ce, irin wannan
ta ci ka muni, ko ta faye kiba da dai sauransu, shi ne yau don na gaya maka daya ranka zai baci, to yi hakuri, ni dai an jima a raka ni na gano Wasila."
Da la'asar sansanya suka shirya zuwa makarantar horon
malamai ta 'yanmata da ke nan cikin Zariya kowanne ya ci ado
da gani ka san wajen 'yanmata za'a ziyara, Awalu ya tsaya ya sayi lemo da ayaba leda biyu ya rikewa Wasila.
Yusuf ya dubi Awalu da gefen ido yace, "Ni fa tsiya ta da
zuwa makarantun nan ayi maka ca da ido ka rasa wanda za ka
tunkara don ya nemo ma ka wanda ka zo nema". Awalu ya се,
"yi hakuri Malan yanzu za ka ga Wasila ta bullo ko daya daga
cikin kawayenta."
Daga can wata doguwar budurwa ta tsinkayo a guje dank
kwali a hannu tana ta haki tare da kyalkyatar dariya ta ce, 'Awal!"
Awalu da Yusuf suka dubi juna su kai dariya shi ma yace, "Ranki
ya dade Wasila, wannan irin gudu haka?" Ta ce, "Awal na gan
ka ba dole na yo gudu ba? To bisimillah ku zo mu je ga kujera
can mu zauna."
Suna zaune an shiga hirar nishadi ta samari da yan'mata
sai ga Fa'iza da Binta sun iso kawayen Wasila ne, ko wacce ta
nemi kujera ta zauna suka gayas da su cikin mutunci.
Zuciyar Yusuf ta shiga tsarguwa yayin da idanusa su ka
tsokalo masa abin sha'awa nan da nan jijiyoyinsa da gangar
jikinsa suka shiga rashin kuzari a dalilin sha'awa da idaniyarsa
ta jawo masa, daga can kuma kokon zucivarsa soyayya na ta yi
31
masa ruru mai radadi ba kowa ba ce Yusuf ya tsunduma da
sonta da kaunarta farat daya face Fa'iza. Yarinya da take lukwi
lukwi jikin ta kamar muzjajjen murjani, fuskarta kuwa yai lumilumi mai idanuwa kamar wadda aka halittasu da ruwan zanzan
don walkiya, tana da fasalin baki mai kama da yankan reza.
lyakan tunanin Yusuf bai taba ganin yarinya da ya rikice
haka ba tamkar Fa'iza, nan da nan tunanin abinda ya gudana
tsakaninsa da Awalu a dazun da safe ya dawo masa, ko dai an
yi wani shiri ne yau a kan shi? Nan da nan ya ture wannan
tunanin shi wanene, me ya ke da shi da har za'a so a raba shi da
Dije a cinna masa Fa'iza? Abu ma fi saukin ganewa anan shi ne
a yau ya hadu da irin matar da ya ke so. Ya shiga iyakar kokarinsa
don ya cinna kaunarsa ga Fa'iza amma yarinya sai kawai ta
dube shi ta yi mai murmushi, murmushin da ya ke kara rudar
Yusuf.
Wasila ta ce, "Yusuf tsakani na da Awal babu yaudara
don haka bana jin zan iya yaudarar wanda ya ke tare da shi, a
gaskiya Fa'iza na da wanda ta ke so, don haka kada ka wahalad
da kan ka". Awal ya ce, "Don Allah ku kyale shi shima shirme
ya ke yi, yau fa sauran kwana arba`in mu dauko masa Dije
amaryarsa", Haba! Tamkar Awal ya soki Yusuf da fadan sunan
Dije a gaban Fa'iza!
Ya zaro ido ya ce, "kai Awalu wa aka sawa rana, don
Allah idan ana wasa ban da wasan karyar aure. Ni dai Fa'iza don
Allah don Annabi ina rokon alfarma ki bar ni na ci gaba da zuwa
wajenki tunda dai ba aure aka daura ma ki ba". A haka dai ya
dami Fa'iza da magiya ita kuma bata son yawan surutu akan
dole ta amince masa amma ba wai don tana son shi ba a ranta.
Fa'iza Abba diyar wani.mai kudice anan cikin Zariya itace
ta farko wajen innarta, kyan Fa'iza da ke kwada maza ta same
shi wajen innarta Hajiya Fatima.
Fa'iza na da samari iri-iri amma wanda yayi tasiri a
zuciyarta şhi ne Isma'il. Isma'il saurayi ne amma mai tashen
kudi cikin matasa. Ransa ne kawai ya ke jin bai iya mallakawa
Fa'iza don tsananin so.
Shekara daya rak ya ragewa su Fa'iza da Wasila su
32
kammala karatunsu na sakandire a yarda Wasila da Awalu suka
tsara tasu rayuwar shine da zaran Wasila ta kammala zai nemar
mata ta ci gaba da N.C.E yadda za'a sami cikakkar malamar
makaranta kafin shi kuma ya gama, ya je hidiman kasa ya
dawo ya nemi aiki sannan ayi biki. Fa'iza kuwa ba su da wannan
ra'ayin ita da Isma'il sun shirya tana gamawa sai aure zai
mallaka matu kasuwancin da zai rinka kawo mata kudin kashewa.
Bayan su Yusuf sun koma dakinsu a can cikin jami` a
Yusuf ya fidda hula ya jefas shi ma Awal ya yi jifa da takalmansa,
Yusuf ya ce, "Amma gaskiya yau ka yin min rashin mutunci
Awal, menene na kawo maganan wata Dije can a gaban yarinya
kamar Faʼiza?" Awal ya harare shi yace, "Ga ka nan mara mutunci!
Wallahi ka ba ni kunya me rana aka aa ka je kai ta rawar jiki akan
'yar mutane?" Yusuf yaçe, "Wallahi Awal da gaske na ke, son
Fa'iza na ke, saboda ita kuma a yau na kyale Dije ko za'a kashe
ni ba na auren Dije ina ganin Fa'iza."
Awalu ya yi shiru yana mamakin yadda dan lokaci kadan
Yusuf ya canza, sai ma ya rinka ba shi mamaki domin wannan
wauta ce saboda dai Fa'iza tafi karfin Yusuf.
"Wai yanzu nan kai da gaske ka ke?" Yusuf ya bata fuska
ya ce, “me ka ke nufi?" Awal ya ce, "Amma da ganin sigar irin halittan Fa’iza ka san ba irin matanmu ba ne. Fai'za siffar matan
masu hannu da shuni ce ba mu ba yan cika takarda da surutu".
Yusuf ya ce, “ka san abinda Allah zai maida mu can gaba?"
Awal ya amsa,” amma yanzu mu ke magana ba lokacin da ba
mu da tabbas ba”.
Yadda duk Awal ya so ya nunawa Yusuf gaskiya amma
Yusuf ya ki amincewa har shi ma ya gaji bayan Yusuf ya ce, to
kai ai shirme ka ke yi domin baka warware baikon ku da Dije ba". Yusuf ya ce, "manta da wa`annan ba matsala ba ce yanzu,
a wajena shawo kan Fa'iza shine matsalar" Awal ya ce, "ka rufa
ma kanka asıri domin zuwan ka Bakori da rashin zuwan ka bai
hana Baba Kado ya kai ma Dije idan ranar da suka diba ta cikа”.
Yusuf ya nisa ya lumfasa ya ce, "ai ko gaskiyarka fa! Ya yi kasake shin me zai yi yanzu? Wasika zai rubuta gida wajen
33
gwoggo Halima da itama Dijen ko ko? To me ya dace yacе
masu? Ya ce kawai a tsayar da biki a mayas da biki sai in har
Dije ta koma karatu ta gama nan da shekara uku, in ko ba haka
ba to aba wani, sai kuma ya canza shawara kai ina dalili ana
auren dole ne ga namiji? ya fada a fili Awal ya juyo ya dube shi
yace "maganar zuci ta fito fili, kada fa Fa'iza ta zauta ka, don
Allah ka bi a hankali an san ba auren dole a yanzu, amma kuma
bin maganan iyaye wajibi ne."
Yusuf ya zurawa Awal ido sannan ya tambaye shi "me
kaga zan yi?" Awal ya ce, "ka samu lokaci ka je ka yi ma Gwoggo
Halima bayani da Mallan Tukur su za su san yadda za su warware
komi."
* * *
Bai dai sami zuwa Bakori ba sai ana sauran sati hudu
bikinsu, amma sau uku yana kokarin ganin Fa`iza a makaranta
babu dai zancen bayas da hadin kai wajen Fa'iza sai dai ya. yi
murna daya, ta ba shi ikon zuwa gidansu haka nan ta yi mai
alkawarin idan ya je gidansu zata ba shi katin gayya na bikin
cikar ta shekara goma sha takwas.
Da yamma likis ya isa Bakori yana bude dakinsa ana kirar
mangarib, ya kunna lantarki haske ya sawwaka a dakin, ya dubi
bangon gadansa sai ya yi ido hùdu da hoton Dije ta zuba masa
ido tana murmushi. Ya ja tsaki da ya dubi kirjinta ya gan shi
kamas a ransa ya ce, kila ma wannan shekara zata fara kidanyar
dangi, sannan ya tuno da yadda ya lakanci kirarta a dakin Inna
Tambai, abin babu dadin tunawa wai shi wace ilar ce ma tasa
ya amince masu?
Dai dai lokacin da ya kan sami sakewa da mahaifiyarsa
wato in dare ya yi suna zaune suna sauraren jakar magori a
redio, sai Gwoggo Halima ta ce "amma na ji daddin zuwan ka a
yau, saboda zanceń masu kankaran dakin can da za`a sa Dije
wallahi sai wasa su ke da aikin don sun ga Malan kwana biyun
nan yana fama da mura."
Yusuf ya dan muskata ya gyara zama ya jawo wani
gwangwani da gwoggo ke aje goro ya dauki daya ya tsaga, a
rike a hannu kamar yaci ama bai iya ci ba, sai ya ce, "gwoggo
34
maganar dakin nan a bar ssi kawai" Ta yi har da ido ta ce
"kamar yaya a bar shi?" Ye ce "a gaskiya gwooggo a yanzu kam
ba zan iya auren Dije ba".
Cikin Halima ya bada wani irin kululu har sai da Yusuf ya
ji rugunniyar a fili ya dan kawad da kai gefe guda a zuciyarsa ya
ce duk na shirya daukar wannan tashin hankalin da zan sa jama'a,
zan daure sai na shawo kan ku.
"Maitama ka san wanda ka ke fadawa wannan danyar
magana?" Kansa a sunkuye bai amsa mata ba, ta sake cewa,
"Maitama na roke ka don Allah don Annabi ka rufa min asiri,
idan har wani ke zuga ka, ko kuma wata diyar ce take daukar
hankalinka, to ka rufa mana asiri, kada kasa naji kunya a garin
nan kun fahimci juna da Dije sannan kuma itace dai dai mu,don
haka ban ga dalilin da zai sa ka ce ka fasa ba, ko wani abu ta yi
maka?"
Yusuf ya sa karamin yatsansa cikin kunnensa yana
girgizawa, ya fada a hankali ya ce, "wallahi Dije bata yi min
komi ba, aurenta ne dai ban yi. Ku yi hakuri Gwaggo da
muguwan rawa an ce gwamma kin tashi."
Halima ta rasa kalmar da zata yi mai anfani da ita don
haka sai kawai ta ta yi tagumi ta sadda kai kasa. Yusuf ya mike.
a sanyaye ya dan rusuna ya ce, "mu tashi lafiya gwoggo", ta
amsa can kasan makogoranta.
Da safe bai shiga gidan ba sai misalin karfe goma sha daya na safe, bayan sun gaisa da gwoggo ya ce mata, "Gwoggo
yau da la'asar na ke son na koma ko goberda safe", ta hade rai
tace, "Amma ya dace ka je ka gaida Malan domin na sanar da
kai bai jin dadi", ya yi murmushi ya ce "Ai gwoggo da asuba ina kare sallah daga masallaci na zarce gidansa na duba sa, ai na ga jikin da sauki ma", ta kawad da fuska ta ce "ka sanar da shi cin
mutuncin da za ka yi min ko a garin nan?" Ya ce, "Haba gwoggo,
wannan ai ku za ku yi mai bayani bayan na tafi amma bai dace
yadda ya ke jin murar nan ba na dame shi da yawan surutu". Ta
galla masa harara ta ce, "sai ni da ka mayas shashasha wadda
ba ka damu da ciwon zuciyartà ba, ai dole ka zo ka jagula min
lissafi, to abinda na ke so da kai shi ne ba za aji wannan zancen
35
a baki na ba, don haka sai ka je ka sanarwa Malan Kado da kan
ka'.
Zuciyar Yusuf ta rinka ukan uku uku, wane irin zance
Gwoggo ke yi haka? Wane shi da tun karan wannan tsoho, duk
da dai bai auren Dije amma yana da nauyin Baba Kado, domin
yadda Yusuf ke ji da Kado tamkar jininsa, haka nan yana tsananin
kaunan Malan Kado har baya son ya tuna cewa `yarsa Dije zai
yì ma cin mutunci, shi dai kawai addu'ar Yusuf ita ce Allah yasa
Malan Kado kada ya dauki zafinsa a ransa domin ya so ya hakura
da Dije albarkacin mahaifinta to sai rabon Fa'iza ya gitta.
Ya ce, "A'a gwoggo. Bai dace ace na tari mahaifinta da
wannan magana ba, ko don kada a bata sunan gidan nan",
tace, "To sai ka je gidan 'yar uwarsa Tambaya amma ni kam da
nauyi ace ni na fiddo da wannan magana cikin zuri'ar su Dije"
Yusuf ya yi godiya a zuciyarsa saboda ta kwana gidan sauki,
abinda zai gaya ma Tambaya bai iya fayyace ma Gwoggo Halima
don haka sai ya amsa mata da saurinsa cewa za shi an jima idan
ya yi la'asar.
Yusuf ya kwanta ya shaki baccin ranarsa mai isarsa,
sannan ya tashi ya fesa wanka ya zuba kayan da suka dace da
shi, ya fesa turarensa, ya ja kofar dakinsa ya rufe ya kama
hanya zuwa gidan Inna Tambaya.
Ita ko mutuniyar tun a daren jiya ta ji labarin zuwan
Yusuf wato Dije a wajen Malan Kado, to har azuhur ta ji bai aiko
mata ba sai ta shirya ta nufi woggo Tambaya ta san dole ya je
can sannan ya aika kiranta.
Tana uwandakin Tambaya tana kwance da wani littafi
Sirrin Boye ta ji sallaman Yusuf ta lumshe ido, ta rufe littafi
tace, 'ka cika dan halas Yusuf angon Kubra' amma cikin ranta.
Tambaya ta watsan da abinda ta ke yi ta nufo falo da
bakonta suka tsinke hira ita da Yusuf shaf ta manta ma da
cewa Dije na nan a daki kwance.
Tambaya ta ce "Yusuf ina kara gaya maka kada ku
matsawa kanku da laihe don haka kada mu ji an ce ka sanya da
wani kaddanárku kamar fegi ko gona wannan aure don kulla
zumunta za mu yi shi ba don wani abun duniya ba, Dije matar
36
ka ce, idan Allah ya azurta ku can gaba komi ka yi mata mutunci ka ne".
Yusuf yace, "Ai Inna, zancen aure nan na mu bar shi." Tambaya ta dafe kirji tace, "mu bar shi kamar yaya?" Ya ce, "E,
Inna ni kam ba zan iya zaluntar kai na ba gaskiya Dije ba irin
matan da na ke da ra'ayi ba ce, don haka nayi tunani karshe na
zo nan gaba na auro irin ra'ayi na ya kasance na ci amanar Dije
kin ga idan na yi haka ban yi ma Baba Kado adalci ba, domin ina
son Baba Kado tamkan yadda na ke son a ce shi ne ubana
sannan ina girmama shi fiye da ko wanne dattijo a garin nan".
Tambaya ta ce, "duk na san wannan, amma abin tambaya
anan shi ne, wai Dijen ka riske ta da wasu halayen banza ne
wanda ba su dace da ra'ayin na ka ba?" Yusuf ya juyad da kai gefe daya yace, "Ka ji Inna don Allah! Ina nuna maki ita kanta fasalin Dijen ne na ke dubawa na san bai yi mani ba, ba wai halin ta ba". Tambaya ta ce “fasali kamar yaya? Dije guda nawa ce? Duka duka yanzu ta shekara goma sha biyar yaushe makerin `yanmata ya gama kera ta? Wannan ba dalili ba ne Maitama".
Yusuf ya ce, “Gaskiya Inna ina son mace mai cikar kirji
sannan tana da tudun mazauni amma Dije fa haka take a
shamude". Makogoron Tambaya ya bushe takaici ya turniketa, abun haushi goma da ashirin, ga yusuf na ta wulakanta mata. diya a gaban ta, sannan kuma tana tunanin yadda zata kalli jama'a idan an ce an fasa wannan aure. Sai ta daure ta ci gaba da lallashin Yusuf.
Ta ce, “ina son na fahintar da kai wani abu daya Yusuf,
ita dai diya mace namiji ke mikar da ita", ya yi sauri ya dube ta
yace, "kamar yaya namiji zai mikar da mace?" Tambaya tace,
"ka san Allah wannan kirjin na Dije da sauran abubuwan da ka ke hange jikin sauran mata, idan ta sami wata shidda nan tare
da kai mikewa zata yi, in dai tana samun cima mai kyau tare
da kwanciyar hakali. Kai kan ka sai ka yi mamakinta, saboda wallahi Dije ba irin busassun matan nan ba ne wahala ce, da
rashin kwanciyar hankali ya takurar da ita haka."
Yusuf duk yana jin abinda Inna Tambai ke fada, a ransa
ya ce, "Ina! Don dai ba ki ga gimbiyar mata ba ne Fa'iza." Ya
27
knfasa ya ce, "inna Tambai ku dai yi hakuri don Allah a baiwa
su Baba Kado hakuri, insha Allah idan hankula suka kwanta
zan sami Baba Kado har gida na kara kwantar mai da zuciya".
Ya rinka duba agogon hannu, wato nuna alamu son tafiya a dai
na bata masa lokaci, ya mike ya ce, "To inna sai na zagayo
gaisuwa wani lokaci."
Tambai a cikin sanyin murya ta ce masa, "Ka sami wadda
ran na ka ke so ko?" Da farko kamar ya ki gaya mata gaskiya,
amma sai ya yi tunanin menene amfanin kin gaya mata zancen
Fa'iza sai ya ce, "E, Inna na sami wadda na ke da sha'awa ta
mallaki duk abinda na ke so a jikin mace".
Tambaya ta zuba tagumi sannan ta sadda kai kasa, ta
manta kwata-kwata a ina take don dacin rai, Yusuf ya sunkuya
ya fita, ya tsugunna bakin kofa yana saka takalmansa amma
bata ji abinda ya ke fadin ba, balle ta amsa masa.
Yana isa gidansu ya tabbata ya dana bom a Bakori nan
da awa daya zai tashi a gidan Baba Kado, don haka ya yanke
shawara ya bar garin komi dare don kada tashin bom din ya
hada da shi.
Dacin ran da ya haddasawa Halima bata yi masa
tararrabin cewa ya fasa tafiyar sai gobe ba domin ganin dare
ya yi, sai kawai ta ce a sauka lafiya.
Sái karfe sha daya da minti tara na dare ya shiga dakinsu,
ya cimma Awal yana ta famar karatu, nan da nan suka dubi juna
suka bushe da dariya, Yusuf ya sunce kayan jikinsa ya fice ya
watso ruwa sannan ya dawo. Awal ya ce, “ina labari mutumin,
na san dai yau hawayen Dije sai da ta cika ma hula taf."
Yusuf ya ce, "kai wa ke ta Dije wannan ai nafila ce, ni
da manya na kafsa masu hau-hauwan jini na samu na shawo
kan su don kada ace na tayas da ciwo Insha Allah komi ya yi
daidai yanzu na shawo kan Fa'iza kawai ya dame ni."
KASHI NA HUDU
Gwoggo Tambaya na nan zaune inda Yusuf ya bar ta,
ta kasa hasala komi, tun tana jin she-shekar kukan Dije har ta
38
rinka jin ta tana kuka wiwi, can tambaya ta nisa ta ja habar
zaninta ta goge hawayen da suka taru gefen idonta, ta се,
"Wallahi dole Dije ki yi kuka Yusuf ya yi mana abinda mafarkinmu
bai taba nuna mana ba, ke ki gane mun yaron wofi sai da mu
ka saki jiki da shi sannan kiris ya rage mana mu kammala shirin
kayan dakinki shi ne zai mana haka? Babu laihi Allah zai baki
wanda yafi shi". Tambaya hawaye, idan ta yi ban maganar ta gaji sai ta yi shiru ta ci gaba da sakar zuci, sannan ta koma
baiwa Dije baki. Dije kam kuka ta ke har bata san abinda zata
koka mava ba, `shin rashin gwarzon masoya Yusuf, ko ko
masifar su gwoggo Ankudi, ko ko surutun jama'a akan an baiwa
Yusuf ita amma ya zo ya ce bai yi?'
Mangariba na yi Tambaya ta je alwala Dije ta sille ta nufi gida, a bisa hanya jahilci ya zo mata wai ma ko ta je bisa titi
mota ta nike ta ta huta da wannan muguwar rayiwa? Sai dai
kuma Allah ya hana ka yanke ma kan ka hukunci komi kunci.
Ta isa gida ta yi sallah ta kudundune, ta yi kuka ta yi kuka, har kuka ya nemi kan shi ya rasa, har garin Allah ya waye
tangaran babu bacci a idon Dije. Da safe zazzabi da haraswa
suka same ta, amma babu wanda ya kula balle ya tausaya mata. Tambaya ta aiko mijinta tunda safe cewa malan kado ya
je tana son ganinsa. Shi kan shi Malan yadda ya ga Tambaya ya
san babu lafiya.
Ta gaya masa Yusuf dai bai yin aure amma bata fadi fallasar da ya yi ma Dije ba. Nan take Malan Kado ciwon kai ya
taso, sai dai babu mamaki domin tun kwanakin baya da Malan
Iliya ya raka shi asibiti an tabbatar da hawan jini a tare da Malan din.
Ya ce, "Tambaya jiri na ke ji idan za'a sami kunkuniya а
kicin din ki samo ki jika min”. Ta mike ta nufi daki ta fito da
kwandaleliyar laya ta mika masa ta ce, "daura wannan Insha
Allah zai laf”. Ya amsa ya daura ya dafe kan yana juyayin abinda
Tambaya ta gaya masa wai Yusuf bai auren Dije! Can Tambaya
ta katse shi ta ce, “A daren jiya Malan ban runtsa ba, nayi
juyayin zancen da yaron nan ya zo ya gaya min duk yadda a kai
Shiga tsakaninsu a ka yi, kuma za ka ce na gaya maka, wannan
39
asiri ne su Ankudi su kai ma yaran nan."
Malan Kado ya dago kai ya tsurawa Tambaya ido babu
tantama ya amince da zancenta sai dai menene abun yi, bayan
bakin alkalami ya bushe.
Ya lallaba ya koma gida Dije na tausayin kanta tana
tausayin mahaifinta domin ta san bacin ran da zai shiga kwatan
kwacin na ta ne.
an ji.
Kwana biyu zance ya zagaye garin bakori har su Ankudi
Da hantsi DDije jikinta ya yi lankam ıa damuwa da bacin
ran da Yusuf ya saukar mata, Ankudi ta zo ta tsaya inda Dije ke
kwance ta sakar mata kafa a kashin baya. Dije ta yi kugi ta се
"Wayyo Allah na!" Ankudi ta yi dariyar mugunta ta ce, "munafuka
ki ke karyar ciwo, ashe inda aka kai tallarki sun ce su ma ba sa
so? Kadan kika garii ja'ira mai bakar kafa, tashi maza ni ki je ga
wanki can na tara ki wanke man."
Dije na gindin rijiya ta yi kokari jikinta ya tsaya daidai
amma ina sai makyarkyata ta ke yi, da ganinta dai ka san bata
da koshin lafiya, ga Sabura da Ankudi na ts aye gefen ta suna ta
yi mata shegantaku da cancakwati wai Allah ya yi ta mara
fasali ga bakar kafa Dije dai na sunkuye: ta na murzar kaya
yayin da idonta ke zubar hawaye.
Malan Kado ya dade da shigewa yana tsaye daga can
kofar shigowa duk irin cancakwatin da su Ankudi ke yi a
kunnensa, da ya lura ba su da niyyar dainawa haka nan babu
mai iya juyowa ta gan sai ya yi gyaran mur ya, gaba daya su ka
juya su kai mai ca da ido.
Ya lumfasa ya ce, "Amma dai kun ji kunya, yanzu ku
idan an ba ku iko ko dan yatsa kuna iya halittawa Dije? Amma
mutane ku zauna ku rinka kushe ma yarinya halitta a gabanta,
to don Allah cikinku duk wanda ya raina tsayuwar wata ya hau
sama ya gyařa".
Ya koma ya fice a fusace ya nufi gidan Tambaya yana
huci ya ce mata, "ina ganin dai duk ayi a kare karshen ta gwauro
zan zauna". Tambaya ta yi zuru da idanu ta dai san matsalar
gidan Malan Kado, don haka bata nemi jin ba'asi ba, sai ta се
40
hakurin nan dai za ka yi amma yanzu duk wani dan motsi da za
kayi Dije za ka kara shaława kashin kaji, ace ka kori matanka
don an ki auren ta, abunda dai baka so shi za ka hakura ayi.
Wato ka ga na dai san mahaifiyarta Amina ba son auren nan ta
ke yi ba tafi kwadayin makaranta, saboda haka don ka fid da
Dije daga wannan kangin fitinar ka ban ita kawai na kai ta wajen
Amina ta samar mata makaranta in ka so ta rinka zuwa ma hutu
kana ganinta".
Malan Kado ya yi tagumi yana shawara da zuciyarsa,
shi kan shi ya san ya dace ace Dije ta sami canjin yanayi ko ta
zama mutun ta sami natsuwa zuciyarta babu kuwa inda ya dace
sai wajen mahaifiyarta Amina. Malan ya dubi Tambaya ya ce,
"kina ganin shu'umin mijin nan na ta zai amince?" Tambaya ta
ce "Haba Malan don ba ka ga yadda Amina ta ke ba ne a gidan
Isa, wallahi daga ita sai 'ya'yanta ka san tuni ya kori waccan
uwangidan na shi da ya ga tana neman ta tsangwamawa Amina
da 'ya'yanta sannan kuma gidansu rayuwace irin ta `yan boko,
ba irin tamu ba, ka san shi Malan Isan ma'aikaci ne haka zuri'arsu
don haka ka da ka damu, ka kwantar da hankalinka."
Ya ce "To shi ke nan bari na koma gida na turo ma ki
Dijen in ya so gobe in Allah ya kai mu sai ku tafi."
Har yanzu Dije na gindin rijiya tana ta fama da wankin
kayan Ankudi Malan Kado ya cimma ta, ya ce, "ke Dije maza
shirya kayanki ki je gidan Tambaya anjima bayan an sakko
masallaci ina nan zuwa". Dije fuskarta a kunbure hatta kwayar
idonta kamar za su zazzago saboda masifar kuka, ta kwashi
abinda ta san tana so ta nufi gidan Tambaya, kai idan ka ga Dije
a wannan lokaci ka tausaya mata, tamkar mahaukaciya sabon
kamu, duk ta kode ta yi jeme-jeme, ga kaya wasu a kwali yayin
da wasu ta yamutsa cikin jakar leda.
Tambaya ta sanya almajiri ya wanke mata kayanta fes,
sannan ta nemi jaka mai dan mutunci ta zubawa Dije kayanta.
Wanshekare tunda safe Malan Kado ya zo raka Tambaya
da Dije tasha, suna tafe yana yi mata nasiha yace, "To Dije kin
ga dai halin da muke ciki don Allah don Annabi ki kama kan ki,
kada ki yadda batanci ya fito daga gare ki, yadda za'a ji dadin yi
41
mana dariya, ki tuna irin gwagwarmayar da mu ke ciki da ni de
ke, haka nan duk halin da ki ka shiga kada ki manta da sallah, ke
da duk nauyin da ya hau kan ki na addininmu ki kula da hakkinsu."
"Ina kara gargadin ki tsare mutuncinki, mutuncin diyɛ
mace shi ne kamun kai, tsare kai daga zina da duk saurar
shedanancin zamani, kada kwadayin abun duniya ya rude ki hai
ki fada hanyar banzu, don Allah ki dangana da abinda zan