An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
KOWA YA RAINA TSAYUWAR
WATA
1
NA
BILKISU SALISU AHMAD
FUNTUA
KAREWA
Ya musulmi `yan uwana don Allah a rinka
kiyayewa a daina shiga kewaye da
litattafanmu domin akwai sunan ALLAH.
Saboda ba shi yiwuwa mu yi rubutu mu
kare mu kasa anbaton Allah a ciki.
Don Allah ina fata ana anfani da
gargadinmu na cewa a daina shagalta da
barin ibadar da ta hau kan mu, kada
karatun littafinmu ya shagaltar da kai daga
barin addininka, in ka yi haka kai da AIlah.
iv
Daga
Anti Bilki
25/11/99.
Malam Kado ne ke tafe ya na janye da kekensa, ga kuma
fatanya rataye a kafadunsa, a bisa dukkan alamu daga gona ya
fito. Can daga nesa amininsa Mallam lliyasu shi ma bisa nasa
keken ya kira Malam Kado in da ya ke cewa "A`aha Malan
Kado, kada dai ka ce har ka baro gonan kenan?" Malan Kado ya
waiwaya ya dubi Malan lliyasu ya dan matse fuska nuna alamun
damuwar ciwo sanna ya amsa, "Bar ni kawai lliyasu ciwon kai
ke neman kai ni kwance. Na rasa wane irin magani zan saya a
kemis ko kuma wane irin sauyu zan jika domin duk wanda na
sani na yi anfani da su har na kai makura".
lliyasu ya kafe kekensa ya rike kan ya zubawa Malan Kado
ido cikin damuwa, ya dan lunfasa sanman ya ce "Malan Kado
ban san ka da kafiya ba, sai akan ciwon kan nan, wai har sau
nawa zan gaya ma ne kaje asibiti su yi maka gwaje-gwaje don
su san abinda ke damunka? Ka ga anan za'a san maganin da ya
dace da irin ciwon ka, amma har yaushe za ka yi kwance a gida
kana shanye-shanyen maganik daban cuta daban".
Malam Kado ya ce "Ai ni tsoro na Allah tsoro na asibiti
yanzun nan sun labta maka cutar da tunda iyayena suka zo
duniya har su ka bar ta ba su taba jin ko sunanta ba amma ace
mutun na da ita, haka nan kuma ga wani tsire-tsire ace kada
mutun ya ci kaza kada yaci wancan, shin ina dalili? An taba
ganin abinci ya haddasa cuta? Sai dai ya yi sanadiyar warkewar
cutar, to ni kaji abunda ke hada ni da asibiti". Iliyasu ya yi dariya
yace, "Har yanzu dai kana nan da halayyarka ta mutanen da?
Don Allah ka janye wannan ra'ayin ka shirya gobe na raka ka
asibiti, yanzu idan da Allah ya raya mana Tasi'u haka zai dinga
wahala da kai akan zuwa asibiti?" Malan Kado ya dan yi
murmushi yace, "Ka san ko Tasi'u har ya rasu ba shi da wani
buri illa na son ya zama likita". lliyasu yace, "Allah ya jikan
Tasi'u ai ga kanwarsa nan Dije na ga tana da natsewa sai mu kai
ta aikin koyon jinya".
Malan Kado vace, "Anya ko hakan na yiwu akan Dije?. Ni
wallahi ma lliyasu duk na kagu na kawas da Dije ko na sami
kwanciyar hankalin iyalina ace kamar su Ankudi da Sabura baza
su zauna lafiya da Dije ba, sai`ya` yan da su ka haifa da cikinsu
sune 'ya'ya? Kai yau da safen nan sai da Ankudi ta rinka tikar
Dije a gabana wai don bata share mata akurkin kajinta ba da
kyau, bayar ga wankin 'ya'yansu na jiran Dije to ire-iren wa'annan fitinu na cikin gidana suke kara haddasa min ciwon kai".
Malan lliyasu ya hasala yace, "Kai ai dai maganinka kenan
su Ankudin, har yaushe yarinya zakakura, zaruma mai hazikanci
kamar Dije za ka hana ta ci gaba da karatun sakandire bayan ta
zo mana da sakamako mai kyau, daga kammala karamar
sakandire ka kama yarinya ka hana ta ci gaba da babbar sakandire
wai don fitinar su Ankudi". Malan Kado ya bata rai yana girgiza
kai yace, "Kai Malan lliya, gara dai na yi ma Dije aure. Ina anfanin
irin zaman da take yi a gidana sai kace baiwa ba `ya ba?"
Iliyasu yace, "To yanzu mijin ta samu?" Kado yace, "A'a tunda
maganar Malan Dahiru ta rushe har yanzu babu wani tsayayye,
sai dai ni a zuciyata akwai yaron nan dan gidan Sarkin Makera
wanda ke karatu a jami'ar Amadu Bello da ke Zaria, wato Yusufa
kasan sa'o'en juna ne shi da Tasi'u marigayi na wajena, to ku
san kullun ya zo daga Zariaya sai ya zo ya gaishe ni, ni kuma sai
na ji dadi na ga tamkar Tasi'u nawa, don haka na ke son Yusufa,
dalilin kenan na kallafa rai da son na ba shi auren Dije.
lliyasu yace, “Ai ko idan a kai haka an kyauta domin ma
ganin natsuwa a wajen Yusufa illa dai kawai na sha jin cewa
ance yace ba zai yi aure ba sai ya mallaki aikin kansa yadda zai
iya tallafa nauyin kan shi da nauyin iyalinsa, domin ka san
mutanen na su ba wani abu ne da su ba”. Nan da nan Malan
Kado ya saki jiki amma sai ya nuna`yar damuwa a tare da shi
yace,`Ahaf lliyasu, ai kai ka san hali na ba wani abu na ke so
ba, ko wani kwadayin abun duniya illa buri na in ga cewa Dije ta
auri mijin da ya san ciwon kan shi sannan sai ga mutuncinta har
bayan ranta, haka nan kuma su mike tare babu wani kace nace,
saboda haka vanzu zan shawarci kanwata Tambaya aminiyarta
ce, kusanma na ce Tambaya ta yi ma gwoggon Yusufa babbar
kawa wadda ta rufa zuwa daki. Abinda shawara ta bayas zan
nemekа."
Suka yi sallama da wannan shawarar ta kulla auren Dije
2
da Yusufa kowanne ya doshi gida kodayake Malan lliya ba
komawa gidan zai yi ba. Ya zauna cefane ya mika ya kara ficewa
zuwa kasuwa wajen harkokinsa na sayar da tabarmi yana ko isa
ya cimma wasu baki sun kawo masa damman tabarmi don ari,
aka shiga ciniki.
Shi ko mutumin sai ya kutsa kai zaurensa yana kokarin
jingina kekensa inda ya kan jingine sa amma ya rinka tsinkayo
kukan Dije daga can tsakargida, zuciyarsa ta kara hasala har
yaushe za'a rinka yi ma budurwa haka, ai kannanta ma sun
rainata, haka nan yaushe wani namijin kirki zai zo auren Dije
gidan nan? Ya shiga gidan zuciyarsa a cike ya dubi inda Dije ke
tsaye tana kuka ya galla mata harara ya ce, "Ke maza daura zani
kada in kara ganinki tsaye sai riga da dan fingilin siket kamar
wata kabila". Ta dafe ido cikin kuka tace `Ai zanin na dakin
Gwoggo Sabura inda ta shake ni da duka kuma idan na koma
kara min zata yi". Yace, "Shige mu je dakin Saburar".
"Ke Sabura ina zanin Dije?" Sabura a fusace cikin tsiya
tace, "Ai kazo tare mata din ne ko? To wallahi sai dai in yau ba
za ka ci abinci ba amma dole sai Dije ta yi yadda na ke so ko za
ka ci abinci gidan nan haka kawai ka daure ma yarinya gindi
daga ni har yaya Ankudi ta mayas da mu banzaye? Daga cewa
je ki ki debo min ganyen gwanda sai ga ta da ganyen zogala, ita
mahaukaciya ce koko karamar yarinya ce?"
Malan Kado ya ce, "Ni kam ban tambaye ki abinda ya
hada ku da Dije ba, na dai ce, a bata zaninta, haka nan ban hana
ku dukan ta ba amma a dai na yi mata tsirara domin shekarunta
sun kai munzuli yanzu".
Malan Kado yasa kai ya shige turakarsa a yayin da ya ga
Sabura ta wurgo ma Dige zanin ta. Ya nemi filon matashi ya
danne kan shi wai ko ya samu saukin azalzala masa da ya ke yi
amma ina! haka ya kasance a kwance babu sauki sai wajen
Allah.
Da azuhur ya lallaba ya je masallaci dan ya bada faralli
bayan ya dawo ya zauna a gindin wani kuturturen dutse da ke
aje gaban gidansa, ya dafe gefen kan da ke masa guda tamkar
zai rabe biyu don ciwo a lokacin wata 'yar filani tare da yarinya
3
mai hura suka ratsa ta gabansa yasa baki yayi kiransıu, ya sayа,
mai rionan ce ma yasa ta dama masa ya kafa baki ya kwankwade.
A cikin gidansa su Sahura da Ankudi ko wacce ta yi
tanadin abinci ita da 'ya'yanta suna ta ci amma Dije na zaune a
falo sanye da abayanta da casbi a hannunta a bisa dukkan alamu
itama sallar ta idas. An daulki lokaci Malan Kado bai ji motsin
sun Ikira Dije sun bata abincin ba, sai yasa baki ya kira ta ya
tambayi ko ta ci abinci? Ta ce, "Tun kokon safe". Ya fiddo naira
shidda yace ta je ta sayi ko da alalan gidansu Talatu ne.
Ta isa gidan su Talatu mai alala amma ta yi rashin sa'a
aka ce, Talatun ta tafi da alalaın talla. Nan da nan ta nufi gidansu
Inna sa'ade tana sayar da shinkafa da wake. Inna Sa'a mahaifiyar
kawair Dije ce, wato Jummai sai dai ita Jummai ta yi sa'a ta ci
gaba da karatun ta na babbar sakandire don haka ne ima ta rabu
da zuwa gidan, haka nan kuma su Inna Sa'ade da saıran matan
anguwa ansan irin azabar da matan uban Dije ke gallaza mata
don haka ko da Malan Kado ya ce zai fidda Dije ya yi mata aure
kowa ya yi murna da jin hakan.
Ta yi sallama Inna Sa'a na shirya ma yaro dan talla shinkafa
da wake, ko da ta hangi Dije da 'yar roba tace, "Kin yi sa'a, 'yar
gidan Baba Kado saura kiris a tafi da ita talla."
a
Dije ta yi murmushi jikinta har rawa ya ke yi saboda yunwa
tace, "Wai, amma na ji dadi Inna domin yunwa ta gallabe ni".
Inna ta yi murmushi tace, "Ai da ganin idanunki an san da labari
cikinsu, to miko min robar, kin ga tuwon shinkafa can da
Babanku ya ci ya rage dauki ki fara ci ko?" Dije ta zauna tana
sharar tuwo miyan taushe don dadi ta rasa a wace duniya take?
Bayan ta gama aka dafe mata roba da wake da shinkafa sannan
Inna Sa'a ta ki amsar naira shidda.
Dije ta iske babanta kwance a dakinsa ta lissafa masa
yadda a ka yi da Inna sa'a, sainnan ta aje masa wake da shinkafar
a gabansa ta matsa masa akan ya tashi ya ci domin ita ta cika
cikinta amma ya nuna mata ba zai ci ba, taci gaba da yi masa
korafi, har ya kare ya shaida mata ciwon kansa ne ya matsa
masa, ta ce, "To Baba na ze da kankara ko na kawo maka ka
danna a kai?" Ya ce, "E, kawo min". Ta zauna a gefensa yana
4
dannawa ita kuma tana fadin "Sannu Baba, Allah ya baka lafiya"
Yana cewa "Amin Dije". Can yace "Dije ki rinka kiyayewa da
neman abinda matan gidan nan za su rinka dakarki kaman jaka,
a kodayaushe ki rinka sauraren aiken da suke ma ki, bana son
yawan fitina ko kadan" Kanta a sunkuye tace, "To Baba amma
Allah ne shaidata sai ko Shehu tunda yana nan ta aike ni domin
da na dawo tace, ba haka ba, shi Shehun ne ya ce, kai gwoggo
zogala kika aike ta mana."
Malan Kado yace, "Bana son tashin-tashi. na ke dai ki
rinka kiyayewa da abinda su kace kin ji."
Wanshekare Malan Kado ya lallaba bisa kekensa zuwa
gidan 'yar uwarsa Tambaya, bayan la'asar sakaliya kenan.
Sun jima suna hiran zumunci sannan Malan Kado ya kawo
zancen da ke tafe da shi. Tambaya ta yi shiru har sai da Malan
yace, "Ya na ji kin yi shiru, ko hadin nawa bai yi ba ne?" Ta yi
sauri ta lunfasa sannan ta gyara daurin kallabinta, ta ce, "Ва
haka ba ne Malan abin ne na yau wuya ne da shi, ka san ita ma
uwar yaron nan ba komi ne da ita ba, haka nan mahaifinsa
mutumin arziki ya rasu sai wannan fitinannen kanin uban na su
wanda bai tsinana masu kome illa fitina ko ka san ya sayar
masu da gonan su Yusufa shi da kannansa? Haliman da zata kai
shi kara amma shi Yusufan ya hana ya ce wai a bar shi da Allah
ai gidan biyu ne. To kaji irin matsalolin da su ke fuskanta don
haka na ke ganin anya Yusufa zai amince da yin aure yanzu
domin ya sha fadan cewa ba zai yi aure ba sai ya mallaki abinda zai rike iyalin".
Malan Kado yace "Ku san duk ina sane da abinda ki ka Ilissafà mani, sai dai abinda na ke son ki fahinta har ki fahintar
da mahaifiyar Yusufa wato Halima shi ne ba komi zai kashe ba
akan auren Dije haka nan wannan gida da suka ci godo inda ita
Halima da kannansa ke zaune anan zai aje Dije in ya so ya tafi Zariya yaita neman iliminsa mu kuma muna nan muna bin su da
addu'a, ko me ki ka ga ni?" Tambaya ta gyara zama tace, "Zancen
ka a bisa hanya ya ke, hakan yayi daidai. Allah kuma ya hada
mana hankullansu, amin."
Malam Kado ya sadda kai yace, "Ni wallahi duk fadin
5
garin nan ban ga yaron da ya kwanta min a rai ba irin Yusufa,
son yaron na ke da zuciya daya, kin ga idan Ubangiji ya hada
hankalinsu da Dije shikenan na huta kunne na shiru da rigingimun
su Ankudi da ita Dijen". Tambaya tace, "To halin su Ankudi da
Sabura ai sai dua'e amma idan. Dije ba wani gari ta yi aure ba
suna ko shafa mata lafiya? Ko ka san don a zauna lafiya na ki
sanar da kai cewa su ne su kai sukar wancan auren na Malam
Dahiru da Dije?" Malam Kado ya bude baki hangangan yana
mai kakahi Tambaya taci gaba da cewa "Ni ma ina kyakwawan
zamana Ladi mai aiki gidan hakimi ta kawo min labarin, amma
don Allah wannan kada ta dame ka, ka ji an ce wani hanin ga
Allah baiwa ne, idan Allah ya bata Yusufa dan makaranta ai ya
fi Malam Dahiru mai neman na tuwo, ni dai fata na da kai idan
har wannan maganan ta kullu kada a bari su ji sai dai su ji
daurin aure".
Malan Kado yasa habar rigarsa ya goge goshinsa yayi
ajiyan zuciya yace, "Duk abinda mutun ya yi shi da Allah, ba su
yi min ba, kan su su kai ma wa. Ina ganin ma idan Allah yasa
Yusufa ya yi na'am da maganar sai su rinka haduwa nan gidan
ki".
"Inna Tambai ce yau a gidan?" in ji basiru kenan daya
daga cikin`ya`yan Halima, ta amsa "Ni ce, Basiru ina gwogwon
ta ku in ce ko tana gida?" Basiru ya aje bokitin da ke hannunsa
wanda ya ke wanke rigunansa da kayan gwoggo Halima ya ce,
"Inna Tambai, gwoggo ta shiga nan makwafta yin barka yanzu
za ki ganta ko kuma na tura Hassi ta kira ta?" Inna Tambaya
tace, "kyale ta Basiru, ina Hassi din ta ba ni ruva a Duta zan yi
alwala domin na ji ana kiran azuhur ko?"
Basiru ya rafkawa Hassi kira ta fito tana tsifar gashi ta
tsugunna ta gayas da Tambaya ita kuma ta umurce ta ta kawo
mata ruwa a buta. Tambaya na tsakiyar sallah Gwoggo Halima
ta dawo bayan ta yi sallama ta aje gyalenta bisa gado ta yi
murmushi tace, "Yau kuma kawalliyata larabar duk ta wace?
Lalle na taki sa'a, dama `yan iya magana kan ce tabawa ranar
samu ko samu da ke ya kara, kamar kin san ina nemanki akwai
wani albishir da zan ma ki". Halima ta fice ta nufi kicin ta dauko
6
masu abincin da ta bar wa`ya yanta su dafa, taliya murjin
hannu, ta zo ta dire gaban Tambaya, sannan ta fice don ta yo ta
ta alwalar sai da ta kammala, ta kwallawa Sarai kira tace, "Maza
kawo mana ruwan sanyi". Ta dubi Tambai tace "Ranki shi dade
Gimbiyata kamar kin san ko da ba ki zo gidan nan yau ba gobe
ni dole in neme ki?" Tambaya cikin murmushi tace, "Me kuma
ya faru aminiyar tawa?" Halima ta ce, "Babu komi sai alhairi.
Wallahi Tambaya wata magana ce na ke ta kunbiya-kunbiya da
ita yau kusan shekara biyu kenan na rasa wanda zan fasa ma ita
wata kin tsane da Malan Tukur mai almajirai na bisa kan kwanar
gidan nan?" "Ke ina yawan ganin shi wajen mai gidanki -
Sarai ta yi sallama ta shiga tace, "Af gwoggo ga wannan gujiya
ce da kindirmon nono da danyen manshanu Malam Tukur ya
aiko Inusa yaronsa har ma na bashi naira goma". Halima ta juya
ta dubi Tambaya su kai murmushi sannan Tambaya ta sadda kai
kasa ya yin da Halima ta dubi Sarai ta ce, "Ina man shanun?"
Sarai tace "Yana kicin, zan soya, ai gujuyar ma danya ce, ni ce
na dafa ta". Tambaya ta ce, 'Sannu Saratu samo kwano ki
zubo mana gujiyar".
Halima ta yi tagumi ta ce "To abinda duk na ke kokarin
bayyana ma ki ya bayyanar da kan shi, ina fatan kin fahinta?"
Tambaya cikin siririyar murya ta ce, "Na fahinci kina son shaida
min Malam Tukur na neman aure, amna kuma na wa?" Halima
ta harzuka tace, "Ban gane ba, kina nufin tsofai-tsofai da shi zai
zo neman auren su Sarai ne ko Hassi?" Tambaya ta ce "ba nufi
na kenan ba ina nufin ko cikin zuri'arsa ya ke son a hada jini?”
Halima tace "Ni da haka ya ke nufi da ban ji sanyi a rai na ba
Tambai? Amma shi Malan wai ni ya ke so da aure, na yi korar
amma ya manne yau shekara biyu kenan yana irin wa'annan
wahalhalun". Tambaya ta sha mur tace, "To ke ko Halima ki
rufawa kan ki asiri mana, aurenki da Malan Tukur ai ba karamin
gatanci ba ne gare ki dà 'ya'yanki saboda mutun ne kamulalle
kuma duk wani hakkinku da akan danne maku da gangan Malan
Tukur zai taimaka ta wani fannin da zai iya a matsayin mijinki."
Halima ta yi jagale Tambaya ta kara tsumata, zuciyarta ta kara
kwadaita da son Malan Tukur nan da nan idanunta suka dan
kada, ta dan girgiza kai tace, "Yadda duk ki ke nufi ba haka nan
ba ne Tambaya". Tambaya tace "To menene, ke dai ba yarinya
bace, haka nan ke ba wani abun duniya ki ka tara ba balle ace
kwadayin dukiya ya kawo Malan, sai dai in ba kya son shi."
"Ko kusa babu zancen kiyayya tsakani na da Malam ina
son Malan Tukıur fiye da zaton dan adam matsala ta daya wannan
yaran Maitama ya tsani maganar aure na da Malan Tukur, na yi
iyakar kokari na don na fahintar da shi amma ya nuna min a
gaskiya mutunci na zai zube idan aka ce na sake aure bayan
rasuwar mahaifinsu wai idan ba kwadayi ba me zan ci da Malan
Tukur?"
Tambaya tace, "Ke ni rigima ta kenan da 'ya'ya maza
muddin aka ce mahaifinsu ya rasu sun fi kowa kishi idan ance
ana sonka"; Halima ta ce, “Ni dai Maitama ne kawai ya kawo
mana tsama armma su Basiru sun runguimi Malan Tukur da hannu
bibbiyu, abin haushin ma shi ne, ya kafa dokar cewa idan na
auri Malan kada ya shigo masu gida, mun ce mun amince domin
Malan yana da wani gida ya ce sai na koma can tare da yara na
domin ba zai hada ni da matansa ba, anan ma Maitama yace
wai bai amince kannensa su je agolanci ba sai dai na tafi ni
kadai. Ke akwai ranar da na yi ciwo Malan ya zo gaishe ni,
wallahi, a rannan Maitama yasa na ji kunya, kiri-kiri ya ki gayas
da Malan sai shi Malan din ya gayas da shi, amma yaron nan ya
amsa a dakale". Tambaya ta yi dariya tace, “Ka ji aikin manya
kenan sai a bisu a sannu."
"To ni abinda yasa ki ka ga ina kyale Maitama yana yi min
gadaza akan zancan aurena da Malan abu daya ne, wato duk
hanyar da zai shiga don ya kare mana mutuncinmu ni da kannan
sa yana yi. Misali wannan shagon na jikin gidanmu shi ne ya yi
iyakar kokarinsa ya ciri ya kullu a irin kudaden da gwamnati kan
biya masu don sayen litattafai ya cira ya zuba mana abin
masarufi, kanin Basiru ke tsarewa anan mu ke fid da na sabulun
wankanmu da man shafawa zuwa ornon wanke wanke hatta
ashana da za mu kunna cikin ribar shag o mu ke ansowa, wannan
kenan haka nan duk inda ya ji wani dlan aiki yana nan manne
idan ya sami alhairi bai tunanin kan shi daga ni sai kannensa,
8
yanzu kwanan baya wani Alhaji mai kudi a Katsına zai yı aike
Kwatano sayen motoci abokinsa ya neme shi da ya bi ayari shi
ma ya tuko mota daya, ya ko je wallahi abinda aka biya shi dubu
biyar. Tun a Kwatanan ya sawo mana shirgegen firij yanzu haka
a rana daya sai mu daura ruwan sanyi zuwa kankara da kunun
zaki kimanin na dari uku, to saboda Allah ko ke ce Tambaya
yaro na nuna maki irin wannan gatancin ai kya danne
kwadayinki?"
Suka kyalkyale da dariya suka tafa hannuwa "To ni kam
kin ji abinda ke damu na Tambai kullun sai kara shishige min
Malan ke yi yayin da na ke kara kaunarsa ina kuma tsoron batawa
Maitama rai don haka na ke son dama na same ki kiyi ma
maigidanki magana ya baiwa Malan hakuri ya nemi wata matar
ni kam ba zan aure shi ba". Tambaya tace "Kina so amma yaro
bai yadda ba?" Suka bushe da dariya ta ce "ke ko da raha ki
ke!"
“To na ji na ki bangaran abinda mu ka yi da maigidan
game da batunku ke da Malan zan sanar da ke sai ni kuma
abinda ke tafe da ni game da yaron ne Maitama Yusufa, yayana
ya aiko ni. Malan Kado yace, shi dai ya hanga ya duba duk
girman garin nan bai ga wanda ya ke so ba irin Yusufa don haka
idan har ba zai takura ma rayuwarsa ba ya je su daidaita da Dije
ya ba shi ita".
Gaba daya dakin su ka yi tsit sai zuwa can Halima tace,
"Ni wannan kauna ta Malan Kado da Maitama har ban san irin
ta ba? Har da karin marigayi Tasi'u fa!" Tambaya tace, "Ai Yusufa
abun so ne, yanzu 'ya'ya nawa ne sao'en marigayi Tasi'u a
garin nan? Amma babu mai kula Malan Kado kamar Yusufa".
Halima tace, "Wannan fa tabbas, idan dai ya sauka a garin kafin
ya anbaci kanin babansu ya ce zai je ya gaida Baba Kado wannan
aure na shi da Dije fa ya yi daidai kadaran kadahan irin wa'anda
suka san usulinmu suka san matsayinmu kin ga har abada raini
ba zai shiga ba, zai juya matarsa yadda ya ke so. Da man tsoro
na Allah tsoro na ya nemo min wa'anda suka fi karfinmu don na
ga bokon na shi ya yi yawa, Allah ya kawo shi wannan satin zan
turo maki shi.
9
Da wannan suka rufe zancen, ta ce a dibar mata nono
da manshanun zawarcin itama ta je gida ta lasa, anan kuma aka
dawo da shegantaka baya kamar wasu 'yan mata.
Yusufa Kanti dan makaranta ya je gida kamar yadda Halima
tace, ta kuma yi masa zancen Dije ya fashe da dariya yace,
"Aure gwoggo, da irin halin matsalar ciyar da kan da mu ke
ciki? Da dai sai