ne sannan zai samu wannan kuÉmɗin. *Karo* na farko kenan a rayuwar shi da ya ji yana so ma ya san wai daga ina kuɗin ke fitowa ne a cikin gwamnatin? Dad dai ya jima yana taɓa harkar siyasa, ya kuma san yana bada gudummuwa sosai saboda tun kafin ya shiga siyasar mutum ne da ya tara tarin dukiyar da ta zarta misali, to amma me ya sa shi baya biyan nasu daga asusun shi idan biyan ya zama dole? Tun fa da ya shiga makarantar soja aka buɗe mishi count ake tura masa wannan albashin, gashi ba ka rasa komai ba na rayuwa, dan haka babu abinda yake da kuɗin face siyan mai tsada ya hau ko ya saka ko ya shafa. Albashin shi kuma yana ƙara bunƙasa harkar noma da kiwon shi ne da har ya gawurta a harkar yanzu haka.
Anna ya sake duba da tausasawa yace " Anna Ina Dad?"
Da sanyayyan murmushi a fuskar ta ta bashi amsa da "Yana falon shi." Jinjina kai yayi kafin ya ɗan miƙe yana aje Islam, saida ya yi tsaye sannan ya kalli Anna yace "Anna, wai daga wane asusu ne kuɗin nan ke fita?"
Wani kallo duk suka mishi musamman ma Anna, sai kuma ta kawar da kai tana wani murmushi tace "Me ya sa ka tambaya? Kai ba'a tura maka naka bane?"
Sai da tayi maganar ma ya ɗan laluba aljihun wandon shi, jin bbu waya sai kawai yace "Tambaya ce nayi."
Sai da ta girgiza kai irin ba zaka ƙureni ɗin nan ba sannan tace "To ban sani ba dai nima."
Ta faɗa tana wucewa dan zuwa kiran Dad ɗin, bayan ta ya bi a nutse zuwa falon, Meem da Angel da suke wasa tare da Islam ƙura masa idanu sukayi, amma suna ganin sun nufi ɗakin Dad sai suka ci gaba da wasar su sun fahimci ba nan zai bar su ba kenan, Manal ce tayi murmushi ta duƙo tana shafa kan Angel tana cewa "Cute baby, idan zan tafi America da ku zan tafi, na san Bro zai sake samo wasu daga Paris idan ya tafi, za ku bi ni?"
Humed da ya miƙe tare da matar shi *Hafsata* yana faɗin "Ba zasu iya rayuwa babu shi ba."
Nawal ce tace "Shi ma kuma haka ba." Taɓe baki Abrar tayi saboda takaicin yadda ita ko kallon ta ma Aswan bai yi ba ya tafiyar shi, ita bata san me ta tsare masa ba? Ko ba ya ƙaunar zaman ta gidan ne ko me? Amma dai gaskiya tana jin haushin shareta da yake yi ƙwarai da gaske. Da sallama suka shiga falon Dad dake shirin fita ya amsa musu har da yin murmushin ganin Aswan a bayan Anna, gaishe shi yayi ya amsa da kulawa kafin suka ɗan zubawa juna idanu na sakanni, kawar da kai Dad yayi yana ƙarasa daidaita zaman hular shi da wani irin murmushin nan saboda ya gane da magana a bakin Aswan yace "Uhum! Ina jin ka?"
Ba tare da kwalo kwalo ba ya ɗan matsa gefen Anna ya zauna kan kujera a ladabce yana duban Dad ɗin yace "Dad, minti biyu dan Allah, zamu iya yin magana?"
Ba tare da Dad ɗin ya kalle shi ba yace "Akan me? Faɗi ina jin ka, ina da fitar gaggawa ne da take da buƙatar sammako."
Sai kuma ya kalli Anna yace "Ni zan fita madame, ba komai?"
Murmushi tayi tana ɗan girgiza kai tace "Ba komai mon Excellence, Allah ya tsare."
Jinjina kai yayi yace "Ok, ba ni agogona a ɗaki?"
Da girmamawa ta nufi ɗakin, sannan yayi tsaye yana fuskantar Aswan ya sake cewa "Ina jin ka?"
Saida ya sauke numfashi ya dubi Dad ɗin yace "Dad, dan Allah ka wa Chef magana, su sassauta hukuncin da suka min, Dad, ba zan iya jurar tashi da safe ba tare da zan tafi CEN ba, please."
Ƙura masa idanu Dad yayi na lokaci, sai kuma ya girgiza kai ya na sakin wani malalacin murmushi ya ɗan juyawa gefen shi yace" Aswan, ni tun jiya na nemi irin wannan alfarmar da kake nemana da ita yanzu a gaban Chef ɗin, amma bai min ba."
Ɗan haɗe fuska Aswan yayi da alamar tashin hankali yace" Dad kai ɗin ma? Amma fa kai da Chef aminai ne, zai iya yi maka komai."
Ba tare da Dad ya daina murmushin nan ba yana ɗan gyara zaman babbar rigar tsadaddiyar shaddar dake jikin shi kalar maroon sai ƙyalli take cikin tausasawa a nutse yace" Yess, ba zai iya bane da ya min, amma da tuni ka samu wata matsayar ba wannan ba."
Gyara zama Aswan yayi cikin kujerar yana ƙanƙance idanu a tausashe sosai yace" Dad, ban fahimta ba? Wace alfarma ka nema a wajen Chef?"
Saida Dad ya kalle shi sosai daidai da fitowar Anna sannan yace" Ce wa nayi ya koreka daga aikin soja kora ta har abada."
A hargitse Aswan ya miƙe tsaye ya furta" What!" Agogon da Anna ta miƙowa Dad ya miƙa mata hannu tana sagala mishi, a rikice ya ƙara matsawa kusa da su yana faɗin" Dad, ba zan iya wani aiki ba aikin soja ba, na fi son shi saboda shi ne rayuwata, Anna..."
Ya kira sunan ta yana kallon ta kamar zaiyi kuka yace" Anna ina son aikin nan, ki wa Dad magana kar ya sa baki a rabani da aikina, ni sam ba zan iya rayuwa ba tare da ina zuwa compg. ba, ba zan iya zuwa wani wurin aikin ba tare da ina jiyo muryoyin mazan da suka amsa sunan maza suna waƙe a lokacin da suke raha ko kuma suna hargagi yayin tashin hankalin su ba, Dad, ba zan iya jurar na shafe wani lokaci ba tare da ina jin sautin fitar harsashi daga bindiga ba, a taƙaice ma Dad, ni fa ina ganin kamar zan cika namiji ne kawai idan ina aikin nan."
Tunda ya fara maganar nan Dad da Anna ke kallon shi kamar baƙo, sai da ya dasa aya Dad ya sauke numfashi yana jinjina kai a nutse sosai yace" E! Na gane, kenan duk mu nan mata ne da bamu saka kakin soja ba Aswan?"
Da sauri ya girgiza kai da ladabi yana ɗan ja baya kaɗan cikin wata kasalalliyar murya yace" Ba haka nake nufi ba Dad, am so sorry."
Tana gama saka mishi agogon ya dube shi da kyau ba alamar wasa yace" Aswan, saurareni da kyau ka ji, an dakatar da kai aiki na wata biyar, ba zaka zauna min haka ba har wannan lokacin, dole ne ka kama wani aikin, zan baka zaɓi uku, kuma dole ka zaɓi ɗaya a cikin su, na farko, akwai matsayin DG na kamfanonina dake ƙasashen waje wanda duk kun ƙi zama can kai da Humed, na biyu kuma akwai matsayi na duk wata babbar kwangila da za ta fito daga gwamnati, to kai ne mai bayar da ita ga wanda ka so, sai kuma na uku shine ka zama DG na masana'antar mai na ƙasa baki ɗaya."
Anna ya kalla dake tsaye tana duban su yace" Idan ya zaɓi ɗaya a ciki ki sanar da ni, kafin magrib matsayin zai hau kan shi da izinin Allah."
Ficewa yayi ya barshi dafe da gaban goshin shi har yana ɗan taune leɓen shi na ƙasa, saida Anna ta kalle shi tace "Tom kaji, wane zan faɗa masa ka zaɓa kenan?"
Da ɗan sauri ya kalli Anna, sai fuskar ta da yanayin ta suka nuna mishi kamar tana son ƙular da shi, dan haka ya rikbceo hannayen ta biyu a cikin nashi yana kallon fuskar ta yace "Anna, idan ba aikin soja ba bana son kowane aiki, son da nake masa ne ma ya sa na kasa yarda wata mace ta shiga rayuwata, saboda idan na fara haɗa aikina da mace to zan fara samun matsala, ina so ne nayi aikin soja da gaba ɗaya rayuwata, idan na tafi aikina to ya zama kune kawai zan kira na gaishe ku, amma ba nauyin macen da kana fagen daga ba za ta iya haɗa maka lissafi da sabgar cefanai, lalle, kitso, fita unguwa, uwa uba kuma ƙorafi akan rashin bata lokaci, wannan ya sa Anna har yanzu na kasa cika miki burin ki akan aure."
Sakin hannayen ta ya yi yana rusuna kallon shi daga gare ta yace" Zan samawa kaina wani aikin Anna, ba sai ya sama min da kan shi ba, sannan, ki gaya masa ya daina roƙon Chef akan ya kore ni a aikin nan, please."
Juyawa ya yi ya fita da sauri zuciyar shi na tafasa sosai yana jin kamar ya naushi wani, magunan shi na hango fitar shi kuma ya nufi ƙofar fita suka bi bayan shi a sukwane, haka ya bar gidan ya koma na shi ya shiga tunanin abubuwa da dama, daga bisani maganar motar asibitin nan ce ta sake dawo masa a lisafi da Col. Garba y yi, wayar da ya bari nan ya ɗauka ya kira ɗaya daga cikin jami'an da sukayi gadi a wannan ranar wanda shi ya saka su, nan jami'in ya tabbatar mishi lallai motar ta wuce amma ta asibitin mahaifin sa ce, sai dai gaskiya su basu san me ye a ciki ba tunda ba su duba ba dan sun gan ta cikin ujila da alama ta ɗauko marar lafiya dake buƙatar agaji. Ya jima wurin nan zaune yana aiki kira da tambaya kan wasu abubuwa da suka shige masa duhu har da kan albashin da ake musu biya shi da ɗan uwan shi da mahaifiyar su da ƙanwar mahaifin su da shi sai yau ne ma ya ji yana so ya san biyan nasu na me ye ake yi? Sannan daga wane asusu ake biyan na su? Yana so ya sani? Dole ne ya sani, dan ba zai juri ganin talakawa na rayuwar ƙunci da neman abinda za su ci ido rufe, amma su da suke da shi kuma ana sake loda musu, ƙarshe sai banzatar da dukiyar suke saboda ba su suka nema da gumin su ba sannan ba su san me za su yi da ita ba?
*YUSRAH TURAKI*
Hannunsa ta kama tana masa murmushi ƙasa ƙasa ta ce" Malamin gidan mu, Autan Mama how far?"
Shima ya yi mata murmushi yana cewa" Sannu da aiki aunty Yussy, bari in kawo miki ruwa."
Duk ya yi maganar ne yana ajiye jakarta a ɗakin su sannan ya nufi tulu ya ciko mata moɗa da ruwa mai sanyi ya kawo mata ɗakin Mama a lokacin da suke gaisawa da Maman, a sanyaye ta gyara zaman ta tare da kamawa Maman ninkin da take yi na mayafanta, kallo ɗaya ta mata ta karanci yanayinta ta ce" Kin yi sallah kuwa?"
Girgiza mama kai tayi tana jiyo muryar Hannah daga ɗakin su dake faɗin" Yussy, rigar ki tayi datti ne na haɗa da ita na wanke miki?"
Yusrah kallon ƙofar ɗakin tayi cikin murya kamar mai jin bacci tace" E aunty, bari na cire."
Sai bayan ta bata amsa ne ta kula da kallon da Mama ke mata, ma'ana tana jiran amsar tambayar ta, dan haka ta sake girgiza kai tace" Yanzu zan yi Mamanmu."
Yunƙurawa tayi za ta miƙe, sai kuma Mama da ta fahimci kamar akwai damuwa a fuskar ta tace" YUSRAH lafiyarki kuwa?"
YUSRAH ta kalli Mama wannan karon ma da kula, ba su saba ɓoyewa mahaifiyar su komai ba, saboda tun suna yara ta yarda ta zama ƙawar su, dan haka ko da suna da ƙawa to bayan aminiyar su (Mahaifiyar) ne, nutse ta ce" Mama, wani abu ya ɗaure min kai, yau wata mata aka kawo, ni na dubata, tabbas tana iya haihuwa da kanta har ma tana daf da haihuwar, sai kawai aka ce ba zata iya haihuwa da kanta ba, kuma kin san mu yara ne a cikin likitocin ba lalle ne a sanar mana abinda ba lalle sai mun sani ba, treatment ɗin ta kawai ya shafe mu, shi aka sanar mana shikenan, sai kawai aka shige da ita ɗakin tiyata, shine abin ya ɗaure min kai..."
Sai kuma ta ƙarasa miƙewa tana ɗan gajeran tsaki tace" Ko da yake yanzu matan masu kuɗin nan basa son wahala, sun fi ganewa aiki fiye da su haihu da kansu."
Da ɗan mamaki Mama ta ce" A'a fa Yussy, in ba ciwo ba anya akwai wanda zai zaɓi a fasa shi a ciro masa yaro? Bayan ance fasawar nan sosai yake taɓa lafiyar mutum? da zarar an fara yiwa mace aiki aka ce ba ita ba aikin wahala in ba haka ba sai ciwon baya, wata ta haɗu da ciwon kai mai tsanani kenan har ta bar duniya, wata hawan jini, ko sutura fa aka ce mace bata isa ta ci gaba da sakawa yadda take sakawa a da ba, saboda wajen da aka yi mata aikin, nan maman su Sudais cewa ta yi shekara uku kenan da aka yi mata aikin nan amma har yanzu bata dawo daidai ba? Dan kawai gudun ciwon naƙuda ko fitowar kan ɗa abu na ɗan lokaci mutum zai siyawa kansa abinda zai zauna masa har ƙarshen rayuwarsa kuwa? Inaga tabbas akwai dalilin da ya sa aka shiga da matar, Allah dai ya bata lafiya."
Yusrah ta sauke ajiyar zuciya a hankali ta ce" Hakane kuma mama, ameen ya Allah, bari in fara yin sallah sai na yi wanka yi wanka, yau muna da hadda wurin Baba."
Ɗakin nasu ta shige ta samu Hannah na ciro kayan da zata yi wanki, kuma ba nata kaɗai ba har da na Safwan da ita kan ta Yusrah, kayan ta ta fara cirewa ta ɗauki zane ta ɗaura a ƙirji ta lulluɓa kallabi sannan ta fito dan ɗiban ruwa.
*_SAJEERAH_*🖊️
*Alhamdulillah.*
23/05/2024, 08:39 - samiraharounayacouba: 👩❤️👨🧕👩❤️👨🧕👩❤️👨🧕👩❤️👨🧕👩❤️👨🧕
*WATA TAFIYA*
👩❤️👨🧕👩❤️👨🧕👩❤️👨🧕👩❤️👨🧕👩❤️👨🧕
_RUBUTAWA, TSARAWA_
*SAJIDA NIJAR*
_TARE DA_
*SAMIRA HAROUNA*
_VIVE LE NIGER_ 🇳🇪
*LITTAFIN KUƊI*
_Assalama alaikum masoya 'yan mutan niger, ga wata sabuwa da yardar Allah, *WATA TAFIYA*, hak'ik'a nasan kun san daga jin *WATA TAFIYA* tare da gwarazanmu a cikin wata sabuwar *TAFIYA* kun san abun zai ƙayatar, ba sai mun cika ku da surutu ba, kun san hannayen mutanen naku na Nijar, dan haka ku garzayo a yi da ku._
_*Farashin mai sauk'i ne* naira d'ari biyar (500) kacal, yan niger kuma dala d'ari ne (500fcfa) zaka samu wannan littafi mai *WATA TAFIYA* ta daban da zata birge ku._
_Domin tura na ka tura ta wannan account *2097292243 Lubabatu Shehu U.B.A Bank*. IDAN KA YI TRANSFERT SAI KA TURA SHAIDA TA WANNAN NUMBER 93 81 16 18._
_'Yan niger kuma sai ku tura katin MOOV ko Airtel ta wannan lambar *94-98-56-52*._
_Bismillahir rahamanir-rahim_
*6*
Saida suka gama cin abinci kafin suka ɗauko kayan karatun su kafin shigowar Baba da sun san yana shigowa maganar da zai musu kenan, hatta da Hannah dake ta sauri ta gama wankin kayan makarantar ta da na ƴan uwan ta da ta ɗauko, ita ma daga nan take bitar haddar ta saboda sanin Baban su bai da sauƙi game da lamarin da ya shafi karatu.
Suna haka Baba ya yi sallama, kusan duk a tare suka amsa mishi tare da yi masa sannu da shigowa, kan tabarmar ya zauna shi ma yana kallon Safwan yace "To babban su, ya karatun naka? Ka haddace dai ko?"
Kallon Yusrah ya yi sannan ya kalli Baban yana murmushi yace "E Baba, na iya duka."
Jinjina kai Baban yayi yace "Ma sha Allah, to matso mu fara da kai."
Matsawa ya yi tare da rufe littafin shi hizib biyar lokacin da Hannah ta zo ta zauna ita ma, cikin nutsuwa ba ɗar ko inda inda ya fara karatun shi, duk shiru tsakar gidan ya ɗauka suna sauraren karatun yaron da bai fi shekara shida zuwa bakwai ba har ya dasa aya. A tare Mama da Baba suka furta "Allahu akbar."
Sai Baba da ya ɗora da "Ma sha Allah, babban su, kana ƙoƙari fa sosai."
Sai kuma ya gyara zama yana karɓan littafin dan ɗora mishi yana sake cewa "Ka ci gaba da haka kaji ko, in sha Allah za ka zama babban mutum."
Da jin daɗi Safwan ya kalli Yusrah ya ɗan yi mata gwalo cike da hura hanci, ɗan hararan shi Yusrah tayi tana murmushi, cikin nutsuwa Baba ya sake ɗora masa wani tare da nanata masa har ya riƙe kafin ya sallame shi ya koma gefe, Yusrah ce ta matso ita ma ta rufe Alƙur'anin hannun ta sannan ta fara da a'uziyya da kuma basmala sannan ta ci gaba da karatun ta.
Saida dukansu suka gama sannan Baba ya dube su dukan su yace "Alhamdulillah, tabbas kuna ƙoƙari, ku ci gaba da kasancewa haka, kuma dama ubangiji ya yi alƙawarin sauƙaƙawa duk wanda ya ɗauri niyyar karatun littafin shi mai tsarki, Allah ya muku albarka, Allah ya baku zuri'a ta gari, Allah ya ci gaba da dafa muku a dukkannin lamarin da kuka saka a gaban ku."
A ladabce suka amsa da" Ameen Baba." Daga nan ya ɗora ma Yusrah sannan Hannah, kafin daga bisani Mama ta kalle su tace" Ku tashi kuyi shinfiɗa ku kwanta ku huta."
Miƙewa Hannah tayi sai Yusrah da ta langaɓar da kai tace" Mama ni kam da waje mukayi shinfiɗa, ya fi sanyi wallahi."
Kallonta Mama tayi tace" Yanzu Yusrah aka ce ki kwana a wajen nan sai ki kwana? Jiya fa kwana akayi ana ruwa yaf yaf yaf, yau ma kusan sau uku ana yayyafi, ƙasa a jiƙe take ba zata kwantu ba ai."
Ba ta ce komai ba ta nufi ɗaki, nan ta kamawa Hannah sukayi shinfiɗa tare da yin duk abinda suka san ya zama wajibi kafin suka kwanta, Hannah da Yusrah ne a yaloluwar katifa d aya, sai Safwan dake gefen su akan bargo.
*AA ANZA*
Wunin yau ɗin sam ba mai daɗi bane a gare shi, haka ya yi shi ba wani armashi sai tarin tunani da ɓacin rai, sallah kaɗai ke fitar da shi daga gidan, har saida ya yi sallah isha'i sannan ya kira Chef ya faɗa masa yana son ganin shi, ko ba maganar aiki ba Chef ya san Aswan mai zuwa gidan shi ne kai tsaye, dan haka ya bashi izinin zuwa kai tsaye.
Cikin wani tsadadden yard ash color ya shirya da takalmi flat ƙirar India sannan ya fito yana zuba ƙamshin turaren Creed, Meem da Angel na ganin shi suka fahimci shirin shi na fita nesa ne kuma wuri mai mahimmanci, dan haka tiryan tiryan suka biyo shi har bakin mota, yana buɗewa ya shiga ya zauna suna tsaye suna kallon shi saɓanin fitar da ya yi ta safe, irin kallon da suke mishi ya sa shi ɗaga musu hannu yana murmushi yace "My baby's, yanzu zan dawo, saboda ku kawai."
Jan ƙofar ya yi ya rufe sannan ya fara baya baya, har lokacin suna tsaye suna kallon shi sai Meem da ke ta ɗan kukan nan irin na mage can ƙasa ƙasa irin dai ba ta son rabuwa da shi, saida ya fice daga gidan kafin suka koma ciki duk babu mai karsashi a cikin su kamar wasu mutane dai.
Babban gida ne da sojawa ke gadin gidan, sanin wa ye shi a sojawa da kuma matsayin sa a gurin Chef ya sa suka sara masa a ladabce sannan suka buɗe mishi ya shige, kai tsaye Chef dake ya san da zuwan shi kuma ya san magana mai mahimmanci ce ta kawo Aswan gidan shi, ƙaramin office ɗin shi dake ɓangaren shi suka shiga suna ƙara gaisawa.
Chef na fuskantar shi tare da karantar yanayin shi yace "Boy, ya ake ciki?"
Ɗan muskutawa Aswan ya yi yana duban Chef ɗin da girmamawa, amma kafin ya yi magana sai aka ƙwanƙwasa ƙofar ofishin, Chef dake ya san ya umarci uwar gidan shi da ta sa ɗaya daga cikin yaran shi wata ta kawo abun sha yace "Shigo."
Buɗe ƙofar aka yi, inda matashiyar budurwat ta buɗa bakin ta a nutse tana faɗin "Assalamu alaikum."
Nutsuwar muryar ta sa Aswan kan shi ɗan juyawa ya kalli mai shigowar, *NABIHA* ce ɗauke da faranti jere da ababen sha, sanye da doguwar rigar atamfa ɗinkin mai kyau, iya ɗan kwalin atamfar ne kawai a kan ta ta masa ɗaurin ture kaga tsiya, a ƙalla Nabiha za ta kai shekara 20 a duniya ko ma ashirin 21, kyakyawa ce kuma fara hakazalika doguwa, murmushin dake kan fuskar ta a lokacin ya sa Aswan ɗn zuba mata idanu, sai kuma ya ɗauke kan shi cike da rashin nuna ko in kula ya bayar kan teburin dake gaban su.
Nabiha kuma na ƙarasowa da wannan fara'ar tace "Yaya AA ina wuni?"
Ba tare da ya sake kallon ta ba kuma ba tare da fara'a ba ya amsa da "Barka."
Ba tare da damuwa da yadda ya amsa mata ba yace "Barka Yaya, ina twins? Da Abrar?"
Ɗan jim yayi yana ƙurawa Chef idanu dake ta doka murmushi, Abrar, shi wallahi sai sunan ma ya so ɓace mishi, ashe fa ƴar gidan su ce, ƴar matar nan ko? To me ke haɗin shi da ita? Jin bai bata amsa ba ga kuma Abban nata da ya mata godiya ya ce ta bar shi ba sai ta zuba ma ya sa ta juya tana faɗin "Yaya, Mom ta ce na faɗa maka saura kayi halin naka wai."
Yanzu kam kallon ta ya yi, dattijuwar nan akwai kamala tana kuma birge shi, ya kuma gane me take nufi da kar ya yi halin, wato kar ya tafi bai je suka gaisa ba, ɗan murmushi kawai yayi wanda Nabiha ma bata san ya yi ba dan har ta fice, Chef dai ya gani yana sake jadadda masa ƙorafin da ya baro tana yi na rashin shigar shi idan ya zo.
Kwalbar lemu ya ɗauka irin masu tsadar nan zai buɗe Aswan ya mishi alamar a'a, sannan ya ɗan ɗauki na gwangwani Shwimpess ya ajiye gaban shi alamar ya ishe shi ma wannan, dan haka Chef ya sake tsura masa idanu yace "Uhm! Ina jin ka my boy?"
Numfashi ya sauke a nutse yana ɗan mamatsa tafukan hannayen shi yace "Chef, hukuncin da kuka yanke min ya min tsauri dayawa, dan Allah ku sassauta min ko da ta hanyar dawo da watanni ne zuwa wasu kwanaki."
Ɗan zaro idanu Chef ya yi yace "Aswan, ka san me kake faɗa kuwa? Hukuncin wata biyar kake so a dawo da shi wasu kwanaki?"
Tsurawa Chef idanu yayi yana kallo, hakan ya sa Chef girgiza kai yace "Ba zai yiwu ba Aswan, da zan iya yin wani abu da na yi tun ranar da abin nan ya faru, ka gane wani abu ɗaya, abun nan ya faru ne gaban idanu dayawa, da a ce da ka shaƙe Col. Garba daga kai sai shi ne haka ta faru, da zan iya sulhuntaku ba sai maganar ta fiya ba, to amma fa sai da ka ƙwace shi a hannun ka, kowa ya gani kuma ya bayar da shaida, sannan a gaban wasu manya aka yi haka, dan haka kayi haƙuri Aswan, ba zan iya yi maka komai ba akan maganar nan."
A raunane Aswan ya sake duban shi yace" Za ka iya Chef, sai dai idan baka yi niyya ba, kai ne babba a wurin nan, idan ka ce ka dawo da ni nan da wasu kwanaki ba wanda zai kalle ka ma bare ya ɗaga maka murya."
Kafe shi da idanu Chef yayi tare da jingina a bayan kujerar yace" Kuma kai ka yarda mu karya dokar aikinmu?"
Ƙurawa juna idanu sukayi, sai kuma ya sake cewa" Ko kana so mu zama ɗaya daga cikin wanda basa