k'are bane,kuma ta rasa me KHUBRAN kewa wannan dariyan a tare da ita,abun ya soma bata haushi....
Ga haushin ta rufe mata k'ofa,sannan ta zo tana mata dariyar rainin wayo.......
Hankad'ata tayi cikin soron,ta shigo tare da maida k'ofa ta rufe.....
Wani gigitaccen mari MA'U ta aikawa KHUBRA da shi,wanda ta jishi,babu shiri kuwa ta had'iye dariyarta.......
Gashin kanta ta dank'a ta jata zuwa cikin gidan,sai zage² take kamar y'ar maguzawa......
Babu zato bare tsammani MA'U ta shiga jibgar KHUBRA kamar ta samu jaka ko ince kayan wanki.....
Tun tana dukanta KHUBRA na iya yin ihun neman ceto har ta koma muryanta ma bata iya fita saboda laushi da jikinta yayi.....
Sai da tayi mata dukan sa'a,sannan ta yasar da ita a gurin ta shige d'aki,ba tare da ta furta ko 'A' ba,zuciyarta kamar zata fito waje saboda haushi.....
KHUBRA dake yashe a k'asa babu,abunda ake iya ji na daga sautin muryanta,banda numfashinta dake fita da sauri²......
Ta jima kwance a gurin,wanda ta gagara koda motsin kirki......
***********
Tun tahowar MA'U da KHUBRA birni,hankalin ABBAN KHUBRA yak'i kwanciya.....
Kullum cikin tambayar LADIYO yake yaushe MA'U zata dawo da ita.....
Amsar dai guda d'aya ce kullum,dazaran lokacin da suka d'auka alk'awari yayi zata dawo da ita.....
Shi kam kullum yana jinta ne,don kuwa ya fuskanci idon MA'U bud'e yake da son nera,tsoron sa d'aya kada su cutar masa da ita.....
Abu sai dad'a gaba yake,LADIYO ta shiga tashin hankali ganin yadda malam en yake neman d'aga mata hankali,har bata so ya shigo ya tarar da ita zaune,yanzun zai dasa mata maganar y'ar tasa mai kama da aljanu.....
Yau ma zaune take cikin y'ar rumfar karan dake bakin d'akin nata,wanda daga nan kana iya hango k'ofar shigowa gidan.....
Zafi duk ya addabeta,daga ita sai d'aurin zani iya k'irjinta.....
Malam buba ya kawo kai zai shigo cikin gidan,da sallama a bakinsa....
Ko amsawa bata yiba ta mik'e cikin hanzari zata bar gurin.....
''Dakata LADIYO,na fuskanci kwanan nan nema kike ki mayar dani wani sha ka tafi''.....
''Ko dai yau ki fad'amin inda y'ata take ko kuma aradu ina mai kai k'ararki gurin MAI GARI''.......
Ido waje LADIYO ta juyo,nan ta shiga bashi hak'uri.....
Saboda LADIYO irin matan nan ne masu d'an karen tsoro,ammafa akwai tsokana....
Idan akwai abunda LADIYO take tsoro a duniyarta kuwa baya wuce MAI GARI ko a ambaci mai bak'in kaya wato ('DAN SANDA).....
Har k'asa ta zube tana masa magiya,akan zata kira MA'U ta dawo da KHUBRA idan ma bata sametaba zata je da kanta ta dawo da ita har gida ba sai maganar ta jega HUKUMA ba.....
Girgiza kai MALAM BUBA yayi,ya juya ya nufi d'akinsa
''Da dai yafi miki kwanciyar hankali''......
Yana fad'a ya k'arasa shigewa ciki.....
LADIYO dake durk'ushe a inda MALAM BUBA ya barta ta d'ago tana dafe k'irji....
Ganin babu MALAM en a gurin tayi wuf ta fad'a d'aki....
Nan ta shiga raba ido kamar shege a rabon gado (yo dama me zai kawo shi tunda yasan bashi da ko allura)?.....
Ita kad'ai ta shiga magana da kanta
_''Ya zama dole nayi aron waya na kira MA'U ta dawo da wannan shegiyar yarinyar mai kamar aljana,tun kafin kashina ya bushe''....._
Ko gama tunanin batayi ba ta zara mayafinta ko riga babu ajikinta,tayi waje......
Bata zame ko inaba sai gidan k'awarta mai suna TABAWA.....
******
TABAWA irin matan nan ne y'an duniya,wad'anda suke da bud'ad'd'en ido.....
Da shigarta ta tarar da TABAWA ta cokalo d'an kwalinta sai zabgawa mijinta rashin mutunci take....
Shi kuwa bawan Allah kansa a k'asa kamar wanda ke gaban uwarsa haka jikinsa sai b'ari yake.....
Bata k'arasa shigowa ba ta tsaya daga bakin k'ofa,tana kallon wannan abun aljabi.....
''Dillah can banza kawai,zaka bani ko kuwa sai na cajeka?
Katabbata idan har na laluba na tarar da kud'i a jikinka,wallahi yau kam babu kai babu cin abinci a gidan nan''.....
Ta fad'a tana hak'ik'an cewa....
Rantsuwa ya shiga yi mata,sai kace d'a da uwa,amma hakan bai sa TABAWA ta yarda ba.....
Rigarsa ta kama ta cukuikuyo shi,ta shiga lalube aljihunansa kaf,sai da ta tabbatar da abunda ya fad'a sannan ta kyaleshi tana fad'in
''Allah ya cece ka''.....
''Amma ba kyaleka nayi ba wallahi,zan ranta maka kud'in cefanen yau,kana samu kayi hanzarin biyana idan kuma ba hakaba,zaka had'u da tijarar da tafi wannan''......
Ita kam LADIYO na nan tsaye tamkar an dasa bishiya,ta lula cikin tunani,har bata san lokacin da mijin k'awar tata ya fita ba......
Dogon ajiyan zuciya tayi,kafin jiki a salub'e ta afko gidan ko sallama babu......
Binta kawai TABAWA tayi da ido
A ranta kuma tana fad'in ko lafiya?
*_~NIKO NACE OHO MUKU.........~_*
*_~KEEP MOVING....~_*😍😍😍
*_REAL SMASHER_* 🤞🏻😘
💠💠💠💠💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*Viawattpad@realsmasher01.*
*©®2018*
*25/mąrcɧ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~__________________________~*
*ADDU'AR SANYA SABABBIN TUFAFI.*
_ALLAHUMMA LAKAL HAMD ANTA KASAUTA NIHI AS'ALUKA KHAIRAHU WA-KHAIRA MAA SUNI'A LAHU,WA'A'UZU BIKA MIN SHARRIHI WA-SHARRI MAA SUNI'A LAHU..._
*~#HISNUL MUSLIM.~*
*~__________________________~*
*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*
_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*0⃣8⃣*
*T*ana nan kwance in da MA'U ta yasar da ita,kamar matacciya,idan ba wai mutum ya kula da yanda chest nata dake shibring ba,za a iya cewa ta jima da mutuwa....
**********
Cikin kwanciyar hankali MA'U tayi kwance kan gadonta,ko kad'an batayi nadamar abunda ta aikataba,bare ta duba taga halin da y'ar mutane ke ciki ba....
Idonta tar kan selling tana nazari kan wannan gidan aiki da ta samu....
Ita kam a nata ganin,da zaran ta samu wani aikin da yafi wannan maik'o zatayi watsi da wannan....
Ko dama ace ba a garin kuwa zatayi aiki ba,ita meye damuwarta,tunda ba ita ta haifeta ba.....
Burinta bai wuce a kawo mata masu gidan rana......
************
Wani uban tsaki TABAWA tayi lokacin da ta kalli LADIYO,da alama tunani take....
Da k'afa ta kai mata hauri...
A firgice LADIYON ta d'ago tana k'ok'arin mai da kallabinta da yake shirin fad'owa....
Jajayen hak'oranta ta bud'e wanda babu abunda ke fitowa daga bakin nata banda wani irin azababben wari,ga su duk sun dafe saboda tsabagen daud'a.....
Kallonta TABAWA tayi tana fad'in
''LADIYO ince dai ko lapia kike irin wannan dogon nazari haka?''.....
''Ke dai bari TABAWA ina cikin tashin hankali wollahi''....
Fuskanta da tsananin mamaki take kallon LADIYON da take koro mata jawabin abunda ya had'o ta da MALAM BUBA akan yarsa......
Dariyar mugunta TABAWA ta hau yi,tana tafe hannunta....
Sai da tayi mai isarta kafin ta saurara,tana k'arema LADIYO kallo,tana tab'e baki....
''Uhmmmm!LADIYO kenan,ni ai a ganina ke kika so,da har kika tsaya MALAM BUBA yake zuba miki irin wannan rashin mutunci,da d'iban albarka haka
Ni baki ganniba,washar da ni,tunda mu ba haihuwa za muyiba,ai gara muyi abunda muke so,kafin dare d'aya suzo mana da maganar k'arin aure''.....
Baki bud'e LADIYO ke kallon TABAWA,da ta tak'ark'are tana koro mata datar......
''Kinga yanzu ba zama ne ya kamacemu ba,abunda kawai za ayi,ki biyo sahuna,mu d'ora daga inda aka tsaya....
Har zamu tsaya ne muna kallonsu,mu tashi a tutar babu,shi kenan munyi ba wan ba k'anin?''.....
Karatun na d'an kama......
"Ina kuma zamu nufa yanzun?"
LADIYO tayi tambayar.....
"Kinga yanzu ba lokacin tsaiwa dogon jawabi bane,idan kina da buk'atar mafita kawai ki taso,bana son dogon sharhi".....
Jiki na b'ari ta mik'e tabi TABAWA a baya,kamar
RAK'UMI DA AKALA......
************
Rashin madafa shi yasa KHUBRA dake kwance,lallab'awa da jan ciki,ta d'ebi ruwa a buta......
Da yake lokacin zafine,ruwan da zafinsa,rana ta gama gasashi....
Haka ta lallab'a ta shige,wanka tayi ta d'aura alwala ko za taji dama²....
Da kyar ta iya mik'ewa tana bin bangon toilet en,ta fito daga ciki,jikinta duk ya mata nauyi....
Haka ta ci gaba da takowa tana d'aga k'afa da kyar,har ta samu ta fito......
'Daki ta shiga da niyyan ta samu ta lallab'a tayi sallah,dan kuwa lokacin har an idar da sallar maghreb......
Ko da ta shiga d'aki da sunan za tayi sallaah......
'Dagowa MA'U tayi,tana K'are mata kallo.....
Cikin tsawa ta hau fad'an da tun d'azun batayiba.....
************
Can cikin wani surk'uk'in hanya suka shiga bi jikin LADIYO sai kyarma yake saboda tsoron hanyan da ko a mafarki bata tab'a tsintar kanta a cikiba....
Bin bayan TABAWA kad'ai take,wacce ita kam ko d'ar bata jin tsoron komai,haka take watsa k'afafuwanta cikin jejin.....
Haka har suka tsinci kansu gaban wata y'ar bukka dake saman wani sand dune hill....
TABAWA da yake tasan kan hanyar yanda ake hawa,haka ta shiga raba k'afafuwanta,har ta ida hawa.....
LADIYO kam ta kasa hawa,sai ta hau sai ta dawo k'asa,jikinta duk ta kurjeshi garin k'ok'arin hawa....
Daga saman dutsen TABAWA ta hango LADIYO yanda take ta faman kaiwa da komawa dariya ta tuntsire da shi,nan ta shiga kokawar komawa k'asa.....
Kokawa suka shiga yi na hawa,in da TABAWA ta rik'e hannun LADIYO kamar wasu k'ananan yara,tana koya mata yanda zata hau,har dai sukayi nasarar hawa saman dutsen.....
Guri suka samu suka zauna kan wasu fatu dake shimfid'e uwa tabarma,suna jiran zuwan mai gurin.....
_KUYI HAK'URI DA WANNAN FAN'S..._
*_REAL SMASHER_* 🤞🏻😘
💠💠💠💠💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*Viawattpad@realsmasher01.*
*©®2018*
*27/mąrcɧ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~__________________________~*
*ADDU'AH IDAN KAGA WANI DA SABON KAYA.*
_TUBLIY WAYUKHLIFULLAHU TA'ALA...._
_ILBIS JADIDAN,WA'ISH HAMIDAN,WA-MUT SHAHIDAN._
*_~#HISNUL MUSLIM.~_*
*~__________________________~*
*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*
_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._
*~__________________________~*
_Aradu kuna bani dariya fan's en *Y'AR GARUWA* ,labarin nan gaba d'aya yanzun aka fara har hanzun ba ayi komaiba,kuci gaba da biyoni dan jin yadda za ta kasance.... *LUV U OLL.*_ 💔
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*0⃣9⃣*
*B*ayyanarsa kawai LADIYO ta gani wanda ba k'aramin tsorone ya cika mata zuciya ba....
Jikinta sai kyarma yake,duk ta firgita,sai neman b'oyewa da take a bayan TABAWA.....
Dariyar da ya kece da ita,wadda ta haddasawa d'an k'aramin forest en amsawa,mai kama da kukan jaki....
Ita ta sake rud'a LADIYO wadda a sanadin hakan har fitsari ta soma,ta mak'alk'ale TABAWA.....
Wata razananniyar tsawa ya mata yana fad'in
''Shiga hankalinki la'ananniya,b'atacciya,duk wanda yazo nan ya tabbata wakilin shaid'an,bama wa muminai aiki....
Idan kin san da sofanen imani a tare da ke maza ki b'ace anan tun kafin yaran shaid'anu su sauke fushinsu akanku''.....
Ya k'arashe maganar yana zare jaajayen idanunsa,masu kama da garwashi......
''A tafiyarmu babu tsoro,bamu san mene shiba bare muyi shi,idan har kin kiyaye wad'annan sharud'a,muna maraba dake yar jakar uba''.....
Ya sake kecewa da wata dariyar da ta fi ta farko....
Ita kam LADIYO yanda yake magana da dariyarsa shi yafi komai tayar mata da hankali.....
Harara TABAWA ta aika mata wadda tasa ta shiga hankalinta,ta zauna sosai,amma da zaka ce mata kyattttttt to kuwa zaka nemeta ka rasa....
Kafin su kaiga yin magana ya tare su yana fad'in
''Bana buk'atar kuce wani abu,nasan abunda ke tafe daku''.....
KEEE ya nuna LADIYO,kafin ya d'ora daga in da ya tsaya....
''Akan mijinki ne da kuma y'ar kishiyarki wacce mahaifiyarta ta rasu''.....
''Me kike so a yi wa mijin naki?
Kina so a kasheshi ne,ko kuwa a rabashi da y'arsa kamar yanda ya rabu da iyayensa, kar ya sake tambayarki in da take,ko kuwa kina so ya koma jin tsoronki tamkar ke kika haife shi?''...
Gyad'a kai tayi cikin farin cikin samun mafita,sannan ta shiga yi masa bayanin abunda take so ayi musu akan MALAM BUBA.....
Haka bokan nasu ya juya yana mai kecewa da dariya ya shige bukkar tasa......
Wasu uban layu ya fiddo ya mik'a mata...
Kinga wannan ya nuna mata wata k'arama daga ciki,zaki sata a cikin matashin kanki da kike bacci (pillow)....
Wad'annan kuma ki samu dai² bakin k'ofar d'akinsa ki hak'a rami ki binne su,idan kikayi haka kuma aikinki ya kammala,sai ki jira kiga mai zai faru''......
Ku tashi ku bani guri.......
LADIYO da shishshigi sai cewa tayi
''MALAM mene ne kud'in aikin nawa?''.....
Tsawa ya watsa mata yana fad'in
''Kaji y'ar jakar uba,mu nan ba a tab'a biyanmu idan mukayi aiki sai bayan aikinmu ya kammala.....
Maza ku bar nan,kada ku sake ku waiwayo''.....
Cikin sauri ko wacce ta suri takalminta suka kamo hanyar barin jejin,ko da wasa babu wacce ta juya,har suka fito daga ciki.....
**********
A fusace MA'U ta mik'e tana shirin dank'o KHUBRA da tayi tsaye....
Ba shiri tayi waje har tana neman fad'uwa du da dama jikintan ba wani k'wari ne da shiba.....
''Da kin tsaya ai y'ar jakar uba,yau da na nuna miki k'aryarki,dan yau na lahira sai ya fiki jin dad'i''.....
Ta fad'a tana huci,sai jijjiga jiki take,uwa wacce take shirin fad'a da sa'anta....
Komawa tsakar gidan tayi,nan ta shimfid'a d'an kwalinta,tayi sallah,ta ci gaba da jiran gawon shanu.....
Sai da ta raba dare a zaune a gurin ba tare da ta motsa ba....
Lokacin da ta tabbatar da LADIYO tayi nisa a cikin baccinta,ta mik'e ta lallab'a....
Gurin kayanta ta dosa d'an ragowar k'uli²n da ABBANTA ya bata shi ta d'auko ta ci,ta sake d'aurewa ta mayar...
Ta d'ebi ruwa ta sha,tayi godiya ga mahaliccinta....
Har ta gama abunda za tayi a d'akin MA'U bata san ta shiga ba.....
Sake komawa ta sake yi ta d'auko zani a cikin kayanta ta fito tare da jaa mata k'ofan....
A inda tayi sallah ta shimfid'a,hijab en jikinta kuma ta cire shi ta lullub'e jikinta....
Takurewa tayi guri d'aya saboda rashin girman hijab en ba zai kai mata ta rufe jikinta gaba d'ayaba.....
A wannan daren sai dai da yake an ce bacci b'arawo ne,amma da KHUBRA zata iya cewa ba zata iya bacciba...
Duk da baccin nata ya kasance rabi² ne....
Sai bayan da tayi sallan Asubah sannan wani nannauyan bacci yayi gaba da ita.......
************
Shigowar MALAM BUBA gida yana ta kwad'a sallama,yaji shiru ba'a amsa ba....
Nan ya shiga kiran LADIYO,jin shirun yayi yawa,ya shiga nemanta lungu da sak'o na gidan,amma ko mai kama da ita bai ganiba bare kuma itan....
Girgiza kai yayi ransa a b'ace yake fad'in
''Duk inda kikaje zaki dawo ki tarar da ni,kuma xa kiyi bayani,wannan iskancin na gaji da shi''.....
Yana gama bambamin fad'an nasa yayi waje......
***********
Kamar yadda ya musu bayani,direct gidan LADIYO suka nufa....
Gidan babu kowa,kasancewarsa haka kuwa da shigowarsu,suka hau dube²,bayan sun tabbatar babu mutum ciki,suka hau aiwatar da nufinsu......
Sai da TABAWA ta tabbatar sun gama aikata komai kamar yadda aka fad'a musu tukun,ta sake d'orata akan hanyar b'ata,wacce su a ganinsu ita ce dai²......
Sannan tayiwa LADIYO sallama,ta nufi hanyar nata gidan,babu fargabar tayi dare bata dawoba,za ta tarar da fad'a......
*********
Sai da gari ya gama wayewa sannan MA'U ta fito daga d'aki....
Kamar kullum cikin al'adunta,tana hamma had'e da mik'a.....
Mutum ta gani kwance,sai alokacin ta tuna abunda ya faru......
Batayi magana ba ta wuce bakin randa,sai da ta cika bokiti da ruwa,ta d'auko shi da k'yaar....
A dai² kan KHUBRA ta d'aga shi ta juye mata shi a kanta....
A firgice KHUBRA ta mik'e tana dube².........
*_~#TEAM KHUBRA...~_*
*_REAL SMASHER._* 🤞🏻😘
💠💠💠💠💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*Viawattpad@realsmasher01.*
*©®2018*
*28/mąrcɧ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~__________________________~*
*ADDU'A YAYIN CIRE TUFAFI.*
_BISMILLAH!!_
*ADDU'A IDAN ZA A FARA ALWALA.*
_BISMILLAH!!!_
*_~#HISNUL-MUSLIM.~_*
*~_________________________~*
_Sisinah ina miki fatan alkhairi arayuwa,ubangiji ta tashi kafad'unki,ina missing enki sosai na rashin kasancewa tare da juna.._
_Wish u a very quick and speed recovery *MY HUBBEEY* ,I so much heart u cweety.._💔💔💔
*~__________________________~*
*_ALLAHUMMAGFIR LII HAYYINA,WA-MAYYITINI,WASHAHIDNA,WA GHA'IBINA,WA-SAGHIRANA,WA-KABIRANA,WA-ZAKHARINA,WA-UNSANA,ALLAHUMMA MAN AHYAYTAHU MINNA FA AHYIHI ALAL ISLAM,WAMAN TAWAFFAITAHU MINNA FATAWAFFAHU ALAL IYMAN,ALLAHUMMA LAA TAHRIMNA AJRAHU,WALA-TUDILLANA BA'ADAHU........_*
_ALLAHUMMAGFIR LI ABIIY WA KULLI JAMI'I MAUTAL MUSLIMIYN,AL-AHYA'U MINHUM WAL-AMWAT...._
*~__________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*1⃣0⃣*
*T*saye akanta taga MA'U da k'aton bocket,tana ta faman aiko mata da uwar harara....
Mik'ewa tayi tana kama kayan tana matsewa...
Sunkuyawa tayi ta kamo zanin da ta shimfid'a...
Ko kafin ta kai ga d'aukowa MA'U dake tsaye bayanta ta d'irka mata hannunta mai kamar na maza a bayanta....
Lank'washewa tayi a gurin saboda azabar dukan da ya shigeta,ko bata fad'a ba....
Kuka ne ya kufce mata,ta shiga rerawa babu saurarawa...
Kamar mutuniyar arziki haka MA'U ta juya,a bakin randan ta ajiye bocket en ta sake dawowa ta wuce KHUBRA dake faman kuka uwa ranta zai fita...
Sai da ta kalleta kafin ta wuce cikin d'akin,ta d'an jima aciki sannan ta fito...
Hannunta d'aya a goye a bayanta,ta nufo inda KHUBRA take sunkuye ta saka fuskanta a tsakanin laps nata...
KHUBRA da bata san meke faruwa ba bare tasan abunda zai faru nan gaba,sai jin duka tayi ta ko ina yana ratsa jikinta....
K'ok'arin karewa ta shiga yi,amma hakan ya gagara...
Gaba d'aya MA'U ta hanata motsi,ta kama ta nad'eta acikin hijab enta....
K'ok'arin guduwa ta shiga yi,ga MA'U bata daina dukanta ba,ganin azaban yayi mata yawa yasa ta dage ta ingije MA'U ai kuwa nan sai ga MA'U a k'asa timmm....
Da gudu ta nufi hanyan fita daga gidan....
''Kada ki kuskura ki fita daga gidan nan,dan wallahi na lahira sai yafi ki jin dad'i yau,yarinya zaki gane ni kika tura na fad'i''...
Tana daga kwance a inda KHUBRA ta tura ta take koro bayani...
Da k'yar ta mik'e daga gurin tana d'ingishi,haka ta koma d'aki tana duba jikinta...
Hannayenta ta k'urje su,ga d'an yatsanta na k'afa da yake mata rad'ad'i....
MENTHOLATOM ta hau gogawa gurin...
Azabar da yake mata ce ta sata bari babu shiri...
Haka ta kafawa d'an yatsan nata ido,ganin ya soma kumbura ta tabbatar ta samu targad'e...
Dafe kai tayi tana jin rad'ad'in da yatsan ke mata har tsakiyar kanta...
Lallai wannan yarinya koi ja'ira,amma babu komai ta ciji lips enta,
''Zanyi maganinki''
Ta furta ciki².....
*************
Haka ta shige d'aki ko tunanin sallah batayi ba,tana shiga kuwa ta turo k'ofar d'akin nata...
Kwanciyarta tayi take kuwa bacci yayi awon gaba da ita....
K'arfe 9:15pm MALAM BUBA ya nufo gidan nasa,da tunanin ko LADIYO ta ga dama ta dawo?
Tun da ya tunkaro gidan gabansa ke faman fad'uwa...
Bai kawo komai a ransa ba,haka ya shigo gidan,k'ofar dake jingine ya d'aga
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 3 Chapter of 41