Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 5
yi mɛ ki ko ita Amina mahaifiyarku. Ni kuma ina nan a kodayaushe zan kasance cikin yi maki kyakkyawar addu'a." Lokaci lokaci Dije na sanya haban farin gyalenta na share kwalla tare da cewa 'To Baba'. Sun sami mota bus kimanin mutun shidda ake jira, suna ciki suna zaune, Dije kusa da taga, Malan Kado kuwa yasa gwiwar hannu ya dogare daidai tagar da Dije ta ke zaune, tare da yir tagumi, kowa ya wuce zai dube shi ya dan tausayawa yanayir fuskar Kado. Ya kira ta a hankali ya ce` Dije', ta amsa "Na'am Baba", Ya ce "idan kin ga Malan Isa na tsangwama maki ki hado kayar ki ki dawo gida kin ji ko?" Ta се, To Вaba'. Mai tallar biredi ya zo ya tsaya a gaban Malan Kado, yɛ ce, "Malan ba za a sai biredin ba?" Malan Kado ya waiwaya ya dubi Dije yace, "ya ki na son birdin a saya?" Ta girgiza kai tace "A bar shi Baba". Tambaya ta dan zakudo tace "wane irin a bai shi? A saya mana ko yara ai ma yi ma tsaraba". Malan ya saya ya mika masu ta taga sai da ya ga tashin su sannan ya tafi gida. Dije ta takure can gefe daya a dakin mahaifiyarta tanɛ sauraron Gwoggo Tambaya tana bayyana dalilin zúwan su, taj Tambaya ta ki fadin irin fallasar da Yusuf ya yi ma halittarta kc me yasa? Nan da nan idonta ya kara cika da hawaye da ta tunc muryar Yusuf na fallashe ta. Amina ta waiwaya ta dubi Dije a sanyaye ta ce, "lalle kina da aiki, don yace bai sonki shi ne abun kuka? In dai sha'anir namiji ne ba ki ga komi ba, ai ni wannan mai kyau ya yi maki, idan da sai an yi auren fa! Ya ce bai yi? Ni dai farin ciki na dayt da za'a bar ta ta yi karatu amma duka duka shekararta nawa de har da namiji zai dada ki da kasa? In don ni Allah ya raka tak 42 gona." A ranar da Dije ta sauka gidan Malan Isa bai kwana ba sai da ya je akan maganan makarantar Dije. A da can Dije na makarantar 'yan mata ta Kabomo ne, da aka yi masu jarabawar zuwa babbar sakandire ita ce ta zo ta daya don haka aka kai ta makarantar 'yan mata ta Malumfashi, saboda haka shugaban makarantar tayi ma Malan Isa alkawarin shigar da Dije aji hudu kamar yadda ta ke, illa dai idan bata yi kokari ba za'a kara barin ta aji hudu yayin da za su biyar. Da wannan bayanin Tambaya ta koma Bakori cike da murna da kyakyawar addu'ar Allah ya baiwa Dije miji wanda ya fi Yusuf. Yawan aiki a gidan mahaifiyarta bai bata isasshen lokacin tunanin da zai haddasa mata kuka ba domin Amina na da sana'a mai karfi kamar dafadukan shinkafa da kunun zaki da fanke ana kai mata karamar hukumar Malunfashi inda kanin mijinta Shittu ke Sakatare a karamar hukumar. Da yamma su zaune lissafin cinikin da aka yi. Dije ta lura da irin kudin da innarta ke samu sai ta amince lalle mai sana'a ba zai yi ciwon zuciya ba. Kwanan ta biyu aka shirya ta zuwa makaranta. A can kuma Bakori bayan tafiyar Dije da kwana daya ciwon Malan Kado ya tsananta dole Malan lliyasu ya nema mota ya kai shi babban asibitin Funtua, babu bata lokaci su ka kwantar da shi. Ya rinka rokon Malan Iliya don Allah kada ka aika ma Dije a kyale ta tunda an ce ta samu makaranta. Can Malam Kado ya dan juyo da fuskarshi daidai saitin Malan lliya ya rage kaimin harshe ya ce, "lliya wai yaya aiken da Malan Tukur ya yi wajen Yusufa, ka ji wani zance mai karfi?" Malan İliya ya dan sunkuyd da kai "Haba Malan Kado kai fa babba ne, don me ba za ka iya sawa zuciyarka dangana ba ne? Ko ka san wannan matsalar ta tayas maka da-hawan jininka, in kuma ba ka fid da damuwa ba a ranka, to likitoci sun tabbatas mana za ka sami shanyewar barin jik. Ka kwantar da hankali, insha Allah Dije zata sami miji wanda ya fi Yusufu." Malan Kado ya fid da wasu kwalla daga idanunsa ya ce, "Ni wallahi ko shugaban kasa zai ce yana son Dije bai kai 43 Yusufa ba a zuciyata, kamar Tasi'u ne fa na ke ganinsa". Aiken da Malan Tukur da Gwoggo Halima su ka yi ma Yusuf a can makarantarsu shi ne, yana cin abinci a daki, Awal ya turo kofa ya shigo yace, "Yusuf ka yi bako". Ya ce “wanene?" Kafin ya rufe baki Basiru ya shigo nan da nan ya hade fuska suka gaisa sama-sama, ya kawo wasika ya ba shi ana tabbatas ma shi aure da Dije babu fashi za'a ci gaba da biki a kawo ta dakinshi in yaso ya bi uwa duniya. Malan Tukur ya snriya wannan dabaran, amma gogan na ku ga amsar da ya rubuta a takaice: Na ji aikenku, to tunda kun zabi Dije fiye da ni, shi kenan ni na yi sallama da ku. lafiya. Ina fatan za ku yi min aikin gafara ku zauna da Dije Danku Yusuf Kanti. KASHI NA BIYAR Da aka yi hutu sai Yusuf ya yi zamansa a Zariya gidansu Awal, kullun yana gidansu Fa'iza zaune wajen masu gadi yana taya su hira domin sai da yayi zuwa hudu sannan ya sami ganin Faiza, a wannan rana sai ya ji kamar an yi masa gafara. Suna zaune a wani yammaci bisa dakalin gidansu Awal sai kawai ya kafta ido ya ga Malan Tukur da Basiru, kunya da mamaki suka dabaibaye shi ya rasa kalmar da zai yi ma Malan Tukur anfani. A karshe Malan Tukur ya ce wai sun zo biko. Sun amince ba'a auren.dole. Yusuf ya yi godiya ya tabbatas masu yana nan tafe nan da kwana biyu. Bayan sun tafi Yusuf ya dubi Awal ya ruke habar baki yace, "Wato da man barazana su kai min, da na firgita da yanzu ina can da amarya sokoko a daki?" Awal rike da casbi a hannunsa yana lazimin ya yi 44 murmushi yace,`ka dai bi a hankali'. Yusuf ya yi shiru tunanin bikin cika shekararFa`iza ya gallabe shi wai wace hobasan zai nuna mata? A ina ma zai samu kudin, duk dai karyar shi bata wuce rufin asirin dubu daya, sai ya kara tuno da wata galleliyar matar da ya ga ta zo wajen Fa'iza, ya tambaya ko shi ne Isma'il din? Ance ba shi ba ne, to har yaushe irin wa` annan na zuwa wajen Fa'iza zai dube ta da kyautar kasa da dubu daya? Ya sami dabara saboda haka dole jibi ya je Bakori. Da la'asar ya isa Bakori ya shiga cikin borin kunya ya gayas da mahaifiyarsa ya lura duk ta dan rame, ya tabbata ba komi ne ya jawo hakan ba illa kin aurensa da Dije. Ya fice zuwa dakinsa don ya yi abinda ya kawo shi, ya jawo wani fayal dinsa inda ya ke aje mahimman takardunsa, ya rinka dubawa daya bayan daya har ya kai bisa ta kan wata gonarsu ta gado, an mallaka masa takardun gonakin su ne da na gidan da suke zaune da wa su feguna guda biyu, shi da kannansa, tun lokacin da kanin babansu ya fara sayarwa yana danne kudin. To yau ma ga Yusuf Fa'iza ta rikita shi zai shiga dukiyar maraya. Bayan ya fito masallaci sallar isha'i bai zarto gida ba sai ya nufi gidan Alhaji Murtala wanda jama'a su ka yi ma lakabi da Ba ruwanka da bashi sai neman arha'. Ya kashe kimanin minti arba'in kafin ya sami ganin Alhajin domin an ce Alhajin na can cikin gida yana yin sulhu akan wani auren diyarsa da ke neman lalacewa. Yana ganin Yusuf ya ce, "A'a Yusufa yai kau ne da kan ka a gidan nawa! Yusufa dan makaranta ya mutan gidan?"; "Lafiya lau Alhaji. Sai Yusuf yasa hannu aljihu ya fiddo masa takardun gona ya mikawa Alhaji ya ce yana son sayarwa ne. Alhaji ya duba, ya duba ya ce, 'Allah ya jikan Malan Kanti', Yusuf ya cе, 'Amin'. Alhaji ya kammala nazarinsa ya ce "menene dalilin sayar da wannan gona ta ku?” Yusuf ya gyara zama ya karkace kai ya ce, "matsala ce ta can wajen fannin karatuna". Alhaji ya ce, "ya yi daidai, haka nan na dade da sanin gonan, amma duk da haka ba za mu yanke ciniki na yızu yanzu, sai gobe ka zo mu je 45 gonai na kara dubawa. Allah ba shi daga can ma ina iya yir cinikin na biya ka, ka amince?' Ya ce ya aminçe. Da ya koma gida ya yi murna da ya cimma Malan Tukur a nan gidansu ya ke, ba batun zuwa hira wajen Gwoggo kenar balle har ta sami halin nuna mai bacin ranta. Ya kulle dakinsa yana tunanin abubuwan da zai yi ma Fa'iza idan ya amshi kudinsa a gobe. Yana kammalawa da kalaci sai gidan Alhaji Murtala. Bа yi dogon jira ba Alhajin ya fito domin yana murna da irin cinikir yara kanana kamar su Yusuf. Suka shiga motar Alhaji su hudu, da Yusuf da Alhaji da yaran Alhaji. Suna isa gonar sai da aka zagaye ta tas, sannar suka ja birki a gindin wata cediya, Alhaji ya ce "Yusuf na ge gona kuma ta yi mani, ko ma bata yi min ba, ni dole ne na saya domin taimakonka tamkar na taimakawa Bakori ne gaba daya. A nawa za ka sayar mani?" Yusuf ya ji dadin kalaman Alhaj yace, "Ai ni Alhaji duk yadda ka saya babu ja a tsakaninmu." Alhaji ya yi dan nazari yace, "Tunda haka ne, zan bake dubu ashirin da biyar?" Gaban Yusuf ya fadi domin shi yasar gonarsu za ta yi dubu hamsin da wani abu. Ya ce "Alhaji ka sar tafi haka". Alnaji ya ce "kai ni fa ban iya ciniki kwan gaba kwar baya ba, to na saya ashirin da takwas". Yusuf ya yi shiru car daya daga cikin yaran Alhaji ya ce, "kai muna da abun yi, yaya za ka debo mu ka kawo mu daji kana wahalasshe mu?" Alhaj ya ce, "Tsaya, tsaya Barau. Idan ya amince dubu talatin ku be shi kudinsa idan bai amince ba ya nemi wani mai saye." Yusuf ya amshi kudi rai bace ya isa dakinsa a shirinse ya so ya sami ko dubu hamsin, ya fara kashe ma Fa'iza da sh kan shi dubu talatin, zuwa can gaba ya kara yi mata hidimai sauran dubu ashirin din. 46 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 5 of 5