Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 5
kai mata wasikar Yusuf. Dije sai da ta gama wanke-wanke sannan ta nufi falo da Sarai in da `yar shinfidar katifar ta ta ke amma wannan bai sa an baiwa Dije`yancinta ba, domin sai ga yaran gidan sun zo sun yi mata cincirindo ana tambayarta cewa, "Dije menene cikin ambulan din? Ko kudi ne aka aiko 20 ma ki ba kya son su Gwoggo su sani?" Haba sai ga su Ankudi tsigil cikin falon ana antayawa Dije zagi, Ankudi na fadin "Ke ja can shashashar banza ina tsiya ina dan gidan mariga Kanti. Me tsiya ta ci ta rage balle har ya tsinana ma ki wata tsiya? Idan ba irin dan gidan Kanti ba, wa zai kwashe ki, shi ne har za ki ma mutane yanga da shegiyar ambulan? Me ya taba baki a garin nan, in ban da alewa da cingam kullun?" Sabura ta ja tsaki ta ce, "Yusufan banza za`a yi mana yanga da aikensa?” Nan da nan Dije ta daga idanu taf da kwalla ta dubi Sarai. Ita ma Sarai ta dubi Dije kowacce ta share kwallan da ke zuba mata. Bayan sun fita ne ta yage wasikar Yusuf sai kawai ta kara tsananta hawayenta, ta dubi Sarai ta ce, "Saratu tun yaushe ne yayan bai lafiya?" Saratu ta ce, "Jiya ne ya dawo daga Zariya yanzu haka ko masallaci bai iya zuwa”. Har ta fara rubuta masa amsa, sai ta ji matsin shigowar Babanta dakinsa, ta yi sauri ta goge fuskarta ta nufi dakin Babanta. Ta durkusa ta ce, "Baba yanzu Yusufa ya aiko Saratu da wannan wasikar, ashe bai lafiya kwarai yana nan gida kwance" Ya ce, “Assha, assha, ciwo tun daga Zariya lalle jiki ya yi zafi, sai ki shirya maza ki je duba shi, kya ce muna gaida shi sai na zo". Nan da nan ta shirya ta fito ita da Sarai suka rankaya a bisa hanya ne ta ce, “Saratu na roke ki don Allah mana”. Ta ce, "Menene?" Dije ta ce, “Don Allah kada ki gaya ma Gwoggo zagin da su Gwoggo Ankudi su kai mana" Sarai ta dan tsuke fuska ta се, “To kо ma an fada mata me za ta yi? Komi mutun ya yi ai kan shi”. Dije ta ce, "A to kin ga ni fa, don haka na ce kada ki gaya mata ran ta ya baci a banza". Suna isa ta dan yi sallama ta daga labulen kofar dakin Yusuf ta ga Garba na yi masa allura. Ta saki labulen da sauri ta ce, "Sannu, ku bari na gayas da Gwoggo. Ta shige cikin gida ta tsugunna har kasą ta gaida Gwoggo ta ce, "Ashe kuma yaya bai ji dadi ba?" Gwoggo ta ce, "E, ai yau ma babu laifi, amma jiya, abun ba a cewa komi". Dije ta ce, "Allah ya ba shi lafiya". Gwoggo ta ce, “Amin". Salmanu ya leko ya ce, "Dije ki je yaya na kira". Ta mike ta nufi zaure inda dakin Yusuf ya ke, ya na kwance duk ya rame 21 ta nemi kujera wadda ta ke ita kenan guda daya dakin ta zauna ta ce, "Sannu Yusut, ya jikin?" Ya ce, "To Alhamdulillahi Dije, yaya su Baba Kado?" Ta yi tagumi nan da nan idanunta sun cika ta ce, "Lafiyarsa lau" Ya ce, "Na gaisheka sai ya zo an jima". Yusuf ya ce, "Wash!" Dije ta kasa cewa uffan domin sai ta ji Wash! din har cikin kwanyarta, a lokacin ba ta ki ba a се ciwon da ke jikin Yusuf ya dawo kan ta. Ta sa bayan hannu ta goge idanunta da karan hancinta. Basiru ya shigo da maheci a hannunsa ya zauna bakin gadon Yusuf yana yi mata hita, nan da nan tunani ya shigi Dije zai fi kyau ta je ta yi masa domin ta san halin Yusuf yanzu yana warkewa zai fara yi mata tsiya cewa ita`yar kauye ce, bata kula da shi lokacin ciwonsa illa sokancin kuka, da dai sauran irin wa`annan maganganun, saboda`yar shakuwar da su ka yi na wata uku ta fahinci halin Yusuf kamar bayan hannunta. Mutun ne mai son komi mace ta yi masa. Don haka ta matsa ta amshi maheci daga hannun Basiru ta zauna bakin gado tana yi masa hita, har bacci ya dauke shi bata daina ba, lokaci lokaci ta rinka sa tafin hannunta bisa gashinsa tana jin yadda zazzabin ke sauka. Bayan awa biyu ya fara zufa kasharban ya aike ta wajen Gwoggo ta amso ruwan kan shi da tawul. sanyi ta zo ta rinka goge masa zuwa wuya Ya fara amai Dije ta tsugunna gindin robar da ya ke aman tana fadin "Yau ni na shiga uku ni Dije kada ka hazas da`yan hanjinka." Nan da nan sai kuka rau rau, tana goge masa jiki tana kwalla. Ta shiga cikin gida ta zud da aman. Ta na wanke robar Gwoggo ta leko ta ce, "To ke Dije haka za`ai jinyar, wannan aikin ma ai na su Basiru ne. Sannan kuma duk kin gwalje idanunki wajen kuka, wa ya ce maki ana yi ma ciwo kuka? Ai sai addu`a, kin ji?" Bayan sallar la` asar Dije na can dakin su Sarai, mahaifinta Malan Kado da Malan lliya da Malan Tukur na zaune dakin Yusufa su na tausaya masa zafin da jikinsa ya yi, a lokacin da Malan Kado ya tashi tafiya ne yà ce ma Dije sai ta rinka kwana nan wajen su Sarai tana duba jikin Yusufa domin dai ko taje gida 22 hankalinta ba zai kwanta ba. Bayan tafiyarsu ne, ta koma dakin Yusuf ta zauna ta zuba mai ido yayin da shi ya sami bacci, tunani barkatai ya rinka zuwa ma Dije, 'to yanzu idan Yaya ya mutu fa? Ga shi ana gaf da aurensu? Auren da ta ke ganin zai kawo karshen duk wani magudin wahalhalun da take fuskanta wajen matan ubanta? Rayuwar da take mafarkin shinfidawa a gidan nan, ita da su Gwoggo Halima da kannan mijinta, tamkar wata rayuwace wadda ta ke jin babu wata diya macen da ta taba dandanar zumar zakinta domin ita a ganinta ko a matsayin ` yar aiki za su dauko ta lalle za ta mori gardin rayuwa fiye da ta gidan mahaifinta Baba Kado. To balle kuma a matsayin matar Yayan gidan? Yayan da babu kamarsa wajen kowa da kowa a gidan, shin wai wacce irin sa`a ce da ita? Haka nan kuma ta zamo daya da daya abar son Yaya Yusuf, yayin da ita ma bata da na biyunsa wajen so da kauna, ta amince ta rasa komi ta mallaki Yaya Yusuf hatta tsananin son karatunta na boko a darajar Yaya za ta iya jingine ilmin waje daya, haka nan a zuciyarta ta na jin za ta iya bautawa Yusuf tamkar yadda take bautawa ubanta, sai dai kash!' ta kawo gwauron lunfashi tare da wasu sabbin kwallan 'yanzu idan na rasa Yaya fa a dalilin wannan shegiyar: maleriyar da ta addabi jama` a? Amma dai na, cika mara sa`a a duniya, saboda a ina zan kuma samo wanda na ke so tamkar Yaya? Na san zan iya samun mai so na kamar yadda Yaya Yusuf ke so na, to amma ni fa?' Ta fashe da kuka a fili wanda har shi Yusuf na jin ta illa dai kawai bai iya ce mata komi domin jikinsa ya yi zafi. Ta yi kuka ta yi kuka na tunanin rashin Yusuf a karshe ta hakura ta mike ta yo alwala ta dawo bisa kafet din Yusuf ta shiga sallar nafila rokon Allah ne dai ya raya mata Yaya Yusuf. Sai misalin karfe goma sha daya na dare, tana makure bisa tabarma a dakin Yusuf, ta yi tagumi tana gyangyadi shi ma Basiru na zaune bisa kujera yana gyangyadin, sai Malan Tukur, ya yi sallama ya shiga, ya ce, "To Dije koma cikin gida mana ki kwanta ai kin ga shi ma ya sami bacci ko?" Ta mike tana mai cewa 'To', ta yi ma Basiru sai da safe. A dakin su Sarai da Hassi ta kwana illa dai ba wani baccin 23 kirki ta yi ba, ta rinka saurare ko Basiru zai ta da Gwaggo ya ce, "Yaya ya rasu." A kalla sai da suka sami kwana biyar ana jinyar Yusufa robar ruwa kuwa an yi mai kari har babu adadi. Dije na zaune bisa tabarma ta ce "Yaya na gama alalen, а zubo maka ko?" Ya dan kanne ido yace, "Kada ki sake ce min yaya din nan, na gaya ma ki bana so". Ta dan harare shi ta се, "Haba don Allah dubi fa girman ka, amma sai na rinka ce ma Yusuf bayan su Sarai na kiranka Yaya? Gaskiya ni ba zan iya ba" Ya ce "Amma ai ni mijinki ne don haka sai ki min lakabin da akan kira miji a madadin Yaya", ta ce, "To rnaigida ga alalan na kammala", ya ce, 'A haf har kin sa kai na ya sara! wannan ai kalmar mutanan da ce, wai maigida kamar wani tsoho, ba na son kauyanci ki rada min sunan zamani dan Allah', ta ce, 'ka yi hakuri ka ci alalen suna kan idan Allah ya yarda ai zan rada ma ne, abinda ma idan na fara lissafo maka sai ka zaba', ya dube ta ya yi murmushi ya ce, " Hadizan Yusuf ko? Ni kin san abinda ya fi ba ni dariya da bahaushe, ko kuma na ce ya fi bani haushi wallahi yadda su ke cima sunayanmu zarafi wai wani abu a rinka kiran mai suna Yusuf dan Yusufulle ko Yusufa don Allah dubi sunan Baba Kado mai dadi amma bahaushe ya watsa shi maimakon Abdulkadir wai kado', Dije ta yi dariya ta ce, 'Au ai gara na ka sunan da nawa suna Khadijah amma an mayas min Dije ko Dijengala haır Ingali ce mani a ke dubi Saratu shi ne Sarai Hafsat am mayas Hassi, malan bahaushe da iya fasali ya ke'. Salmanu ya yi sallama ya leko ya ce, "Gaskiya yau Dije alalenki ta yi mugun dadi", nan da nan Yusuf ya sha mur ya ce, "Kai Salmanu daga yau kada na ji ka kara kiran ta Dije, Khadijah fatan za ka sanarwa da su Hassi." za ku rinka cewa ina ta Bayan Salmanu ya tafi Dije ta dubi Yusuf ta yi dariya ce, 'To anan ai ba ka yi adalci ba, don me za ka ce Hassi itama sai ka ce a gyara mata na ta', Yusuf ya ce, 'wannan bai shafe ni ba, na matata na sani itama mijinta ya mai da mata Hafsat idan ya na da sha'awa', Yusuf ya kara kashe ido ya nutsar da kwayar idon sosai ya lumlumshe fuska ya ce, 'Kin ma san wani abu Hadiza?" Ta dan grigiza a hankali domin irin kallon da ya ke 24 mata ya kashe mata jiki, illa tsigar jinkinta ta rinka yarari ya ci gaba da magana a hankali cikin natsuwa da rudar da mace, ya ce, "ran da duk ki ka kammalu a dakina a daren da zan fara shiga daki, kin san irin kazar nan da ango ke kawe ma amarya? To ni zabuwa zan sawo ma ki amma ta radin suna ce" Dije cikin siririyar murya ta ce "wane irin suna kuma haihuwa na yi?" Ya yi murmushi ya ce, "A'a sunan ki dai zan rada ma ki sunan da ya dace da ke, sunan da aka yi dace na fi so a rayiwa ta", ta dan lumshe ido ta ce, "yaya sunan ya ke?" Ya ce, "KUBRA kuma ba zan yadda kowa ya rinka kiran ki da sunan ba illa ni kadai Yusuf". Ya bude kwanan alale sai ya yi murmushi ya dubi Dije ya ce, "Ya ya a kai ki ka san alalen gwangwani na ke so? Wallahi na tsani alalen ledan nan", Dije ta yi dariya ta ce, "Gwoggo ta sanar da ni har yadda zan hada yajin alalen ita ta koya min". A haka dai Dije ta sami kwana bakwai cif gidansu Yusuf soyayya cikin ruwan sanyi ya ke koyar da ita irin ta samarin ilmi wadda tafi zuma zaki sannan tafi kudi gardi da dadin gani a ido. Yusuf da kan shi ya raka Hadizarsa gida ya iske Baba Kado suka gaisa ya sanar da shi kwanan baya ya je Malunfashi inda mahaifiyar Dije ke aure ya gaishe ta har sun ce a gaishe su. Malan Kado ya yi murna da jin haka. Sai su kai sallama a kan gobe zai koma Zariya. Wanshekare Malan Kado ya je wajen 'yar uwansa Tambaya bayan sun gama gaishe-gaishe da juyayin awon Yuşuf wanda ya gigita su, sai ya zarce da zancen da ya kawo shi, ya ce, "Tambaya na ga ya kamata ki shirya gobe ki je Malunfashi wajen Amina mahaifiyar Dije ki kai mata na ta kason na sa ranar bikin Dije da Yusuř ki shaida mata Dijen ma na nan zuwa ta yi mata kwana biyu kafin bikin, sai kuma shawara ta biyu ga dubu goma sha biyu na kulle ina son ki yi hikimar da za ki yi, ki ga kin sai ma Dije gado mai fameka da kabet din sa da madubinsa sannan da 'yan kujeru guda biyu, da ledar tsakar daki, sauran 'yan kwanoni abinda Allah ya sake ba ni daga baya na kawo ma ki". Tambaya ta ce, "Tirkashi! Na yi zaton Malan za kai kokarin ko da dubu ashirin da biyar a samu a sai mata masu kwari? Don samu za'a samu na hakan to amma kwana biyu sun karye balle 25 dakin yaro", ya ce, "wallahi Tambaya Idan da hali abinda ya fi haka sai na yi ma Dije, babu ce ta sa hakan, ko kin san dubu hudun ma Malan lliyasu ya ba ni su da ya lura abubuwan sun cude min?" Ta ce, "Insha Allah, Allah zai rufa mana asiri baza mu ji kunya ba". Wanshekare karfe goma sha daya na safe Tambaya na dakin Amina mahaifiyar Dije. Tambaya ta dubi Amina ta ce 'Wai ke don Allah ba kya tsufa ne dube ki shar da ke sai ka ce yau aka kwareki a leda', Amina ta yi ma Tambaya gatsine ta се, 'Eye! Sannunku ai-so ku ke ku rinka gani na a matse kuna min jaje? To ina nan shar kuma kwalelenku nan ga ni nan bari kun ji!' Tambaya ta ce, 'Allah ba da hakuri, ga haihuwa Amina! To na ce yanzu dai kin hakuri ki bar wa diya ta fagen haihuwar ko?" Amina ta yi tsaki ta ce, "ina kuma ruwa na da haihuwar diyarki ni zan goya mata? To bude kunne ki sha labari haihuwa yanzu na fara", Tambaya ta ce, "ke dai ki ka sani, ni ga goronki na sa rana aka ce na kawo ma ki, amma banda na wajen iyayenki su an kai masu na su, wannan na ki ne da dangin mijinki na nan." To yanzu Amina ta saki layin wasan kanin miji da su ke yi da Inna Tambai albarkacin aurenta da Malan Kado, ta zauna ta takure kafafu ta bata fuska da gani ka san maganan auren nan ba ta gamshe ta ba. Ta waiwayo ta dubi Tambaya ta ce, 'Wai ke yanzu saboda Allah Tambai ba kya iya baiwa Malan shawara yaya za ai a yi ma wannan 'yar mitsitsiyar yarinya aure? Bayan ko wani kugun kirki bata da shi haka nan ga shi muna zamani na ci gaba wajen ilimin 'ya'ya mata, wallahi diyarsa ya kashe, domin in dai mazan nan na yanzu kiri-kiri nan gaba zai watsar da ita ya debo ma`aikaciya`yaruwarsa, ta zaune su mayas da ita yar bora'. Tambai ta tarbi lumfashinta ta ce, 'Haba Amina ba kya tausaya ma Dije irin zaman da su ke yi da su Ankudi?" Amina ta ce, "shi ne me, in ce wuya ba ta kisa, kuma ai gara wuyar gidan uba da ta gidan miji, in dai ya yi hakuri ai wucewa komi zai yi", Tambai ta ce, "Ke ma fa kin yi magana anan Amina, illa dai kawai hankalinki ba zai tashi ba sai kin shiga gidan Malan Kado kin ga yadda rayiwar Dije ta ke, to ni kuma da ya dace ace ta zauna a hannuna kin ga lalurar irin auren da na ke yi, wato Malan dan ci rani ne, yвu muna Kano gobe muna maiduguri, kai wannan shokarar dai na ce masa mu hakura haka nan, in ko ya ce sai ya je, to ya yi amarya', Suka bushe da dariya Amina ta ce, 'Tambaya da Malan Iro masu auren zobe ba saki ba yaji kishiya har abada'. Ta ci - gaba da cewa "To ni dai farin ciki na ma daya ne anan da wannan auran dan gidan marigayi Kanti, yaro ne da ya yi tasiri da halin manya kuma sanin halin Halima tun muna `yanmata da tsegumi ko ganin kyashi to kin ga anan za ai zaman ganin girman juna da mutunta juna kuma Yusufa ma fa yaro ne karami har da girman jiki ko kin san sai watan gobe ya ke cika shekara ashirin da uku?" Tambaya ta rike baki tace, "A gaisheki raskwana uwar lissafi, amma fa Amina ba kya da mantuwa, irin wannan tantancewa?" Amina tace, 'Ba haka ba ne Tambai, kin san kwana uku ne tsakanin wannan yaron mai rasuwa da Maitama domin bana mantuwa ina kwance a ranar da Halima ta aiko min da kunun jego da kauri na kwana uku nace ma` yan aiken suce ma Halima iina nan zuwa da yamma na ga jariri, amma ina! kafin la`asar ni ma na haihu, to kin ji abin da yasa lissafin su Maitama bai shige min'. Tambaya ta ce, "haka ne, kin ga ashe ba mu fi shekara talatin da takwas kenan a' duniya ba amma shine ne wannan takadarin yaron Maitama ya so ya hana Halima aure ba don Malam na waje ną ya bude mai nasiha ba'. Amina ta yi murmushi tace, "E haka na sami labari Halima ta auri Malam Tukur nace, ta dai kyauta ma kanta aure ai yafi zama haka nan, ka zubawa iyaye da `ya` ya ido'. Tambaya ta warware ma Amina yadda su kai da Malan Kado game da batun sayen gadon Dije, Amina ta yi iyakar tunaninta sannan tace ma Tambaya "babu komi, a yi na dubu ashirin din, akwai wani dan marakin ta zata aika a sai da mata shi don haka za ta aiko ma Tambaya da kudin. Batun tarkacen daki kuma duk sun hada ita da 'yan uwanta sai lokacin biki za 27 su kawo, suka fara batun towe-towe kaman su alkakı da cin cin da nakiya zuwa su manja da man gyada, Tambaya ta ce ta dauke wannan nauyin. KASHI NA BIYU Usilin Malan Kado wato uban Dije mutanen Bakori ne iyaye da kakanni, garin Bakori gari ne mai albarkar jama'a haka gari ne mai anfanin gona. Darajarsa da kimarsa ta kara fitowa a dalilin fuskar garin da shi ainihin garin ya fito a fili ne bakin hanya ba sai an yi kurda-kurdar shigansa ba duk da bai faye girma ba Ubangiji ya albarkatai da jama'a masu dinbin ilmi da fasaha zuwa hazikanci, haka nan matasa sun rinjayi ainihin garin Bakori. Abdulkadir wato Mallam Kado ya taso matashi abin alfahari ga karaman hukuman Bakori domin a kalla yana daya daga cikin manoman garin wanda karaman hukuman ke amfana da albarkacin nomansu. Yana gaban kuruciyarsa ya kallafa ransa akan Amina bata ko isa auren ba iyayenta suka wanke ta suka ba shi, kwanci tashi ta haifa masa Tasí`u; bayan Tasi` u ya sami shekara uku ta haifi wani dan amma bai zo da rai ba saboda bakwaini ne. Tasi`u na da shekara takwas cif aka haifi Dije. Tasi`u ya zama abin son Mallan Kado ko ina yana nan tare da shi, don haka ne ma abokan Tasi'u kamar su Yusufa suka saba da Mallan Kado a wannan lokacin kwatsan Tasi'u ya sami shekara goma a duniya Dije na da shekara biyu kenan me zai faru? Wata alhamis su Tasi'u da su Yusufa sun je kogin da ke can hanyan Kabomo yin kurme irin na yara, sai gawan Tasi'u aka kawo ma Mallan Kado anan ne fa Yusufa ya rinka kuka yana kumaji shi a doje sai a rufe su tare da Tasi'u. Haka Allah ya nufa, to abin karewar zama a daidai wannan lokaci rudani da rikiwar mutuwar Tasi'u sai ta sa Mallan Kado ya tsani komi hatta Amina sai ya dora mata karan tsana, da abinda ya isa fada ba sai ya fada mata da fada wata ran ta nuna masa damuwanta game da abinda ya ke mata, sai ya bude baki yace, "zama da ke bai zame min tilas ba, na rasa Tasi'u ma balle ke?" Sai ta ce, "au haka ne, 28 to iná shaida" Nan da nan ya ce ya sake ta saki daya. Wannan shi ne mafarin rabuwan Kado da Amina, bai shiga nadama ba sai da aka ce yau Amina ta cika idda har Mallan Isa mai aiki a ma'aikatar gona a Malumfashi ya fito neman aurenta, nan da nan da Amina ta lura Mallan Kado zai matsa mata aka daura mata aurenta da Mallan Isa wanda ya ke da mata daya sai dai babu haihuwa. Mallan Kado ya hura wuta akan son Amina amma ina! Isa ya kwace, don wauta ya ce, a ba shi diyansa Dije, su kuma suka ba shi. Bakin ciki goma da ashirin suka tararwa Malam Kado, a dole yayi hakuri ya auro Ankudi, aiko ko wata uku ba a yi ba Ankudi ta soma ganawa Dije azaba, da shi kan shi Mallan Kado. A haka nan Dije ta sami shekara tara cikin azaba, shi kuma Mallam yayi alkawari bai sake sakin aure domin sakin Amina ya zame mashi darasi, don haka sai ya nemo auren Sabura, wai don dai Dije ta ji sanyi. Da-farkon auren Sabura bata fara fid da maitata a fili bа, domin Malan Kado tun farko ya ce zai aure ta ne don ta rungumi Dije saboda haka ta fara nunawa Dije gatanci domin har gyara ta ake yi, haka nan idan ta ga Ankudi ta bata aikin da ya fi karfinta ita Saburar kan amsa ta yi. To ganin haka yasa Ankudi ta canza dabara, inda ta rinka jan ra'ayin Dije a siyasance a hankali a hankali ta rinka cusa mata mugayen akidodi, na guje ma Sabura wanda ta kai su ko dakintaa ka haramta mata shiga kai ta kai lokacin kiri-kiri aike wannan Sabura ba ta isa ta aiki Dije ba' to sha'anin yaro kenan bai san makircin wasu tsaffin ba. Ita kuma ganin haka Sabura ta tettara Dije ta watsar muguwan tsana ta shiga tsakaninsu, a karshe Ankudi ta janye ta suka game gam, suna ta zuba 'ya'yansu tare da mulki mai radadi ga su Dije. 'Ya'yan Ankudi Shehu da Kuluwa da Juma sai Sabura tana da Laraba da Munari. A ko yaushe soyayyar Amina ta juyo ma Mallan Kado ya kan shiryawa Dije ya ce ta je hutu, daga nan yana kulla wa Dije ce wa ta rinka zuga Amina ta dawo gidan su ko ta huta da azaba, to a irin wannan hirar ne Malan Isa ya ji Dijen na lallashin Amina ta koma gidansu amma sai ya ji ita Amina na cewa, 29 Cya yau kada ki kara zuwa min da maganar gidanku ance maki ni yanzu ko mutuwa mijina ya yo inma da sha'awar gidanku?" Wannan shi ne dalilin da Malan Isa ya tsani ganin Dije a gidan sa har wataran Amina ta tambaye shi wai ko Dije ta yi masa laihi ne? Ya amsa da cewa, "Munafinkin ubanta ne kawai ya hada mu, domin kwanan baya na ji zancen da kuke da ita, idan tana son ki koma gidansu saboda ita, anan 'ya'ya nawa ki ka haifa min ko su ba 'ya'ya ba ne? Kuma tun farkon aurenmu ai na yi alkawarin rike Dije amma ya nuna zuciya ya karbe ta, to shi ne yanzu don munafunci zai rinka aiko ta don ta kashe mana aure?" Amina ta ce, "To ni dai ka yi hakuri ka daina tsuke mata fuska tunda ka san yarinya ce wadda bata mallaki hankalin kan ta ba". Ya ce, "shikenan zancen ya wuce, ai tun farko na ji kin gyara maganar. Ire-iren wannan tsegumi na ciwon son Amina ke jagula gidan Malan Kado, sai su Ankudi su debi tsanar su dora kan Dije. KASHI NA UKU A jami'ar Amadu Bello ta Zariya a can sashen maza a dakin su Yusuf shi da Awalu wanda suke dakinsu daya. Yusuí na daga kwance ya yi rigingine yayin da ya dage kafafunsa ya kurawa wata kalanda da ke rataye jikin bangon ido, ya kira sunan Awalu ya ce, "ka san kuwa duk a yi a kare karshenta a kawo min Dije dakina ran laraba domin haka na ga ranan ta nuna a jikin kalandar can". Awalu da ke zaune yana `yan rubuc rubucensa ya ce, "yau sauran kwana nawa kenan?" Yusuí yа сe "Arba'in babu daya". Awalu yayi dariya ya dubi Yusuf yaca, "Yusuf angon Dije yau fa ake zuwa ziyarar yara ina faten da la'asar za ka raka ni na gano tawa amaryan". Yusuf yayi murmushi yace, "kai ni fa ban manta nan shiga makarantun yau matan nan ba, sun faye innaranci `yan sakandiren nan". Awalu yayi murmushi yace, "kai dai ka mallaki Dije kawai shi yasa yanzu ko wacce mace tsananta ka ke, ka san wani abu Yusuf 30 wallahi na raina maka yadda na ga hoton Dije, saboda sanin halayyar ka akan 'yan mata kowacce sai ka yi mata sharri, sannan ga ka da shegan farin jinin 'yan mata amma ace farin jinin ka ya kare akan wannan yarinyar mara fasali, kai Yusuf a gaskiya Dije ta kwareka!" Yusuf ya yi galala yana kallon Awalu, yace, "Amma a gaskiya Awalu ban taba ganin mutun mai cin fuska irin ka ba, w annan yarinya ba ka san yadda mu ke da ita ba da har za ka fara kushe ta, haka nan ba ka san dalilin da yasa zan aure ta ba, а gaskiya ka daina irin wannan cin fuskar bai da anfani". Awalu ya ce, "Ashe babu dadi ka ke kallon budurwa ka

Chapter 3 of 5