na shi shiryeshiryen. Saboda haka da aka je kai kayan sa rana har da
akwati shidda na lehe. Nan da nan Bakori ta diba diyar
Baka Kado lehenta. rabin dozin,yan kari kuma suce dozin.
Wannan zance ko ina ne a garin Rakori da Malunfashi む
anobal STAA DA Dnuol lla at d stes eb saaoda
TSyniKASHI NA GOMA SHA BIYU
anntum anag met ey венс аg ay ab lsa sad syitaS
Hadiza na zaure suna kallon wasan Samanja a talabijin
sai ga kaininta mai bi mata dan wajen Yayaı Amina ya isko
ta Keduna, nan talke Hadiza ta san babu lafiya ko kumas
akan zancen suren ta ne, ta zare ido tace, "Saminualafiya,lullec
me yasfanu, to Yayasceabaalafiya?" Ya sadda kai yace, yaw
"lafiyarta lau, Alhaji Kado ne dai/babu lafiya yana asibitin
Funtua kwance Bney em iria lusY anitods an emuk sd sindA
Hadiza ta yi luu bisa kujera sai hawaye rau rau, "me studA
ya same shi Saminu?5Yace, "An ce wai kewayar gona yaddiisl
je sai dai aka maido shi gida barin jikinsa ya shanye." ed em irla
Karfe shidda na yamma Hadiza da Saminu sun iso gud
asibitin Funtua, hankalinta ya kara tashi yadda ta ga bakin Alhaji Kado ya jirkice tayi kuka ta yi kuka har sai da ta san vavix
kuka ba zai mata maganin komi ba sannan ta hakura. Tana erda
nan zauna tare da su Malan Iliyasu can wajen karfe tara nalauek
dare sai ga suInna Tambai, anan suka dawo da wani sabon
kukan.stnores s вnenлu ly usb st awuat ly et aslulleo isa
Inna Tambai ta lallashi Dije suka tafi Bakori ta kwanaA
a can amma asuba na yi ta dawo Funtua gani take ta yisogal
kamar zarta iske ya mutus sy syhams haао ву вyhsb ly вy ise
Misalin karfe daya da rabi na rana Armiru ya iso yace
mata ya yi waya ne Kaduna matar Baba Garba ta ke sanar 00 61
masa garabinda ya faru shi ma daga Abuja ya ke. Tace,
"Wallahi ciwon Baba kuma ya tashi". Amiru ya ce, "Dama yayi masa kárfi haka?" Tace, E' yace, "Amma Hadiza ya
dace mu kai shi wata asibitin da tafi.wannan". Tace, "in dai
law
sbud
cayill
57 82
on samu ne na fi son A.B.U. Zariya". Yace, "A to barı mu
ja mu ga likitan wannan asibitin ko?" Suka jora zuwa
ofishin likita suka yi masa bayanin bukatarsu ya dauko katin
Alhaji Kado ya duba sannan ya rubuta takarda wadda za'a
kai can A.B.U. Zariya.
Ya debe su a motorsa sai Zariya sai da ya tabbatas
an duba Alhaji an bashi gado sun shiga yi masa abinda
ya dace, sannan yace Hadiza ta zo ya kai ta G.R.A gidan
abokinsa da safe sun kawo ta shi kuma ya wuce Kaduna.
Kimanin kwana biyar haka Amiru ya rinka jele hanyar
Zariya har sai da ya ga sirikinsa ya fara gane mutane, sanna
kuma kullun zai ga Hadiza ta rungume shi tana ba shi
abinci. Sai hankalin Amiru ya kwanta ya ci gaba da harkan
kasunwancinsa. Da zai tafi Lagos sai ya bar wa Hadiza
cellular din sa ya ce "idan akwai wata damuwa ki yi min
waya, da zarar na sauka Lagos zan sanar da ke lambar
wayan daki na, haka nan ga ta ofis din mu na Kano da
Abuja ga kuma na abokina Yusuf shi ma yana aiki ne a
Abuja sannan ga ta mahaifina!" Hadiza ta bude ido ta се,
"lah ba na iya yi ma Baba waya," ya ce, "haba Hadiza ashe,
shi ma ba Babanki ba ne, in dai ki na cikin damuwa, ki
buga mashi."
Ta raka shi har gindin mota, tana yi masa Allah ya
kiyaye, hanya, ya ce, "kin tabbata dai wa'annan kudin sun
ishe ku?" ta ce, "Haba Amiru sai kace wadda zata sai rai,
yaushe zamu kashe wa'annan kudade."
Tana zaune kusa da Babanta tana bashi ruwan lemo
sai cellular ta yi tsuwa, ta dauka ta yi kunnenta a zatonta
ko Amiru ne, sai ta je an ce, "Ina Amiru" ta ce, "ya je
Legos?" aka ce, "wa ke magana?" ta ce "matarsa ce Hadiza"
sai ya yi dariya ya ce, "Ran amariya ya dade, idan ya bugo
ace ina san magana da shi abokinsa ne Yusuf daga Abuja;"
ta ce "zan sanar da shi, sai anjima."
Alhaji Kado ya rinka badardarawa maganarsa guragura
wai menene kuma wannan? Hadiza ta yi mai bayani. Ya
bude baki numa alamun yana mamaki. ita da su Malam
Iliyasu suka rinka yi mai dariya..
58
Ana ta murna sauki na ta samuwa, daga Legos Amiru
ya yi mata waya ya ce, "yau dai sauran kwana ashinrin da
biyar bikinmu. Ubangiji Allah ya ba Baba lafiya don mi ji
dadin shagali." Hadiza ta ce, "amin" ya ce, "ki gaida min
Baba, sai na zo gobe."
Da azuhur bayan su Malam lliya sun yi mai alwala
sun kawo dutse ya yi sallah. Kafin ya kwanta, sai shakuwa
har idonsa na kafewa. Nan da nan Hadiza ta ruga kiran
likita, suna isowa tana rike da hannun likita. Likita na duba
Alhaji Kado, amma i.na, babu Abdulkadir, ya amsa kiran
sarki Allah.
Hadiza ta yi waya dakin Amiru amma shiru ba'a dauka
ba, ta yi ofis din su nan ma ana ta surutu bisa layin, kwatsam
idonta ya fada bisa lambar Yusuf. Ta na yi bugu daya,
Yusuf din ne ya dauka, ta ce, "don Allah ka nemi Amiru ka
sanar da shi sirikinşa ya rasu yanzu a nan Zariya." Kafin
Yusuf ya yi wata tambaya, ta kife layi. Tana sharan hawaye
a fice zuwa bakin titi, ta nęmo masu motar haya wadda
zata dauki gawar Alhaji Kado.
Kafin mangarib har an kai shi makwancinsa, ya bar
su Hadiza da juyayin rashinsa da sauran rigingimun duniya
wa'anda ba su karewa sai in irin wannan ta afku.
Ana sallar mangarib, yaya Amina da mijinta suka
iso amma ita anan zata zauna har sai an yi sadakar uku.
Kashegari Hadiza da Inna Tambai suka gyara dakin
marigayi Kado suka shinfida dardumarsa inda za su rinka
zama kenan. Ita da yaya Amina da Inna Tambai da mutanen
da suka zo masu ta'aziyá, koda yake inna Tambai bata ga
ta zama ba domin Hadiza ta bayas da kudi an yanka rago
sannan an sawa buhun shinkafa ta ce a dafa saboda zuwan
baki na nesa.
Aiko misalin sha biyun rana sai ga motoci biyu ta
maza da mata daga Kano iyayen Amiru. Inna Tambai ta yi
murna da shawarar Hadiza da suka gyara dakin marigayi
da ina za su saka wa'annan kosasun mutane? domin dakin
su Ankudi, zaman shi sai ka daure.
lyayen Amiru har da daron sinasir da daron waina
59
da na shinkafa suka zo suka ce a baiwa jama'a sadaka,
sannan kuma ga buhun suga da buhun shinkafa, suka ce
daga mahaifin Amiru shi ma yana nan zuwa gobe, sannan
Amiru ya ce, ayi masu gaisuwa kamin dare yana nan zuwa
yau.
Inna Tambai ta yi hanzarin sauke abinci sannan ta
zubawa bakin Kano. Sai da suka yi Sallah sannan suka kara
bada hakuri suka Kano, suna yabon Hadiza akan lalle Amiru
zai mori mata ga kyau ga addini sannan ga natsuwa.
Tsakanin ta da kowanne bako ya shigo gaisuwa a
natse cikin mutunci sai ta juya bisa karatu wani dan karamin
kur'ani da ta ssyo a Madina. Idan har ta yi magana mai
tsawo, to da Inna Tambai ne, ko ana bukatar wani abu.
Rasuwar Baba Kado ta kama alhamis ne, saboda haka
a lokacin da Yusuf ya sanar wa Amiru a waya yana shaida
masa Hadiza ta yi waya tana sanar da shi mutuwar Babanta,
gaba dayansu mutuwar ta bugi zukatansu, domin a gaskiya
Yusuf, koda bai san kowacece Hadizan ba, ya tausaya mata
a bisa yanayin sautin muryarta, sai ta dawo mai da tunanin
ta shi mutuwan mahaifin, tabbas babu abinda ya fi mutuwa
ciwo, radadinta a zuci duk yadda dan adam yaso ya bayyana
bai iyawa, sai dai ran da a kai ma ka, sai ka ji abinda kowa
yaji.
Saboda haka, sai Yusuf ya rinka ba Amiru hakuri har
ya ce, "ina fatan zaka shigo jirgin Abuja don mu raka ka
Malunfashi wajen ta'aziya;" Amiru na so ya ce masa "ai a
Bakori ne" amma sam maganar ta kasa fita bakinsa saboka
juyayin tsohon Hadiza sai dai kawai yace; "To ina nan zuwa."
Falanke ma da ya ji tafiya ce wajen kauyensu sai ya
ce, "yallabai zan biku", suka ce "Bissimillah!"
A ranar jumma'a suka baro Abuja. A motar Amiru su
uku ne da Yusuf da wani direban kanfaninsu sai wata
galleliyar motar Yusuf da ya shigo da ita kwanan nan daga
Hong-Kong su Falanke ne da wani abokin su da direban
Yusuf.
Sun iso Zariya ne Amiru ke cewa ina fatan ka zuba
komi da komi a sabon gidanka na Bakori dòmin ina ganin
60
anan zan zauna har sai an yi sadakar bakwai, kasan mahaifin
Hadiza mutumin Bakori ne." Yusuf ya juyo ya dube shi ya
ce, "amma ce min ka yi yar Kaduna ce, iyayenta ne a
Malunfashi;" Amiru ya ce, "kai labarin Hadiza na da tsawo.
Ainihin mahaifinta ma dan Bakori ne, uwarta ina jin aure ne
ya kai ta Malunfashi koko yar malunfashin ce, shi ne ban
gane ba, idan de mun je gidan, kila kai ka gane tunda dan
gari ne."
Shi ma kan shi Yusuf sai labarin ya dan rikice masa
ko me yasa, oho! Suna isowa Bakori gidan Yusuf yana a
bakin hanya ya ce, "ga fa gida Amiru mu tsaya mu aje
kayanmu tukun?" Amiru ya ce, "haba mu dai fara isa gidansu
Hadiza, ka san kuwa ban san wannan shi ne gidan ka ba?
domin kwanan baya mun zo nan Bakori da Hadiza har ta ke
cewa, kai amma gidan nan ya birge ni, na ce mata, ai dole
ya baki sha'awa domin irin wannan gidan a kauye?"
Yusuf da Amiru su kai dariya. Me kuma zai faru,
kwatancen da Amiru ke yi ta inda suke bi duk hanyar gidan
Malam Kado ce, har aka isa kofar gidan.Yusuf ya amince gidan Baba Kado ne, ya dora kan shi cikin tafukan hannunsa,
nan da nan idanunsa suka yi jajur sai kwalla shar, da ya tabbatar dai Baba Kado ne ya rasu.
Mutuwar ta bugi Yusuf tamakar yadda ta bugi Hadiza
domin har ga Allah Yusuf yana son Malam Kado kamar yadda Kado ke son Yusuf. Su Malam Tukur ne da Malam
Iliyasu da sauran dattawan gari ke zaune a zaure, suka zauna
suna juyayi.
Malam Tukur ya ce, "Yusufa ashe ka ji mutuwar?" Yusuf ya ce, “E to". Sai kawai ya kara fashewa da kuka da ya tuno yau shekara daya kenan rabban sa da zuwa wajen Baba Kado suka mike za su shiga cikin gida, a bisa hanya
ne Amiru ke cewa, "ashe ka ga ne Baban?" Yusuf ya ce, "Wallahi Amiru, ina son tsohon nan tamkar mahaifina."
Suna shiga dakin da Inna Tambai ta ja su, wato inda Hadiza
ta ke, anan ne kuma Yusuf ya kara zubewa da ya sha wani mamakin da ya ga Hadiza.
Itama Hadiza ta dubi Yusuf ta juya ta maida kallonta
6.1
akan Amiru sannan ta sadda kai hawaye shar suka rinka
fita.
Koma mai Hadiza ta canza, babu tantama yasan
wannan Dijensa ce, itace Amiru zai aura, lalle wannan abu
da daure kai. To amma abin mamaki daya ne anan, me
yasa ako yaushe yazo Bakori mahaifiyar sa Gwoggo Halima
ta ke damunsa da fadan ya yi aure, bayan ta san Hadiza na
nan bata yi aure ba amma ta ki gaya masa? Ya kawad da
wannan tunanin ya daga kai ya dubi Dije tabbas itace.
Mutuwar Baba Kado ta dawo ma da Yusuf da
mutuwar mahaifinsa danya.
Hadiza ta daga kai tace, "Amiru kana nan ko har
sai lahadi idan an yi sadakar uku?" Ya dube ta yace, "ina
nan ma har sai an yi sadakar bakwai, saboda ina ma da
masauki gidan wannan abokin nawa da na ke gaya ma ki
Yusuf."
62
DANDANO DAGA LITTAFI NA UKU
Bayan an yi sadakar uku ta marigayi Alhaji Kado ran
lahadi kenan, Amiru na can gidan su Hadiza sai ya dawo
gidan Yusuf don ya dan kwanta yà huta, me zai faru? Yusuf
ne a dakin da ya zauna ne Amiru yayi masauki duk ya yi
dai dai da kayan Amiru, ga hotunan Hadiza nan kaca-kacă,
sannan yana ta bincike masa takardu.
Amiru ya tsaya bakin kofa yana kallon ikon Allah,
yayin da Yusuf ya yi kasake na rashin gaskiya. Na lokaci
mai tsawo sannan ya ce," Amma Yusuf ka ba ni kunya, me
za ka nema wanda ba za kà iya tambaya ta ba?
Tabbas na san dai bai shige al'amuran Hadizan ka ke
neme ba, kana zaton zan rubuta wayar matata ne a takardu
ko adireshin gidansu? Niko wane irin dakiki ne da ba zan
iya harda cewa ba a ka? idan su ka ke nema ba ni biro na
rubuta maka.Kana tsammamin Hadiza wawa ce kamar kai
da har zata iya saurarenka! Ka tuna fa kai ne ka ce baka
aurenta don rashin fasali har dakin innarta? amma ka ba ni
kunya kai ba amini ba ne maci amana ne."
Yusuf ya daga mai hannu ya ce, "Dakata dan Allah
Malam, maganar fa ta isa, sai ka ga ya min waye baya
kuskure? Na yi kuskure kuma na gane kure na, duk abinda
za ka yi sai ka yi dan zan koma neman Dije kuma Insha
Allah ni ne mijin Dije ba dai kai ba, komi ka ke takama
wallahi akan Dije na shirya..."
63
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels