Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 5
nan da shekara uku ne kila da sauki sauki amma ni yanzu ina tunanin tafiyar makarantar Salmanu wato polytechnic Katsina ina naga wani abun aure?" Halima tace, "Duk Allah zai rufa asiri domin Malan Kado ya yafe maka komi" Yusufà yace "To Gwoggo ba kya tunanin zaman ita yarinyar a gidan nan shi ma wani nauyi ne?" tace, "Kai dai ka cika kakale ba ka ji abinda aka ce ba ne? Aure fa babbar rahama ce ga baligin da ya isa". Ya yi shiru ya ce, "To Gwoggo ku ba ni lokaci idan na koma makaranta zan yi tunani komi kenan idan na dawo za su ji." Cikin sati uku cif Yusui dan makaranta ya sake dawowa garinsu. Yau Jumma`a da la` asar sakaliya Yusuf na sanye cikin T-shirt baka an yi rubutu da manyan haruffa da kuma jan launi inda aka rubuta `I'M PROUD TO BE A MOSLEM', wandon jikinsa fari ne sol yana kwance bisa irin kujerar nan wato (kwanta ka huta) gadonta ya yi wajen mahaifinsa Malam Kanti, ya yi zurfi wajen karatun wani novel na ches. Inuwar kukar kofar gidansu ta kara saukar da ni`imar sakaliyar la`asar. Can daga sama ya ji an ce, "Yusufa za ka sai goro?" Ya karkato fuskarsa zuwa inda ake magana ya aje littafin da ke hannunsa bisa kirjinsa ya dubi yarinyar sosai tana sanye cikin irin abayar nan ta `yan İslamiya a bisa kanta akwai farantin goro, da goro farare tas. Ya yi murmushi sannan ya dan yunkuro kadan ya zauna a karkace ya ce, "Wai shin ke don Allah me yasa ki ka bar makarantarki sai tallace tallacen tsiya?" Ta sauke turen ta durkusa ta yi murmushi ta ce, "To ina yini?" Ya amsa "Lafiya lau". Tа ce "Wallahi ba laifi na ba ne, ina son karatu fiye da komi a rayuwata amma Babana ya ce karatun ya isa haka to ya zan yi tunda ni abun ikonsa ce?" Ya ce, "E, haka ne kin yi gaskiya, to 10 amma yaya Baba Kado zai amince ki rinka talla?" Та се, "Кa san Allah bai sani ba, su Gwoggo Sabura ne da Gwoggo Ankudi. Ya san dai suna sayar da goro kuma ana zuwa saye, amma da zarar sun lura ya tafi cin kasuwar wani kauye dole mu je talla ni da kanne na, wato `ya`yansu". Yusuf ya girgiza kai ya ce, "Allah ya jikan Tasi` u idan da yana da rai wane su da dora maku tallah?" Suka yi shiru kanta na sunkuye tana kallon fararen goro yayin da Yusuf ya sami damar kallace sirrin fuskarta, E to, Dije na da kyau amma ba irin kyan da Yusuf ke kwadayin samu ba, illa dai kawai ya san Dije na iya shiga cikin fararen mata itama ayi da ita hakan idan fannin wankan tarwada ne, Dije na iya sajewa cikinsu. To ya amshi wannan kyautar Malam Kado ba wai don yana da kwadayi ba sai dai mu ce kila wahalar Dije ta zo karshe amma da ma maza `yan wa` anda suka cudu da rayuwar jami` a zai fi kyau a kyale su da irin ra`ayin `yanmatan da su ke da sha`awa domin mafi akasari ba su cika yin jami`a ba sannan su nemo`yanmatan jami`a suna da irin wa`anda suke da ra`ayi na kashin zuciyarsu. Ya ce, "Dije wannan goron ya yi na nawa? Ta ce, "Na naira ashirin ne amma na yi cinikin naira biyu a hanya". Ya fiddo naira ashirin ya mika mata ya ce, "Sai ki koma masu da goron su". Ta dafe kirji ta çe, "Ashe ko yau da na ba ni ace wa ya ba ni?" Ya yi dariya ya ce, "Ki ce saurayinki!" Sai ta yi wal da idanu ta dube shi duba na rikita da tsananin kauna a cikin idon Dije, nan da nan'wannan kallon ya huda so a zuciyar Yusuf. Yace, "kina nufin ki ce min duk garin nan ba ki da saurayi?" Ta kara rusunar da kanta a kasa yace, "En Dije?" ta amsa "To ka tambaya mana" yace "Ni ba zan tambayi kowa ba sai ke. Don Allah gaya min samarinki" ta yi`yar sheshekar dariya tace, "To tsokana ta kake son yi". Ya ce, "To idan kin je gida ki ce masu Gwoggo mijinki ya hana ki tallah! ta kara yi mai wal da idanu tace, "Ka san halin su Gwoggo kuwa?" Ya kyalkyale da dariya yace, "Ai miji ya fi su gwoggo idan kin je islamiyya ki tambayi malaminku, ba ni goro guda biyu sauran ki kai ma inna Tambai kice ina gaishe ta gobe mu hadu gidan inna Tambai kamar yanzu akwai abunda na ke son gaya ma ki, ta zabi goro biyu ta mika 11 masa suka hada ido aya yin da hannunta ke ba shi goron su ka yi ma juna dariya mai faranta rai, ya fada a hankali goron auren Yusuf da Hadiza, Allah shi yarda; ta sa hannu ta rufe fuska yace, Dije sarkin kunya, ke banda shirmenki wa ke jin kunyar miji? tace, wallahi miji ko shi ne abin jin kunya; yace, Dije kin iya magana ko? na ga ni da ke wa ya fi baki? tace `To ko dai jakar magori za'a kai mu sai jama'a su tantance mana? yace, "Lalle za'a yi da ke Dije!" Ta isa wajen Inna Tambai a lokacin Tambaya na gindin rijiya tana tatar koko. Dije ta dauki wata `yar karamar, kujera `yar tsugunne ta isa inda Tambaya ta ke ta zauna suka gaisa ta ce, "Gwaggo kawo na karasa maki tatar". Ta ce, "A`a rinka zubo min ruwa ai na kawo karshe." Suna cikin tatar ne Dije ke cewa, "Gwoggo ba ki san wani abu ba wannan Yusufan dan dan aminiyarki ya aiko ni na kawo maki dukkan goron da ke bisa farantin can". Tambaya ta yi dariya ta ce, "A gaida dan arziki haihuwar albarka". Dije ta kara rankwafar da kai ta ce, "Ya kuma ce wai na zo nan gidan gobe za mu hadu da shi akwai abinda zai gaya min". Gwoggo Tambaya ta ce, "Mun dai godewa wannan yaro dan albarka Allah ya ida nufinmu akan ku, Allah ya nuna min na ga ranar da zan kama hannunki zuwa gidan angonki Yusufa Maitama". A hankali Gwoggo Tambaya ta warware ma Dije yadda Malam Kado ya aike ta gidansu Yusuf akan ya ba su ita. Dije ta yi tsit tana saurare a zuciyarta duk murna da dadi sun baibayeta wai yaya a kai ra`ayinsu ya zo daya da na mahaifinta? Domin a duniya ba ta da mutumin da ke burgeta a rayuwarta irin Yusuf, don haka ne ma take murna da taliar da su Gwoggo Ankudi kan dora mata don kawai ta je layin su Yusuf ta yi masa talla, a duk lokacin da ya ke a gida. Duk wata addu arta mafi akasari akan Allah ya bata Yusufa ne ko kuma miji kamarsa, to a yau gashi Allah ya bata. Kamar yadda ya umurceta Dije ta sami mahaifinta a daki bayan sallar azuhur ta ce, "Baba Yusufa ya aiko na je gidan Gwoggo Tambai anjima da la`asar". Ya dan gyara zama.cikin 12 jin dadi ya ce, "To ai sai ki shirya ki je. Kya ce ina gaida Gwoggon ta ki". Dije ta sheka wanka ta fiddo atamfarta wakas mai tambari wadda Babanta ya yi mata da sallah ta daura, tun safe ta wanke abayarta fes ta dora a bar ta, ta ce ma su Gwoggo za ta gidan Gwoggo Tambaya, suka kalle ta shekeke, suka ce, "Wani ya се kada ki je? Kya dai karaci gulmarki". Bayan ta fita Sabura ta ce, "Ko wanne makircin ake kuilawa gidan Tamban?" Ankudi ta ce, "Bai dai wuce zancen neman miji! Kin san abunda ya damu uban kenan". Sabura ta ja tsaki ta ce, "Mahaukatan banza in dai don wannan `yar ta shi mara fasali sai dai ya gaji ya bada ita sadaka, kin gane min yarinya somaye kamar wadda ta shekara tana jinya? Duk namijin arziki ai bai auren wannan in dai da kudinsa, banki ba idan sadaka za`a ba shi". a Ankudi ta ce, "Wo ni ko sadakar ina amsarwa dan uwana wannan? Ai kowa na son ya auri iri mai kyau, can dai na su gada, sun gama kumbiya-kumbiyarsu shi da makirar kanwarsa muna nan labari zai zo mana, wai don sanabe har da daura` yar atanfar ta ganin Sarki". Dije na bullowa ta lungun hagu na gidan Gwoggo Tambaya shi ma Yusuf na bullowa ta titin da ke kallon yamma na gidan Tambaya. Yana sanye da wani yadi fari kar da ganinsa maí arha ne ya yi janfa da wando amma an zizira wani adon sirfani a wuya da hannu, kube ya saka mai dinkin zare baki da ruwan kasa takalmansa silifas ne`yan Italy. Suka tsaya bakin zauren gidan Inna Tambai, ko wanne cike da annashu dauke da murmushin kauna, babu wanda ya iya cewa komai sai Dije ta cije ta ce, "Lah Yusuf mun iso tare ko?" Ya ce, "Kin ga na fi ki zafin nama ya dace a ce kin riga ni isowa fiye da awa daya, ko dan ki kara gyara `yan like-liken na gazar da jan baki idan kin je an ce, "Dije ga Yusuf nan ya zo". Suka kyalkyale da dariya ta ce, "To mu karasa mana cikin gidan, amman ni dai ina tabbatas maka na fika hanzari anan". Ya kira sunanta cikin jan hankali irin na maza ya ce, "Dije". Ta amsa 13 cikin dariya da nuna jin dadin yadda ya kira sunan ya ce, "Ina so ki rike abu daya a yau kada ki yadda ki manta da abinda zan fada maki a yanzu, wato na fi ki hanzari amma zan tabbatas ma ki da haka ran da duk muka yi aure abinda duk zamu fara haihuwa Insha-Allah zai kasance namiji". Ya shige gaba zuwa cikin gidan su Inna yana dariya yayin da ya bar Dije lullube da gundumemiyar kunya, domin ya bantaro mata wata irin magana da ba` a taba yi mata irin ta ba. Inna ta rinka taya shi dariyar duk da bata san abinda suke ma dariya ba. A nan gidansu Inna Tambaya yayi sallar mangariba, a nan yayi issha`i, aka sako masa tuwo. Dije ta kawo masa ya ce ta zo su ci tare idan ba haka ba bai ci, a dole Dije ta zauna suka ci a kunyace. Malan, mijin Inna Tambaya ya leko ya ce yana son magana da Yusuf. Yusuf ya mike ya nufi zaure wajen Malan ya ce Dije ta jira shi zai raka ta gida. Maian ya ce, "Yusuf kada ka zargi kowa a bisa dalilin wannan kira da na yi maka. Wallahi! Wallahi!! babu wanda ya sani, ni ne kawai tunani na ya ba ni naga ya dace na shawarceka, kuma shawara zan ba ka idan ka ga bata yi maka ba, ka bar ta anan inda mu ka yi ta bana son kowa ya ji. Akan zancen Malan Tukur ne da ku ke ta korarsa kai da mahaifiyarka? Nan da nan sai Yusufa ya murtuke fuska ya bata rai sosai ya ce, "Mu ke korarsa kamar yaya? Malan ni fa ba yaro ba ne na san ciwon kai na don me zai nemi ya matsa mani ne?"Malan ya ce, "Ni ma don na san kai ba yaron ba ne shi yasa na ke son mu yi zancen manya da kai, ko ka ga na nemi su Basiru? Abinda na ke son ka fahinta anan shi ne, matsayin mahaifiyarka itama fa mutum ce, haka nan akwai nauyi akan ta na aure tunda bata wuce shi ba. Abinda za kai la`akari anan.shi ne zamanin da mu iyayenku mu kai aure ba daya ba ne da na ku, wanda sai yarinya ta sami shekara ashirin gaban iyayenta na karatun boko ba`a kai ta dakin aurenta ba, mu kuwa an kawo mana iyayenku suna yan shekara goma sha biyu. Lokacin da ta shekara bivu da aure, sai haihuwa to idan ka lissafa ba su shige shekara goma sha hudu zuwa sha biyar ba za su haifi dan su na fari. To ka lissafa mani, 14 shekara nawa ke tsakaninku ku diyansu na fari? Na san dai yanzu baka wuce shekara ashirin da biyar ba idan ka hada da sha biyar ka ga mahaifiyarka bata wuce shekara arba`in ba. To yanzu kai ina mutuncinka ace tana zaune babu aure? Domin akwai sauran kuruciyarta dole ne kuma maza su yi sha` awarta in ta fito waje." "Babban farincikin mahaifinka ace yau ta auri wanda ba mutumin banza ba sannan ya rungume masa zuri` arsa wannan shi ne fatan duk wani namijin kwarai. Tabbas akwai ciwo idan aka ce wani dan duniya ko yaro karami ta rakito ma ku, amma kamar Malan Tukur me za ku ba shi sai dai ya yi ma ku domin arzikin auren mahaifiyarku. Ina son. ka yi tsam da ranka anan tun kafin ka zo duniya ake mutuwa ake kuma auren matan wa anda suka 'rasu, kai bari ma na tuna maka idan ka manta ingantaccen hadisi ya zo mana Annabin Rahama (S.A.W) kusan duk matansa zawarawa ne in banda Nana A`isha ita kadai ya aura budurwa. Yawancin zawarawan nan kuwa wa` anda mazajensu suka rasu ne, to kai don me za ka harantawa mahaifiyarka abinda ya halatta gare ta? Haba Yusufa uwarku fa natsatså ce don haka ne ma Ubangiji ya kawo mata natsattsen miji kamar Malan Tukur". Anan idanun Yusuf su ka dan canza launi sannan gashinsa ya rinka fitas da zufa ya fid do hankicinsa ya goge zufar ya yi ajiyar zuciya ya dan dago kai ya dubi Malan na Tambaya a sanyaye cikin natsuwa da jin nauyinsa fiye da da. Ya yi godiya ya mike ya ce, "To Malan na fa gode zan koma sai mun sake zagayowa", ya koma cikingida. "Salamu Alaikum Inna Tambai, kar dai na ce wannan malalaciyar bacci ta ke yi?" Inna Tambai ta yi dariya ta ce, "Ba ka dai gajiya da zolayar diya ta daga ka ganta a kwance bisa tabarma? Hira dai mu ke yi". Ya ce, "To in banda lalaci hira a kwance Inna? Ni taso mu je na rage maki hanya tunda dare". Dije ta mike tå gyara daurin kallabinta zuwa daurin zaninta sannan ta dauko abayarta da ke jikin kofa ta dora, duk Yusuf ya yi mata kyar da ido, har yasa Inna Tambai ta ji nauyin kallon ta kawad da fuskarta gefe daya. 15 Dije ta dubi Yusufa ido cikin ido ta ce, "To na shirya mu je ko?" Shi ma ya nutsar da na shi idon ya dube ta, nan da nan sai suka kyalkyale da dariya. Tambaya ta ce, "Kai wa`annan yara dariya ba ta yi maku wuya". Dije ta dubi Tambaya ta ce, "Gwoggo sai da safe". Ta fara fita sannan Yusufa ya bì bayan ta, suka jera suna tafiya cikin nishadi, su ka isa bakin wani shago ya ce, "Tsaya nan na sawo maki cingam ko kya wartsake gyangyadinki" ta yi murmushi. Ya fito rike da bakar leda ya sawo mata cingam da biskit da alawar akelas, sai ya zaro cingam biyu ya bare masu ya jefa daya a bakinsa ya mika mata daya. Ta ce, "Nagode". Ya ce, "A`a bari saurin godiya ni ma wata ran za ki sai mani sannan ki bare mani ki kuma fara tauna mani kafin ki ba ni" Ta kyalkyace da dariya ta ce, "Ni kam ban taba jin inda aka taunawa wani cingam ba, to ai zakin ya kare, gam din na baka kenan" Ya ce, "Yauwa shikenan kin ga mun zama gam-gam" Yusufa ya cе, “To gobe fa na ke son komawa Zariya makaranta idan zan dawo me zan kawo maki?" Ta yi murmushi ta ce, "Kai da za ka makaranta? ina dai son ka kawo min irin litattafanka na sakandire" Ya fiddo ido ya ce, "Kina da sha awar karatu ne nan gaba Dije?" Ta ce, "Kwarai kuwa, ai kai ba za ka bar ni na wuce ba nan gaba?" Ya ce, "Wallahi ban yi wannan tunanin ba, amma me zai hana na bar ki ki ci gaba da karatunki. ko yanzu ni da Baba Kado zai amince min Dije ai makarantar zan maida ki domin lokacin da za ki gama babbar sakandare ni ma lokacin zan dawo hidimar kasa kin ga ai dai dai aurenmu kenan". Dije ta nisa ta ce, "Anya Baba zai amince kenan? Amma ka yi tunani kafin ka san dabarar da za ka yi masa ni ma kam da an taimaka min". "To Dije bari na bar ki anan domin ga Baba Kado can ina hangensa zaune shi da Malan lliya sai in ce sai na dawo bayan sati biyu ko?" Ta ce, "Aí ba za ku je ku gaisa da su Baban ba?" Ya ce, "A`a da dai ba tare mu ke ba, kya dai ce ina gaishe shi sai na zo zan zo mu gaisa, mu kwana lafiya". Sai da ya ga shigarta cikin gida sannan ya yi murmushi ya juya, ya yi nisa da tafiya sai dai ba gida ya nufa ba, ya je ya 16 nemi wani lungu inda babu yawan jama` a ya yi zaune a gindin wani durimi ya shiga lissafin duniya inda duk ya auna maganar mijin Inna Tambai sai ya ga gaskiya ya sanar da shi, amma da ya tuno fuskar Malan Tukur zai shigo gidansu sai kishi ya turnike shi, amma idan ya tuna mahaifiyarsa ya tuna irin kuruciyarta da yadda take zullumin kin kada ta bata masa rai sai ya rinka jin tausayinta lalle ya zalunce ta har na lokaci mai tsawo domin ta ba da abinda ta ke so saboda shi, a karo na biyu kuma ya dawo da tunanin Malan Tukur shi ma anan sai kunyar sa da tausayinsa ya kama shi domin sau tari da yawa Malan Tukur na stian gamuwa da shi ya nuna son girmama Yusuf amma sai shi Yusuf ya rinka isgilanci a gare shi. Jikinsa ya yì sanyi ina shawara? Ya mike a sanyaye ya tafi, bai zame ko ina ba sai anguwar su Malan Tukur. Ya hango Malan na zaune bisa wata makekiyar darduma, manyan malamai sun kewaye shi yana yi masu karin karatu. Ya dauki lokaci yana tsaye yana kallonsu har su ka kai aya a kai addu`a kowa ya shafa, shi ma Yusuf ja ke can nesa ya shafa. Ya yi tattaki inda su Malam su ke ya yi sallama gaba daya aka amsa masa. Malan Tukur ya dago ya dubi Yusuf sosai, mamaki da al`ajabi suka cika sa nan da nan ya mike ya mikawa Yusuf 'hannu, a haka hannuwansu na rungume suka zaune kowanne cike da anņuri a fuskarsa. Sai bayan da Malan ya yi sallama da almajiransa sannan Yusufa ya kara matsawa wajen Malan ya rusunar da kan shi sosai tamkar dai yaron da ya je gaban mahaifinsa neman gafara. Yusuf ya ce, "Allah gafarta Malan na zo neman gafara a bisa wani shishigi da na so na yi maku, amma idan an yi la`akari da shekaruna za`a ga ban kai munzulun da zan lakanci komi na al`amuran duniya ba, ku yi hakuri Malan ku zartas da sunnan Manzon Allah Annabi Muhammadu (S.A.W) kamar yadda ka bukaci yi akan mahaifiyata. Ubangiji Allah ya ba ku ikon fahintar juna da cimma rayuwa mai albarka". Malan dai ya yi kasake yana sauraron Yusufa, tunda ya fara magana bai tari lunfashinsa ba, har sai da ya dire, amma a zuciyar Malan ta yi kal saboda zai cimma ribar hakurinsa akan 17 kaunarsa da Halimatul Sa` adiya. Ya ce, "Haba Yusuf na gafarta maka, ai babu komi. Haka ake son samun namijin duniya, ina anfani a kyale gida sakakah wannan wofi yazo gobe ma yaron da bai isa ba ace ya zo neman auren mahaifiyarka ai ka ga martabarku da kimarku ta zube a idon mutane". Yusuf ya gyara zama ya ce, "Malan idan zai yiwu ina son ka zo mu je yanzu wajen mahaifiya ta a gabanka na nemi gafarka domin ni gobe zan koma". Malan ya dan sosa kai yana dariyar jin dadi ya ce, "Anya ko haka ta yiwu Maitama?" Yusuf yana murmushi ya ce, "Allah gyara aikin Malan me zai hana? Ai gara mu je domin duk abinda ke gudana bata da ma saniya" Malan ya mike ya kira daya daga cikin yaransa ya ce, "Kai zo nan ka zauna ko an zo nemana ka ce na fita, ina zuwa yanzu in Allah ya yarda". Suna tafe suna hira Malan na buga wata lafiyayyar sandarsa. Alhaji Uba ne ma ya sawo masa sandar har da lema daga kasar Alkahira. Suna isa kofar gidan Malan ya ja tunga a zaure sai Yusuf ya dube shi ya ce, "In ka so shigo abin ka daga yau gida ya komo mulkinsa a hannunka". Malan ya ce, "Au to haka ne?" Yusufa ya ce, "Kada ka ji komi Allah gafarta Malan" Gwoggo Halima na zaune bisa tabarma tana gyara wani daushen goro, sannan ta karo karar rediyo lokacin da ta ji an fara labarun dare na karfe goma, ta fara tunanin yau ina kuma Maitama ya je doguwar hira. Ta saba a irin wannan lokacin idan har yana gari ya na nan dakinta suna hira. Bata kai karshen tunanin Yusuf ba, ta ji sallamarsa amma a yadda ta ji hayaniyar gaishe-gaishe a tsakar gida ta san ba Yusuf ba ne shi kadai. Ya dage labule ya shiga ya na kwashe kayan da ke bisa kan wata kujera ya ce, "Gwoggo tare fa mu ke da Allah Sabbinani", kafin ma ta kai neman karin bayani Malan Tukur abin son ta ya bayyanar da kan shi a dakin. Duk dai bayanin da ya dace Yusuf ya yi a gaban Malan da mahaifiyarsa ya yi amma Malan din ne ke kokarin amsa masa, Gwoggo Halima ta rasa abin cewa, har Yusuf ya fice ya bar ta da Malan. 18 Da misalin karfe sha daya na safe Yusuf ya kammala shiryeshiryensa zai tafi Zariya ya shiga dakin mahaifiyarsa don su yi sallama, bayan sun gama zantuttukansu wanda ya shafi gida ya mike zai tafi sai Halima ta dan kawad da fuska ta ce, "Au maganar Malan fa na manta na sanar da kai wai yau da azuhur za su je can Danja wajensu Baba Karami a dauro aure". Yusuf ya yi murmushi ya ce, "To madalla, Allah yasa alhairi amma fa nan gidan za ki ci gaba da zama sai dai shi ya rinka zuwa". Tа се, "To daman ka ji wani ya yi zancen zan tashi ne?" Ya sasa kai kai ya tafi abinsa a rannan aka dauro auren Malan Tukur da Halima, a wannan rana ya fara kai ziyara gidan amaryarsa. To sai me kuma zai faru? Wata daya, wata biyu zuwa wata na uku bayan aurensu Malan da gwoggo Halima, a kodayaushe Yusuf na zuwa gida amma sai ya rinka samun sabon canji a gidan na su, misali kamar ita kan ta gwoggo Halima da kannensa a kullum suna cikin daukar karatu a wajen Malan to shi ma Yusuf sai ya kashe duk wani karatun novel ya rinka zama da yamma anan kofar gidansu wajen Malan ya rinka kwasar karatu. Haka nan kuma ya yi farin ciki da yadda yanzu kofar gidansu ta kan cika da jama` a albarkacin Malan Tukur wanda ko zamanin mahaifinsu ba` a cika haka. Sai wani karin budi shi ne abinci a gidansu, yanzu kámar gidan wani hakimi, bai zullumin ko ya kawo ma Gwoggonsa kudi ko bai kawo ba domin Malan Tukur ya dauki nauyin komi. Akwai wani zuwa da ya yi ya samu Gwoggo Halima na ta yin kunshi ta sanar da shi za ta biki Faskari wanshekare amma abin mamaki a wanshekaren har la`asar bai ga Gwoggo ta yi tafiyar ba sai ya ce, "Wai Gwoggo ba na ji kun ce za ku Faskari ba ne?" Sai ta dan yamutse fuska ta ce, "Malan ya hana wai sai dai shi va jë mun bikin, ko ina ya taba ganin namiji a bikin mata?" Yusuf ya noke ya rinka dariyar mugunta ya ce, "Kash! Gaskıya babu dadi, ga shi kuma har kun yi kunshi". Ta galla masa harara ta ce, "To shi ne me? Ko da ma can ai ina da niyyar kunshi na, da za ka ce babu dadi, ni abokiyar wasanka ce? Kai ne har za ka tausaya min don an hana min zuwa anguwa?" Ya 19 dai fice zuwa dakinsa na zaure yana yi ma Gwoggo dariya. Wannan ma yana kayaten da zuciyar Yusuf wato kullen da Malan ke yi ma Gwoggo domin a da kusan kullun Gwoggo sai ta fita anguwa, yanzu kuwa shi bai iya tuna ranar da ya zo bai cimma Gwoggonsa a gida ba. To shi ma a can Malan Kado ya gamsu ya amince a cikin `yan watannin nan uku Yusuf ya amince da Dije idan ya lura da irin dawainiyar da ya ke yi mata, ba su dai shige`yan kayan ciye-ciye ba kamar na naira hamsin, zuwa dari sai ko tsaffin litattafansa. Malan Kado sanin cewa Malan Iliyasu dan uwa ne ga Malan Tukur sai ya nemi lliya ya yi ma Malan Tukur magana azo a ja bikin Dije da Yusuf. Da farko da Malan din ya nemi Yusuf akan maganar sai Yusuf ya ce, no za`a yi hakuri a mayas da Dije makaranta, in ya so idan ta gama shi ma ya gama ayi bikin?" Malan ya sha mur ya ce, "A kul na sake jin.wannan maganar, ka san dalilin da ya sa ya hana diyarsa karatun? Ka dai kyale shi ya yi iko da diyarsa yadda ya ke so." Aka ja ranar bi' wata biyu domin a lokacin Yusuf ya ke ganin za su sami hutu mai tsawo. Bayan kwana goma da sa ranar auren Yusuf da Dije sai ga Yusuf ya dawo cikin matsanancin ciwo wanda ba komi ke damunsa ba illa maleriya da ta yi mai kamari, daga zazzabi mai zafi sai ciwon kai mai radadi sannan yawan haraswa akai-akai. Da ya kwana daya a kwance a gida abokinsa Garba nas ke zuwa duba shi da yi mai allurai akai-akai, sai ya daure ya rubutawa Dije wasika domin ya san bata san halin da ya ke ciki ba. Tana tsakar wanke-wanke, Sarai kanwar Yusuf ta yi sallama ta

Chapter 2 of 5