Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
mafita akan yadda zasu b'illowa al'amarin.... Suka yi masa sallama... Ta hanyan kasuwa yabi dasu,da mamaki KHALEEL yake binsa da kallo,sai dai bai kai ga tambayarsa ba yaga ya fice... Cikin kasuwan ya shiga da tambaya ya samu store en,tun da akayi maganan photo zuciyarsa ke ayyana masa abubuwa da dama,shi ya sama yanzun ba tare da yayi shawara da kowa ba ya shiga siyan kayan zane abun mamaki kamar wani Artist haka ya siya kayan,yaran store en suka bishi da kaya fal hannunsu... Cikin ZUHRA ko KHALEEL babu wanda yasan me yake shiryawa kamar yadda babu wanda yaga kayan da ya siyo aka zuba masa su a booth... Ya sallamesu suka kama hanyan komawa store,shi kuma ya shiga motor en yayi mata key zuwa gidan su KHALEEL... 《《》》 Tun safe kowa cikin su biyu BABA ZUWAIRA da kuma KHUBRA suka kama hanyar sana'arsu... 'Bangaren KHUBRA babu wani damuwa da yake a ranta wanda har zai dinga damunta a wannan lokaci,burinta bai wuce ganin ta kafa kanta a rayuwa ba,shi yasa ta jajirce dan ganin rayuwarta ta inganta.. Can k'asan ramin ta gangara,gurin babu mutane sosai sai y'an tsirari da suke d'iban ruwa suma,har ta gama tana shirin barin gurin wata matashiya ta matso kusa da ita fuskanrta a sake,da sallama a bakinta dai² lokacin KHUBRA tana niyyar haurawa sama "Sannu baiwar Allah" "Yawwa sannu" KHUBRA tana kallonta da mamaki ganin babu wanda ta sani a garin.. "Suna na HAFSAT ina zaune cikin garin ZAKIRAI,babana shi ne SARKIN KASUWA" "Allah sarki na gode" KHUBRA ta fad'a tana d'an murmushi.. "Kefa baki fad'amin naki sunan ba" "Suna na KHUBRA" "Amma ke bak'uwa ce a garin nan ko?naga ban san fuskarki ba" "Ehhh!haka ne,ban jima da zuwa garin nanba" "Allah sarki na gode sosai,sai mun sake had'uwa" Kowacce ta kama hanyanta,da yake ita KHUBRA ta riga ta gama abunda ya kawota gurin,ita kuma HAFSAT zuwanta kenan shi yasa tafiyan nasu ya bambanta...... 《《》》 "Oyoyo TAKWARA yau kam ina da manyan bak'i,yaushe rabona da ganin k'afarki a gidan nan,gaishe nima da kuke zuwa kun daina yanzu, ince ko HAJIYA MURJA ta hanaku zuwa??" "Wallahi UMMI abunda na fad'a kenan lokacin da KHALEED ya sanarmin wai nan zasu yini" Harara BB ya sakar masa ba tare da yayi magana ba... "Ai kuwa dai gaskiya KHALEED ya fad'a,kai dan gidanku idan kaje a matsayin wa kake zuwa??" "Aaaaa!UMMI nifa na fishi zuwa kinga kuwa dole na zama d'an gida,shi kuma idan ya zo nan bak'o ne" "A'a ni d'ana ba bak'o bane a gurina,kai ne dai ka maida minshi bak'o" "Yawwa UMMI gara da kika fad'a masa dama na fad'a masa ni ba bak'o bane a gurinki" "K'warai kuwa ka wuce matsayin bak'o a gurina,bama kaiba ko da wani ka kawo gidan nan wanda ban saniba ai bazan kira shi da bak'o ba,saboda matsayinsa ya wuce haka" "Lallai yau zuwanka yasa UMMI ta mai dani gefe kun had'emin head kai da UMMI,sauk'i d'aya Allah yaso nima ga k'anwata da yau ina jin sai nayi kuka" Yanda yake maganar ya bawa kowa dariya cikin parlor.... Yini guda sun k'auracewa gidan MAMA,sai dare suka yi niyyan komawa gida,turaruka masu kyau da tsada UMMI ta bama ZUHRA,suka rako su har bakin mota,sai da suka ga fitarsu daga gidan sannan suka juya.... 《《》》 Tun bayan fitarsu ZUHRA daga gida MAMA ta rasa abunyi,kallon y'ar lelenta tayi fuskarta duk ta soma tasawa saboda dukan da ZUHRA tayi mata... "Kin ga irin abunda nake fad'a miki ai,duk lokacin da kika takali yarinyar nan da fad'a sai nayi miki magana,daga yau ai ba sai na sake ce miki komaiba,gobema kya k'ara" "To ni MAMA me nace mata bayan itace bata da gaskiya dan kawai nayi magana shi ne ta zage nifa" "Ni dai ai bance miki komaiba,amma dai kam wata rana zaki ci ubanki a hannun YAYANKU,kinsan ba a tab'a ZUHRA a gabansa" Tura baki gaba ASHNA ta shiga yi dama gashi ya kumbure,abun dai sai wanda ya gani.... Yinin ranan MAMA tana zuba idon ganin ta inda su ZUHRA zasu shigo gidan amma shiru kake ji wai "MALAM YA CI SHIRWA"..... *8:40* MAMA ce cikin parlor sai kaiwa da kawowa take,abun duniya duk yayi mata yawa,ita kad'ai sai surutai take,ga wayan a hannunta amma ta kasa kiran KHALEED bare ta tambaye shi ina suka tafi,ganin ta rasa mafita yasa ta nemi guri tana shirin zama,horn data jiyo shi ya bata daman sake mik'ewa ta nufi hanyan fita daga parlorn.... A haraban gidan suka had'u lokacin yana k'ok'arin fitowa daga mota... "Kai daga ina kuke tun safe da kuka fita sai yanzu" Babu wanda yayi magana cikin su biyu,suka kama hanyan parlor,binsu ta shiga yi har cikin parlorn yanayin fuskar BB ya hanata sake yin magana dan ko yanda ya had'e fuskansa za kayi tunanin bai tab'a sanin wani abu da ya danganci dariya ba,wannan yanayin da ta gani shi yasa ta kasa sake yin magana.... Ita ko ZUHRA suna shigowa ta kalli BB da ya zauna tana fad'in "YAYANAH sai da safe" Kansa ya kad'a mata ba tare da yayi magana ba... MAMA sai kallonsa take amma ta kasa magana kan dole ta jaa bakinta tayi shiru,dan tana da tabbacin ko tayi maganar ba kulata zaiyi ba,tunda y'an miskilancin suka motsa.... Zaman gurin ne ya isheta haka ta tashi ba tare da ta samu abunda take nema ba,tana barin gurin shima BB ya mik'e da niyyar barin gurin har ya d'auka hanyan bed room ensa,ko me ya tuna kuma ya dawo,fita yayi har parking lot,booth ya bud'e duk kayan dake ciki ya fito da,d'iban kayan yayi a hankali ya shiga dasu bed room en... Fito dasu ya shiga yi d'aya bayan d'aya ya baje komai,k'aton allon ya kafe a tsakiyan bedroom en nasa yanda ko da mutum ya tashi daga bacci da shi zai fara arba... Toilet ya shiga ya sakarma kansa ruwa,ya jima k'asan shower kafin ya fito,ba tare da ya b'atawa kansa lokaci ba ya zira farin singlet da boxers,sai sprays da perfume's da ya bajewa jikinsa kamar ba gobe... Bacci ya k'auracewa idanunsa ,dai² lokacin wall clock en d'akin ya nuna 10:30pm.... Idanunsa ya rufe yana tuna wasu moments nata,a hankali ya bud'e idanunsa masu haske ya sauke su kan allon da ya shimfid'a white card board paper... Sake rufe idanunsa yayi bayan ya d'auki alk'alamin,cikin nutsuwa ya dad'a bud'e su,a hankali ya shiga zane saman paper en,abun gwanin sha'awa haka yake sarrafa hannunsa da yake d'auke da alk'alamin... Bayan shud'ewar wani lokaci ya dakata yana k'arewa zanen dake kan board en kallo,dai² lokacin idanunsa sun gama k'ank'ancewa kallon zanen dake jikin paper yayi,ya saki wani k'ayataccen murmushi,shi kad'ai yake surutansa,bed ya nufa bayan ya gama sumbatan picture en ya kwanta,dai² lokacin 12:00am... Bacci mai nauyi ya d'auke shi cike da mafarkin KHUBRA...... Da safe misalin k'arfe 11:00am ya fito cikin shiri hannunsa rik'e da paper ya fito sai k'amshi yake bazawa,har ya fita babu da wanda ya had'u haka ya fice daga gidan... Direct police station ya wuce,sergent da suke kan counter suna ganinsa suka shiga gaidashi saboda sun ganeshi office en D.P.O suka raka shi,dan sun san basa rakiyar banza... After sun gaisa da D.P.O ya shaida masa abun da ya kawo shi,take kuwa ya buk'a ci ganin pic en yarinyar da ya fad'a masa ya zo da shi,babu b'ata lokaci ya mik'a masa... Duk abunda ya kamata shi D.P.O suka tattauna akan yadda za a yad'a photon cikin garin Kanon dabo... BB ya masa godiya ya fito dan tafiya gida,wanda k'arshe ba shi ya bar station enba sai da D.P.O ya had'a shi da y'an sandan da zasu yi masa aiki suka gaisa,sannan ya wuce..... 《《》》 Kwanaki sun ci gaba da gangarawa b'angaren KHUBRA rayuwarta cikin nutsuwa babu wani abu dake damunta rayuwarta take babu takurawa... Kulawan da BABA ZUWAIRA ke bata ko lokacin da take gida hannun iyayenta bata samu irinta ba,shi yasa ta saki jikinta sosai babu damuwan komai cikin ranta.... Duk lokacin da BABA ZUWAIRA ta kalli KHUBRA tana tausaya mata irin rayuwar da take ciki,duk da ta kafu akan sana'arta ta *GARUWA* wanda yanzun ta kai duk line da zata gifta cikin garin na ZAKIRAI an santa,duk inda ta gifta za kaji ana fad'in *KHUBRA Y'AR GARUWA*,wannan d'aukaka da ta samu kan sana'arta yana mata dad'i da yadda mutane ke yabon halayenta cikin garin.... Wannan kenan...... *~KEEP FOLLOWING........~* *~TEAM KHUBRA.~* *_REAL SMASHER._* 💠💠💠💠💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *23/ʝųŋɛ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* _AS'ALULLAHAL AZIIYM RABBAL ARSHIL AZIIYM AN-YASHFIYAKI *7_ _GWS duarling sis @CWEET HUBBEEY._ *~________________________~* _*AUNTY G & AUNTY U* suna matuk'ar godiya da sadaukarwarki garesu gurin taya su murnan zagayowar ranar haihuwansu,fatan Allah ya k'ara zumunci da k'aunar juna.....Ameen..._ _@CWEET HULBATEEY._ *~________________________~* *DEVOTED TO:* _BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_ *BESTOWED TO:* _MURJA SALIS (NA'IKKE)._ *AND* _FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._ *3⃣2⃣* 🇹un bayan zuwansa police station lokacin da ya kai photon da aka buk'ata,yake jiran jin sakamakon binciken daga wajen D.P.O amma shiru,har ta kai ga yau tsahon kwanaki bak'wai amma shiru kake ji.... _WAI MALAM YA CI SHIRWA...._ B'angaren Police kuwa da aka had'a BB dasu tuni suka fara aikinsu ba tare da sanin HAJIYA MURJA ko HAJIYA LAURA ba,dan ko kowacce akwai masu kula da al'amuranta duk zirga² da suke a idon hukuma suke aiwatar da hakan... Shirun da BB yaji kwana biyu babu labari ne yasa shi kiran D.P.O yana neman k'arin bayani game da case en b'atan KHUBRA.... Cikin yanayin sarewa ya shiga kiran line en D.P.O,wanda cikin nasara ya d'auka ba tare da b'ata lokaci ba... "Hello!yallab'ai barka da rana,ya aiki?" Daga gefen D.P.O aka amsa masa "Lafiya,Alhamdulillah!" "Yallab'ai dama kira nayi na maka tuni naji kwana biyu shiru babu wani k'arin haske kan b'atan yarinyar nan" Daga gefen D.P.O aka amsa da "Ehhh!toh gaskiya nima dai abunda ya jima yana bani mamaki game da wannan case en shi ne,tun bayan da ka kawo photo da muka buk'ata aka watsa shi a kafafen sadarwa amma shiru har yanzun babu wani bayani da muka samu daga gurin al'umma,munyi nema munyi cigiya amma shiru har yanzun babu wani ci gaba,ina ganin dai kam sai mun k'ara hak'uri,mun kuma k'arawa abun lokaci muga yadda Allah zai yi ikonsa.. Amma har yanzun muna kan bincike da izinin Allah zamu sameta"..... Dogon ajiyar zuciya BB ya sauke kafin cikin kasala ya furta "Allah ya bayyana ta" D.P.O ya amsa da "Ameen" Sannan ya d'ora da fad'in "Ina fatan dai yaran da muka turo suna kan aiki,babu wata matsala da ake fuskanta" "Ehhh!Yallab'ai babu wata matsala,aikinsu yana tafiya yadda ya kamata babu wata matsala" "Ok! Babu matsala Allah ya bayyanata,amma a k'ara hak'uri" "In sha Allah yallab'ai,na gode sosai" Sukayi sallama,bayan BB ya ajiye phone en ya jima yana nazari kan wannan case en,shi kad'ai kuma ya mik'e ya zari car keys ensa ya fice... 《《》》 Tsaye take cikin super market en *JIFATU STORE* dai² b'arin y'an rugs tana dubawa... Wayanta ne yayi k'ara a hankali ta bud'e jakarta ta fito da ita.. Rashin gaskiya ne yasa ta juyawa tana kallon yanayin gurin,babu kowa a arean da take shi yasa ta d'auki kiran ganin sunan dake lilo kan wayan... "Hello HAJIYA MURJA kiyi hak'uri bana gida ne,shi yasa ban d'auki kirankiba,amma ki bari na k'arasa gida,yanzun ina *JIFATU* naje siyayya" Daga gefen da aka kira cikin fad'a² ake magana wanda har wayan me magana ta farko tana amsawa k'asa²,ta yadda idan akwai wani a kusa zai iya jiyo abunda ake fad'a... "Haba HAJIYA LAURA tun yaushe nake kiranki kink'i amsawa,idan abun nan ba mai yiwuwa bane yaci ace kin sanar dani,amma kin barni kara zube... Waima dan Allah wasu sha³n kika sa suka yi aikin nan?" "Haba HAJIYA MURJA nafa fad'a miki bana gida,kiyi hak'uri zan kiraki idan naje gida" "Kinga HAJIYA LAURA dakata bana son jin wannan maganar daga bakinki kawai idan zaki tsaya muyi magana to idan kuma ba hakaba,wallahi zan zare hannuna a ciki duk lokacin da wannan lamarin ya kwab'e kada kiyi kuka da ni,kiyi kuka da kanki... Kina da damar aikata duk abunda kika so,zab'i ya rage ga mai shiga rijiya.... Ko ki bani had'in kai muyi magana yanzun ko kuma ki kashe,duk lokacin da kikaga dama kya neme ni".... Tana kaiwa nan tayi shiru tana sauraren jin me HAJIYA LAURA zata ce... A gefen HAJIYA LAURA kuwa jin furucin na k'awar tata ya so ya bata tsoro amma ta dake tare da cizon leb'enta na k'asa,sai da tayi gefe da wayan sannan ta saki k'wafa.... "Babu damuwa muyi maganar yanzun" Murmushin mugunta HAJIYA MURJA tayi sannan ta fara magana "Ai ke nake sauraro naji baki cemin komai game da tambayan da nayi miki ba " "Wane tambaya kenan?" "Ce miki nayi wane sha³i ne suka yi wannan aikin?ina nufin wane gidadawa kika sa suka zo gidana ranan da aka sace yarinyar nan?" Maganar HAJIYA MURJA ba k'aramin b'atawa HAJIYA LAURA rai tayi ba,haka ta danne tana bata amsa.. "Wasu yara ne da sukemin aiki,wani abu ya faru ne?" "A'a kawai dai ina son sanar dake ne duk inda suke idan har suna cikin garin KANO to suyi gaggawar barinsa domin kuwa yaron nan ya tsananta bincike... Sannan abu na gaba idan har sukayi abunda ya janyo aka kamasu to ki tabbatar musu da kada su sake suna na ya fito a cikin bakunansu... Kuskuren dake cikin ambaton suna na dai² yake da rasa rai,na fad'a miki saboda haka ya rage naki,ko ki jaa musu kunne ko ki k'yalesu su aikata hakan" Cikin sanyin jiki HAJIYA LAURA ta amsa,amma cikin zuciyarta cike take da tarin k'unci... "Sannan abu na gaba ina so ki kula da duk wani al'amura naki,idanuna suna kanki,kuskure d'aya kikayi zaki ki hannun hukuma".... Ita dai HAJIYA LAURA bata iya cewa komaiba,baya ga zuciyanta dake tafasa,wanda idan ka kalleta zaka iya gane tsananin b'acin rai da take ciki a kan fuskanya..... Bayan sunyi sallama ne HAJIYA LAURA ta fara magana cikin b'acin rai ta furta "Lallai HAJIYA MURJA wato ni take son mai dawa bagidajiya,to wallahi sai na koya miki hankali,zaki san dani kike zanc en".... Cikin b'acin rai ta fice daga gurin ba tare da ta siya abunda ya kawota ba,ta kama hanyan komawa gida.... Zuciyarta tayi k'unci da maganganun da AMINIYAR tata ta gama yab'a mata,ita kad'ai take k'wafa idan ta tuna abun duniya duk ya isheta...... 《《》》 "Hello!sir" Aka ambata daga b'angaren mai kiran,wanda yake magana k'asa²,da alama kuma akwai wani babban al'amari a tare da shi da yake son sanarwa... Bayan an amsa masa ya shiga koro jawabi... "Yallab'ai akwai wata mata daga cikin assignment da aka bamu, yau nabi bayan matar zuwa *JIFATU STORE* dake kan hanyar *OBASANJO ROAD*... Tabbas yallab'ai akwai wani al'amari a tare da matar,kuma daga dukkan alamu matar bata da gaskiya duba da yanayin yadda take magana a waya,da kuma yanayin data fito daga *STORE* en..." "Cikin wane irin yanayi kaga ta fito?" "Yallab'ai yanayin da ta fito yana nuna tana cikin tashin hankali" "Shin akwai wani abu da ya faru? ina nufin wani abu ya faru da ita bayan shigarta gurin siyayyar?" "Ehhh!yallab'ai bayan shigarta da kamar minti uku (3) naga ta d'auko waya a cikin jakarta ta hannu,to yallab'ai bayan ta amsa kiran wayan ne naga hankalinta ya tashi ta fito"... "Lokacin da take wayan kana ina kai en?" "Yallab'ai ina cikin gurin da ta shiga" "Ok!ina fatan babu wanda ya kula da binta da kake" Cike da ladabi Sergeant en ya furta "A'a yallab'ai babu wanda ya gani" "Da kyau aikinka yana kyau,abunda nake so da kai kaci gaba da bibiyarta,har mu tabbatar da gaskiyan abunda muke hasashe. Allah ya taimaka"... Daga haka sukayi hanging wayan... Tunani BB ya tsaya bayan ya gama answering call en daga sergeant en,akan hanyarsa ta zuwa gidansu KHALEEL... Da kyar ya katse abunda yake yama motan key zuwa gida,dan ji yayi bazai iya zuwa ba,hakan ne yasa shi canja shawara ya koma inda ya fito.... 《《》》 Kwanaki sun ci gaba da giftawa kamar ana ingizasu.... Ta b'angaren binciken neman da akewa KHUBRA abu ya faskara dan ko zuwa wannan lokaci har an gama fidda rai,anyi cigiyan anyi neman amma shiru kake ji uwa an shuka dusa,wannan dalilin yasa BB yanke shawaran sawa a tsananta yin rok'on Allah game da matsalar duk da kuwa dama anayi amma yana da burin na wannan lokacin yafi na baya... Haka kuwa akayi ko da ya tuntub'i KHALEEL bai yi k'asa a guiwaba ya amsa masa da fad'in "Tabbas wannan ma shawara ce ya kamata muyi hakan,Allah dai ya bayyanata idan muna da rabon sake ganinta" Suka amsa da amin cike da jimami.... 《《》》 Zaune take cikin parlor ta hard'e k'afafunta d'aya akan d'aya,ta cije leb'e ta gama cika tamkar zata fashe... Iska ta furzar mai d'umi tare da fizgo wayarta tana latsawa cikin fusata take magana.. "Haba BIGGY sau nawa zan sanar maka da ina nemanka,ko kuwa so kake sai raina ya gama yin duhu kafin ka zo?" 'Dan dakatawa tayi tana sauraren me zai fad'a "To amma me yasa baka sanarmin da bakwa garin nanba ka b'oye??" "Tuba nake ranki ya dad'e amin aikin gafara" "Shi kenan amma magana nake son yi da kai mai matuk'ar muhimmanci,wanda bana son kowa ya sani,bayan ni da kai sai kuma yaranka,ka dai fuskanci me nake nufi ko?" "Ehhh!HAJIYA amma idan babu damuwa kiyi maganarki yanzun kawai saboda bana son zuwa gidanki saboda tsaro... Idan kuma wani aiki nema kiyi min bayanin yadda kike so ya kasance,za ayi miki duk abunda kike buk'ata"... Jin furucin BIGGY ne yasa ta sakin murmushin mugunta kafin ta fara magana "Toh! shi kenan,amma da san samu ne da ka zo gida ka same ni idan ya so sai muyi maganar,amma tunda ka sanarmin uzurinka na karb'a hakanma babu damuwa".... Sai da tayi shiru na wasu y'an lokuta sannan ta soma magana "Ka san me nake so da kai BIGGY?" Daga gefensa ya amsa mata da fad'in "A'a HAJJAJU" "Ina son duk inda kuke ku je gidan dana saku aiki kwanakin baya,akwai wata yarinya da nake son ku satomin,amma idan kun sace ta kuyi nesa da ita bana son kuma a samu matsala kan wannan aiki,ina son kafin ku satota kuyi bincike sannan kuma ku tabbatar da babu wanda ya ganku... Zan turo maka da photon yarinyar da zaku sato sannan ku tabbatar idan kun saceta kun sanar da ni a lokacin bayan kun d'aukota... Ina fatan ka fuskance ni ko?ni kuma zanyi maka bayanin abunda zakuyi bayan nan,da fatan baka manta kwatancen gidanba"... Dariya BIGGY yayi mai isarsa kafin yayi magana "Amma HAJIYA ba dai yarinyar da muka sace ce ta dawo ba ko?" "A'a wannan daban da waccan,wannan da nake son ku sato ina son 'DAUKAR FANSA ne akan mahaifiyarta,saboda ta nunamin ban iyaba shi yasa nake son ajiye mata DARASIN RAYUWA".... "An gama ranki ya dad'e kamar anyi an gama wannan aikin,za muyi duk yadda kikace" Sai da suka gama kitsa duk wata mugunta sannan sukayi sallama... Zuciyar HAJIYA LAURA fal da farin cikin wannan al'amari tana zaune tana kad'a k'afa sai sakin murmushin mugunta take....... _AYI DAI MU GANI...._ 《《》》 *3 MONTH LEAP.* KHUBRA ce rik'e da kuran ruwanta na sana'ar *GARUWA* k'afarta sanye cikin takalmin *FILLO SHOES* daga saman kanta ko ta kifa *HAT* na gargajiya,takalmin duk ya sha d'inki saboda gajiya da yayi.. Wani yaro ne ya gifo a guje daga wani k'aramin gida yana fad'in *"Y'AR GARUWA* ki kawo ruwa gidanmu za a siya" A hanhali taja hulan dake kanta baya kad'an tana kallonsa,fuskanta da d'an fara'a duk da yadda tayi duhu fatarta duk tayi wani iri abun tausayi... "To amma zo nan" Ta umarci yaron da yake shirin komawa a guje,jin ta kira shi ne ya matso.. Kunnensa ta d'an kama a hankali tana fad'in "Suna nane baka saniba ka kirani da *"Y'AR GARUWA"* ko kuwa iskanci ne yasa kayi hakan?" "A'a na sani" Ya fad'a yana dafe gefen fuskarsa ta side en da ta rik'e kunnensa.... "Daga yau naji ka sake fad'in wannan sunan sai na mareka,kaji ni ko?" Da sauri yaron ya gyad'a kansa alamar yaji kuma ya bi... "Yawwa k'anina,maza to ungo wannan" Ta sa hannunta cikin jakar dake d'aure jikin west enta ta fiddo da sweet.... Da murnansa ko ya karb'a yana tsalle,yana fad'in "Daga yau idan ban sake fad'a ba zaki dinga bani alawa?" "K'warai kuwa zan dunga baka" "YEEEE!ya" fad'a yana tsalle "Idan zaki dinga bani har YAYA zan dunga ce miki kinji ADDA KHUBRA" Murmushi KHUBRA tayi tana shafa kansa cikin so da kulawa.. "Maza to jeka gida gani nan zan kawo muku ruwan kaji?" A guje ya juya ya shige gidan cike da murna... Tana kallon shigewarsa ta d'an tsaya tana murmushi ita kad'ai tasan halin da ta shiga lokacin da taji yaron ya kirata da ADDANSA,wani siraran hawaye ne yayi layi akan fuskanta,da kyar ta tsaida hawayen nata tana mai goge su....... ~Ni da nake gefe cike da tausayin halin da take ciki "nace KHUBRA har yanzun kina nan da halinki na son kuka"...~ ~My HULBATEEY kuwa hawaye naga tana sharewa kan tsananin tausayin yadda taga KHUBRA ta koma....~ *_~KEEP FOLLOWING FAN'S....~_* *~TEAM KHUBRA.~* *_REAL SMASHER._* 💠 *Y'AR GARUWA......* *(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).* 🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹 *©®2018* *24/ʝųŋɛ,2018* *ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ* *ცყ* _HAWWA M.U {$мaѕнer}_ 🕊🕊🕊🕊🕊 🌹🌹🌹🌹 _BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._ *~________________________~* _Wannan page tukuici ne gareku masoyana tabbas ina jin dad'in kasancewa tare daku kuma ina jin dad'in addu'o'inku gareni Allah ya bar k'auna,jinjina gareku *Fatima Ibrahim,Fatima

Chapter 15 of 41