๐๐๐๐
๐น๐น๐น
*ยฉยฎ2018*
*20/mฤ
rcษง,2018*
*สษฌฦกrแง ฤ
ลษ wrฤฑษฌษษล*
*แชแง*
_HAWWA M.U {$ะผaัะฝer}_
๐๐๐๐๐
๐น๐น๐น๐น
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~__________________________~*
_Ina mai baku hak'uri na rashin jina da bakuyi,duk da wasu sunsan uzurina na rashin mahaifina da nayi a safiyar litinin, *12/03/2018* ina fatan zaku tayani addu'ar samun dacewa da rahama a gareshi da sauran al'ummar musulmi baki d'aya, rayayyu daga ciki da kuma matattu,Allah yasa muyi kyakykyawan k'arshe......_
*AMEEN...*
*~__________________________~*
*_INNALILLAHI MAA AKHAZA WALAHU MAA A'A'DA WA KULLI SHAI'IN INDAHU BI AJALIN MUSAMMA FAL TASBER WAL TAHTATHEEB..._*
_Ya Allah Kaine mafi sani da abunda ke b'oye,na zahiri,Wanda zai faru gaba,da Wanda ya faru a baya,Allah kayiwa mahaifanmu rahama,gafara,afuwa,ka sadasu da rahamarka......Ameen thumma ameen._
*~_________________________~*
_Ya Allah ina rok'onka da sunayenka tsarkaka,Allah ka dubi halin da y'ar uwata take ciki,ka bata lafiya,ingantacciya mai d'orewa,Allah ka tashi kafad'unta....._
_Wish u a very quick and speed recovery *MY SISI HUBBEEY.*_ ๐
*~_________________________~*
_Kun nunamin karamci a rayuwa,soyyaya,k'auna,Wanda baki ba zai iya jurar furta kalamai garekuba,hak'ik'a ku en masoyane na asali,ubangiji ya biyaku da mafificin alkhairinsa..._
*ONLINE WRITER'S TARE DA READER'S* daga ko wane gida,ina alfahari da kasancewa tare da ku,ina jinjina gareku musamman wad'anda ke cikin wad'annan gidaje....._
*SMASHER & HUBBEY NOVEL GROUP.* ๐โฃ
*REAL SMASHER NOVELLA GROUP.* ๐โค๐
*A LAUNI HAUSA NOVEL.*๐
*TIME WRITER'S.* ๐
*WRITER'S ONLY.* ๐๐
*RAYUWAR BASMA.* ๐น
*WRITER'S VILLAH.* ๐๐
*MUSAN JUNA ONLINE WRITER'S.* ๐๐ป๐ค๐ป
*KANAWAN DABO WRITER'S ROOM.* ๐ค๐ป
*OUR LADIES OUR PRIDE.* โค
*PRECIOUS FAMILY.* ๐จโ๐ฉโ๐งโ๐ฆ
*BA NI NAYI KAINABA FAN'S.* ๐
_Ina godiya sosai,wacce bata da limit a zuciyana,bisa ta'aziyyan mahaifina,Allah ya bar k'auna..._
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM ๏ผY'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*0โฃ4โฃ*
*T*afiya kawai suke ba tare da *KHUBRA* ta san inda suke nufaba,sai kalleยฒ take a haka har suka fito bakin hanya...
Kafi babur suka tare,MA'U ta tak'ark'are ta hau yi masa bayanin rijiyar lemo zai kaisu......
Kud'in da ya yanko mata zata bayar,ta tsaya wangale da baki,nanfa suka tsaya ciniki,yi take kamar ba za a dainaba,d'an adaidata da yaga bazai iyaba,yaja kekensa yayi gaba.....
Duk Wanda za ta tsayar idan taji bai mata yanda take soba sai dai yaja Babur ensa ya k'ara gaba.......
Son kud'i irin nata ya hana su tafiya.......
Sun jima tsaye ba tare da sun samu abun hawaba.....
Ita MA'U son kud'inta da ganin tsada ya hanata ta biya akaisu inda zasu.....
Haka sukaci gaba da jira,yamma na dad'a kunno kai......
'Bangaren KHUBRA kuwa wata azababbiyar yunwace tafi addabarta ga bakinta da ya bushe saboda tsabar k'ishi da ya dameta.....
Rashin sanin abunyi da kuma hali irin na MA'U yasa ta ja bakinta tayi shiru,sai raba ido da take akan hanya......
Ganin tsaiwa bazai kai musuba,da kyashin biyan kud'in motar yasa MA'U juyawa ta kalli KHUBRA,tana yatsina mummunar fuskarta......
Tunda nake a rayuwata ban ta'ba zuwa na b'ata lokaci a tsaye ba tare da samun abun hawaba sai yau da na d'auko MAI BAK'IN JINI......
Jin furucinta na k'arshe yasa jikin KHUBRA dad'a yin sanyi....
Ba tare da ta kalletaba,haka bata ce uffanba.......
''Yanda kikaimin bak'in ciki na rasa abun hawa haka wallahi saina fanshe kud'ina tare da ke MATSIYACIYA Y'AR MATSIYACI''.......
Maganan da ya fito daga bakin MA'U kenan wanda ba k'aramin sosawa KHUBRA rai yayi ba,take hawayen da bata son fitowansa ya b'alle,ita kam da ita ta zaga babu da zai sa ta damu,abunda yafi komai bak'anta mata rai zagin ABBANTA da MA'U tayi....
Ko ganin girmansa batayiba,bare d'aga masa k'afa a matsayinsa na miji ga yayarta.......
Wannan shi ne abunda ya jawo mata ZUBAR HAWAYE.....
Dad'a sunkui da kanta tayi k'asa,ta shiga goge face nata,dan ta tattabata idan MA'U ta san halin da take ciki tana mai iya jibgarta a gurin tamkar kayan wanki......
Sake tsaida wani tayi,babu ko ciniki ta afka tare da cewa ''idan kinga dama kya taho mu tafi.....
Jan k'afafunta tayi ta shiga,duk da haka bata tsiraba,k'arshema sai cikin booth d'in mashin en ta zauna,tun daga kasuwar ta y'an kaba har zuwa unguwan na rijiyar lemo......
**************
Sun is a unguwan ana sallan Maghreb,yana saukesu ta laluba cikin d'an topinta ta zaro masa kud'insa....
Kud'i sosai KHUBRA ta gani ta fito da shi,nan ta tabbatar matar tana da bak'in hali....
Tunani ta shiga yi,na irin rayuwar da zata fuskanta nan gaba,ko yaya zata kaya tsakaninta da MA'U๏ผ........
*_Ni ko nace ai KHUBRA bakiga komaiba......._*
*_~Kumin uzuri fan's in sha Allah next page zaizo ba kamar wannan ba..... ~_*
*_Masoya novel ena na RAYUWAR WANI kuyi hak'uri na jina shiru kwana biyu in sha Allah zanci gaba daga inda na tsaya,na gode sosai_*
*_~IYA WUYA MUNA TARE......~_*
*_~KEEP MOVING.....~_* ๐๐๐
*_REAL SMASHER ๐ค๐ป๐_*
๐ ๐ ๐ ๐ ๐
*Y'AR GARUWA......*
*(ษฌษงษ mฦกสษฌ ษงษฤ
rษฌ ษฌฦกลณcษงฤฑลษ สษฌฦกrแง).*
๐๐๐๐
๐น๐น๐น
*ยฉยฎ2018*
*21/mฤ
rcษง,2018*
*สษฌฦกrแง ฤ
ลษ wrฤฑษฌษษล*
*แชแง*
_HAWWA M.U {$ะผaัะฝer}_
๐๐๐๐๐
๐น๐น๐น๐น
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~__________________________~*
*ADDU'AH KAN ABOKIN GABA...*
_ALLAHUMMA ANTA ADHUDHIY,WA-ANTA NASIYRIY,BIKA AHULU,WA-BIKA ASUULU,WA-BIKA UK'ATILU......_
_ALLAHUMMA INNA NAJ'ALUKA FIY NUHURIHIM,WANA-UZHUBIKA MIN SHURIRIHEEM......_
*_~#HISNUL MUSLIM....~_*
*~__________________________~*
*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*
_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM ๏ผY'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*0โฃ5โฃ*
*B*inta kawai KHUBRA take a bayaยฒ har suka k'arasa k'ofar gidan.....
Mukulli ta zaro irin wanda ake kira da (KUBA) en nan ta shiga murd'awa a jikin k'ofan,da kyar ta samu ta bud'e saboda taurin da k'ofan yayi.....
Gidan bak'i k'irin da shi,ga uban daud'a da yayi,kai saika rantse bai tab'a ganin wani abu mai kama da tsintsiyaba.....
Kunna kai tayi ciki ba tare da ta damu da addu'ar shiga gida ba,duk dama dai bana tunanin ta iyata....
KHUBRA dake baya,ta tsaya k'ofar gidan kafin ta shigo....
Sai da tayi addu'ah ta sanya k'afanta cikin gidan,kasancewar mahaifinta yana koyar da ita ilimin FIQHU,AZKAR da sauran abunda ba a rasa ba na zamantakewar duniya......
Bata tarar da MA'U a tsakar gidanba,guri ta samu ta zauna gudun kada tayi laifi,coz ta san yanzun sai ta bi a hankali,tunda tasan halinsu ba k'aunarta sukeba......
Tayi nisa cikin tunani,kan mafarkinta...
Abunda take son fuskanta kan mafarkin ya gazawa tunaninta....
Tashi tayi tana k'ok'arin shiga band'aki danta samu ta rama sallolin da ke kanta,nan ta bar kayan ta shige.....
Ko uzurin da ya kaita bata k'arasaba ta tsinkayo muryan MA'U daga tsakar gida tana surfawa iyayenta zagi....
K'irjinta ta dafe had'e da zaro ido,dan ko ba a fad'a mataba tasan laifinta.....
Addu'ah ta hau yi a zuciyanta,tana me neman tsarin ubangiji tsakaninta da MA'U da kuma zaman da zasuyi nan gaba......
Fitowanta ta tarar da ita tsaye ta rik'e k'ugu kamar wata k'aramar yarinya sai girgiza take.....
Kallo d'aya ta mata ta d'auke idonta a kanta,ta sunkuya ta fara alwala......
''Don ubanki ni zaki mayar mahaukaciya ina magana ki juyamin baya,ko ubanki wannan matsiyacin bai isaba wllh''...
Maganar da ta biyo bayan hucin da take kenan kamar wata KUMURCIN MACIJI.......
K'in magana,duk da kalmomin da tayi amfani dasu sun shigeta,shiru tayi har sai da ta idar da alwalan,sannan ta juya tana bata hak'uri......
Wata uwar harara ta rakata da shi kafin ta figi kayanta tayi cikin d'aki.......
Gajiya da tayi da tsaiwa,ganin ank'i kulata bare ta samu a kirata,kan dole ta nufi hanyan d'akin bakinta na d'auke da addu'ah....
A kwance ta tarar da MA'U,nan ta tsaya tunanin koh wane hali mahaifinta yake ciki a yanzun......
Tsayawan mutum MA'U ta gani kanta cikin sauri ta bud'e idonta,tana zabga mata harara....
Kameยฒ KHUBRA ta fara kafin da kyar ta iya furta
''Dama abun sallah nake so''...
Bata tanka mataba,haka bata tashi ba,saima dad'a rufe idonta da tayi,tana daga kwance kan gadon k'arfe irin na da ennan.....
Ganin tsaiwa bazai kai mataba,ta kabbara sallah daga inda take tsaye.....
Tana sallah tana dafe cikinta da yake ihun yunwa,a haka har ta samu ta idar ba tare da ta kai GA fad'uwaba.....
MA'U kam bacci ne ya kwasheta nan,ba tare da tunanin tashi ta gaida mahaliccinta ba.....
Har bacci ya fara d'aukanta ta tuna da k'ullin kayanta dake waje,cikin hanzari ta fita ta d'auko bata dawo d'akin ba saida ta tabbata ta kulle k'ofar gidan.....
'Dakin ta dawo ta hau bud'ewa,can k'asan kayan ta binciko wani k'ullin leda da ABBANTA ya bata tun jiya....
Bud'ewa ta hau yi,k'uliยฒ ne mai d'an yawa irin wanda ake yinsa da sugar ennan.....
Ci ta fara,kamar wacce ta samu nama,haka ta far masa,sai da taci mai yawa,sannan ta hak'ura ta d'aure ta mayar cikin ledan......
Waje ta sake komawa cikin randa ta d'ebi ruwan da tasan zata iya shanyewa....
Godiya tayiwa Allah,sannan ta koma d'akin ta kwanta a k'asa daiยฒ inda ta idar da sallah.....
Take kuwa bacci yayi gaba da ita......
************
Daf da kiran sallan assalatu ta farka,kasancewar ABBANTA kullum shi yake tashinta idan zashi masallaci sallah da asuba....
Fita tayi ta d'auro alwala,tsakar gidan da duhu sosai,haka ta daurewa zuciyarta tayi sauri ta dawo d'akin.......
Har ta idar da sallan MA'U ko juyin farko batayiba,haka itama KHUBRA batayi gangancin tashintaba.....
Gefe ta koma,ta had'a kai da gwiwa,tana tunanin duniya da makomar zuwanta wannan gari,tasan dai babu komai cikinsa face zallar wahala......
Ganin tunani ba kaimata zai ba,ta shiga karanta AZKAR na safiya,tana zaune har gari ya k'arasa wayewa......
Hijab dake jikinta ta cire ta fita tsakar gida......
Tsintsiya ta d'auka ta hau shara,kafin wani dogon lokaci har ta kammala,sai ga gidan yayi haske daga bak'ar daud'ar da yayi.....
Har tayi wanka MA'U bata san me yake faruwaba...
'Dakin ta dawo,da tunanin ta tasheta ko kuwa......
Tsayawa tayi tana nazarin ta inda zata fara,amma fargaba ya hanata tab'uka komai.....
Kan dole ta hak'ura,ta zubawa sarautar Allah ido......
*************
Sai misalin k'arfe 8:00am ta farka tana ta faman zabga hamma,had'e da mik'a....
Da kyar ta iya tashi tayi waje,ganin tsakar gidan a share tas,ta tab'e baki,ta rarumi buta tayi band'aki,ta jima aciki,tamkar wacce ta sami d'aki,zuwa can kuma ta fito,ta sake d'iban ruwa a bokiti ta koma....
K'arar ruwa kawai kake ji kamar wacce taje suuuu kogi,haka ta shek'ashi a jikinta ta fito,cikin abunda bai wuce minti 5 ba.......
Alwalan ma bujiยฒ akayi aka fad'a d'akin.....
Shigarta ta tarar da KHUBRA har ta gyara d'akin tsaf duk ta gyare tarkacen dake cikin d'akin.....
Babu ko sannu bare an gode,saima ladan gaben harara da yatsina da ta shiga yi......
Shiryawa tayi cikin gaggawa,tasa wata atamfa riga da zani,taja gazal a idonta......
Takalminta ta sharfad'a tayi waje ba tare da yin ko da sallan da akayi alwala domin taba......
Babu magana bare KHUBRA ta sa ran ganin abinci tayi waje,tana gaisheta ma ko ta kanta bata biba.....
Ta k'arawa k'afafuwanta mai.......
*_~ALLAH YA SHIRYA.......~_*
*_~KEEP MOVING....~_* ๐๐๐
*_REAL SMASHER๐ค๐ป๐_*
๐ ๐ ๐ ๐ ๐
*Y'AR GARUWA......*
*(ษฌษงษ mฦกสษฌ ษงษฤ
rษฌ ษฌฦกลณcษงฤฑลษ สษฌฦกrแง).*
๐๐๐๐
๐น๐น๐น
*ยฉยฎ2018*
*22/mฤ
rcษง,2018*
*สษฌฦกrแง ฤ
ลษ wrฤฑษฌษษล*
*แชแง*
_HAWWA M.U {$ะผaัะฝer}_
๐๐๐๐๐
๐น๐น๐น๐น
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~__________________________~*
๐๐พ๐๐พ๐๐พ๐๐พ๐๐พ๐๐พ๐๐พ๐๐พ๐๐พ
*APPY APPY BUFDAY*
_Hope your birthday blossoms into lots of dreams come true! May today be filled with laughter and love._
_Happy Birthday and many happy returns of the day._
๐พ๐๐พ๐๐พ๐๐พ๐๐พ๐๐พ๐๐พ๐๐พ๐๐พ๐
*HAPPY BITHDAY 2 U!!*
H B Z
A U
Y A B
A A
T B I
R
A
*(YAYA HAYAT) ADMIN OF ADMINS.......*
_Wannan ranar taka ce,babban Admin mai kundin novels, *WRITER'S* naka *REDER'S* naka,kana k'ok'aree gurin nishad'antar da d'aukacin members enka dake cikin_
*COOL NOVELS GROUP'S 1,2,3,4 & 5, MAKEUP ND KITCHEN GROUP* _Allah ya k'ara 'daukaka,ya k'aro maka shekaru masu albarka,kana mai wadatuwa da imani,kwanciyar hankali........_
_Wannan page en naka ne kai d'aya kayi yadda kaso da shi....._ โ๐ปโ๐ป
๐พ๐พ๐ *HAPPY BUFDAY WULLNUP ADMIN...* ๐๐พ๐พ
*~__________________________~*
*ADDU'AH YAYIN TASHI DAGA BACCI*
_ALHAMDULILLAHIL-LAZIY AHYANA BA'ADA MAA AMATANA WA-ILAIHIN-NUSHUUR..._
_ALHAMDULILLAHIL-LAZIY AFANIY FII JASADIY WARADDA ALAIYYA RUHIY WA-AZINALIY BIZIKHRIY....._
*_~#HISNUL MUSLIM...~_*
*~_________________________~*
*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*
_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM ๏ผY'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*0โฃ6โฃ*
*I*ta d'aya zaune tayi shiru,abun duniya duk ya taru ya mata yawa......
Tunanin gida da mahaifinta duk shi yafi damun zuciyanta,ko a wane yanayi yake๏ผ Allah shi ne masani......
Ganin babu sarki sai Allah,shi yasa ta bawa zuciyanta hak'uri......
'Daki ta sake komawa,bayan ta tura k'ofan gida,da yake ta san ita kad'ai ke gidan,gudun kuma kada wani abu ya faru......
***********
Tafiya take duk inda ta samu watsa k'afafuwanta take,tamkar wacce zata tashi sama.....
Son kud'i irin nata ya hanata neman abun hawa......
Sai da tsakiyan rana,ganin babu haza yasa ta hak'ura ta nemi keke napep,daga UNGUWAN KURNA zuwa RIJIYAR ZAKI,a ganinta nan ne unguwar masu kud'i,za tafi samun gidan aiki,idan bata samuba kuma,zuwa gobe sai ta nausa cikin gari......
Zafin rana da k'ishi su suka haddasa mata tsaiwa,ta nemi abun hawa,idan yaso sai ta k'arasa,in da ta nufa......
Ta tsayar da masu napep sama da guda goma,amma da sun tsaya suke k'arawa babur en nasu wuta suyi gaba.......
Da kyar ta samu abun hawa,kan neman ragi irin na MA'U......
Yinin ranar yawo ta dungayi gidaยฒ take bi a unguwan na rijiyar zaki,kan neman gidan da suke neman Y'AR AIKI.....
Sai da ta sha wahala,kafin ta samu gidan da suka nuna mata suna buk'ata......
Sun gama ciniki kan dubu biyar per month......
Duk iya yinta na su k'ara mata wani abu,hakan ya faskara....
Gudun kada tayi asara gashi wannan d'inma da kyar ta samu,bayan yini da tayi tana GARARIN DUNIYA yasa ta amince,akan zata kawota daga zaran sun gama shiryawa......
Abinci matar ta kawo mata da ruwa mai sanyi.......
Ta gama d'amke cikinta,sannan tayi mata sallama........
Godiya tayi ta tafi da alk'awarin nan da Sati d'aya zata dawo......
***********
Kwance take tana ta faman bacci wanda bata san lokacin da ya d'auketaba,tayi nisa cikin baccinta.......
**************
Tun daga nesa ta hango ingarman dokin wanda akewa lak'ani da KILI ( wato mai fari biyar),kansa mutum ne zaune,cikin farare tas en tufafi......
Matsowa yaci gaba da yi,wanda har sai da yazo daf da ita sannan ne ta iya gane mahayin murmushi d'auke kan fuskansa......
Sai da ya zo gabanta,sannan yaja linzamin dokin ya tsaya.....
Har lokacin tana tsaye fuskanta cike da mamakin ganinsa......
Mutumin daya ce bazai sake dawowaba yau shi ne a gabanta yau.......
Saukowa yayi cikin isa,ya tako har zuwa gabanta....
Cikin wani irin voice da bata tab'a jin irinsa ba tunda take a gaba d'aya tsawon rayuwanta,ta tsinkayo shi yana fad'in
_''Amincin Allah yaci gaba da tabbata agareki''........_
Kasa amsawa tayi saboda tsananin mamaki da yak'i barinta har yanzun......
Hannunta ya kama cikin wani irin salo,ya jata jikinsa.....
_''Haba wifey,ni en ne baki ganeba ko kuwa na zame miki wata sabuwar halitta๏ผ''......_
Kuka ne ya kufce mata,jikinta banda rawa babu abunda yake,tsabar tsoro ta kasa magana,sai hawaye dake ta ambaliya a fuskanta.....
Duk k'ok'arinsa da son ganin ta bud'e baki tayi magana abun ya gagara......
Janta yayi ya had'a jikinsu guri d'aya,ganin yanda jikinta yake ta faman b'ari......
Maimakon a samu sauk'i saima k'aruwa da aka samu.........
Kukantane ya sake tsananta,kan dole ya raba jikinta da nasa....
Fuskanta ya kama ya d'ago,tsura mata ido yayi
_''Shin bakiyi farin ciki da ganinaba ne wifey๏ผ''...._
Kai ta girgiza masa,alaman
A'a
_''Baby maganafa zakiyi,bana son wannan nodding en''......_
Cikin hanzari ta bud'e baki da niyyan magana
_''A'a,ina mamakin yanda ka dawo gareni ne,alokacin da bantab'a tsammaniba''........_
Fuskanta ya shiga goge mata,yana murmushin jin dad'i......
**********
k'afafuwanta tamkar wacce taje sharan gona,sunyi futuยฒ kamar basu tab'a ganin mai ba.......
Sai murna take na samun gidan aikin da tayi,haka ta sauka a napep en da ya sauketa bakin titi.....
Ta sake ninkawa ta shiga cikin unguwan,a k'ofar gida taja burki,ganin k'ofan a rufe,ta shiga huci.....
Bugun k'ofa ta shiga yi,jin shiru ba a bud'eba,ta shiga dukanta da k'arfi tamkar zata karya.......
************
Cikin baccinta mai dad'i mai cike da mafarkin da a kullum shi ne birinta....
Ta tsinkayo bugun k'ofan da tamkar a tsakiyan kanta ake......
Bud'e idonta tayi,cikin sauri ta mik'e ta nufi k'ofa,har tana had'awa da d'an gudu,wanda saura kad'an ta fad'i,amma haka ta daure ta tunkari k'ofan..........
*_~Uhmmmm ko me KHUBRA zata tarar yau kam.......~_*
*_~KEEP MOVING...~_* ๐๐๐
*_REAL SMASHER ๐ค๐ป๐_*
๐ ๐ ๐ ๐ ๐
*Y'AR GARUWA......*
*(ษฌษงษ mฦกสษฌ ษงษฤ
rษฌ ษฌฦกลณcษงฤฑลษ สษฌฦกrแง).*
๐๐๐๐
๐น๐น๐น
*ยฉยฎ2018*
*23/mฤ
rcษง,2018*
*สษฌฦกrแง ฤ
ลษ wrฤฑษฌษษล*
*แชแง*
_HAWWA M.U {$ะผaัะฝer}_
๐๐๐๐๐
๐น๐น๐น๐น
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~__________________________~*
*ADDU'AR SANYA TUFAFI.*
_________________________
_ALHAMDULILLAHIL-LAZIY KASANIY HAZAS-SAUBA,WARAZAK'ANIHI MIN GHAIRI HAULIN MINNIY WALA KUWATTA......._
*_~#HISNUL-MUSLIM.~_*
*~__________________________~*
*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*
_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM ๏ผY'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*0โฃ7โฃ*
*K*okawa ta shiga yi da k'ofan,wanda da kyar ta samu ta bud'e......
K'ofan na gama bud'ewa idanuwanta sukayi arba da MA'U tsaye,idanunta sunyi jajur dasu kamar garwashi.....
Kamar ance ta kalli k'afarta,ai kuwa nan ta hangi k'afar tayi busuยฒ,dan k'ura da daud'a......
Duk k'ok'arinta na ganin ta kaucewa yin dariya abun ya faskara....
Nan ta fara tuntsirar dariya,kamar kwancen mahaukata.......
MA'U dake tsaye tana jiran a bud'e mata k'ofa,taga ta tsaya tana mata dariya.....
Tsaiwa tayi ta dafe saman gini,tana kallonta,sai dariya take,kamar sabuwar kamu.......
Tsabar mugunta irinta KHUBRA har dafe gefen cikinta take,ita bata matsa daga kan hanya,ta bawa MA'U guri ta wuceba,ita kuma bata tsaida dariyan taba......
Kallonta MA'U taci gaba dayi,ganin abun nata ba na
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 2 Chapter of 41