Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 4
Mama ya dauki matarshi ya kai ta gidan Ahmed don ta gano Wasila matar Ahmed da dansu Khalifa, anan suka hadu da Ahmed da Amin har da Wasila- suka yi ta rarrashinta akan ta tausayawa mijinta ta koma gida.Asma'u ta ce "Shin me ku ke so na gaya wa Mama bayan na riga na ce mako biyu zan yi gidanta?" Anan Ahmed ya shirya mata dabara don haka tana komawa gida ta yiwa Mama Karya ta ce "Rijistar da suka yi kwanan baya KarKashin 65 fungiyar manyan likitoci yanzu an fara neman su zasu yi course na makonni biyu." Mama ta ce "Tun da haka ne sai ki koma gida saboda Abba ya sami rangwamen kaiki da daukoki." Dare na yi Aminu ya zo ya tafi da matarsa, daga nan suka sake bude sabon shafi na rayuwa. Haka dai rayuwar wadannan ma'aurata ta kasance cikin soyayya da Kauna da kulawa da juna wannan shekara ne ta kammala karatunta na likitanci cikin nasara, sai dai dan laulayin da take fama dashi, yau da lafiya gobe babu, gashi likitan da yake dubata ya ba ta tabbacin 'ya'ya biyu ne cikinta twins amma kuma duk scanning din da ake jariran suna cikin Koshin lafiya. Satin da ya zo Asma'u ta ji dadin weekend din dan ko manyan bakinta Salim da Mina ne suka zo musu Sallama kafin su wuce Abuja, wani sabon asibiti da Salim zai fara aiki, wanda mahaifinsa ya gina gami da hadin gwiwar wani attajiri amininsa mazaunin Abyja. Asma'u ta yi mamakin yanda Mina ta dawo sai ka ce Balarabiya pashi cikin ya karbcta, ta Kara kvau, ta yi bul-bul da ita sai ka rantse bata taba zaman Kauye ba, gashi abin sha'awa cikinta ba mai laulayi ba. 66 Salim ya dubi cikin Asma'u yana dariya "Gaskiya babynan namu yana wahalar da ke. Amin ya gaya min wai kin daina cin nama, tuwo ne kurum abincin ki. Shi ne nake zaton duk yanda aka yi manomi za ki haifar mana, in ban da manomi ne bebin mu ta ya ya zai hana Mamanshi cin komai sai tuwo." Kwanansu biyu suka wuce Abuja. Watanni suka ci gaba da shudewa, cikin Asma'u na dada girma, har watan haihuwar ta ya kama ranar da ciwon naKuda ya kamata da gaggawa ta dannawa Mama waya ta iso cikin hanzari, suka tafi asibiti, lokacin Aminu baya nan yana can bakin aikinsa ranar jirgi mai zuwa London zai tuKa daga Mama har Asma'u ba wanda ya sanar dashi halin da ake ciki. Suna isa likitansu ne ya karbi haihuwar tata kuma cikin ikon Allah komai ya zo da sauKi, Asma'u ba ta wahala ainun ba. Cikin awanni biyu ta haifi jariranta guda biyu tagwaye. Mama cikin tsananin muma ta rungume 'yan samarin har kuka suka sa ta saboda tuna baya. Bayan Aminu ya dawo gida aka sanar dashi rashin lafiyar Asma'u. kidime ya garzaya zuwa asibitin, amma abin farin ciki yana isa sai ya tadda 'yan jariransa gado suna boxing muma dai gurin 67 Amin ba sai an fada ba, ga 'yan jariransu sun fito duniya ga kuma Ma'unsa ta sami lafiya. daren ya yi ta buga waya yana sanar da jama'ar su haihuwar Asma'u. Washe gari Goggo da mahaifiyar Salim suka iso Kano ganin baby. Momy ta kwana daya ta koma yayin da ta bar Goggo gidan Asma'u suna da kwana hudu, Hajiya Hadiza ta iso daga Kaduna tare da tawagarta, wannan shi ne zuwanta na farko gidan diyar tata, tun bayan aurensu ba ta taba zuwa ba, saboda kawaici. ranar ne dai Salim ya iso tare da matarsa da kuma dimbin sayayyar kayan baby mai jegon kanta ya yi mata dinkuna sama da kala goma. Ranar suna an bar wajariran sunansu Hassan Ca Hussaini, gaskiya bikin sunan ya yi armashi 9sai, kusan duk danginsu sun sami halattar sunan 'yan tagwayen 'yan uwansu na Sokoto da na Kano dana Kaduna duk sun zo, hatta 'yan uwan Salim ba barsu baya ba, dalilin zumuncin da ke tsakanin Salim da Asma'u kowa ya ga irin kyakkyawar alakar da ke tsakaninsu abin ya kan bawa mutane sha'awa, gashi dai duk sun. yi aure amma zumunc! bai yanke ba, an dai yi taron suna an gama lafiya, duk mutane sun koma garuruwansu. 68 Goggo kakar Asma'u ita ce ta zauna gidan mai jegon, saboda kula da jariran, yayin da Mama ta kawo musu mai reno. Haka gaba dayansu suka maida hankali ga kula da jariran Asma'u Allab- Allah take ta yi arba'in ta je Kaduna wurin mahaifiyarta amma ana saura kwanaki biyu su yi arba'in sia ga wayar Salim, yana shaida musu Mina ta haihu ta sauka lafiya da diyarta budurwa. Asma'u ta yi muma Kwarai kwanansu uku ta isa Abuja harda Goggo da kuma mai renonta, 'yar kyakkyawar jaririyar ta fi kama da uwarta, daga haihuwa Salim ya yi wa 'yarsa huduba da sunan Asma'u, abin ya burge Aminu sosai. An yi shagalin suna Abuja, bayan an gama kowa ya watse aka taKaita sunan jaririya Asma'u aka dinga kiranta Asma. Bayan 'yan tagwayen Asma'u sun yi Kwari sai ta fara services dinta da yake jihar Kano aka bar ta. Tana kammala bautar Kasa ta fara aiki babban asibitin Murtala Muhammed dake cikin bimin Kano. Hassan da Hussaini suna da shekara daya da watanni biyu Asma'u ta sake samun ciki, da da farko duk ta damu amma da ta ga yanda Amin yake masifar dokin cikin sai ta haKura domin dai ta san ko duk shekara za ta rnnka haihuwa ba zai bari ta yi p/anning ba, tunda burinsa kenan ya ga vida ya cika da 'ya'ya. Da cikin Asma'u ya isa haihuwa sai ta sake haifo 'yan tagwaye suma maza, lallai rabo sai mai shi. Ranar suna aka radawa jariran Ahmed da Muhammad Salim, shekarar ne kuma Salim ya sami tafiya wani course Kasar Amurka tare da iyalinsa, KarKashin Kungiyar manyan likitoci ta duniya. lokacin sun yaye diyarsu Asma'u junior. Mina kuma tana da Karamin ciki, kuma dai duk shekarar ne Zaliha Kawar Asma'u suka dawo daga London ita da mijinta da yaransu guda biyu mace da namiji. Jariran Asma'u suna da watanni uku ta koma bakin aikinta, da yake Asma'u yarinya ce mai Kwazo fannin aikinta ta Kwarai sosai aikin likitanci tana taimaka mata da Kananan yara ta sami daukaka asibiti, ta sami nasarori, 6angarenta ta zama babbar likitan gani duk wata lalura da ta shafi mata Doctor Asma'u ta laKanceta babu wata cuta za ta shafi mace wacce Doctor ba ta sani ba, dan haka mata masu matsala suke rububinta, kowa buri yake ya ga garni gynic) Doctor domin akwai ta da bincike sosai. Mata masu ciwo suna 1ya ganinta sau uky sati gata da tausayi da tattalin mara lafiya. Bayan shekaru hudu da haihuwar su Ahmed Juniorta sake samun ciki ta haifi diyarta mace aka sa mata sunan Zaliha aminiyar Doctor. Haka rayuwa ta ci gaba da wakana tsakanin Doctor Asma'u da mijinta da yaransu guda biyar. l_okuta da dama akan ce wai maza basu da tzbbas, to shi dai Aminu ya ba mara da kunya kuina ya karyata wannan suna ya wanke miliyoyin maza dan kuwa ya yi wa matarshi Asma'u rikon mutunct sun yl zama na amana, suna tafiyar da rayuwarsu cikin soyayya, Kaunar su kullum gaba take ba baya ba. AlkKawarurrukan da ya caukar tata babu wanda bai cika ba, bashi da wani buri rayvuwa da ya wuce ya farantawa matarshi Asma'u. Komai ya samu daga ita sai 'ya'yanta, ga kudi har kudi sun mallaki dukiya ta kece raini, ga wadata suna cikin daula ga arziKin kyawawan 'ya'ya Allah ya basu, ga ilimi da wayewar kai, ga kuma uwa uba sun gina rayuwarsu cikin soyayya, tsananin Kauna da kulawar da Asma'u take samu wurin maigidanta abin har ya wuce misali, ya hadata ita da 'ya'yanta ya rungume. Koda yake itama akwai biyayyar aure. Tamat Bi Hamdullah, sai mun hadu littafina mai suna ALHINI. Daga 'yar uwarku, Kawarku, abokiyarku, antinku, Momin wasu daga cikin, ta ku kullum Zainabu Abu Lawan Birget (Mrs Lawan Mu'azu) 08029460293. Har kullum shirye nake da amsa wayoyin makaranta, ina maraba da saKonninku, mu kan so yi mana tsokaci ko sharhi game da rubucerubucenmu muna karbar gyara ko shawara ko suka mai ma''ana idan an ci karo da kuskure yi mana afuwa, mu ma mutane ne kamar kowa, wadanda bamu wuce kuskure ba, duk dan Adam ajizi ne, muna jiran ra'ayoyinku. fhMu hadi littafi na gaba mai suna ALHINI. An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 4 of 4