cewa
"Barni Fannah tafiya zamuyi Umaimah muje dan Allah dare na dada yi".
"In zaki tafi ga hanya nan ban riqe ki ba amma ni kam se naga kwal uwar daka, daga zuwan mu kice mu tafi ba wannan maganar" tana rufe baki kiran Mama ya shigo wayarta data ajiye akan Table
"Kin gani ko gashi nan Mama tana kiranki kar ki jawa kanki wani Fadan ki tashi kawai mu tafi" Rumah ta fada a rikice kamar ita ce tayi laifin
"Ai se kiyi, kona koma yanzu ko ban koma ba duk daya fada ne sena sha shi toh in zaki zauna ki zauna idan kuma tafiya ce a sauka lafiya" ta bata amsa tana kashe wayarta gaba daya dan tasan Mama yanzu idanta dosa mata kira ba haqura zatayi ba, kuma dai laifi ne dai ta rigada tayi tunda kafin Magriba akace ta dawo gashi har isha ta wuce bata komaba.
©️2️⃣0️⃣2️⃣3️⃣
*DAGA ALQALAMIN MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*MARUBUCIYAR*
*WATA KISHIYAR*👹🥰
*And now*
*HALIN KISHI LITTAFIN KUDI NE*
*KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA*
*07061838488*
*A BIYA A KARANTA*
Free page 2
Biki yayi biki, an raqashe anci an sha yammata sunyi rawa, Umaimah bata an kare da lokaci ba seda aka tashi ta kunna waya lokacin qarfe goma harda rabi tayi, daga gurin zuwa gidansu kuwa taci kusan Minti talatin a qiyasi dai sha daya ce zata kaita gida lallai kam yau ta taro Match me zafi dan tasan ma kafin taje tuni an kulle gida.
A motar Mijin Fannah suka tafi da yake hanyar su daya, ita bayin daren ne yafi daga mata hankali ba, Aa Abayar data saka da zata fito ta barota a gidan Maman Nana saboda bazata shiga jakarta ba kuma batayi zaton zasuyi dare har haka ba.
Cikin taraddadin abinda zata tarar suka sauketa a qofar gidan su, jiki a sabule ta sauka tana gyara yafen dan babban mayafin data samu sukayi musanye da Fannah ko ta dan qara rufe jikinta. A darare ta qarasa jikin qaramar qofar Get din da niyyar bugawa dan tasan dai an kulle se taji takun takalma a bayan ta.
A mugun zabure ta matsa, Abbane, da torchlight a hannunsa saboda an dauke wuta yayi mata kallo daya kafin ya saka muqulli ya bude gidan ya shiga ba tareda ya ce mata komai ba haka ta bishi zugui zugui a baya, ganin yayi kamar ma besan da wanzuwarta ba yasa ta kwasa da saurin gaske tayi ciki tana qara godewa Allah da ya saka babu hasken Nepa kuma be haska jikinta da fitilar hannunsa ba balle yaga irin shigar da tayi.
Dan dama daman da ta sake ji dayaga dawowarta ba ita kadai ba dan seda Fannah ta fito ta bude mata murfin motar da ya samu matsala, yanzu da ace saurayi ne ya ajiyeta a daren nan tana ga kawai tsirenta za suyi su huta.
Dakinsu ta fada tana sauke numfashi, bata tsaya ba seda ta tube kayan ta jefa can cikin wardrobe kafin tayi maza ta fada bandaki ta watsa ruwa tareda Alwala. Tayi mamakin ganin harta idar da sallah babu wanda ya biyo sahunta, amma tasan tarko ne. Tana jin yunwa haka nan ta haye gado ta kwanta, tunda dai ta shigo gidan zance ya qare duk wacce zaayi ayi da safe ai.
Washe gari ta kama Asabar, yanda taga babu wanda ko a fuska ya nuna mata tayi laifi jiyan ya fara daga mata hankali, tana so ta tafi gidan su Halima Daurin aure tana tsoron abinda tambayar hakan ze janyo mata.
Wuraren 11 tana zaune a dakinsu, tsoro take ta fita tsakar gidan su hadu da wani daga cikin Mama ko Abban ga Yunwar data kwana da ita ta hadu da ta safiya tana ta sakudarta. Nuratu Yayarta da take bima ta shiga dakin da farantin qosai da kofin da ta zubo kunun gyada ta nemi gefen gadonta ta zauna tana aikawa da Umaiman harara dan daman tun Asuba data farka ta ganta bata ce mata komai ba sedai idan sun hada ido ta maka mata harara kawai.
Ganin qosan da kunu ya qara wutar rura yunwar da take ji amma yanayin fuskar Yaya Nuratun yasa ta kasa ce mata zata ci, gashi babu motsin kowa a tsakar gidan qannensu duk sun tafi Tahfiz bare ta yafito wani ta saka ya debo mata. Ganinfa tana neman illata kanta dan damanita bame jumurin yubwa bace yasa ta yunqura da niyyar ta roqi yayar tata sega sallamar Qaninta.
Daga bakin qofar yace
" Yaya Umaimah kije inji Abba yana kiranki" ya juya abinsa. Seda cikinta ya bada wani qulululu, ashe ba kyaketa akayi ba jira suke gari ya gama wayewa tas ayi mata taron dangi dan taji shigowar Baba Abdullahi da Yaya Aminu babban Yayansu gidan.
"Yaya Nuratu dan Allah ki bani ko kunun ne nasha wallahi banajin zan iya tafiya ma yunwa nake ji" ta fada a marairaice dan gara ta karya bille ta roqeta, bata sani ba ko baa girka da ita ba kar taje garin diba ta qarayin wani laifin.
Banza Nuratun ta mata seda ta sake roqonta kafin ta turo mata kwanon qosan da kunun da ko rabi bata ci ba dan tana yi tana duba wani texbook nasu na yan medicine tace mata
"Gashinan Mayya se kici ai"
"Idan ni mayyace ke ma ai mayyar ce" Umaimah ta fada cikin qunquni ta ja kayan ta fara ci hannu baka hannu kwarya cikin dan lokaci ta cinye tas ta zura dogon Hijab har qasa ta fita tana nanata La'ilaha illah anta subhanaka innikuntu minazzalimin a zuciyarta harta isa qofar Sitting room din Abbansu.
Ta shiga da sallama kai a qasa kamar ta Allah ta rabe a bakin qofa tana gaishe su ba tare data bari sun hada ido da kowa a cikin su ba. Yaya Aminu ne ya daka mata tsawa yace
"Zaki matso ciki ne kose na zo nan na tattaka ki mara jin magana kawai"
"Barta Aminullahi fada da hargagi baya gyara, nasihar dai ita zaa ci gaba har sanda Allah ze sa ta dena abinda takeyi" Taji Muryar Baba Liman Aminin Abbansu ta katse hargagin da Yaya Aminu ya fara yi mata. Wata nutsuwa taji ta dan saukar mata dan ko ba komai akwai me kareta dan baze bari su mata komai ba amma da ta gama saddaqarwa yau kashinta ya bushe dan daga Yaya Aminun har Baba Abdullahi babu me sauqi, Abba kuwa zuba ido zeyi su caskalata babu abinda ya masa zafi.
"Ina wayarki take?" Baba Abdullahi ya fada cikin zafin nan nasa, seta daga kai ta kalleshi aranta tana cewa
"Toh takunkumi zaa sakamun kenan a hanani fita a karbe mun waya tab aikuwa da sake"
"Ba magana ake miki ba?" Aminu ya sake zaburowa, qasa qasa ta harare shi kafin tace
"Tana cikin gida"
"Kije ki dakkota da duk wani abu da kika san Qasim ya mallaka miki ki kawo nan" Baba Liman ya fada.
"Duk abinda tasan nasa ne ko tsinke ne ta hado" wani mutum da sam bata lura da shi a palour bama ya fada se faman girgiza qafa yake kamar ana yaqi, Se ta dago tana kallon shi dason jin qarin bayani, amma yanayin da tagani akan fuskar Abbanta da irin hararar daya watsa mata tasa ta miqe babu shiri.
Sabuwar Iphone din da Qasim ya siya mata bayan kawo kudin auran su da kwana biyu ta dakko tana jujjuyawa, to me ya faru me zasuyi da wayar? Kuma ai ce mata aka yi ta dakko duk abinda ya mallaka mata kenan ba wai kwace wayar zaayi ba wani abun ne daban.
Tunanin me dame ma Qasim din ya taba siya mata ta shiga yi, shi ba gwanin siyan kaya bane gara dai kayan maqulashe duk zuwa da abinda ze kawo mata. Wardrobe ta bude ta zaro lesina guda biyu daya dinkakke ne dayan baa dinka ba se Atamfa guda daya itama dinkakkiya kayan toshin wannan qaramar sallar da yayi matane, ta saka Atamfar Leshin kuma daman yau tayi niyyar saka shi.
Ragowar tarkacen Jaka da takalmi da mayafai ta debo ta hada cikin babbar Leda, ta kalli turarukan dake kan Mudubin su wanda suma a cikin kayan take ta tabe baki a fili tace
"Bazan hada dasu ba tunda bansan me zaayi ba" Nuratu dai se kallonta take ta zare cajar wayar daga soket ta hada ta sake fita.
A tsakiyar ta dire musu ledar, mutumin dazu ya jata gabansa ya hau duddubawa yana cewa "su kenan dai ko? Ko da yake idan ma da saura zan tambaye shi muji" ya miqe yana sabar ledar Yaya Aminu yayi saurin dakatar dashi da cewa
"Dan jira dan Allah" ya saka hannu ta dauki wayar dake saman ledar ya miqa mata yana cewa
"Budeta ki goge komai na ciki"
Umaimah da tayi mutuwar zaune saboda mamaki ta karbi wayar tana juyawa, tsawa Abba ya daka mata yace
"Zakiyi abinda akace ne ko kin tsaya kina kallon mutane".
Jiki na rawa ta cire password din wayar ta shiga setting nan take tayi resetting nata komai ya goge. Bayan wayar ta bude ta zaro allura ta zare Sim dinta da rigar wayar dan zuwa yanzu ta gama fahintar abinda yake faruwa tana gamawa ta miqa musu wayar.
"Ita rigar wayar fa" Mutumin ya fada da ganinsa irin mara mutunchin nan ne daman, dake gidan tsiwar ya tarar kai tsaye tace masa
"Ai ba shi ya siya mun ba"
Shidai ya kinkimi leda yayi waje suka rakashi da kallon takaici.
"Gara da Allah yasa akayi haka ashe dan qananan mutane ne bamu sani ba gara da Allah ya kiyaye mu hada zuri'a dasu" Baba Abdullahi ya fada.
"Karo na Uku kenan Umaimah karo na Uku, na rantse da girman Allah ku zama sheda,saura wata biyu ta kammala karatun ta, idan har aka kai wannan lokacin bata fitar da tsayayyen miji ba a masallaci zanyi shela duk kuma wanda ya nuna yana son ta zan bashi ita sadaka. Badai juninki rashin mutunchi da rashin jin magana ba toh kici gaba, nidai bazan bari baqin cikin ki ke kadai ya dameni ba tunda haka kika zaba wa rayuwarki shikenan" Abba ya fada cikin kaushin murya
"Aa Alhaji kausasa kalami ba naka bane, Addu'a dai da nasihar ita za'a ci gaba dayi mata amma irin wadannan kalaman su suke sake ta'azzara al'amuran a maimakon a samu sassauci se kaga abu na qara lalace wa. Ke kuma Umaimah ki nutsu, ki sani fa kullum girma kike qarawa ba wai baya kike komawa ba. Me yasa zaace kullum aka tashi kwatancen rashin kirki kece a gaba yanzu jin dadin kine ace an fasa auranki har sau uku cikin abinda be wuci shekara daya da rabi ba?
Toh kar kiga kina samun maneman duniya ta ringa miki kida kina taka rawa. Duk namijin kirkin da ze zo neman auranki aka gaya masa an taba fasawa da wasu har sau uku se ya nemi jin ba'asi kuma bakisan abinda zaa gaya masa ba, ki yiwa Allah ki kama kanki ki san me kikeyi ki qyale zukatan iyayenki su huta" Baba Liman ya saka baki.
Nasiha yaci gaba dayiwa Umaimah dake faman rusa kuka. Bata taba jin baqin cikin fasa auranta da akeyi ba irin na Alqasim dan da gaske take son sa kuma yayi daidai da irin mijin da take mafarkin samu a rayuwarta amma daga faruwar dan wancan abin shine zece ya fasa auranta har ya turo a karbar masa komai nasa da yake gidan su bayan koma menene shine sila ai, akan me ze kula wata mace suna tare bayan yasan Irin HALIN KISHIN ta, sam ba jin Baba Liman din ma take ba harya gama nasihar sa yace ta tashi taje wanda ba haka Yaya Aminu yaso ba, yaso ya mammaketa dan tun jiya Mama ta gaya masa fitar da tayi da sanda ta dawo yaso amma ze bita cikin gidan seya ci ubanta wallahi.
Kuka wiwi ta fita tanayi, sam ta manta da tasu da Mama kai tsaye dakin ta ta wuce ta zube tana ci gana da rusa kuka kai kace mutuwa aka mata. Mama dake sallar walaha ta sallame tace
"Idanna idar na tarar dake a dakinnan Umaimah sena lahira ya fiki jin dadi ki tashi ki fita karki qara mun baqin ciki akan wanda nake ciki"
"Ai wallahi ko kashe ni zakiyi babu inda zanje, gurin wa zanje nayi kuka idan ba dakin uwata ba" Umaimah da har sannan bakinta be mutu ba ta fada tana ci gaba da rusa kukan ,kwafa Maman tayi ta tayar da sallarta, harta idar kuwa tana zaune bata tashin ba tayi kuka kana ganinta kasan daga qasan ranta take kukan nan.
"Mama ya zanyi, kullum ina roqon Allah daya ragemun zafin kishi, wallahi Mama ji nakeyi kamar zuciyata ta kama da wuta idan na ganshi da wata macen, me yasa shi ya kasa kiyaye wa ko ze kula mata me yasa zeyi akan ido na?" Ta fada cikin tsananin kuka.
"Dan ubanki keba musulma bace? Duk girman abinda kike ji idan kika nemi taimakon Allah zakiji sauqin sa, amma seki biyewa zuciya ki zama kamar mahaukaciya kiyi abinda ranko ya raya miki se saga baya kizo kina Nadama toh kici gaba Nadama kuwa yanzu kika daura dambar yinta. Ina jiye miki tsoron gaba Umaimah idan baki canza Hali ba wata rana sekin tsinewa wannan mummunan HALIN KISHIN naki" Mama ta fada tana ficewa daga dakin, ga tausayin Umaimah ga takaicinta.
Ranar haka ta wuni zur tana aikin kuka, idan ta tuna wai fa Qasim ya fasa auranta se tayji duniyar ta mata zafi ita yanzu ina zata kuma samun kamar sa Dan gayu daya iya daukar wanka ga kalamai masu sanyaya zuciya, duk idanta hau zafin ta yasan yanda yake bi ya lallabata, gashi ya mata alqawarin idan ya aureta har mutuwa ita kadai ce matarsa har rabtsuwa ya mata da Alqur'ani amma shine daga dan wannan abin zece ya fasa auranta.
Tunawa tayi da Ibrahim saurayinta na farko da aka yi musu baiko tun tana Aji biyar na secondary, shima fa akan kawai ta mari wata yar iskar Cousin dinsa da take sonsa, suka tareta a islamiyya ita da qawayenta kowa ta mata mari biyu tana dawowa gida da daddare se ji tayi wai Babansa yace baze aureta ba.
Bayan shi se Lagin, koda yake shi daman tafiyar su bazata zo daya ba dan namamajone, daya rabu da tarin tarkacen yan matansa ya gwammace ya fasa auranta bayan har an saka musu rana wata shida yace ya fasa yanzu ga Qasim, a qarshen watannan fa suke zancen saka rana tunda watanni biyu suka rage mata ta kammala HND dinta.
Sun gama tsara komai daidai da gidan da zata zauna ya kaita ta gani wanda aka tsara shi iya tsaruwa kadan ya rage a kammala, kullum cikin tura masa irin kayan da take so ya saka mata a lefe take shi kuwa yana lafta kudi yana siya yanzu shikenan wata banza zeje ya kaiwa?
Abinda ya faru yasa ta manta da batun zuwa yinin Halima gashi babu waya bare su kirata, washe gari da take Lahadi ma a gida ta wuni cur ba um babi um um fuska duk ta kode saboda kuka. Mutanen gidan kuwa babu wanda ya shiga sabgarta gara ma Anty ita ce me leqata har ta kai mata abinci wanda a gurin Umaimah ba gwaninta take mata ba dan data fita zata rakata da harara.
Ranar Monday tana da Test dan haka dole ta shirya fita makaranta dukda babu abinda ta karanta saboda wancan satin duk sun qarar dashi a yawon shirin biki, Lahadi da tayi niyyar zama a gida tayi karatun kuma ga yanda abubuwa suka kasance.
A tsakar gida ta tarar da Abbansu yana sallamar Anty dake da girki ranar, kallo daya ya mata ya ci gaba da magana da Antyn ko gaisuwar da tayi masa be amsa ba dan tun wacceb ranar ya dena Amsa gaisuwarta haka babu sakin fuska ko yaushe suka hadu harara ce take rabasu.
Gaba tayi da niyyar fita ya daka mata tsawa yana tambayarta ina zataje, se ta lumshe Idanunta da suka kawo hawaye ta juyo murya na rawa tace
"Makaranta zanje ina da Test yau".
Be tanka mata ba haka itama bata motsa daga inda take ba harya yi sallama da Anty kafin kamar baya so yace mata " muje" yayi gaba ta bishi a baya.
A motarsa ya kaita har cikin makarantar, tafiyar kurame sukayi dan babu me cewa wani qala se sheshsheqar Kukanta dake tashia hankali duk a sonta na tausayinta yayi tasiri azuciyar Abban saboda sam baya so yagansu a damuwa amma kamar dutse ko ajikinsa.
"Qarfe nawa zaku tashi" ya tambayeta yana miqa mata naira dubu, ta karba tace
"Qarfe sha biyu ne test din, se kuma ina da practical 2-4pm"
"Karki kuskura na rigaki komawa gida, idan kuma ba haka ba zamu gauraya" ya fada a kausashe kafin yaja motar ya fita.
Kujera ta samu a gurin ta zauna kawai ta fasa kuka, ita ya zatayi? Ko tausayin abinda ya sameta bazasuji ba kuma se abi a ringa tsangwamarta ana daure mata fuska.
A gurin Su Fauziyya da Nabila suka sameta dan daman nan suka saba zama su jira junansu
"Umaimah lafiya zaki zauna kina rusa kuka kamar wadda akawa mutuwa jifa har kin fara tarawa kanki mutane ana kallonki" Nabila ta fada tana kama hannunta
"Toh ina ruwan wani dani kowa yaji da damuwar sa mana an san abinda yake damuna ne da zaa zo ana kallo na" ta fada cikin kukan.
"Kinga tashi mu bar nan, ga Malam Tsalha guntsi fesa can ta taho tun kafin ta debi wani sharrin taje tana yayaki a gari" Fauziyya ta fada ganin wata course mate dinsu Jamila ta nufo gurin, irin masu dan banzan gulma da sa idon nan ce, zance kuwa na kowa a makarantar nan kaji shi a bakinta shi yasa suke ce mata Malam Tsalha.
A hanya suka hadu da Rumasa'u da shigowarta kenan suka rankaya cafteria suka samu guri can baya suka zauna anan take basu labarin fasa auranta da Qasim yayi.
"Amma gayen nan dan yarfi ne,yanzu akan dan abin nan shine zece ya fasa auranki? koda yake kansa yayiwa dan dai nasan baze taba samun hadaddiyar baby kamar ki ba wallahi dan wahala shi yayi Asara. Seki share hawayenki da kyanki da quruciyarki bazaki rasa mijin aure ba. Kuma duk mutumin ma daya kasa haquri da halinka tun kafin ya aure ka ta yaya zaku zauna dashi bayan aure ki manta dashi kawai" Nabila ta fada.
"Amma fa Umaimah kema da laifinki ko nace laifinki ma yafi yawa, kishi ai ba hauka bane amma ke idan naki ya tashi rufe miki ido yake kiyi tayin abu kamar wata me tabin hankali. Jifa yarfin da kika masa ranar a gaban mutane dan Allah, be yi fushi ba ya dauke ki har mukaje gida kina zaginsa shi da iyayensa kika sauka kika kuma qara masa, ina ke kika ce idan ya haifu cikin uwar sa ya je ya auri Siyaman ke ya qyale ki? Gashi kuwa ya nuna miki ya haifu saura ki jira ganin IV auran sa da ita nan gaba kadan" Ruma ta fada iya bakin gaskiyar ta.
"Ai ke daman kina baqin ciki da duk wani farin cikin Umaimah a rayuwa ni na dade da sanin kina baqin cikin tarayyarta da Qasim waya sani ma ko da sa hannunki a ciki? Toh Umaimah dai nan gani nan bari duk mugun abin mutum sedai ya koma kansa saboda ke kin rasa mashinshini shiyasa kike farin ciki dan ta rasa nata" Fauziyya ta hayayyaqo mata, seta miqe tsaye itama tana kallo ta tace
"Dani dake babu meyiwa wani gorin ya rasa mashinshini dan gara ni ana gani ana yabawa ke fa? Cusa kai kike amma mazan yi suke kamar basu san da wanzuwarki ba. Ita gaskiya daya ce daga qinta kuma se fada, the earlier da kika gane laifinki kika gyara the better. Amma idan kinga zaki ci gaba da zama da maqaryata suna dora ki a keken bera shikenan, nidai har a gurin Allah na fita dan na fada miki gaskiya ruwanki ki gyara ruwanki kiqi amma Umaimah babu Namijin da ze aure ki da wannan mugun HALIN KISHIN naki" Rumasa'u ta qara fada idon ta akan Umaimah da tayi shiru.
"Kut baki kike mata na karta auru? Toh wallahi tun wuri Umaimah kisan abinyi dan bamu san irin bakin ta ba, Mune shaida" Nabila ta fada cikin son qara kambama abun.
"Ke kika hadu da ita rana tsaka dab haka ke zamu bincika muji ko kina da mugun baki amma ni ki tambayeta ta sanni ta san asalina, kuma duk wanda ze so Umaimah a cikin ku baya nane dan ni son tsakani da Allah nake mata ina kuma so ta gyaru ta rabauta ba irin naku na son zuciya da sake ingizata zuwa ga Halaka ba" Ruman ta fada a fusace kafin ta juya ta bar gurin, a ranta ta qudurce ko Su ne kadai suka rage da zatayi qawance dasu a rayuwa ta haqura, ita Nabila zata kira Mayya?
Umaimah kuwa zama sukayi a gurin Fauziyya da Nabila na sake yi mata famfo da gaya mata kalam da suke fasa mata kai take ganin takai inda bata kai ba. Basu bar gurin ba seda lokacin shigar su test yayi suka tabbatar da sunyi brain washing nata ta hanyar nuna mata daidai abinda take aikatawa da kuma cewar duk wanda ya rabu da ita shi yayi Asara ba ita ba.
Haka suka shiga test din babu wadda ta karanta komai a cikinsu, daman ita ce me qoqarin da take goyasu to yau itama batayi karatun ba gashi anyi fada da Ruma bare ta basu Amsa. Da suka fito daga practical ma sun so su jata wai suje gidan Halima dan tun safen ta ke musu waya suje ita bata zo yin test din ba se taqi saboda tuna gargadin Abba na dazu, haka suka rabu a get ta kama hanyar gida ita kadai dan Ruma da gaske ta dauki fushi ko sashin da suke bata sake kallo ba.
*DAGA ALQALAMIN MARYAM FAROUK*
*(UMMU-MAHEER)*
*MARUBUCIYAR*
*WATA KISHIYAR🥰👹 (ALKHAIRI CE KO SHARRI)*
*RUBUTACCIYAR QADDARAH AND NOW*
*HALIN KISHI*
*HALIN KISHI LITTAFIN KUDI NE NAIRA 500*
*GA DUK ME SO ZE TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SE A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
Free page 3
Sosai take jin ta a takure saboda rashin waya, idan taje makaranta ta dawo sedai ta zauna shiru in ta gaji ta dauki littattafanta ta duba dan har yanzu babu me shiga sabgarta a gidan se Anty ita kuma ba kulata take ba.
Ita bata ga abin da zesa gaba daya su wani dauke mata ba bayan ita abun jaje ya sama kamata yayi ataru a tayata amma duk an tsangwameta hatta da Yayyanta da suke gidan Aure kowa tazo harara da zagi ne yake raba su a cikin wannan yana yi taci sati biyu, sauqin ta ma bata zaman gidan sosai saboda gabatowar jarabawa da zasu fara ta qarshe kusan idan ta fita makaranta takwas se biyar take dawowa.
Tana da buqatar waya saboda harkar karatu wani abun softcopy ne zaa bayar dole seda wayar ko system hakan yasa ta niyyaci tunkarar Abban su da zancen siya mata waya.
Bayan sallar Isha ta same shi a palour sa, sam ta manta da Mama ce da girki seda tayi sallama ta shiga ta tarar da ita tana hadawa Abban shayi, kamar ta juya amma ba hali tunda sun tigada sun ganta haka ta nemi guri ta zauna ta shiga gaishe su kai a qasa.
"Ya akayi Hajia Umai" Abba ya fada cikin sakin fuska ba kamar yanda yake mata tsahon kwanakin ba hakan ya bata kwarin guiwa ta gyara zama tana cewa
"Daman Abba saura sati uku mu fara jarabawa ne, kuma handouts da yawa softcopy ake bamu, bayan nan wani lokacin ina so na danyi browsing babu dama tunda bani da waya"
"Yanzu me kike buqata" Abban ya tambayeta, seda ta kalli Mama da tayi kamar babu ita a gurin kafin tace
"Waya nake so dan Allah Abba ko taka ce ka ringa bani aro in zan duba abu"
"Tawa kuma Aa salon kiyimun jagwalgwalo, bari dai zanyiwa Yayan ku magana se a samo miki ko qarama ce" Abban ya sake fada. Da alama yau yana cikin yanayi me dadi, kamar tace Aa karya saka Yaya Aminu dan tasan da wuya idanze bari a bata sedaita kanne tayi masa godiya kafin