Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 6
annabi Yaya ki yi hakuri, kin ga abin rai, ina iya yin hatsari a yau na mutu ga shi ki na hushi da ni, me zan ce ma Ubangijina?" Amina ta yi jigum zuciyarta s natsu tace, "Tashi ki tafi Allah ya tsare, na hakura." 45 KASHI NA GOMA Tana zaune bisa tebir din ta aiki ya cukume mata wayar da ke gefenta na dama tayi kara ta dauka, sai ta ji ashe shugabansu ne gaba daya nan da nan ta kara kwantar da murya alamar biyayya ya ce, yana son ganinta yanzu yanzu. Ta shiga ofis din Yallabai ta tsaya cikin girmamawa sai da ya umurce ta da ta zauna sannan ta zauna, yace, "А sashen ofishin da ki ke wato (Banking Office) a koyaushe daga ofishin gwamnati akan baiwa wannan ofis alfarmar kujerar Makka to a cikin sa'a wannan shekarar kujerar а hannunki ta fada." Hadiza Abdulkadir yarinya mai cike da sa'a ta yi luu da idanu kamar zata some don murna sai dariya kawai, ta rasa bakin magana, duk irin kalmar da ta furta sai ta ga kamar bata yi daidai ba. A wannan dare ta rasa yadda za ta yi ta runtse ido, ga murna ga tunanin Mahaifinta Baba Kado saboda tun tana yarinya babu bukatar Malan Kado irin yaje dakin Allah, domin bata mantawa ko labari ya ji ance ga wani za shi aikin hajji sai ya yi kokari ya je gidansa ya roki alfarma cewa don Allah in ya je ya roka masu suma Allah ya kirasu su je wannan waje to ita yanzu yaya za ta yi ta tafi ta bar mahaifinta? A gaskiya bata iyawa duk inda zata ci rance insha Allah ita ko za ta cu su tafi tare. Kashegari tana isa ofis abinda ta fara yi shi ne cekin din kudinta na ajiya tabbas tana da kudi da za su kai shi amma babu guzurin kirki ita kuma bata son ta kai shi ya shiga matsala, ga shi yana da lalurar rashin lafiya a tare da shi. Sai ta yi ma Hadizan Jos waya ta gaya mata zancen tafiyarta, ta yi mata murna tace ita ba don ciki ba da sun je, sai Hadizan Bakori tace, "Matar Dakta taimako na ke so." Tace, "tunda ki ka hadani da rabin raina za ki samu fadı na ji." Tace, "wallahi tafiyar nan ce bana son yi ba tare da Babana ba, to amma kudina basu kai ba shi ne na ke neman rance, in Allah ya dawo da mu lafiya na amshi ariyas dina zan maido ma ki." Ta ce, "Gaskiya kin kyauta fadi min ko 46 abinda ki ke so da nambar akwatun ki na banki insha Allah gobe suna iske ki." Hadiza ta fadi mata. Ta shirya ta je Bakori tace, "Baba ka shirya za aima hoto zan tafi da shi domin na biya maka kudin kujerar Makka ni kuma gwamnati ta ba ni a wajen aikina." Malan Kado ya saki casbahar da ke hannunsa yа се "Ke Dije! Kin san abinda kike fadi kuwa?" Tace, "Baba amma ai kun fi karfin na ja ku da wasa." Malan ya sadda kai kasa kwalla ta fara taruwa masá. Hadiza tace, "Haba Baba ai tsakanina da kai sai addu`a, babu zancen kuka anan." Yace, "Bań ni Dije wai yau ke ce kika biya min zuwE Makka? Ni ko idan ban yi kukan dadi ba me zan yi?" Bayan ta kammala da Bakori sai ta zárce Malunfashi ta sanarwa da Yaya Amina. Amina ta yi murmushi ta ce, "To yanzu ke da kina da aure ai da tafiyar ta ku tafi armashi." Hadiza ta dubi uwar a kunyace tace, "kai Yaya in Allah ya yarda zan yi auren ne." Tace, "Ke dai ki ka sani." Duk shirye-shirye sai da Hadiza ta kammala masu, da lokacin tashinsu ya yi ta je Bakori da miotar ofis din su ta dauko Babanta, su Malan Iliyasu da Inna Tambai kamar za su lashe Dije har Kaduna sukai masu rakiya sai da suka ga tashin su sannan suka koma Bakori. Hadiza ta cika `ya hazika, jarima kamar namiji domin sai kace ta taba zuwa aikin Hajji komi ita jke ma ubanta, idan masallaci za su tana nan rike da shi, idan wajen cin abin ci ne mai kyau ta ke zuwa tana sai mashi. Hadiza bata mantawa suna dawafi tana makale da kafadar mahaifinta sun isa dai dai indararan rahama ta ji Baba Kado na sheka mata albarka tare da rokon Allah ya baiwa Dije mijin kwarai, itama a lokacin tana rokon Allah ya gajarce mata wannan zama ya kawo mata mijinta, jin abinda mahaifinta ke fada sai ta ji idonta ya cika da kwalla taf domin tausayinsa. To haka dai aikin hajjin su Baba Kado da Hadiza ya kasance, bayan an sauka arfat an kammala da jifar shedan da dawafil ifada sai Hadiza ta dauki Baba Kado suka shiga tsarabe-tsarabe, ita kam ta sawo akwatuna uku da kaya a 47 a ciki sai abin hannun zinari guda hudu da sarkan zinari cikakken saiti, to sauran sayayyar fa duk na'urorin kicin ne, idan ta yi aure ta zuba a kicin dinta. Baba Kado yace, "Wai Dije wa'annan injinan na mene ne? tace, "Baba akwai na hada biredi a kuma gasa cikin `yan mintoci haka nan akwai na daka nama ayi danquu nama akwai na daka sakwara akwai ma wanda zai fere maka dankali duk cikin dan kankanin lokaci, wannan tukunyan kuwa zata iya dafa kafar sa ko kan rago cikin 'yan mintoci." Malam ya dafe baki yace, "ke Dije ba ko karya suke ma ku ba dan dai ku yi masu ciniki ne?" Tace, "Haba Baba duk muna anfani da irin su gidan Baba Rilwan." Tafiya ta yi kyau domin su Alhaji Kado an dawo gida lafiya, a kullun zauren nan na shi shake ya ke da dattawa kaman su Malam lliyasu, Alhaji Kado ne zaune bisa wata sabuwan darduma ya zuba jallabiya fara sol mai dogon hannu ya dora rawani da kanbun wuya, da gani dai ka ga sabon Alhaji, ba su komi sai sauraren Alhaji Kado yana bada labarin kasa mai alfarma. Malan lliyasu ya ce, "to Alhaji yaya ciwon ka fa, ina ta yi maka zullumi kada ciwon nan ya hana ka sukuni?" Alhaji Kado ya ce, "abin mamaki, sam bai taso min ba, in ban da sau daya a Madina muna shirin barin ta, ai ko sai ciwon kai ya taso min nan da nan Hajiya Dije ta kai ni asibitin larabawa kada ka so kaga irin magungunan da suka hada min yanzu haka ina nan da su cikin jaka, cikin ikon Allah dan lokaci kadan na nemi ciwo na rasa, na tambayi Hajiya Dije ko nawa ta biya? tace min ai su can kasan magani kyauta ne, ko aikin tiyata za a yi ma mutun duk a kyauta ne." To haka dai Alhaji Kado ya kasance, yayin da Hadiza ta adana saye-sayen aurenta a karkashin gadon Inna Tambai ta sallami kowa da tsarabarsa sannan ta zarce Malunfashi ta ba su tasu, ta kwana bakwai a can tana baccin gajiya kafin ta koma Kaduna. Abuja ma kwananta daya wajen Hadizan Jos, a Jos ne bata samu kwana ba domin tana son ta dawo Kaduna da wuri ta gama shiriya-shiriyan ta kaman su gyaran gashi AR a salun zuwa kai sabbin dinkunanta domin washekare zata koma aiki saboda aikin na su ne babu isasshen hutu. KASHI NA GOMA SHA DAYA Yau kimanin wata daya kenan da `yan kwanaki da dawo war su Hadiza daga kasa mai tsarki, karfe goma sha daya na safe tana zaure bakin aikinta, Asabe wata `yar kabilar ibira ta zo wajen Hadiza ta zauna tace, "kai Hajiya Hadizz kowa idan ya je aikin Hajji yana yin baki amma ke sai kyau naga kin kara." Hadiza ta yi murmushi tace, "ke ko ga ni fa ga Babana me zai dame ni?" Suka bushe da dariya Hadiza tace, "Hala baki da aiki ne ko ki ka bar mazauninki?" Asabe tace, "Wannan ofis din za'a rasa aiki na dai zo ne na shaida maki muna da walimar suna ran asabat din nan a gidanmu." Hadiza tace, "Idan har ba zani Malunfashi ba insha Allah za ki ganni." Daga bayansu aka rinka yi masu sallama Asabe ta juya ta dubi mai magana suka amsa masa. "AMIRU NE” ya ce, "Asabe na je mazauniki ban iske ki ba aka ce min kina nan." Asabe ta mike da sauri tace, "lah har ka įso, yaya kaga manaja?" Yace, "har akawuntan ma na gani mun gama da su, komi ya kammala", tace, "yayi kyau" Duk maganar da su ke da Asabe yana satan kallon Hadiza, daga karshe ya kara gayas da ita itama ta gáyas da shi cikin nuna damuwa, sannan ya yi mata sallama suka fita tare da Asabe zuwa gindin motarsa, tace, "yaushene tafiya Japan din?" yace, "Ban fidda rana ba amma dai ban wuce sati daya yace, wai Asabe na tambayeki mana", ta kara matsawa kusa da shi tace, "me ya faru?" Yace, "Don Allah wannan yarinyar matar aure ce?" Tace "lah Hadiza bata taba aure ba." Ya ce, "kina ganin idan na ce ina son ta zata yadda ta aure ni?" Asabe tace, "E to babu ruwan ta dai da kowa, amma kila mijin ne bai zo ba." Amiru ya ce, "yanzu ga ni na zo" Suka kyalkyale da dariya, yace, "kina da wayanta ta gida?" Tace, "E amma ban rike da ka ba sai dai ga ta ofis." Ta fada masa yace yi mani kwatancen gidansu 49 anan ma Asabe ta yi masa yace, "ki taya ni addu'a Allah ya ba ni sa'ar Hadiza" Ta yi danya ta ce, 'To amin'. Ta koma wajen Hadiza a guje tana murna, tace "Albishir Hadiza sai kin ba ni goro." Hadiza dai sai dariya ko da Asabe bata gaya mata ba ta san sakon domin ita dai ba yarinya ba ce irin kallon da Amiru ya rinka satan yi mata ta san kallon so ne, ire-iren kallon da maza kan yi mata ne, amma yau na Amiru ya sha bamban da na kowa. Asabe tu dauike jakar Hadiza ta balle ta zari naira dari cif ta ce "wannan shi ne lada na, domin samun miji kamar Amiru sai yar gata wajen Allah. Gaskiya kina da daurin gindi ga wanda ya yi ki Allah!" Hadiza ta yi dan murmushi tace, "kai Asabe wai ke ki ka daura mana auren ne da shi sai cewa kike mijina". Asabe tace, "Amiru dai ya amshi kwatancen gidanku da lamban wayarki ta nan ofis don Allah Hadiza kada ki watsa mana kasa a ido in dai kina so ki ji dadin rayiwar aure to ki mika wuyanki ga Amiru." Mahaifin Asabe ya zo Kano fatauci, to a gidan kakansu Amiru ya zauna a karshe suka rinka hulda da mahaifinsu Amiru to wannan itace dangantakar da ta kulla zumunci mai karfi a tsakanin zuri`a biyu, duk su Asabe a Kano aka haifesu, gidansu Amiru tamkar gidan mahaifinsu ne, yanzu tana zaune ne gidan babban yayanta da ke aiki a wani kanfanin kusa na Alhaji, Baban Amiru anan Kaduna itama. Asabe ta kammla jami` arta. A daren jiya ne Amiru ya je gidansu wajen yay..ta akan huldansu ta kanfanin Alhaji to anan ne ya ke cewa, "Asabe gobe zan zo bankinku don wasu kudi da na ke so a tura su zuwa Japan." Amiru na shiga matarsa wajen cin abinci ya nufa, yana tafe a motarsa yana tunani me ya hana wannan kyakyawar yarinya aure? Kuma da alama babu alamar sakarci a fuskarta domin mace mazinaciya kallo daya namiji zai yi mata ya gane, ya fada a fili, "kodayake komi fa mukaddari ne, kila lokacin auren na ta ne bai zo ba." Yana isa Arewa Chinese Restaurant bai shiga ba sai ya kashe motar ya fito ya tsaya ya jingina jikin motarsa ya 50 jawo wayarsa ceilular y narsa lambobin Hadiza na ofis, ta dauka yana jin muryara sai ya ji kamar ya saki wayar duk ya bi ya rude, hai dauka haka zai tsinci kan sa ba, amma kuma vana tsoron kada ya zama ragon maza. Sai ya daure yace, "Hello Hadiza, Amirun ki ne, kin ga ne ni?" Nan da nan itama Hadiza ta ji wata irin kasala da gajiya sun dirar mata kai wannan wane irin mutun ne ko halinsa bata sani ba, amma har taji ta bada ran ta gare shi, ta jure ta yi murmushi tace, "har ka zama nawa, ashe abin ba bu wuya?" Ya kyalkyale da dariya yace, "To me ya yi saura idan ka ga abinda zuciyarka ta amince mawa ai sai ka mika ma abin nan sauran gangar jikin ka, ita kurna ta shiga kasaftawa amma don Allah Hadiza idan an tashi kasafta ni a bi ni a hankali domin na dade ina neman wadda zan mallakawa kai na na rasa sai yau ke Allah ya baiwa." Hadiza ta lumshe ido ta yi ajiyar zuciya tace, "Don Allah ka bar ni na yi aiki, ka ko ga tulin aikin da ke bisa tebiri na?" Ya ce, "zan iya barinki amma saii kin ba ni wayarki ta gida". Ta sanar da shi, yace, "sai kin ji waya ta anjima". Tana isa gida aka sanar da ita wayar Amiru uku, а ranta tace, lalle mijina dai ya zo; kafin ta yi komi wanka ta fara yi wai ko taji karfin jikinta, akwai aiki kam a ofis amma tunanin Amiru ya fi saukar mata da gajiya. Ta gama cin abin ci ta hau gado don ta dan huta ta san kila yanzu Amiru zai sake yo waya amma sai maigadi ya sanar da matar gidan wai ana magana da Hadiza in ji Amiru. Yana zaune cikin motarsa amma kofar motar a bude take don haka ya dan zararo kafafunsa waje, ya saka kaset na wakar Sirajo mai Asharalle a cikin wata waka da ya yi masu a birnin Kano a lokacin bikin wani abokinsu. Hadizan ta iso vana rangwada kai da gani ka san saurayi ne ya yi kiran, ta yi mai sallama, ya juyo ya amsa salamarta sannan ya fito sun gama gaisawa ya leka cikin mota yana kashe kaset din Sirajo taca, "Haba don mi za ka kashe? Ai ko wakan da dadi." Yayi dariya yace, "Idan kina so bari na ba 51 S S 1823 ki aron kaset din, tunda kina son wakan Sirajo ashe ran bikin mu zai cashe kenan" ta yi murmushi tace, "kai ne dai yau Allah ya hada ni da mutun mai yanke komi da kan shi". Yace, "Haba Hadiza duban ni fa na zama tuzuru saboda zaman jiranki? Ya dace ace yanzu ina da 'ya'ya biyu amma rashin samunki kinga ko daya ba ni da shi". A zuciya Hadiza ta rinka raya mata kai lalle Amiru ya yi gaskiya babu wanda rya dace da ita face shi, ita kam ko wane irin hali gare shi ya yi mata ta na son shi yanzu ta ga mijin aure. Ta daga kai ssuka hada ido sai kowanne ya yi ajiyar zuciya.e Yace, "Hadiza abinda zai tabbatas min da cewa kina SASO na shi neina son ki ban tarhinki kaf amma don Allah har sida labarin samarinki domin na san dai kamar ki ba kya rasa ewexsmai so. bbaw nemen eni abeb sn nimob iletnsd zid Ta murde hannayenta bisa kirjinta tana kallon kasa ta warware ma Aminu labarunta kaf illa dai kawai wajen labarin wahalas su Ankudi bata fadi mashi ba haka han wajen sdaurenta da Yusuf sai tace za a yi mata auren zumúnci da yrdan uwanta a zamanin tana firamare sal shi dan üwan ya ki yace ta yi masa kankanta. amiins a Amiru ya yi shiru yace, "lo yanzu fa da ki ka girma ai 6anya dace ya dawo me ya hana?" Gaban Hadiza ya fadi bata smnhyi wannan tunanin ba, don haka sai ta yi shiru can kuma ta yi munmushi ta ce, "kila rabonka ne mai karfi shiya hana sushindawonwa" Haba! Ai nan take Hadiza ta warvare wa Cegis Amiru lissafi ya ji kamar ya kamo ta ya rungume doh dadi. ni eBabisan wannan itace Hadizan da abokinsa Yüsuf ya wulakanta ba a shekaran baya da suka wuce r saud a terorYa bata nashi tarihin usili dan Kano uwa da uba yana ssen! yawan zama Abuja, Lagos, Kano, harkokin Babansa yece gastafiya Japan a gabana amma wallahi Hediza ba na jin neibzaniya tafiyar har sai na ga maganarmu ta je Bakori da y Malunfashi, ina son kuma a karshen satin nan muje Bekori nennda Malunfashi wajen Yaya Amina kice mata ge mljinki ya 66sxz0 don haka kada ta kara bate ran akean/Yallabar Mamud." Hediza ta yi dariya yace, *Don Allah shiga ki kao min hoto domin kila gobe idan kin ba ni izini za ni Kano kin ga 52 zan nuna ki a gida, bиk сtel mmcip er Tace, "Amiru, Allah ya yi ka da doki wai haka ka ke ma sauran yanmatanka?" Ya kyalkyale da dariya yace "Wa va gava ma kimuna yi ma`yan mata dariya ai mu yanzu maza isadar tsiya mu ke, sai wajen irin ku yan mutunci mu ke dariya muna nuna zumudinmu. Ta yi mai wani irin kallo ta juya ta nufii gida ta zo mai da wani hoto mai kyan gaske da ta daukaa Jidda, ya duba ya ce, "kin ce yau kada na yi bacci kenan wannan irin hoto?" Ta dan harare shi tace, "To ba ni hottona tunda kasa bacci za ka yi". Ya yi mumushi tare da kanne ido yace, "irin wanınan kallon da ki ke min cikin harara shi zai hana ni fita yawo idan mun yi alow aure." Ta kara dishe ido tace, "Allah da gaske ka ke?" Ya kara jin wani yar a jikinsa kai a cikin mata irin Hadiza nawa ake samu ne? Shi kam godiya kawai zai yi ma Ubangiji da samun mace irin IHadiza kallo ma kawai ta tsinke masa komi na jikinsa bai da sauran wata sha'awa in ba ta Hadiza oba ebni ba. smm one nimutu nsnnay adsd A um en aDa lallashi ta samu ya tafi domin ta san lokacin 90ey kwanciyan Baba Garba ya kusadellA eb niim en ing Kashegari kafin Hadiza ta bar wajen aiki wayar Amiru biyar kamar. daren jiya haka ya zo amma har da kyamare suka yi hotuna, tace "ya batun zuwa Kanon fa?"ce, eWaliahi na je kin hana ni kwana dole na yi abinda zan iya na dawo, gobe ina iya komawa, a to ya na iya?" Haka dai hirar ke gudana kamar zai sace Hadiza don tsananin so da kauna. en isa lbsb lem eonss uded uaney nimob bili eniboH e A ranar asabat ya dauke ta daga shi sai ita zuwa Malunfashi, kamar yadda yace mata, haka ko ta ce ma Yaya, "To Yaya yau Allah ya yi ga mijina ya zo." To Hadiza ta san Yaya na dan jin kunyar ta amma dai yau, sai Yaya taji kamar ta nutse a kasa don kunyа6 foniur Har azuhur suna garin Malunfashi, ko wane ya zo ya ga Amiru ya yaba da kamanninsa da dabi unsa, aka rinka injinawa Hadiza, Habi anguwar zoma ce ta shigo tace, "A gaisheki Dije lalle jinkirinki bai zama na banza ba, kin zo bmana da dan manyan mutaneisdmel nt 53 Sun isa gidan Baba Kado bayan la'asar. Alhaji Kado na kishingide a kofangida bisa tabarma ga `yar rediyan shi aje gefe guda, a lokacin an fara labarun duniya na rediyon tarayya Kaduna don haka Alhaji Kado ya tattara dukkan hankalinsa akan labaran da ake yi, sai da ita Hadiza tace "Sannu da hutawa Baba" kamar sau biyu kafin ya juyo wajensu. Tana gaba ta sha kwalliya Amiru ma na bayanta ya sha manyan kava na alfarma kai da ganinsu ka san dai daga bariki suxe, Alhaji Kado yace, "A`ah Hajiya Dije saukar yaushe? Tace, "Isowar kenan Baba, mu je zaure ko Baba?" A zauren an shinfide shi ruf da tabarmi don haka suna shiga Amiru ya nemi waje ya takure ya dan kwale hularsa baya don girmamawa sannan ya sadda kan shi kasa, ya rinka gaisawa da Alhaji Kado a sunkuye Alhaji Kado yace, "Samari daga ina kenan ko kai ma kaninsu Rilwanu ne?" Hadiza na can labe bakin kofar shiga cikin gida tace, "A'a Baba wannan mutumin Kano ne, amma ba inda kasuwanci bai kai shi a cikin manyan biranen nan na mu, shi ne mijin da Allah ya kawo min." Alhaji Kado ya sunkuyad da kai yana murmushi yace, "ikon Allah, ai ni ban fahinta ba. Masha Allah, kai ina DanBala ya zo maza ya kira min Malan Iliyasu su gaisa." Hadiza ta shiga cikin gida ta turo DanBala suka gaisa da su Gwoggo Ankudi tace, su kintsa zata shigo da Amiru su gaisa. Ai fa nan da nan suka shiga kaye kaye ana rawar jiki domin yanzu babu zance mai dadi sai na Hadiza. Bayan Amiru ya gayas da su Ankudi ya mikawa Hadiza dubu daya ta ba su, ya koma zaure ya cimma Malan liyasu anan aka shiga wata sabuwar gaisuwar Malan lliyasun ne ma ya yi mai`yan tambayoyi har suka gane mahaifinsa. Da suka tashi tafiya Alhaji Kado yace, "To Hajiya ba ku sha ko hura ba?" Tace, "Ai, Baba mun ci abinci a Malunfashi kuma gidan Inna Tambai za mu yanzu." A nan ma ya kawo dubu biyar ya baiwa Alhajin da Malan lliyasu su ka sa masu albarka da fatan alhairi." Inna Tambai ta shiga hidima da baki kamar wa`anda 54 zasu kwana a Bakori, shi kan shi Amiru ya ji dadin yadda Inna Tambai ta yi masu har ya dubi Hadiza yace, "kin sani ko Hadiza?" Tace, "Me kuma na sani?" Yace, "Randa duk Kika haifu a gida na, da kaina zan zo na dauki Inna Tambai ta zauna mana har sai jaririnmu ya yi girma". Ta dan harare shi tace, "Ba ka ce wa sai mun yi ma jaririn aure sannan ta dawo Bakori?" Ya yi murmushi yace, "yauwa kinga har kin fara yi min kallon da na ke so, duk yau sau biyu na samu". Tace, "A yi hakuri na daina". Yace "abin ma `yar yanga cе ko, bari na kai kara wajen Inna". Ta harare shi ta ce, "ka san maganar da ka ke kuwa?" Yace, "Don na kai karar iyalina suna ---" a dai dai nan suka ji tafiyar Inna Tambai nan da nan Amiru yana ba'a ya dan gyara zama domin ada yayi rasherashe an shiga fagen soyayya tamkar wanda ya ke gidansa. Ya sunkwui da kai ya kwantar da murya yace, "sannunku dai Inna". Inna Tambai tace, "Haba dan nan ai ku ke da sannu wa'anda suka sha tafiya tun daga Kaduna?" Ta shiga aje masu abinda ta shirayo masu. A nan dai Amiru ya ga Inna Tambai irin tasu ce sai kawai ya dai na dari-dari ya saki jikin sa sosai, har wata shagwaba ya rinka yi ma Inna, yace, mata ba zai jira yangan Hadiza ba sati mai zuwa zai turo iyayensa. Haka din ko aka yi sati mai zuwa iyayen Amiru maza suka zo Bakori da kudinsu dubu hamsin na gaisuwar iyaye. Amiru ya je Abuja da niyyar kwana daya saboda tafiyarsa Japan, a daren nan ya isa gidan Yusuf kamar kullun gida cike da yanmata ana ta sheke aya, Amiru ya janye Yusuf zuwa shagon Falanke yace, "kai ni fa kamar yadda na gaya maka ta waya aure fa zan yi". Yusuf yayi dariya ya ce, "Wace ce wannan mai rabon shan dukan?" Amiru yace, "shan duka kamar yaya?" Yusuf ya ce, "kana nufin yanzu su Jummai da Hajiya Ramma wadda ka kashe ma aure shi kenan?" Amiru ya ce, "kai idan na auri wannan yarinyar ba abinda zai hada ni da su Ramma, wannan ba irin matan da ka taba sani bace ko ni na taba sani, wata 55 sAllah ce wannan." Ya bude walet dinsa ya fiddo wani dan karamin hoton Hadiza ya mikawa Yusuf yace, "tana aiki a C.B.N Kaduna tana nan zaune a Anguwar Sarki har Malunfashi da Bakori naje wajen zuri'aisu". Yusuf yace, "me ya zaunan da mace kamar wannan ba aure, ko dai irin mutanenmu ne shigar da kai ta yi?" Amiru ya yi murmushi yace, "Bari sai ka ga Hadiza ido da ido ka tabbatas wa kan ka, da laile cewa Hadiza irin ajiyar Allah din nan ce, ka san Allah yanzu ni ko sha'awar zama kusa da wadancan gungun cutar ba ni yi yanzu ni da ku sai anan shagon Falanke, ko idan mun hadu a Masallaci". Yusuf ya yi dariya ya ce, "Muna nan idan an shanye man amarcin ka neme mud оNBy Amiru ya mike ya duba agogo yace, "To mu kwana lafiya nina yi Japan sai ka ji waya ta warnus dY .sensbig A kullun da daddare Amiru ke ma Hadiza waya daga Japan minti biyar din nan sai ya kashe ma Hadiza su. sh sl uk A ranar da ya sami kwana tara da tafiya a wannan daren da ya yi mata waya ta ce, 'Amiru yace, "yes my dear? Tace, "wai sai yaushe za ka dawo ne?" Ya dan runtse leWE ido murna ta cika shi domin ya tabbata Hadiza bata lyavgaa fadin abinda ya ke ba da-gaske ba, lalle tana cikin damuwar slbeH rashinsa, ya dan yi gyaran murya yace, "kin san ko ina nan ina hado maki lehenki, da zaran na kammala zuwa jibi zan guE taho." Zuciyar Hadiza ta yi fari tas, ko shakka babu aure dai ya zo. sbodsa eysb snew eyyin sb ejudA si ey unimA Bayan ya dawo da sati daya iyayen Amiru mata suka zo Bakori don asa masu ranar biki. Alhaji Kado yayi masu alkawari zai aiko har Kano idan an yi shawara da uwar yarinya.ey wauy."ly nar st aws syew af skem evad ev mulluk Svnei sbbay ayheb Ya aiko Inna Tambai har Malunfashi zancen sa rana, Amina tace duk yadda aka sa duk daya ne a wajenta, InnaA Tambai tace, "yaran dai sun bar mani sallahu ya kasanceun lokacin da ita Dijen zata dauki hutu". Yaya Amina tace, "Wai zata ci gaba da aikin ne? Tambai tace, "kwarai kuma,BA zata zauna Kano ko Abuja yace inda duk take so nan zai 56 22 S nemar mata taran sufa." Lokacin biki ya kama 10/Nov a bisa lissafi sauna kwana talatin da uku. Wai da aka ga ya wa Amiru kamar ya kamo kwanakin duık da shi ma dai zai yi

Chapter 5 of 6