Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 6
a kauyenku Bakori?" Itama ta yi dariya tace, "Ke ko meyasa ki kai min wannan tambayan?"`Yar Jos tace, "To na ga kowa yace yana son ki ba kya yadda ya-zo gida ma sai ki bata maganar, sannan na lura kin faye zurfin ciki shi ne na yi tunani kila kina da wanda ki ke so, ba ku gama shirye-shiryenku bane." Hadiza tace, "Bana son na karyata ki amma ke saboda Allah duk wanda ke nuna suna so na kin ga ya dace na aure su?" 'Yar Jos tace, "Me zai hana su ba maza bane?" Hadiza tace, "To shikenan na amince da ke anan mu bar wannan labarin amma bari na ba ki tarihin aurena da wani dan kauye dan uwana." Hadizan Bakori ta warware mayar Jos tarihin rayiwarta har zuwa ranar da ta dawo gidansu. Hadiza `yar Jos ta baro gadonta ta dawo gadon Hadizan Bakori tace, "yanzu Hadiza wa'annan matan da mu ke zuwa sune suke gana maki irin wannan wahalad? Ta amsa "Wallahi kuwa yadda ki ka gan su a raine din nan sai mugun abu da bakin wulakanci iri-iri." `Yar Jos tace, "kai lalle akwai maza `yan garari`yan iska a duniya yanzu shi wannan Yusuf duk irin kaunar da ya rinka nuna maki amma shi ne a lokaci guda ya je ya yi maki irin wannan cin mutuncin a gaban Inna Tambai mata mai mutunci da ita? Wai ko dai tabin hankali ya same shi iyayen ba su gane ba? Amma ni yanzu ina ganin mai kyau kamar ki a fadin jami`armu? Kin san Allah wani lokaci har tunani na ke yi na ce ko mutumin kauye zan aura domin ni sai na ga mutanen kauye kun fi mu kyau". Hadizan Bakori ta cе, 341 "Ina son ki ko don seli ki mai suman." Hadizan Jos tace Ya Ubangiji Allah ka hada ni da wannan Yusuf sai na rama maki wulakancin da ya yi maki, shi din me? Don Allah ba ki ji labarin inda ya ke yanzu ni ko ne mabuta masa na zage shi tas, wai ke don Allah wace irin zuciya gareki da har kika kyale shi, ai idan nice har gaban Gwoggo Halima zan same shi na wanke shi tas." Hadizan Bakori ta ce, "Wallahi ban kara jin labarinsa ba. Tun tamba yar da na yi ma Babana a hutuna na farko da na ba ki labari amma ran da mu ka je Bakori na hada ki da inna Tambai ki sha labarin inda ya ke clomin ta sani sai dai ina tabbatar maki idan don ni za ki yi nnasa tsiya don Allah ki bari domin idan na yi haka ban gode wa Allah kenan ba a bisa baiwar da ya yi min, lalle na san na shiga fitinu a dalilin shakuwa da kaunar da na ke ma Yusuf, amma kuma canjin rayiwar da na rinka samu a dalilin rashin aurensa sai ta zamar min kwanciyar hankali da daukakar rayuwa." "A gaskiya na san na so Yusuf amma na san ina kara son shi ne saboda zan bar azabar gidanmu na sami yancin kaina to irin rayuwar da na samu a gidan mahaifiyata da ci gaban makaranta ta sai suka gusar min da Yusuf a raina, sai kuma Allah ya kara yi min wata daukaka ta basirata wadda a dalilin ta na zo wannan gida, kin ga na sami ci gaban rayiwa, domin rayuwa ma a wannan gida makaranta ce, yanzu dubi ko na'urorin da ke kicin idan ba dalilinBaba Isa ba yaushe zan zo nan har na san su? Ki tuna fa ki ga yadda gidan mahaifina yake to yau y shi na zo gidan da zan kwaba kek ko burodi cikin minti goma a injin sannan na gasa cikin yan mintoci, da sauran girke-girke, haka nan yau ni Hadiza Dije na iya tuka mota bayan mahaifina keke gare shi? Kin san Allah ba na jin haushin Yusuf da rashin aurena domin ko da zan sami irin wannan rayuwar a gidan sa karshenta zan sha wuya can gaba, domin na lura namijin zara ne. Kin ga ran da ya sami dadin raina min wayau zai yi yace zai auro `yar duniya kamar shi su ci duniya yace ni yar kauye ce, domin sai yanzu na ke tsanar tsarin rayuwarsa cika son komi na `yan duniya ni kuma a lokacin rashin ye 35 wayau sai na rinka biye masa wai don kada ya kira ni bakauya. Suka yi shiru na dan lokaci can Hadizan Jos tace, "Kai! Ni kam Allah ya hada ni da Yusuf na fada masa magana domin wanda Allah ya ba mata mai hali irin na ki ya gama mallakar komi a rayuwa amma don tsageranci irin nasa zai ma Baba Kado haka, a gaskiya Hadiza akwai yarinyar da Babanta ke son ta kamar ki?" Hadizan Bakori ta kyalkyale da dariya tace,`Kin ji sokoncin naki ba, ba ga ki ba da Baba Rilwan ba?" "Yar Jos tace, "Wai ba kya jin yadda ake kwafdata da zagi wani lokacin?" Hadiza tace, "Ai ba kya ji ne kamar wata yar bebi, kyan ki Dr. Sani ya nemi bulala, idan mun kai mashi ke". Ta kyaikyale da dariya tace "Sai ya nemi bulala biyu kenan." * Abba Abba ya hakura ya sakawa Hadiza Abdulkadir ko a ranar da suke sallamar ban kwana, wato a rannan zai koma Bauchi mahaifarsa ya kammala jami'ar Jos. Suna tsaye ya dafe hannunsa jikin dalbejiya yayin da ita kuma Hadizan ta mikar da dogon hannunta tana tsinko ganyen dalbejiya, ya yi gyaran murya, yace, "Hadiza na ji sakonki wajen Hadizan Jos amma ni ban dangana ba ina tabbatas maki wata ran sai kin yi da nasanin kin amincewa da ni, amma dai ga adireshina nan da nambar talfon din gidanmu ina saurarenki ako dayaushe, zan yi zaman jiranki ko nan da shekara nawa ne, har zuwa ranar da ki ka janye sarautar haranta ta soyayya a tsakaninmu". Ta yi murmushi tace, "Ni kam na fi daukar kauna ta yanuwantaka da mahimmanci fiye da kaunar soyayya wadda ke karewa balle a zamanin nan namu mai cike da rudin kwadayi." Abba yace, "Kwadayi kamar yaya?" Tace "E mana yanzu za ka kulla soyayya da mutun dan lokaci kadan zaı iya barinka a dalilin ya ga wadda ta fi ka, kyau, ko ta fi ka kudi da dai sauransu duk me ke kawo haka in ba kwadai ba? Abba yace, "Haka ne amma ni ina daukar wannen 36 dama can ba soyayya bace ta gaskiya ta riya ce, amma kuma wani lokacin skwai fa kaddara". KASHI NA TARA A kullun dai su Hadiza suka ziyarci mahaifinta a Bakori ba shi da wata magana irin ta, "Wai Dije yaushe za ai aure ner" Ta kance, "Wallahi Baba da zarar na sami mijin zan kawo maka shi da kai na ni kai na ina son na yi auren saboda danmiwar da na lura kana nunawa haka nan kuma ganin yanzu ni ce babba a gidan nan". To irin wa'annan kalaman na Dije ta samu ta danne zuciyar Malan Kado daga zancen aurenta sai ya rinka tausaya mata yana ganin kamar da gaske bata sami mijin ba ne, ya yi alkawari a ransa zai daina damunta da magana ya shiga yawaita yi mata addu'a. A babban bankin C.B.N Rilwan ya samarwa Hadiza da Hadiza aikin hidimar kasa na Kaduna. Suka zauna a gidan Baba Garba cikin Anguwan Sarki shi ma Baba Garba kani ne wajen su Rilwan yana aiki a matatar mai. Bai fi wata uku ba kacal su kammala hidimar kasa a wani lokaci sun je Jos hutun kwana uku da yamma Mama Binta ta duba firij din ta na kicin ta ga bata da kayan salad sai ta kwallawa su Hadiza kira. Hadizan Bakori ce ta fito a guje tace,`Ga ni mama'. Mama tace, `Ina daya Hadizan?" Yar Bakori tace, "Tana wanka, kin san Dr.Sani ya yi waya daga Legos yace ga shi nan zuwa". Mama ta yi murmushi tace, "Shiririta ni dauki makullin karamar mota ki yi sauri ki sawo min kayan salad da alayyahu don Allah maza ki kawo min." Hadizan Bakori ta fito sanye cikin kyakyawar shiga ta yane kanta da wani gyale na zamani ta fito tana sulbi ta nufi inda ake aje motoci, ta shiga ta tayas. Maigadi ya dage mata koía ta fita da sauri. Daga can gefe su Rilwan ne da abokansa suke hira, a cikinsu har da babban bako Mai Martaba Hakimin wani gari ne a can cikin jihar Katsina, shi ma kusa ne a gwamnatin tarayya amma samun sarauta da tara dinbin dukiya ya sa 37 ya yi sallama da siki ya rungumi sarautar da yan kanfanonin da ya kafa. Wannan mutun shine yallabai Mamud, idonsa fes akan Hadizan Bakori, ya tambayi Rilwan "shin wai ina ku ka sami waccan yarinyar ne dazun na ganta ta gitta ita da Hadizan gidan nan yanzu kuma ta fita da motar gidan?" Rilwan yayi dariya ya bashi cikakken bayanin Hadiza, yallaba Mamud yace, `Idan haka ne ko ina son ta zan ko aure ta'. Rilwan ya kara dariya yace, "Sarkin hadama kana nufin ka yi mata uku?" Yace, "shi ne me, ba basarake na ke ba?" Rilwan yace "Na yi zaton sarautar`yan boko a ke". Mamud yace, " Yan bokon yanzuai ba sa anfani da turancinsu wajen tara mata, sai`yan bokon da waton na zamanin 1960". Rilwan yace, "To ni sai na ce Allah ya bada sa'a ai ba na hana yallabai diya ta ba." Can muna iya kiran lokacin karfe tara saura`yan mintoci na dare dn karamin yaron Mama Binta yayi sallama dakin su Hadiza yace, "Anti Hadiza Baba yace ki yanka lemo ki kai falon baki". Ta mike da sauri ta yi abinda aka umurceta. Ta yi sallama ta shiga sai Yallabai Mamud kadai zaune a falon, zata aje a bisa tebir yace "Kawo min nan gaba na, ke ce Hadizan Bakori?" Ta dube shi a tsakiyar fuskarsa tace, "E ni ce, a kira Hadizan Jos ne?" Ya kyaikyale da dariya yace "Amma fa wannan lakani na ku da ban sha'awa ya ke, sai dai Hadizan Bakori na ke son magana da ita". Hadiza tace, To' ta nemi waje ta zauna. Ya shiga tambayarta labarin yadda a kai ta zo jami`ar Jos ta bashi bayani, sannan ya nemi jin labarin iyayenta duk ta gaya masa, ya dan fito daga cikin kujerar ya tsura mata ido yace, "Hadiza a yau na ganki na kuma yaba da abinda na gani don haka ina gayyatanki da ki zama ivalina?" Tamkar ruwa ya ci Hadiza ita ko me yasa rayuwa ke latsa ta ne irin haka? Ita dai ta san ba kowa bace illa talaka likis wadda bata a bakin komi gidan. Ubanta na son ta yi aure fiye da zaton dan adam ko don ta farantawa Baba Kado rai to amma me yasa take cin karo da mazan da bata so? 38 Tabbas babu abin ki wajen Mamud sai dai kawai ba irin rayuwar da ta ke son samu bane a gidansa domin tuni ta sha jin labarin gidan sa wajen Hadizan Jos. Gidan Mamud babu abinda bai mallakawa wa` annan mata na shi guda biyu ba, to amma babu zaman lafiya; bala'in kishi suke yi tamkar su halaka junansu, ashahadu a wuyansu an ce akwai dan amaryar da ya rasu ana kyautata zaton uwargidan ta kasheshi don kada ya girma ya gaji Mamud. Yallabai yace, "Ba ki ban amsa ba Hadiza". Ta dawo daga tunanin rayuwar gidansa ta ce, "Ka ba ni lokaci zan yi tunani". Yace, "Ban dai yi maki ba kenan, kila na yi ma ki tsufa?" Ta yi mai wal da 'yan kyawawan hakoranta ta сe, "Lah wallahi babu zancen tsufa, ka san komi yana son a yi nazari". Sai ya ji Hadiza ta kara shiga mai cikin rai, wannan fara'ar da ta yi tabbas tana son shi sai ya ce ya amince. Mama Binta tace "To Hadizan Bakori ya kamata dai ki kwantarwa da mahaifinki rai inda duk ake son samun miji yallabai Mamud ya kai miji sai dai kuma idan akwai wani kudirin a ranki". Hadiza ta ce, "A gaskiya Mama ina ni, ina fitinar matansa wallahi ban iya wa". Mama Binta ta 'sha mur tace, "Kina nufin shi ma watsa maganar ta shi za ki yi? Karyarki ta sha karya in don maganar matansa na yi mai wannan maganar ya ce ba gida daya zai aje ku ba, su suna can inda suke a Katsina amma fa ba za ki yi aiki ba." Yar Bakori ta daure rai ta shiga tunanin abinda zai je ya komo a kanta, ita kan gaskiya ba za ta cuci kanta ba ta auri gidan da ake bala'i kiri-kiri, yadda duk Mama Binta ta uya Hadiza ta ki amincewa, domin a san ran Mama Binta ayi bikinsu gaba daya nan da wata uku idan sun kammala hidimar kasa. Kashegarin da su Hadiza za su koma Kaduna tare da Mamud a kai tafiyar motar su Mamud na gaba ta su Hadiza na baya har su ka isa gidan Baba Garba. Mamud ya kebe Hadizan Bakori yana ci gaba da kokarin shigar da kansa amma abisa dukkan alamu bai samu fuskarta ba, ya kawo kudi dubu ashirin ya bata, da farko 39 an ta ki amsa amma sai ta yi tunanin don ta raba shi da wa'annan kudi har wani abu ne a wajensa? Sai ta amsa ta yi godiya. Ko sisi bata taba ba ta adana a banki ma`ajiyar kudinta. A wannan dare kwana sukai zance daya na Mamud Hadiza da Hadiza. Bayan sati daya Mamud ya sake dawo wa Kadina wajen Hadiza har ya shaida mata idan zai koma Katsina zai biya ta Bakori ya gaida Malan Kado Sannan ya shiga Malunfashi ya gaisa da su yaya Amina. Hadiza dai bata ce masa komi ba domin a ganinta ta kai matsayin a bar ta ta zabin mijin aurenta da kan ta, saboda ta wuce zamanin auren dole. A ranar da yaje Bakori tamkar an yi ma Malan Kado gafara kowa ya gan shi ya san yana cikin murna, domin Allah ya kawo masa mijin Dije miji kuma na fada aji ako ina cikin fadin kasar nan, lalle Allah na amsar addu`o` in bayinsa in dai sun roke shi, wai yau kamar Dijen da ake muzantawa gidan sa itace babban mutun irin Yallabai Mamud ke tsananin so da aure? Baba Kado ya je masallaci ya yi nafila raka'a biyu yana ma Ubangiji godiya. a A Malunfashi ma gidan Yaya Amina bayan tafiyar su yallabai Mamud, maigidanta Malan Isa ya shigo suka zauna a daki suka zubawa kudin da ya ba su ido, Amina tace, "Yanzu Malan duk fadin jihar nan ta mu wanene bai da labarin wannan mutumi da kyawawan halayensa?" Malan Isa yace "Ke maganar jaharmu kadai ki ke yi, gaba daya kasar za ki ce, a gaskiya wannan yarinya ba karamar sa`a gare ta ba a rayuwa sai kawai ki shirya ki je can Jos din ki ji yadda aka tsayar da ranar bikin waccan Hadizan sai a zo aje Bakori a samu a daidaita ayi masu biki rana daya kamar yadda shi Alhaji Mamud din ya bukata". Amina ta sadda kai tace, "Ai ni Malan tsakanina da zuri arku bani da kalmar godiya sai addu`ar fatan alhairi kawai, duk abinda za ai ma yaro sanadiyar arziki sun yi ma wannan yarinya ko `ya`yan da muka haifa da kai iyakar dai zumunci kenan." Ya ce, "Wannan duk ba wanı abu bane 40 mu dai fatanmu Allah ya daidaita Dije da wannan bawan Allah yasa itace sanadiyar zaman lafiyar gidansa domin na san aminin Rilwan ne ba tun yau ba." Amina bata tsaida ranar tafiya Jos ba tana ta yan kintse-kin tsenta a tsanake, yayin da hankalin yallabai Mamud ya jirkita ya dimauce bai ganin kyan wata diya mace face Hadiza a kullun yana bisa hanyar Kaduna yana kuma dankara mata iyayen kudi ita kam Hadiza tana adanawa a banki. Suna kammala hidimar kasa shugabansu na wajen aiki yayi mata alkawarin sun dauke ta aiki, saboda haka wannan ya fi komi farinciki wajen Hadiza domin tana tunanin yadda zarmanta zai kasance a Malunfashi kafin ta sami aiki domin tana ganin bata iya zama Jos babu Hadizan Jos kuma Mama Binta na so ta auri Mamud. Suna isa Jos komi ya kacame na shirye-shiryen bikin Hadizan Jos da Dr. Sani inda zai aje ta Abuja wato inda ya ke zaune kenan da kanfaninsa. Kusan a wannan lokacin kowa ya azazzalawa `yar Bakori ganin ta sami miji mai son ta. Yaya Amina ta iso, sai da ta turke Hadiza a gaban Mama Binta sannan ta ji wannan danyen labari wai bata son Mamud, kafin Hadiza ta ankara har idanun Amina sun juye tamkar an watsa mata barkono tace, "Tafdijam! Ai ba ki isa ba dan ubanki, tun yaushe na ke jin labari kina samun samari kina basarwa, to wannan kam tunda ya nuna kauna babu abinda zai sa a fasa." Hadiza ta bata rai ta dan muskuta tace, "Ni wallahi Yaya bana aurensa, tunda na ce bana iya rayuwar iyalan sa, ban ga dalilin da zai sa ku tada hankalinku ba." Amina ta harzuka zuciya ta zo mata wuya, ta ce, "To sai ki fada mana wanda kike so tunda mu ba mu isa ba." Tace, "Ni a yanzu ba ni da kowa a dai kara min lokaci." Hadizan Jos na zaune can gefe daya ta yi tagumi tana jin badakalar da ke faruwa akan Hadizan Bakori, ita kanta ta dan tsani Hadizan Bakori anan domin bata son taurin kai iri wannan, tunda tace babu tsana tsakaninta da Mamud me zai hana ta hakura da yadda iyayen ta ke so? 41 ita kuma wadda ake abun don kanta ta kakure ta na, ts shakar kuka. Mama Binta tace, `A gaskiya Hadiza ki baiwa kan ki shawara wannan ba zancen bata rai ba ne har ayi kuka, zancen gaskiya ne randa ka rasa mai fada maka gaskiya ka shiga uku, ki jure kawai ayi maku bikinku hankulanmu su kwanta, ba kya tausayin tsohonki? Wallahi Mamud yace da suka je gaishe shi kamar ya hade su don murna, amma kuma ace duk ke kadai ki watsa farin cikin kowa?' Wasu hawayen suka taho a guje da ta ji an anbato Malan Kado, tasa hannu ta goge ta murje hancinta ta ce, *Insha Allah zan yi masa bayani zai fahinceni." Amina ta ja tsaki tace, "Zancen banza me ke gareki wanda za ki fadi mashi, to ko wannan dan iskan yaro Yusufa ki ke zaman jira?" Hadiza ta yi war da idanu bakinta a bude, itama `yar Jos ta bude bakin suna mamakin maganar Yaya Amina. Yaya Amina ta cigaba da cewa, "Idan shi kike kunata kina da wahala, domin uwar da ta haifeshi ma ance yanzu kuka take da shi, saboda ya yi kudi don kudi amma yana can ya budewa kadangarun bariki kunne, iyakar su da shi ya aiko masu da kudi amma shi yana can yana shagalinsa, yanzu wannan ne abin saurare?" Hadizan Jos daga can gefe tace "A'a Yaya ku daina wannan maganar ko ni na isa shaida Hadiza bata jiran Yusuf." Amina tace "To ta fadi mana uban da take jira yaya zata mai da mutane wawaye?" To iyakar fada na iyaye Amina da, Mama Binta sun yi ma Hadiza amma zuciyar Hadiza ko gezau. Tsana da kananan maganganu babu wanda Hadiza bata samu ba a lokacin bikin Hadizan Jos, kowanne ya tsinci kansa cikin jin dadi a zamanin bikin amma ban da yar Bakori. Wani karin bacin rai ma shi ne a lokacin bikin kusan Mamud anan ya tare yana lallashin Hadiza wanda har ya sa Rilwan ma ya tsoma baki ya rinka lallashin Hadiza wannan shi ya kara tayas da ran Amina. Wai Dijen da ba kowan kowa ba za'a zauna ana lallashi bayan da can an ba 42 wani yaro mara kwabo yace bai so amma a yau tana yi ma mai hannu da shuni yanga. Bayan ta koma Malunfashi Amina ta shirya ta je Bakori gidan Inna Tambai ta sa mijin Inna Tambai ya nemo mata Malan Kado ta sanar da shi halin da Dije ta ke, shi kan shi bai ji dadin labarin ba, hankalinsa da na Tambaya ya tashi suna al`ajabin me ya sami wannan yarinva. Tambaya tace, "Malan ko dai tun farkon yarinyar nan su Ankudi sun yi mata asiri ne abin fa da ban tsoro, yanzu idan ka tara`yan mata dari akwai mai kyan diyarmu Dije! amma ace wai bata yi aure ba har yanzu kai Malan da sake." Amina tace, "kada ku zargi kowa isgilanci ne irin na dan yau, ai ni yanzu wannan yarinyar har tsoro take ba ni, na yi fadan na yi amma ko gezau, sai shegen kukan tsiya?" Malan Kado yace, "yanzu yaushe zata zo nan Bakori?" Tace, "Na ji tana cewa dai zata zo cikin satin nan idan ta sami hutun kwana biyu ka san ta fara aiki anan Kaduna inda tayi hidimar kasa sun dauketa aiki." Malan Kado yace, "Wa'annan mutane suna fa da mutunci sun kama ta sun rungume ai bai dace ayi masu haka ba." Tambaya da Amina suka ce, "Sabo fa da Allah!" Yace, "Ku ban ni da ita zata zo ta same ni in Allah ya yarda karshen watan nan za'a daura masu aure." Ta sha ado da wata doguwar riga mai kamar alkyabba ta yane kanta da gyale mahadin rigar kai da ka ganta ka san girman jami` a ne, domin ilimi ne ke bugun kyau yayin da kyau ya gogu da jin dadin rayuwar gidan masu da shi, kai da ganin launin fatar`yan yatsunta ka san sun murzu da shafar mai mai gyara launin fata." Tana rataye da`yar jaka a kafada yayin da dandako ya ke gabanta dauke da akwati don karami na zamani, ta doshi gidan Inna Tambai, Hadiza Abdulkadir kenan. Suna shiga gidan Inna ta amshi akwatinta ta balle jaka ta mikawa yaro naira goma sabuwa fil. Inna Tambai tace, "Eye ka ga fa mutanen banki!" Sai da mangariba Baba Kado ya iso wajen bakuwar tashi suka hadu shi da Inna Tambai inda suka shiga ba nan 43 su ke fita ba, ita dai kanta a sunkuye lalle bata da mafita sai wajen Allah domin wanda take sa ran samun jin sanyi shi ma bayan su ya ke. Tace, "Baba ka duba matsala ta don Allah da kyau wallahi wallahi na yi kokari na ga zan iya auren wannan mutumin ko don saboda kai ma amma na ka sa, dalilina daya ne Baba shi ne iyalen sa." Ta fayyace masa labarin irin zaman matan Mamud kaf sannan ta kara da cewa, "to Baba wai shin ko ya aje ni gidana daban ai dai zaman matar shi na ke wata ran dole ne mu hadu kuma idan mutun mai mugun abu ne ai ko ba gida daya kuke ba sai ya sami hanyar da zai tsangwameka, ni kam Baba na sha wuya a zamanin kuriciyata bana son na kara fuskantar irin wannan matsalar ko kuma dan da zan haifa. A gidan Mamud fa har dan amaryar ake zargin uwargidan ta baiwa guba yaci ya mutu sabada masifar kishi yanzu Baba ina mu ina irin wannan rayuwar? Ka yi hakuri Baba.insha Allah aurena ya kusa domin ina ji a jikina." Malan Kado ya dubi Tambai yace, "idan haka ne ke ai Dije tafi mu gaskiya." Tambaya ta ce lalle mu bamu san tarihin gidansa ba, ina fa dalili za mu kai yarinya cikin fitina balle kishinmu na mata yanzu suna jin ya aje ta gidanta daban za su dirar mata." Malan Kado ya aiki Inna tambai Malunfashi akan ta baiwa Amina hakuri a kyale zancen Mamud, ita ko Hadiza ta koma fagen aikin ta a kaduna tana zaune abinta cikin jin dadi a gidan Baba Garba a kullun kwanan duniya sun kashe fiye da awa suna hira da Hadiza daga Abuja maganar dai kenan "Wallahi yar Bakori ki yi aure ashe babu abinda ya fi aure dadi idan ka sami masu halin kirki kamar irin su Dr. Sani." To irin wannan labarin na `yar Jos ya kan tayas da hankalin Hadiza har ta ji kamar ta yi ma Abba Abba waya akan ya zo su yi aure amma kuma babu sha`awa wadda zata haifar masu da jin dadi auren." Yau ma laraba aiki ya kacame masu don haka bata sami dawowa gida ba sai gab da sallar mangariba, me zai faru ta cimma a falo, ita da Baba Garba da matar Baba Garba tace, Lah! Yaya sannu 44 da zuwa saukar yaushe?' Kallo ma bata ishi Amina ba balle ta tsinka mata, ta gayas da su Garba da matarsa, sannan ta subuls jakarte daga kafada tare da takardun da ke hannunta ta shige daki ta aje ta fada kewaye ta yi alwala ta fito ta vi sallar mangariba sannan ta koma falo ta nemi gefen kalet ta zauna tare da hade kafafunta. Amina ta juya a fusace ta dubetta ta ce "Munafukar banza munafukar wofi, kin je kin shiryawa ubanki karyar da ki ka saba, shi kuma don rashin tunani ya hau kai, to Allah ya ba ku sa`a tunda ba mu da mutunci ba mu da daraja a idónku ai ban ga anfanin zamanki ba anan, domin Rilwan da Isa da Garba duk daya ne sai ki koma can gidan ubanki ki karaci sakarcin ki." Nan da nan Garba ya dakatar da ita yace, "Haba! Haba!! Yaya Amina menene na gorin gida? Mu mun fid da tsammanin Hadiza ta rike `ya yanmu, idan ta rike kanınanta ai mu ta yi mawa, ban ji dadin wannan magana taki bia, don Allah idan rai ya baci a san abinda ya dace a fadi." Duk wannan bai sa Amina ta saurara da bala'i ba haka nan sam bata amince da zamanta ba, sai dai ta koma can Bakori har sai da Garba ya yi ma Rilwan waya yayi ma Amina fada sannan ta dan sausauta amma da sharadin kada Hadiza ta sake zuwa wajenta a Malunfashi. Hadiza ta yi kuka ta yi kuka kamar ranta zai fita ta kwana tana rokon Amina amma kemerme Amina ta ki janye hushin ta. A kodayaushe tana kokarin rubuta mata wasiku na neman gafara amma dai babu amsa. A wata jumma'a ta shirya taje ta yi kwana biyu a Malunfashi, babu dai maganar arziki a tsakaninsu sai dai akwai banbanci tunda ta gaisheta ta amsa. Lokacin da zata koma Kaduna ta shirya tsab, kkarsierita maza suka daukar mata kavanta ta durkusa gaban Amina tace, "Don Allah don

Chapter 4 of 6