dawowan nasa gida a kan lokaci yanzu shekara biyar ke nan fa da ya gama karatun sa wai sin bashi aiki a can england din.
Duk wani aiki da zaiyi can yanzu akwai makamancin shi a na kasan amma ita ta ki ta gane hakan sun hada kai dashi duk lokacin da zan mai maganar gida sai ya kai karana a gurin ta nasan kuma ba komai bane sai dan abinda take ganin yana dan turo mana nan ne yake tsone mata ido kawai.
Tun da ya fara magana ido kawai ta tsura mai tana sauraren shi har lokacin da taji yayi shiru ga maganan shi ta sauke ajiyan zuciya tana fadin.
Nima dai wanan zaman da yaron nan ke yi kasan masu jajayen kunnuwan nan bai kwanta min a rai ba sam duk da na gari ai gida aka sanshi ka gama abinda ya kai ka sai kuma ka dawo gida a san ka gama amma may ye amfanin zaman shi a can shi ba iyali ya ajeba.
Balle a ce don su yake can zaune wani kasan kuma da hakan ne ma ai hankalin kowa zai fi kwanci dashi koda yana can din.
Sai dai ina ganin ita uwar bata tunanen hakan gare su don dan abinda suke aiko mata din dashi nan tana famkama wa mutane ita ta iya haihuwa.
Kamar tasan abinda Allah zai mayar da sauran yaran nan gaba idan Allah ya raya muna su ai shi mutum ba a gama hallitan sa sai ranan da ya mutu.
Zaman su gida shine kimar mu da cikar kamalan a garin nan don ba abin alfahari bane ace danka ya tsabbari ya koma wata kasan na uwan duniya ba tare da iyali ba.
Alh sani ya sunkuyar da kanshi kasa yana nazarin maganan tsohuwar daya girgiza mashi zuciya ya kasa furta komai ga hakan .
Sai dai a zuciyar sa yana nasawa dole ne yaran nasa su dawo gida yanzun don gaskiya mahaifiyar tasu ta fada yanzun don haka zai dauki mataki a kan komai.
Da haka ya tashi yai mata sallama tare da yaran ya nufi hanyar fita daga part din cikin sanyin jiki bayan yai wa mahaifiyar tasu sallama.
Yana aiki a shago kira ya shigo mai bai dakatar da abinda yakeyi ba don kada lissafin ya kubce mashi sai da wayan ya tsinke inda ba lokaci wani sabon kira ya kara shigowa again.
Don haka ne ya dakatar da aikin ya rarumi wayan nasa a ciki fushi sai dai ganin wanda ke kiran shi ne yasa ya katse fushin yana mata sallama.
Tare da fadin Allah ya barmin min antyna ta kaina ya gida ya waje su inna kuma ?
Tace Amadu lafiya ba lau ba da sauri ya tare ta yana fadin anty may ke faruwa a gidan ?
Tace wallahi jikin baba ne yaki dadi yau kwana uku ke nan yau ma dai jikin nasa yafi tsanani gaskiya.
Cikin kidima ya furta subbahanallahi anty shine ba wanda ya kirani ya fada mi ko jiya fa munyi waya da Abu bai fada min komai ba.
Tace baban ke fadin kada a fada ma a tayar ma da hankalinka zai samu lafiya da ikon Allah sai dai kuma har yanzun jikin ba dama gaskiya.
Yace yanzun dare yayi anty amma gobe da yardan Allah da safe zan shigo garin sai a zauna da shiri idan nazo zamu wuto asibiti dashine don wanan karon ba zan yarda da zancen a barshi a gida ba.
Asibiti zamu zo dashi gobe a duba shi tace Allah ya kaimu Amado gaskiya yanzun kan dare yayi sosai sukai sallama ya kashe wayan lissafin da bai tsaya ya karasa ba ke nan ya nufi gidan uban gidan shi wanda yanzu ya zamay mai kamar mahaifi a gare shi.
Bai samu kowa a farfajiyan gidan ba don haka ya nufi hanyar shiga gidan kai tsaye Ahmed da yanzu ya goge ya zama dan birni sosai ga ilimin bokon daya samu har master sai da yayi ga na arabiya.
Don hakane yake aiki da ilimin shi duka biyu wurin gogayya da al,amuramshi na kasuwanci har kasan waje yake fita ya odo masu kaya irin wanda suke bukata a kasuwancin su.
Daga kofa ya tsaya yana kwala sallama bai yarda ya shiga ba kai tsaye duk da yasan baida shamaki yanzun a gidan.
Sallama biyu gana uku yaji zazzakan muryan salma na amsa mashi sallaman nasa ko ita yayi dace ne ta fito sashen Amma a lokacin wanda ba kasafai take zuwa ba sai idan taga dama takan dan je suyu barkwanci da tsohuwar.
Salma na farin cikin da zuwan Ahmed gidan su kodai da take kokarin boye hakan a zuciyar ta bata son wani ya fahinci hakan musaman ma hajiyar su data dauki karan tsana ta sakawa yaron.
Ahmed yayi aure farko a nan kano inda ya hadu da wata yarinya Alh sani ya tsaya mai har akai auren shida su Amma, gurin haihuwar farko matar tasa Allah yai mata rasuwa ta bar yaron da ta haifa har wanan lokacin bai kara wani aure ba.
Ita salma da farko bata dauka son Ahmed takeyi ba sai daga baya ta fahinci ta fada son Almajirin gidan nasu kamar yadda hjyn su take kiran shi idan ya bata mata rai.
Ya fahince ta sarai sai dai bai yarda ya bata fuska ba ko kadan sanin halin mahaifiyar ta da yayi ba mutunci ne da ita ba ko kadan .
Don hakane yake kara kaucewa duk wani abinda zai hada shi a gida Alh sani da ita balle kuma salma ba irin choce din shi bace don yana son mace mai addini da tarbiya ba wace zata iya yiwa babba rashin mutumci ba kamar uwar ta.
A cikin dakewa yace ke Alh yana kusa ba tare da ya bari magana komai ya shiga tsakani su a gurin tace yana falon shi a sanyaye.
Ya wuce baiko kara waigo ta ba yabarta a tsaye tana kare mai kallo murya mahaifiyar tane take fadi salma yaya haka kuma ?
Salma tayi saurin fadin ni da dan rainin wayau nan ne daga zuwa yana tambaya wai Alh na ciki ne kamar ya aje ni a nan.
Wanan yaron ai gani yake wuyan shi yayi kauri yanzun shiyasa yake ganin kamar daidai yake da kowa a gidan nan.
Salman tayi kwafa ta wuce ba tare da ta tsaya jin sauran maganan uwar nata ba don zata iya jin abin haushi a wurin wanda zuciyar ta ba zai so ba.
Ahmed ya tsaya daga falo yana ma Alh salma sai yaron wurin hjy maryam ya leko don ganin maima Abban su salma a lokacin.
Yana ganin Ahmed yaron ya washe baki yana fadin kazo min da keke na Ahmed yace bako gaisuwa boy don haka suke kiran yaron dashi.
Yaron yace ina wuni yana dariya sai daga ciki Alh yai magana yana fadin ba zaka bashi wuri ya shigo ba ka tsare shi da magana.
Yaron yana kokarin juyawa Ahmed din ya kama mai hannu suka shiga falon tare inda baya salman da ya kara yi ne ya shigo falon.
Gaida dattijon yayi da wuni wanda ke mashi kallon mamaki don ganin shi gidan a wanan lokacin do basu dade da rabuwa ba.
Wuri ya samu a kasan kafet din ya zauna kamar yadda ya saba yi idan ya shigo falo ya fara gaida Alh dake mai kallo mamaki har wana lokacin a fuska shi
Baya gama gaisuwan su ne Alh ke tambayan shi ko lafiya yace Alh da sauki yana gyara zaman shi a daidai lokacin da Alh ke tambayan shi may ke faruwa hjy jummai ta shigo falon tana cika tana batsewa.
Ahmed yace yanzu nayi waya gida suke fada min mahaifina baida lafiya sosai shine nake son gobe idan Allah ya kaimu in yi asubancin zuwa gidan in dubushi.
Sai Alh sani yace ka duba shi kodai azo asibiti dashi ai asibiti yakamata kaje ka dauko shi kuzo zai fi.
Yace haka nake so idan Allah ya kai mu din idan naje yace subbanallahi ubangiji ya bashi lafiya Allah yasa kafarane hakan Ahmed yace amin.
Hajiya jummai dake zaune kanzil bata ce dasu har addu,an da Alh sani yayi bata karba ba sai wani kada kafa da takeyi a saman kujera inda take zaune.
Alh sani ya juya wurin ta yana fadin Ahmed ne yazo yanzu ashe mahaifi shi ba lafiya kuma yanzu fa muka rabu ance baya baida kadan?
Tace Umm,wummm Allah ya sauwaka taci gaba da kada kafan ta da takeyi su kuma suka fita batun ta suna magana akan ciwon tsoho.
Addah ta koma ta barmu da kewan ta bayan tayi muna sati biyu tana duban mahaifiyar ta kamar yadda take muna tun lokacin da mukazo misau din.
Tun tafiyan ta sai gidan ya koma muna babu dadi zaman dai ga munan ne a cikin sa haka yasa na dan fara shiga gidan su Atika don in debe damuwa a raina na rashin Addah.
Tun ina kunyan su na kaurace masun da nayi na kwana biyu don zuwan Adda din har yakai na sake jikina mun koma kamar yadda muke a baya don banga wani alaman sauyin fuska ba a gare su kaf gidan.
Sai dai yanzu ina zuwa makarata ban yarda in daga kafa da zuwa school din tunda Addah tayi min nasiha akan hakan.
Irin nasihohin da taimin ne ya ratsa min jikina na daina fashin zuwa karatu har da islamiyan da Atika ke zuwa yanzu a tare muke zuwa kullun.
Haka yasa wani irin natsuwa ya fara shigana a hankali wanda ban san inayi ba sai dai nakanji mutane na fadin zuwan Addah ya canza ni kwanan nan.
Nidai sai murmushi nake masu a dole ina son fita daban da yaran gidan baffa da Addah tace tana son inyi ga kuma manjo kamar zuwan Adda tazo mata da maganine don ta samu lafiya yanzu sosai ba kaman can baya da take a rabke ba.
Don Addah taja min kunne sosai kan in kula da Manjo don kada in rasata don in manjo ta halaka ni zanfi kowa shiga damuwa.
Banso abinda zai taba manjo har yakai ga halakata don haka na daure ko bayan wucewan Addah ina kula da kakata yadda ya kamata kamar yadda na Adda tana mafa data zo.
Sai ga tsohuwa tana samun sauki sosai ashe dama damuwa da kuma yunwa ne yake batun halaka yar tsohuwar a gidan.
Ko baffa Adda bata kyaleshi ba akan kula da mahaifiyar tasu haka yasa yanzu duk dare sai ya dan sawo mata dan abin kwadai ya miko muna da yake dakin mu ba a cikin part din matan shi yake ba mu muna daga waje farkon shigowa gidan.
Wani lokaci dan kunshin nama ko burodi da kayan shayi ba tare da iyalin shi sun san yana hakan ba don idan sun sani ba zasu bari ba.
Ranan da baida zarahi kuma yakanzo yai tabata hakkuri kamar wanda zaiyi kuka a ranan hakan ba karamin fahintar dani darajan iyayye a guri da yayi ba.
Kamar yadda na canza hakane yake sa ko na dan shifa gidan su Atika ban dadewa koda yaushe kazo gida zaka samay ni a dakin mu ko ina wani aiki wa kakata.
Sai dai haka bai hanani aikin wahala ba a gidan Baffa din inda hakan ke bata ran manjo tayi fadan haka din har ta gaji basu daina ba.
Don haka na taso aikin wahala baya damuna ko kadan sai dai abinda ban sani ba a gamay dani ashe kafin tafiyan Addah sun zauna sunyi magana a kaina.
Inda Adda ta zaunar da manjo cikin hikima da dabara ta fahintar da ita illan barina in tashi a gidan baffa da suka hango min itada mahaifiya ta.
Wanda hakan yasa jikin manjo yayi sanyi don jin ance zan iya lalacewa ko samarin gidan Baffa su lalatani yasa tsohuwan saurin yarda da shawaran su din wanda bata fatan haka a gare ni .
Ni da take gani yanzu farin cikin rayuwanta kamar don ni ni kadai Allah ya bar muna ita tace ba wani gardama duk sanda mahaifiyata ta shirya tazo ta dauke ni.
Ta Amincr da zamana a gurin ta muddin rayuwana zai inganta a can kano din da wanan maganan suka tsaya har ta tafi.
Yadda Ahmed yaje gida ya samu mahaufin shi hankalin shi ya tashi sosai inda ba bata lokaci ya dauko shi zuwa kano ko ina bai tsaya dasu ba sai asibiti
Hjy maimuna bata sanda zancen ciwon mahaifin Ahmed ba sai washe gari takd ji a gurin gwagon ta da maigidan su ne ya fada ma mahaifiyar shi zancen.
Batai kasa a gwiwa ba wurin kiran Ahmed din tana tambayan shi jikin mahaifin nasa lokacin suna hanyar kano daga katsina.
Ya dauki wayan bayan sun gaisa take fadin Ahmed ashe abinda ke faruwa ke na yanzun nake jin wanan maganan a gurin gwago.
Yace hakanane hjy yanzun haka muna nan hanyar kano zan shigo dashi asibiti tace subbahanallahi ashe jikin sosai ne Allah yabashi lafiya ya kawo ku lafiya ta kashe wayan.
Ajiyan zuciya ya sauke yana mai jin dadin kiran da taimai din don ta kula da abinda ya shafe shi sabanin hjy Jummai da agabanta ya fada ma maigidan nasa amma ba wani damuwa data nuna akai.
Sai dai shi Alh sanin yana ta kiran su koda yakai can ma sai da sukai waya da majincin kan shine yace azo dashi asibiti a duba shi.
San nan tsohon ya yarda zaizo don yana ganin zai dorawa mutane lalura ne kaishi can din da Ahmed yace zaiyi.
Shine Ahmed din ya kira Alh sani don yaiwa tsohon magana ko zai yarda su zo dashi asibitin.
Suna zuwa ba,a tsaya wani abuba gado aka basu inda aka daura mai drip aka fara gwaje gwaje akanshi.
Ana haka hankalin Ahmed a tashe saiga hjy maimuna sunzo ita da hadiye da Amma niki niki da kayan abinci da sauran abubuwan bukata har Alh sani kanshi yana asibitin akan tsohon don kafin su kawo kano ya gala baita sosai.
Sai zuwan su ne ma ya tuna da abinci da bai sawowa sauran mutanen da suke tare ba a lokacin yaji dsdin hakan inda ya kara ganin mutunci da kimar hajiya maimuna di sosai a idon shi.
Haka sukai ta zirga zirga akan tsohon kafin agane abinda ke damun tsohon wanda sai an mashi aiki dole akace .
Hjy maimuna bata gaji ba wurin hada masu abinci kullun sau uku a rana Ahmed din ke zuwa ya dauko ko ita da hadiye su kai masu asibitin.
Inda take shan zagi sosai a wurin kishoyin nata sai dai hjy maryam takan dan leka asibitin wani lokaci ta gaida su sai dai su basu sani ba.
Hakan ba karamin Alheri ya jawowa hjy maimuna a wurin maigidan nasu don bayan kimar da tayi har da alheri take samu wurin yin hakan ga maigidan nasu.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
YA ALLAH KA SAKAWA IYAYYEN MU DA GIDAN ALJANNA, KASA MUTUWA TA ZAMO HUTU A GARE SU ALLAH KA RAYAWA KO WATA UWA DAN TA TAFARKIN ADDIN MUSULUCI KAYIWA ZURI,A ALBAKA ALBARKAN ANNABIN RAHAMA AMIN INA TAYA KOWACE UWA FATAN ALHERI GA ZURI,ANTA HAPPY CHILDREN DAY,, , , , , , , , , ,
Ina kwance dakin mu barci ya soma daukata hayaniyar dake tashi daga tsakar gidan mu ne ya falkar dani dagaz barcin dana soma din a lokacin.
Dagani har Manjo saurara abinda ke faruwa daga wajen gidan mukayi wanda hayaniyar ba iya cikin gidan mu kawai ya tsaya ba har wajen gidan muke jin hayaniyar yana tashi.
Hankali tashe muka fito daga dan dakin mu don ganin abinda ke faruwa a wajen kada a rutsa damu a ciki.
Mun isa wurin daidai lokacin da wani mutum ke fadin ku dai bakuyi halin mahaifin ku ba mutumin kirki duk unguwar nan kowa yasan mutumin arziki ne.
Don ba abinda ya taba hadashi da wani a cikin unguwar nan na assha amma ku, kun addabe mu kun hana mu zaman lafiya.
Kuna nema ku gurbata muna tarbiyan yaran mu a cikin unguwa yanzu may ye amfanin irin wanan ki dinga jawo muna mazan banza a unguwa suna zuwa suna tayar muna da hankali a cikin unguwa.
Yanzu may ye amfani irin wanan abinda ya faru daidai lokaci muna guri yake ta rabtako bayanin shi a hasale.
Manjo ke tambayan na kusa da ita abinda ke faruwa duk da matar bata sheda manjo sai fadi take .
Wallahi fa wanan fitsarar yarinyan gidan nan ne saliha tana tare da wani a mota suna iskanci ashe kuma ta gyayaci wani shi fada ya kaure a tsakanin su har da fashe fashen kai .
Salati Manjo da muke rike da hannu juna sarke da juna ta saka tare da fadin kai wanan yarinyar batai gadon arziki ba nasan fitsaran yaran nan zai kaisu ga hakan.
Da sauri ta tasa keya na muka koma daga ciki don kada mu karasa jin abin takaici yau ace jininta ne akewa wanan shedar haka ba dadi ji a bainar jamma,a.
Duk da naso in tsaya inji kan maganan don ban fahinci komai da matar nan ta fada muna ba sai dai ba yarda zanyi dole in bi manjo mu koma ciki tunda haka take bukata din.
Shigar mu gidan ba daki muka shiga ba daga waje tsakar gidan muka tsayawa tayi waje anan tsakar gidan tana surfa masifa tare da nuna yaran halin iyayyen su mata suka biyu ba jinin ta ba.
Har tayi ta gama basu kulata ba da kyat na jata zuwa dakin mu ranan dai ina ganin batayi barcin kirki ba saboda bacin ran abin kunyar da jikanta ta jawo mata a gari.
Washe gari da safe kamar yadda baffa ya saba zuwa ya gaida manjo kafin ya fita yauma haka ya shigo daga kofan dakin mu inda muna ciki kwance don sanyin da akeyi.
Mukaji muryan shi a sanyaye ba kamar kullun ba shima dai ko ba a fada ba nasan da bakin cikin abinda saliha tayi jiya ya kwana dashi.
Ciki ciki manjo ta amsa mashi jin hakan ya bani haushe don lokacin wayau na bai kai ba don haka banga laifin baffana a cikin maganan ba sai laifin iyayyen su mata da basu son aiwa diyan su fada naji.
Don haka na amsa mai da karfi yadda zai fahinci ba barci mukeyi ba a dakin hakan yasa ya cire takalman shi ya shigo dakin da ganin yanayin sa yana a cikin damuwa sosai.
Ya samu wuri ya fara gaida mahaifiyar tashi ya samu ta karba mai da kyat tana cika tana basarwa sai dan shiru ya biyo a dakin ganin haka yasa na fara gaida shi da kwana.
Sai lokacin ya dan sake fuska yana fadin fatima kun tashi lafiya yaya daren kuma na amsa da Alhamdullahi ina kokarin tashi don in fice a dakin don ba zan so manjo tai mashi magana ba a gabana.
Ya dan dade a dakin kafin ya fito ranshi bace ya fice daga gidan duk da iyalin nasa duk suna waje bai samu wanda yai mashi a dawo lafiya ba daga cikin su.
Sai ni dake tattara kwanukan da akai amfani dasu a daren jiya don in wanke nake fadin Baffa a dawo lafiya yace dabi tare juyowa Amin yar albarka.
Wanan kalman yana mun dadi idan yana fada min hakan bayan fitan shi baiko gama ficewa ba naji muryan mama saude na fadin wa yanda ba,a sawa albarkan ba ace su mutu.
Ina jin ta ban dago ba sai danaji muryan yaya hashimu yana fadin ai wanan shegiyar yatinyar iyayi ne da ita da sanabe ya fita baicewa kowa komai ba sai itane mai mashi a dawo lafiya.
Haushin maganan shi naji nace babu ruwan kowa dai dani tunda ba mutum nacewa hakan ba dama yafi kowa zama dan iska a gidan.
Don sai yayi kwanaki bai leko gida ba yana can gurin shaye shayen shi ko dabanci da yakeyi aiko ban san ya taso ba yana bayana sai jin gau gau ya sharara min mari har biyu a kumatu na.
Wani irin kara na sake daya ruda gidan wanda yasa manjo yin tsale daya sai gata waje daga dakin mu tana fadin kai kai may ye hakan may taima ka doke ta ?
Yace ko zaki rama mata ne kin wani fitowa kina tambaya a tsawace tace nace may taimaka ka doke ta da safen nan haka ?
Bai ankara ba yaji duka a jikin shi dim dim sake baki yayi yana mata kallon mamaki ta juya tare da ja min hannu tana fadin bar dan banza wanke wanke ma ba zakiyi ba su da suka bata su wanke abinsu ba baiwa na kawo maku ba ai a gida.
Muna shiga dakin daki tace garin nan zaki bari maganar Addan ku ya soma zama gaskiya zaman ki a gidan nan ba zai yuyu ba don yaran nan suna iya illanta ki wata rana.
Cikj turo baki nace ba nace maki mu koma misau ba kin ki tace bana ki bane A ruwa lafiyata nake nema a nan idan bashi ba may zai kaini zama wannan gidan ina ganin bakin ciki tunda baffan naki bai iya tsayawa ga iyalin shi.
Nace manjo may ye laifin baffana a nan dole fa ya fita ya samo abinda za a ci tace nasan da hakan.
Matan kirki ne dai bai aurowa diyan shi ba tun farko ai wanan halin daga gun uwayen su suka kwaso shi nidai yanzu so nake yar nan tazo ta tafi dake kano wurin ta hankalina zaifi kwanci gaskiya idan kin daga daga gidan nan.
Da sauri na dago kai tare da fadin kano kuma manjo ni dai gaskiya ban zuwa kano ki mayar dani misau mukoma can ko gurin Addah.
Kano gidan da basu son bako gidan da ba,a fita kullun ana daki gidan da suke fada kullun ni gaskiya ban son kano din nan manjo ko kadan.
Bata tankani ba sai dai shirun da tayi tana tunanen tunda nace ban zuwa kano sai dai ta hakkura ta koma misau inda muka fito duk da gidan namu yanzu duk ya lalace yana son gyara yana daya daga cikin abinda ke kara maga gwiwa da komawa misau fin don gidan ya tsufa sosai.
Da taji na matsa da mita akan kanon sai tace to ai shike nan tunda bakya son can din sai muyi hakkuri mu zauna a nan din kafin Allah yayi muna