ABBA ba ya kama hany ya tafi....
Idan baka manta ba ai ka tuna lokacin da akace ABBA yayi accident ko?"
Nanma kai KHALEEL ya sake d'agawa...
"Abunda ya faru a wannan lokacin duk shiri ne wanda MAMA da babbar aminiyarta HAJIYA LAURA suka shirya duk dan kada duniya ta zagesu akan abunda ya faru shi yasa suka b'atar da hankulan jama'a amma ABBA yaba raye,k'asar ya bari gaba d'aya"...
Shiru BB yayi yana dafe kansa,KHALEEL dake zaune ya hau fad'in
"Toh!amma ta yaya kai kasan wannan labarin?"
Sai da yayi wani murmushi mai ciwo tukun sannan yace
"A lokacin da akace ABBA ya rasu idan zaka tuna ai ba a kawo gawaba ko?
Toh bayan y'an zaman makoki sun watsene na samu MAMA kan maganar,akan lallai sai ta fad'amin abunda yake faruwa ita kuma tak'i bayan na takura matane kan zan sanar da hukuma idan har bata fad'aminba shi ne ta bani wannan labarin da kaji a yanzun"....
"Innalillahi wa-inna ilaihi raji'un"
KHALEEL yake ta maimaitawa had'e da dafe kansa,ya rasa me ke masa dad'i.....
《《》》
Mik'ewa ZUHRA tayi a fusace daga kan MAMA da ta fad'i tana fidda hannu ta wankewa FATAHIYYA fuska da mari
"Ke wace irin sha³ ce da zaki fad'a mata wannan maganar bayan kina kallon yanayin da take ciki?"
Bata iya maganaba saboda tsananin b'acin rai da kuma haushin FATAHIYYA da take jin kamar ta rufe ta da mugun duka a guje kuma ZUHRA ta juya ta yanki hanyan cikin parlor,a wayan MAMA ta lalubo number BB..
Kira ta shiga danna masa amma sam yak'i d'aukan ko guda d'aya,ga phones en a gabansa,sai dai baya jin zai iya d'aukan kiran nata...
Ganin bashi da niyyan d'auka KHALEEL ya mik'a hannu tare da answering call en,yanayin muryanta ya tabbatar da ba lafiya k'alauba....
"Hello BB dan Allah ka dawo gida babu lafiya"
Duk maganar da ZUHRA ke yi bata fuskanci ko dawa take maganaba,sai da taji yayi magana
"Me ya faru?"
"Wayyoo Allah!dan Allah MALAM ina mai wayar?shi nake nema please"
Jin abunda ta fad'a yasa ya d'ago yana kallon BB tare da mik'a masa wayan..
Ko kallonsa BB baiba bare yasa ran zai amsa wayan,hakan da yayi ya tabbatar masa da ko kwana ne zasuyi a haka..
Hands free yasa wayan,cikin sheshshek'ar kuka ZUHRA ke fad'in...
"Hello!Hello!!
Dan Allah MALAM ka bawa mai wayar tun kafin mu rasata"...
Fizge wayan yayi a hannun KHALEEL cikin wani irin voice yake tambayanta
"CWEETY me ya faru kike kuka?"
Duk yanayin yadda yajita ya gama d'aga masa tunani..
"Hello BB dan Allah ka dawo gida MAMA ce ta fad'i kuma bata motsi"
"What!!!" ya fad'a yana mik'ewa...
Ko gama sauraren abunda zata fad'a baiba yayi hanyan fita,da gudu-gudu,shima KHALEEL cikin sauri ya mara masa baya...
Ko kafin ya fito har BB yayi waje,haka ne yasa shi saurin yiwa motan key ya fice daga gidan...
Fitowansa ya tarar har yayi nisa cikin tafiyan da bai saba irinta ba,sai dai da gani kasan yana cikin damuwa...
Tun kafin KHALEEL ya k'araso yake masa horn bai tsayaba,har ya k'araso kusa da shi,motan ya bud'e tare da masa magana
"MAN ka dakata hakanan da wannan tafiyan kazo mu wuce"
Juyawa yayi ya kalleshi cikin sakanni ya fad'a cikin motan,da mugun gudu suka bar unguwan sai gidan su BB.....
《《》》
Gudu suke shek'awa cikin mota, kamar wad'anda zasu tashi sama,duk da sun tserewa gurin da mutane zasu iya samunsu su cimmusu hakan baisa sun saurara ba...
Fizge² take yi cikin motan duk kan ganin ta kub'uta,sai kai hannunta take tana k'ok'arin jan handle en dake jikin k'ofan...
Mari BIGGY ya shek'a mata had'e da tsawa mai k'arfi wanda ta maidata cikin hayyacinta...
Kanta ta kifa bisa cinyoyinta ta shiga rera kuka,su ko na cikin motan suna saurarenta amma babu wanda yayi yunk'urin dakatar da ita,ratse hanyan suka dinga yi wanda k'arshe dai sai gasu a *NA'IBAWA FLYOVER* nan suka ci gaba da fella gudu babu sassauci....
Straight suka yanki hanyan *BAUCI STATE* ba tare da sun sauraraba..
Tun ASHNA na kallon hanya har ta b'ingire take bacci yayi gaba da ita ba tare da ta shirya masaba...
《《》》
Ko gama tsaiwa motan baiba ya fito dan baya jin zai iya tsayawa har BABA MAI GADI ya bud'e musu get..
K'ofan ya tura ya shiga,a nan yayi arba dasu duk sun lullub'e MAMAN ko isashshiyar iska bata samu,ba tare da ya kulasuba ya shiga maidasu gefe,yana yin arba da MAMA bai jira jin komaiba kuma ba tare da yayi shawara da kowaba ya shiga k'ok'arin d'aukanta...
KHALEEL da ya gama parking a gurin ya fito cikin sauri,kama masa MAMAN yayi suka sa a mota,ZUHRA tuni ta shige back seat kusa da kan MAMA suma suka shiga KHALEEL ya felli motan a 360....
*AKTH* suka wuce da ita direct babu jimawa aka shiga da ita EMERGENCY...
Sama da 2 hour's likitoci na kanta babu wani ci gaba da aka samu...
Zagaye gurin kad'ai BB yake hankalinsa duk ya gaza kwanciya,ZUHRA ko banda kuka babu abunda take,KHALEEL na kusa da ita sai hak'uri yake bata kan tayi shiru komai zai zama dai² amma abu ya faskara,saima k'aimi data k'arawa kukan nata...
Fitowan babban likitan yasa su mik'ewa,wanda bai tsayaba saima cewa da yayi su biyo shi office..
Binsa kawai suke har suka isa office en sai da ya tabbatar sun zauna tukun ya shiga magana
"Amm!kune wad'anda kuka kawo mara lafiyan ko?"
KHALEEL yayi k'arfin halin cewa
"Ehh!doctor"
"Ok toh amma yaya alak'arku take da ita?"
Nanma dai ya sake bashi amsa da
"Y'ay'anta ne"
Sai da DR en ya kallesu tukun,ya mik'a hannunta saman pore head yana share zufan da ya tsatstsafo masa da handkeey
"Am so sorry...
Gaskiya mara lafiyanku sai dai kuyi hak'uri...............
*~Wayyooo shi kenan MAMA ta auza,ta wula.......~* 😨😨
*~#KEEP FOLLOWING........~*
*_REAL SMASHER._*
💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*©®2018*
*26/ʝųŋɛ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*3⃣5⃣*
*"S* ai dai kuyi hak'uri amma gaskiya mara lafiyan naku tana cikin mawuyacin hali wanda tun shigarmu har kawo lokacin dana fito bamu samu ta farfad'o daga dogon suman da tayiba...
Amma abunda ya d'auremun kai kuma abun damuwan shi ne akwai wani al'amari da ya faru wanda yayi matuk'ar tsoratar da ita da yayi sanadiyyar fad'awarta wannan hali,bayaga numfashinta da yake fita da sauri²...
Cikinku akwai wanda ya sanar da ita wani abune?ko kuwa kun san abunda faru da ita?"
A tare suka kad'a masa kai,alamar babu...
To gaskiya sai kun kiyaye ba ko wane irin lokaci ake sanar da mutum wani abu da ya faruba,matuk'ar tsoro ya bayyana a tare da shi ko a tashe shi daga bacci dan sanar da shi hakanba,dan kuwa yin hakan ka iya jawowa mutum matsalar k'wak'walwa,wanda ba a fatan hakan ya faru...
Sannan abu na gaba gaskiya muna buk'atar namiji babba,idan kuma kuna da wata da zata iya kula da ita to ya kamata ace kunzo da ita duba da har yanzun bata farfad'oba sai dai munyi nasaran saita numfashinta"....
Shiru sukayi dukansu suna nazarin al'amarin,a hankali BB ya d'ago kansa idanunsa sun soma sauya colour zuwa red,a kan ZUHRA ya saukesu,sam ya kasa magana sai kallonta kad'ai da yake yi,zuwa wannan lokacin damuwarsa ta dad'a ninkuwa fiye da kowane lokaci da ya wuce....
KHALEEL ne yayi k'arfin hali bayan dogon ajiyan zuciya daya sauke,sannan ya bud'e baki da k'yar ya fara magana,dan kam suna buk'atar k'arin bayani kafin du samu mafita kan nemo wanda zai zauna da MAMA
"ZUHRA me ya faru da MAMA ne kafin muzo gida?"
Sai da ta saita kanta ta kuma goge fuskarta da tayi kacha-kacha da hawaye sannan ta kallesu su duka ukun DR,BB da kuma KHALEEL en,wani sabon hawaye ne ya sake tahowa,suna shirin zuba ita kuma sai kokawa take yi da su gurin ganin ta hana hakan afkuwa...
"BB ASHNA"
Abunda ta iya fad'a kenan hawayenta suka k'arasa zubowa...
Wani uban tsaki BB yayi wanda yasa su kallonsa,tabbbas KHALEEL yasan mutumin nasa yana cikin matsananciyar damuwa...
Hannunsa ya d'ora kan sholder ensa yana d'an shafashi kad'an alaman rarrashi
"MAN take it easy,anything will be fine,ok?"
Bai kula shiba kamar yadda ko kallonsa baiba,saima k'ure ZUHRA da yayi da kallo wanda har yafi na farko,burinsa bai wuce tayi magana ba,amma ita ta kasa gane hakan dan ya gama damuwa yaji,k'arshe kuma sai kawai ta wani ambaci sunan ASHNA kuma tayi shiru,to shi ina ruwansa da wata ASHNA?yarinyar da sam ba ganin girmansa take ba,shi duk zaman gurinma ya isheshi saboda takaici,a fusace ya mik'e tare da hararan ZUHRA dai² lokacin ta d'ago idanunta suka sauka kansa yana cillo mata wata uwar harara.....
Shirin barin gurin da sukaga yana yine yasa su kallon-kallo,a hankali ta rik'o hannunsa tana kad'a masa kai....
Cike da fushi ya juyo
"Da Allah ni sakeni kin sa sai jiranki muke muji abunda ya faru kin tsaya jama mutane rai,ko an fad'a miki MAMA jiranki za tayi ki gama kukan kafin ta tashi??
To idan baki saniba daga nan zuwa kowane irin lokaci zata iya mutuwa"...
Da sauri ta d'ago ta kalleshi,dan tunda ya fara mata masifar ta sunkuyar da kanta,hawaye nabin fuskarta take fad'in
"Dan Allah YAYA kayi hak'uri zan fad'a"...
"Yi shiru ZUHRA ki sanar damu abunda ya faru kinga lokaci na dad'a k'urewa,kuma kinga DR mu yake jira yaji abunda yasa ta shiga wannan halin kafin musamo mafita....
Maza kinji fad'a mana me ya faru".....
Har lokacin BB na tsaye kamar wanda aka sama pause,ya kasa barin gurin kamar yadda ya kasa raba hannunsa dana ZUHRA...
Shi kuma DR yana zaune sai kallon ikon Allah yake tsakanin wad'annan mutane..
Abunda ya faru ta kwashe ta sanar da su tun daga shirin tafiyansu school har zuwa lokacin da MAMA ta yanke jiki ta fad'i....
"Innalillahi wa-inna ilaihi raji'un"
Shi ne abunda ke fitowa daga bakunansu,ba iya su kad'aiba hatta da DR en shima abunda yake maimaitawa kenan...
Office en yayi tsiit babu wani sauti dake fita a cikinsa,sunyi shiru kowa da abunda yake tunani...
KHALEEL ne ya katse shirun bayan ajiyan heart da ya sauke tare da fad'in
"Dude gaskiya bai kamata muci gaba da zama a nanba,yanzun yaci ace mun sanar da hukuma b'atan yarinyar nan,tunda kaga wannan shi ne na biyu ya kamata ace mun dakatar da faruwar hakan".....
Ko kallo bai ishe shiba bare ya sa ran zai motsa daga inda yake,kallon mutanen gurin kad'ai yayi tare da ficewa cikin sauri kamar zai kifa...
A baya ZUHRA ta shiga binsa da gudu-gudu saboda yayi mata nisa sosai lokacin da ta fito.....
《《》》
Daf da zasu shiga garin BAUCHI ya d'auki waya yana pressing,number HAJIYA LAURA ya laluba tare da kara wayan a kunne...
Bata wani b'ata lokaci ba ta d'auka maganarta cikin isa da tak'ama
"Hello!BIGGY ya akayi kuma?ina d'azun muka gama magana?"
Yana dariya cikin wani irin voice had'e da shafa face en ASHNA dake tsakiyansu tana shek'a bacci yake fad'in
"HAJAJJU!Allah ya taimakeki, yau dai munyi nasara kan wannan yarinyar,dan yanzunma haka mun d'auki hanyar BAUCHI saura kad'an mu k'arasa"..
"Kaiii amma nayi farin cikin da na jima banyi irinsa ba...
Ammmm!yanzun ina zaku sauka kenan?"
Tayi tambayan tana jiran taji me zai ce da ita..
"HAJIYA ina ganin da mu kama hayan gida kawai kinga sai mu ajiyeta a nan har zuwa adadin kwanakin da za muyi"
"A'a BIGGY kada ku fara,taya zaku samu gidan haya a hannun mutanen garin da basu sanku ba,bayan wannanma idan aka ganku da yarinya me kuke so ayi tunani,kana dai sane da cewa mutane zasu sanar da hukuma muddin aka ganku da yarinyar nan.....
Abunda za kuyi kawai ku kama hotel a matsayinku na matafiya.....
"Gaskiya HAJIYA bana jin hakanma mafita ce,dan kuwa duk wanda ya ganmu da yarinyar nan tabbas zai gane satota mukayi dan kuwa yarinyar kayan makaranta ne a jikinta...
Ni ina ganin dai gaskiya ko dawowa za muyi KANO muna da gida kuma babu wanda zai san wani abu da yake faruwa"...
"To kai da kasan da haka har ka bari kuka bar garin ko ma?"
"HAJAJJU! wallahi na shiga wani shu'unin ne shi yasa na kasa tunawa,amma bari kawai mu dawo,tunda tahowarma ba wani amfani garetaba"
"Ehhh!toh amma BIGGY kana ganin dawowarku a wannan lokacin babu wata matsala da za a samu?"
"Babu hajiya,ina ganin tun kafin lokaci ya k'ure mana gara mu dawo kawai,ko ya kike gani?"
Cike da jin dad'i HAJIYA LAURA ke magana,tana sakin wani uban smiling
"A'a!tunda ka ce babu wata matsala dan kun dawoma babu wata damuwa kuyi hakan"....
Juyawa BIGGY yayi ya kalli ASHNA da ta zame ta jingina a jikinsa tana bacci,sai da ya lashe lips ensa garin tunani har baima san lokacin da HAJIYA LAURA tayi magana ba...
"Hello!hello!!
BIGGY kana jina kuwa?"
Yanayin yanda tayi maganar yasa shi dawowa daga duniyar da ya lula
"Ehhh!HAJIYA ina saurarenki"
"Yawwa to ina so ku kula da hanya,sannan kada ku kuskura kuyi saken da za a gane inda kuke...
Ina fatan dai ka fahimci abunda nake nufi ko?"
"Ehhh!HAJIYA za a kiyaye"
"Toh shi kenan sai na jiku,Allah ya kiyaye hanya"
Daga haka sukayi hanging kiran,kowa ya shiga duniyar tunani....
《《》》
Yau tun safe da ta tashi take jin jikinta na mata ciwo,wanda ta rasa dalilin faruwar hakan..
A haka ta lallab'a ta shirya,ko abinci bata ciba take shirin fita...
Kuran ta shiga kiciniya zata fita da ita BABA ZUWAIRA ta dakatar da ita
"Haba KHUBRA yanzu haka kika zab'i zama?"
Tsayawa tayi tare da juyowa tanama BABA ZUWAIRA kallon rashin fahimtar tambayanta,kafin ta bud'e baki tana shirin magana BABA ZUWAIRA ta rigata..
"Yanzu fisabilillahi ace ki tashi ba tare da kinci komaiba kuma ki hau shirin fita...
To waima idan kin tafi baki ci komaiba zaki iya aiwatar da abunda kika fita dominsa?"
Shiru tayi ta ci gaba da tsaiwa a gurin,sai dai wannan lokacin kanta na k'asa ta kasa magana...
Jikinta ne ya sake yin sanyj jin furucin BABA ZUWAIRA,inda nan take ta tafi tunanin rayuwarta ta baya..
"Lokacin da take neman abinci ido rufe ta sanya a cikinta,a lokacin da take daf da mutuwa,amma ta rasa mai taimaka mata,yau gashi a rayuwarta taci karo da inda ake mata fad'a idan zata fita ba tare da taci abinciba"...
Wasu siraran hawaye ta juya ta goge,sannan ta k'irk'iro murmushi lokackin da ta baro gurin da take
"Eyyah!BABA yau tun da na tashi ne bana jin dad'i shi yasa banyi tunanin cin komaiba"
Sai da BABA ZUWAIRA ta wurga mata harara kafin tayi magana
"Dama haka za kice,abu da ko zuba abincin kikayi ba wani cin na kirki kike ba,kina cin abinci kamar ana bawa kyanwa"
"Haba BABATA ina cifa da yawa"
Harara ta dad'a wurga mata
"Ke tafi can kya dai fad'awa wanda bai saniba,amma ba dai ni ba"
Dariya sosai KHUBRA tasa,ta jima tana dariyan wanda har tasa BABA ZUWAIRA tsayawa da abunda take tana kallon ikon Allah......
《《》》
"Dan Allah BB ka tsaya ka ji"...
ZUHRA ce mai yin wannan maganar lokacin da ta kusa taradda shi,k'in tsayawa yayi ita kuma ta ci gaba da bagging ensa kuma ba tare da ta saurara da binsaba...
Daga bayanta ta tsinkayo maganar KHALEEL
"K'yale shi kawai ZUHRA kada Allah yasa ya tsaya"
'Dan juyawa tayi kamar za tayi kuka
"Dan Allah YAH KHALEEL kace ya tsaya....please"
"K'yaleshi dan kansa zai dawo kinji"
Kanta ta d'aga alaman ta ji,sannan suka jera suna tafiya kowa da inda zuciyarsa ta karkata...
Dai² d'akin da aka kwantar da MAMA suka k'araso anan suka tarar da BB zaune ya dafe kansa da hannayensa duka biyu yayi shiru...
Tunaninsa bai wuce ta yaya zasu samo wanda zai kula da MAMA ba a zaman da za tayi a asibitin...
Yayi zurfi cikin tunani KHALEEL ya zauna kusa da shi yana kallosa,phone ya d'auko cikin contact nasa ya shiga bincike,nan ya lalubo number D.P.O,har ya gama magana da shi BB bai saniba...
Magana ya shiga yi masa amma sam bai san yana yiba har sai da ya girgiza shi,sannan ya kalle shi da rinannun idanuwansa da b'acin rai ya gama rine su
"MAN yanzufa ba lokacin tunani bane mafita ya kamata mu nema...
Waye ya kamata mu samu da zata zauna da MAMA?"
Shiru BB yayi ya kasa magana zuwa wani lokaci cike da jimami ya fara magana
"Irin abunda nayita fad'awa MAMA kenan lokacin da nake tambayarta danginmu...
Yanzun ga irinta nan,waye zai zauna da ita a wannan halin?duk dad'in k'awaye bai kai d'an uwaba,amma MAMA tayi watsi da danginta da dangin mahaifinmu"
Kallonsa kawai KHALEEL yake cike da rashin fahimta
"Kamar yayafa dude?"
Murmushi yayi mai ciwo kafin cikin jimami,takaici,haushi ya fara magana
"Tun bayan dawowarmu garin nan daga DUTSE dai² da rana d'aya MAMA bata tab'a komawa garin nanba,y'an uwanta da suke ganin tana cikin rufin asiri zata taimaka musu,k'arshe duk wanda yazo sai dai ya koma yana k'unar zuciya,saboda MAMA korarsu takeyi bayan ta ci musu mutunci"
"To amma duk da haka MAN ya kamata mu hanzarta nemo wanda zai zauna da itan"
Duk sunyi shiru sun kasa tsai da matsaya akan wanda zasu samu ya zauna da MAMA a wannan yanayin da take tsakanin *RAYUWA DA MUTUWA*.........
*~Fan's ku taimako da d'an jinya,kunga dai MAMA ta koma.... Please ba don halinta ba..~*
😤😤😤
*_~TEAM KHUBRA.~_*
*~REAL SMASHER.~*
💠
*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*
🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹
*©®2018*
*28/ʝųŋɛ,2018*
*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹
_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*
_Gaskiya na yarda kamar yadda kukayi alk'awari na gani kuma na tabbatar,babu abunda zanyi na saka muku face ci gaba da posting a duk lokacin da Allah ya bani ikon yin hakan,ina godiya kuma naji dad'in comment's enku.._
_Saboda haka zamu ci gaba daga inda muka tsaya in sha Allah SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV da kuma AUFANA suna tare da ku a ko wane lokaci kuma zamu ci gaba da tafiya tare,Allah ya bar k'auna da zumunci..._
_jinjina ga d'aukacin group's en_
*SMASHER & HUBBEEY NOVEL'S GROUP 1 & 2.*
*SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE NOVELLA*
*SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE COMMENT'S ONLY*
*MUSLIM LADIES WW*
*SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE KITCHEN*
*BARRISTER ALEEYAH & MUHIBBAT NOVEL'S*
*SAWWAMA NOVEL'S*
*LEEMA NOVEL FAN'S*
_Allah ya bar zumunci da k'aunar junah..._
*~________________________~*
*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_
*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._
*AND*
_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._
*3⃣6⃣*
*K* allon da taga BABA ZUWAIRA nayi mata ne yasa ta gimtse dariyar tata,tana d'an murmushi ta k'arasa kusa da ita ta zauna tana dafa k'afarta
"Allah kuwa BABATA ina cin abinci dayawama bakiga nayi kiba ba,kuma nayi k'arfi....
Kallifa kiga yadda nake iya d'aukan wad'annan robber en"
Kallonta kad'ai tayi ba tare da ta iya maganaba saboda yadda taga ta hak'ik'ance akan maganar ne yasa tayi murmushin yak'e wanda akance "yafi kuka ciwo"...
Kafin ta samu k'arfin guiwar yin magana
"Kayya dai KHUBRA wannan ba bigiren k'arfi bane,banda abunki ina kika tab'a ganin mace tayi irin wannan sana'ar?
Baya ga hakama su kansu mazan bakiga yadda suke wahalaba,kuma duk da haka ba kowa ne yake juran wahalar da wannan sana'a take da ba..
Ni kaina dan dai tun farko ina tsoron rasa ki,abu na biyu kuma tausayinki da rashin sanin hannun da zaki fad'a yasa ban musanta miki sana'ar nan da kika ce ita kike so...
Amma har ga Allah wannan sana'a bata kwantaminba"...
'Dan murmushi tayi ba tare da ta sake cewa komai akan abunda BABA ZUWAIRA ta fad'aba ta hau fad'in
"BABA bani abinci naci sai na tafi kinga dama ban shirya da wuriba,kada rana ta yimin a hanya"
Itama BABA ZUWAIRA ganin KHUBRA ta bagarar da maganar yasa tayi shiru bata sake cewa komai ba,saima abincin da ta mik'o mata...
Duk wani motsi da abunda take yi tana cin abincin,idanun BABA ZUWAIRA na kallonta...
Ita kad'ai tana cin abincin kamar bata so tana yi tana yatsina face enta kamar wacce akawa dole haka take cin abincin...
Da kyar take iya had'iyan abincin kamar mai shan magani....
Kai BABA ZUWAIRA ta gizgiza tana kallonta da tausayawa,yau kam ta rasa dalili da yasa y'artata take wannan abun
"Jikin ne yake damunki?"
Tayi tambayar tana dad'a k'ureta da ido..
'Dago idanunta tayi ta kalleta tana kad'a mata kai
"Wollahi BABA kwana biyu ina jin jikina babu dad'i,kuma na yau sai nake ji yafi na ko wane lokaci"
"Ayyaahh!sannu,amma toh me yasa kike son fita duk da bakya jin dad'i kam?
Ina ganin dai yau kam ki hak'ura da fita,idan Allah ya kaimu gobe sai ki je ko?"
Shiru tayi bata sake magana ba,har BABA ZUWAIRA ta gama shirinta,sai da tazo fita ta kalli KHUBRA
"To ni dai zan fita,kuma abunda na fad'a miki d'azu kiyi zamanki a gida gobe idan Allah ya kaimu kya fita,kin ji ko?"
"Toh BABA Allah ya kiyaye hanya,Allah ya
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 17 Chapter of 41