waje ganin basu kusa yasa nayi wuf zan shige dan dakin mu wurin Manjo.
Naji an kai min duka a kai kumb tare da fadin shegiyar yarinya dazun da ake maki magana kika gudu gidan uba kika je har wanan lokacin ?
Yakara kai min wani duka ban san lokacin dana sake wani ihu mai kara ba da ya karkato da hankalin kowa gare mu.
Yar iska ba kina ganin Manjo na kama maki ba agidan nan yasa kike abinda kikaga dama yanzun.
Cikin kuka da jin zafin rikon da yai min nace may nayi ma da zaka mare ni don anga banda uwa a gidan nan kowa ke dukana haka ?
Shegiya an duke ki din kira uwar ki ta rama maki ihun dana sake yasa kowa na gidan fitowa a lokacin dama dukkan su hake suke dani.
Karawa yar iska marajin magana yarinyar nan yanzu ta fitsare a gidan nan da kike fadan haka wani ya kori uwar taki a gidan nan halan ?
Ummatu ne ke wanan maganan uwar gidan Baffa wani ihun na sake sakewa mai karfi don Manjo taji tazo ta cece ni don naga su ba hakkuri zasu bada ba sai ma zugashi yai min tsinanen duk yadda yake murdai murdai din nan.
Aikuwa manjo najin kuka na tun ihuna na farko ashe tana can tana kokarin tasowa daga daki ne sai muryan ta mukaji tana salati a bayan mu.
Tana fadin yau naga abinda yafi karfin ganina a gidan nan yanzu sadi kashe yar marainiyar Allahn nan kake son yi ko may ?
Wanan irin duka da kake mata har a dakina ina jin kara tana karasowa gurin take magana tana zuwa ta sa hannu zata kwace ni daga hannun shi ya kare rike gam don kada ta kwace yana min ketan daya saba.
Tana jan hannu na tana fadin shikata dan banza mara hankali da tunane yar nan kwara daya ta tsone maku ido a gidan nan .
Ina ga kannen ka nan baka tsawata masu su daina yawon banza ba sai wanan da aka san inda take ina nan gidan makwabta take shiga duk iya yawon nata.
Da taga yaki saki hannu nawa takai mai duka a baya tim yace wai wai wai manjo akan wanan yar kika dukeni haka yau ko sai na balla ta a gidan nan inga iya fitinan ki.
Baka isa ba dan banza uban ka ma yayi kadan ya balla ta balle kai yaron kawai sauran mutanen gidan sai abin ya koma basu dariya.
Don shi a zolaya yake mata magana inda manjo iya bakin gaskiyar ta take fada dashi zata kara kaimai duka ya sake ni da karfi na fada jikin ta da kadan mun fadi kasa Allah ya kare bamu kai kasan ba.
Tace dan kawai na gane so kake ka karasani bawai a yar abin naka ya tsaya ba yace in karasa ki in gane may manjo ki dai ji da kafan nan naki tukun.
Na dai gane zaman mu a nan ne baku so zan koma azare inda na fito da yardan Allah goben nan zamu bar maku gidan tunda na gane nufin ku.
Haba yar nan ita kadai ce a gidan nan kowa ya tashi dai A ruwa dau a ruwa yace ai da na kamata yau yadda nake so data zama a wuta.
Tace kai tafi can dan kawai kai kan bakayi hali mahaifan ka ba sam wallahi daka biyo su daka dace.
Yace halin ki na kwaso ai bakiga muna kama dake ba ta kara sukewa da yaron tana fadin ke kuma shige mu tafi kar ya karasa min ke don ba mutunci ne da su ba.
Har mun dan gwauta muryan ummatu mukaji tana fadin gaskiya babba ki dinga barin suna hukunta wanan yar.
Yanzu gashi akanta kike zagin wanan yaron haka kina wufinta shi akan yar da kika fi so a gidan koma dai yayane su duk ai jikokin ki ne kaf a gidan nan.
Saude zaki fita idona ko sai na bata maki don banyi tsufan da har sarakuwa zata wufintar dani a gidan nan daga can gefe nace Manjo kyalesu mu tafi ina jan hannun ta.
Bayan mun shiga dakine ta juya gare ni tare da fadin ke ma kingane ki bakya jin magana .
Kinfi son ko da yaushe su dinga dukan ki kamar sun samu jaka ko ?
Haka kike yi da muna gida ina kike fita yanzun kinzo nan kin koyi halin yaran banzan nan da uwayen su basa son ai masu magana.
Yanzun akan na hana yaron nan sadi dukan ki yasa saude ke son fada min maganan banza goben nan idan Allah ya tashe mu lafiya zan bar masu gidan nan indai akan nasa ido haka suna ci muna fuska ne.
Na bata rai tare da fadin nifa manjo ba da gangan naki dawowa gida da wuri ba kin ga kaina dole malle ta kwance min kai aikai min kitso an gama kuma tace sai nayi wanka naci abinci zan dawo gida saboda tasan halin gidan nan.
Tunda na dade haka ba lalai bane su bani abinci don ba bakin, ta suke ba gun sanin halin su malle tace to kin gani har makwabta sun san da bakin halin su.
Ki kama kan ki cikin yan uwan nan naki na kula ba son ki suke a cikin su ba don hakane nima bana raga masu ko kadan.
Wallahi Manjo dukan da yai min ai banso ki masa kadan ba tace rufe min baki iya karafina ke nan da dukan bai maki ba ai sai ki ramawa kan ki.
Ni dai abinda nake so dake ki koyi natsuwa ki kama mutuncin kan ki kodan mahaifin ki dake kasa kwance.
Ina jin haka bace manjo yanzun banda natsuwa ne ko may ina fadin haka na koma daga karshen dakin na zauna na bata baya alaman nayi fushi ke nan.
Kyale ni tayi na dan lokaci nasan ba zata juri ganin fushina ba da ita sai naji can tana fadin ga abincin naki dauka ki kara don nasan ma basu saka maki ba kada ma ki tambaye su don ba baki zasu yi ba.
Kyaleta nayi kamar banji ta ba sai can tace ke dadina dake baki da fahinta da wayau ni ina nufin ba baki da natsuwa bane ina nufin ki kara kama mutuncin ki da kowa mutuncin mace kimar ta.
Nagane may take nufi wanan maganan dashi na bude kunnuwa na a gurin ta kullun nasihan manjo ke nan a gare ni tun ban fahinci mai take nufi da hakan ba har na gane .
Mikewa nayi ba tare da nai magana ba na dauki kofi nayi hanyar waje tace ina kuma zaki bazaki zauna kici abincin ba nace ruwa zan debo a famfo.
Da na debo ruwan na dawo na dire a gabanta tare da dauko mata abincin data ce inci don nasan tun dan abincin rana data dan taba bata ci komai har wanan lokacin da take kokarin sadaukar da yuwanta ta bani rabon ta inci.
Dago kai tayi ta kalle ni tare da fadin yaya kuma kika aje a gabana nace Manjo kici ni a koshe nake wallahi na fada maki naci biski a gidan malle sai dana koshi .
Kai ta gyada tare da saka min albarka kamar nice na girka abincin ko na sayo aka girka nace baffa ya kamata ki sakawa albarka shida ya kawo aka dafa.
Bude abincin tayi ta ja tsuki don can yake manne a kwano har yayi sanyi kalau sosai tana shirin magana mukaji sallaman Atika a kofa.
Tana tafe da kullan abinci ta shigo ta dire a gaban manjo tare da gaishe ta tace manjo biski ne malle tace a kawo maki tasan kya so.
Manjo na washe baki tace usse, usse, malle ko ta kyauta min yau tayi min abinda naji dadi sosai ga abinci ga yar nan ta koma goshi na mata kyalli saboda gyara.
Atika tace Manjo don ma Fatima bata so gyara aida tasha gyara gun malle to ita fatiman ne idan an mata gyara sai an dauki lokaci bata kara ba.
Malama ban fa son kushe kin fini gyara ne ko may na fadi ina hararan Atikan sama da kasa da sauri tace , a,a ni na kai can.
Dallah rufe mana baki ke badon Allah yayi ki fara ba ai da bamu san iyaka ba kin gode kin kwaso iyayyen ki duka a gurin fari har makin so ki fisu da kina gyaran jikin ki aida kyaun ki badai nan ba.
Bude kulan da Atika ta shigo dashi nayi sai kamshi ya tashi a daki yana daukan ido nace kinga Atika manjo fa bataci komai ba tun kan na fita gidan nan dazun har yanzu don Allah bari ta danci wani abu kada ta fadi muna.
Nan na tursasa manjo taci abincin taci abinci ni kuma na hau ba Atika labarin yadda muka kwashe da yaya sadi lokacin dana dawo gidan ina sanda.
AMERICA
Yana zaune ya