An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
Izgili
SARAUTA
JAMILAH MUHD, AHMED
(Mrs Bashir Salisu the Door)
IZGILI JAMILA MUHAMMED
HAKKIN MALLAKA
Jamila mohd ahmed
SHEKARAR BUGU 2014
GODIVA
Ga Allah S.WA) ya bani ikon yin wannan
rubutu, salati mara adadi ga shugaban halitta
annabin mohmed (S.AW)
GARGADI
Ba'a yarda wani ko wata ya sauya
wannan littafi ta wata siga ba, ko daukar wani
abu a ciki ba tare da izinin mai littafin ba, a
kiyayc
Ban yi wannan littafi dan cin zarafin
wani, ko wata ba, kagaggen labari nc, da na
rubutu shi dan nishaɗantar da masu karatu, ba
dan cinzan ko tuno asirin wani ba, dan haka
IZGILI JAMILA MUHAMMED
IZGILI
C
ikin mutukar nutsuwa take
takunta wanda yawancin
samari da mutane suke ganin
yangance da ita amma kuma ba haka
bane haka Allah yayota, ita bata sanin
sanda take yin yangar haka tafiyarta take,
dan ita a rayuwa bata iya sauri ba, komai
nata cikin nutsuwa take yinsa gami da
wata irin rausaya tamkar bishiya kuma
natural ne daga Allah amma bayin kanta
bane, dan ita bata sanin sanda take yi, sai
dai ta ji kawayenta suna fadar wai ta ci ka
yanga komai zata yi a yangance take
yinsa duk sanda suka fadi haka sai dai ta
yi dariya dan ta san idan zata kwana
dubu tana gaya musu ita bata san yadda
ake yin yangar ba bare ta yi, baza su
yarda ba, dan haka take rabuwa da su,
5
IZGILI JAMILA MUHAMMED
dan ta san haka take ba wata yangar da
take yi.
Tun da ta taho ya kura mata ido kur
ko kiftawa ba ya yi gaba daya hankalinsa
baya kan abokin nasa da yake ta faman
rattabo masa bayani ina shi kuwa
hankalinsa ya yi gaba bai ma san me yake
ba, gaba ɗaya yarinyar ta gama burgeshi.
Nutsuwarta da shigarta sun burgeshi.
Sanye take da dogon hijabi ruwan toka
har kasa da duk alamu hijabin Islamiya
ne dan tun ɗazu yake ganin 'yan mata
masu kalar Hijabin su na wucewa sai dai
ita har da nikabi a fuskarta kuma
hijabinta har kasa ne saɓanin na wadanda
ya ga ni, wata dai-dai gwiwa ne wasu ma
dai dai cinya shi dai tun dazu daya fara
ganinsu suna wucewa bai ga mai hijabi
kamar nata ba saboda ita har wajen idan
sahu yazo mata.
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Ta wuce ta gefensu idanunsa kyam
akanta suna yi mata rakiya.
Alhaji Umar mai akwai da yakewa
abokin nasa baya ni. Ya ji ya yi shiru ya
dan kalli inda yake sai ya kula gaba daya
hankalinsa da nutsuwarsa suna wani
gurin can, basa kansa.
Ya lura ya kurawa guri daya ido ya
kalli inda yaga yana kalla bai ga komai ba
sai kawai mutane da ya ga suna zirga
zirgarsu yawancinsu duk 'yan Islamiya ne
da suke ta tururuwarwar tafiya zuwa
gidajen iyayen su. Ya dan taɓa kafaɗarsa
gami da kiran sunansa.
Alhaji Mansir dan kimanin shekaru
saba'in da biyar, ya yi firgigit ya juyo
gare shi tamkar wanda ya ta shi daga
barci ya ce, “Am! Alhaji Umar me kake
cewa ne?"
7
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Alhaji Umar ya ce, "Ina hankalinka
ya tafi ne?"
Alhaji Mansir ya ce, "Na dan tafi
wani tunani."
Alhaji Umar ya ci gaba da yi masa
baya ni ya ce, “Mun yi dai dashi Nan da
sati hudu zai turo mana da cikwan kudin
dan wallahi sai da nai masa jan idanu, in
shi yana takamar dan zamani ne to ni
nashekaran jiya ne, dan na ga jiya naga
yau, kuma sai dana jaddda masa in har
lokacin yayi na ji babu labari to wallahi
kotu zan maka shege dan baka ga yadda
ya dinga bani hakuri ba da ya ga na je
masa ba sauki yana ta makyarkyata da ya
ji zancan Kotu yana bada hakuri nan na
taho na barshi. ".
Alhaji Mansir ya ce, "To shi ke nan
ni zan tafi yadda mu kai da Alha ji Auwal
game da aikin titunan nan zan ma waya.'
"
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Alhaji Umar mai Akwai ya ce, "To
babu damuwa,"
Su kai Musabaha. Alha ji Mansir ya
shiga dankararriyar motarsa ya tafi.
Zaune take atsakar gidansu tana
tankaɗan dawar tuwan dare Innarsu
Kuwa tana daga can gefe tana kaɗa miyar
Kuka, kuma suna ɗan taɓa hira
mahaifinsu ne Malam Usuman ya yi
Sallama gaba ɗaya suka amsa masa ya
shigo hannunsa rike da dan autan Innarsu
ɗaya Hannun kuwa bakar leda ce yake
rike da ita Inna Lariya ta saki Kadin
miyar da take yi ta shimfida masa wata
sabuwar tabarma da take jingine gefe
guda tana masa sannu da zuwa Hadiya da
sauri ta karɓi ledar da take hannunsa ita
ma ta nai masa sannu da zuwan Inna ta
dauko kofin silbar dake ajiye a gefe guda
9
IZGILI JAMILA MUHAMMED
wanda aka ci ka shi da sassanyar ruwan
Tulunta ta a jiyewa maigidan tana karai
masa sannu.
Ya sha ruwan sosai sanyinsa ya
ratsashi sannan yayi hamdala ya dire
kofin shima ya nai mata sannu da gida.
Aliyu dan Autan Inna yana daga
gefe sai murmushi yake faman dukawa
gaba daya ji yake tamkar an sakashi a gidan Aljanna saboda dadi ya san tunda
yaga Abbansu da leda yasan yau da cin
kayan dadi, shi yasa ji yake tamkar zai sume saboda murna, shi ma zai nunawa
su Abdul Abokinsa kayan dadin da
Abbansa ya siyo musu ko sa dainai masa
gorin babbansa baya siyo musu tsarabar
kasuwa kullum, Abdul sai ya yi masa
dariya saboda shi Abdul din babansu ko
da yaushe ya dawo daga kasuwa sai ya siyo musu kayan dadi su lemo, ayaba,
.
10
IZGILI
.
JAMILA MUHAMMED
abarba, Kwai, dafaffe, Biskit, youghort,
wata rana har da gasheshen nama ko
Kaza kuma ko babansu bai dawo da wuri
ba to da sassafe sai Abdul ya ajiye ya
nuna masa dan haka shi ma yau tunda
Abbansu ya siyo musu tsarabar kasuwa to
shi ma ba zai ci ba sai ya ajiye da safe ya
nunawa Abdul ya dai nai masa dariya
yana cewa babansu baya yo musu tsaraba
idan zai dawo daga kasuwa, kalubalenku
iyayan yara gaskiya da yawa iyayen yara
abinda muke bama kyautawa yadda
zamu dinga bawa yaranmu abu suna fita
da shi suna nunawa yaran makota ko
kuma yaran abokan zaman mu idan gidan
haya ne ta yadda zaki ga an bawa yaro
abu ya fita da shi cikin yaran gidansu
yana ci a irin haka ana samun matsala
babba, saboda wani yaran zai ‘yan musu
wani kuwa sai dai ya ɗagawa sauran
11
IZGILI JAMILA MUHAMMED
yaran hankali suna gani yana ci ba zai ba
su ba, haka za ki ga yara suna rusa kuka
duk su dagawa iyayen su mata hankali
dole sai an basu irin abinda wane yake ci
kun san yaro da gasa wata uwarma zaka
ga ita ke tura yaranta waje cikin yara ya
ci abin sai ka ga ta dauki abu ta ba shi sai
ta maza je ka gurinsu wane ku yi wasa
ko kuma fita tsakar gida gurin su wane ka
ci mana, to gaskiya irin haka babu dadi
ke dan asan kuna cin abu sai kin tura yaro
dan a gani alhalin yana dagawa yaran
mutane hankali.
Akwai matan da suke cewa yaransu
kada ka cinye duka mana ka rage da safe
ka nu̟nawą su wane, da dai ire-iren haka,
gaskiya mata mu daina irin wannan idan
ke kuna da halin cin abu bai ka mata ki
dinga turo yaranki suna dagawa wanda
12
i
IZGILI JAMILA MUHAMMED
kika san basu da halin wannan abin dan
Allah mata mu daina Allah ka iya mana.
Inna Lariya ta juyo tana kallon
Malam din fuskarta fal da farin ciki ta ce,
"Malam yau dai da alamar dawa Tai
nama.? Tun da na ganka da leda.'
"
Shi ma murmushin ne akan fuskarsa
ya ce, "Yau kam Alhamdulillah babu
abinda zamu ce sai godiya."
Ta ce, "Gaskiya kuwa, ba ka ga
auta ba ma baki yaki rufuwa yarasa inda
zai sa ransa saboda murna sai wata dariya
yake ɓangalawa gaba daya su kai dariya
har da Hadiya wadda take kaɗe zaninta
ta matsar da garin tana cewa.
"Abbu Kalli irin zaman ma da yai
."
har da tankwashe kaafu.'
Suka kuma yin dariya.
Malam Usman ya ce, “Bari dai in
bude tsarabar nan in raba kowa ya dauka
13
IZGILI JAMILA MUHAMMED
dan naga dattijo na ya kagara kowa ya ci
ko ba haka ba."
Ya ce, "Hakanne Abbu su ka kuma
yin dariya."
"
Malam Usman ya kalli Hadiya ya
ce, "Zo ki dauka ki wanke.
Ta ce, "To"
Cikin nutsuwarta ta dauki ledar
daya tureta gefe ta dauko wata 'yar
madaidaiciyar roba ta juye abin dake ciki
mangwaro nene lafiyayyo lafiyayyo masu kyau
manya manya. Ta wanke su tas sannan ta
kawowa Innarsu dan ta san ita zata raba
dai dai nan Bintu tai sallama ta shigo
mallam ya kalleta ya juyo da kallonsa ga
Innar da take raban Mangwaron ya ce.
"Wai shin Lariya bansa dokar fitar
yaran nan waje ba, In dai fitar ta wuce
cikin wuce wannan lokacin.
14
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Cikin tsananin ladabin Innar har da
dan dukawarta daga kan kujera ‘yar
tsugunne da take kai ta ce, "Ka fada.?"
Ya ce, "To to raina ni a kafara yi da
zance bana san abu ayi sanin kanki ne
babu abinda natsana irin a dinga barin
yara mata suna kaiwa magriba a waje, har
nake kafa miki misali da cewar ko aike ne
in har magriba ta sawo jiki to ki dinga
hakura har na dawo ni sai in je, shi ma
dattijo sai da nai masa faɗa, da har na
same shi a waje yana wasa ke kuma babu
ruwanki da kisa ayi kiransa ya dawo gida
tun da yamma ta yi ko.?"
Inna Lariya cikin ladabi gami da
kwantar da harshe ta ce, “Ka yi hakuri
Malam dan Allah Allah ya huci zuciyarka
wallahi dole ce ta sa na aiketa kuma
bama ta da lafiya ba, gidan babansu na
aiketa dan dazu Iya Saude ta aiko min
15
IZGILI JAMILA MUHAMMED
idan nadaka garafuni in bata to nai duban
duniyar nan ban gan shiba sai bayan ɗan
aiken ya tafi sannan na ganshi dan sai da
na caje ɗakina sosai to shi ne da suka ta
so Islamiya na ce tai maza ta dawo amma
dan Allah ka yi hakuri insha Allahu haka
ba zata kuma faruwa ba, ya sauke ajiyar
zuciya ya ce,
"Allah yasa."
Ta yi saurin cewa "Amin"
Tai wa Abbu Sannu da zuwa sannan
ta mika ledar da Iya ta aikota ta kawowa
Innarta su Innar ta bude taga curin fura ne
da kuma nono mai kyau ta ɗaure ta kalli
Malam ta ce, "Yau shi kenan ba za a ci
irin tuwan nawa ba dan ga shi nan iya
tayi maka haji da Umra."
Malam Usman ya saki dariya ya ce,
"Lallai kuwa yau tuwanki ko kallo bai
ishe ni ba dan haka yi maza ki dama min
16
"
*
IZGILI JAMILA MUHAMMED
kafin in dawo daga masallaci dan ga kira
nan a na yi."
Yana gama maganar ya karɓi butar
da Hadiya ta miko masa ya fara alwala su
ma gaba daya suka mike dan bada farali
Aliyu auta ne yai zaune yaki ta shi. Inna
ta ce, "Ya dai dattijo.?'
Ya ce, "Inna mangwaro."
Nan tai dariya ta ce, "Kayi sallar
mana tukunna ko kaga nace su dauka kai
kuma na hanaka.”
"
Ya mike da sauri damin yabi
Abbansu masallaci dan in dai bai je ba zai
iya cewa kada a bashi mangwaron tun da
bai bi jam'i ba.
****
Yau ma kamar ganin da yai mata
kwanakin baya sai dai yau tana rungume
da alkur'ani ta zo ta wuce ta gabansa
cikin nutsuwar nan tata ya rakata da idanu
17
IZGILI JAMILA MUHAMMED
tana dan yin yanga baya ya ji samarin da
suke kofar gidan da yake makoftaka da
gidan Alhaji Umar mai akwai daya
saurayin ya san shi dangi tane ɗaya ne bai
sani ba, ɗaya saurayin ya ce, "Gata nan fa
mutuniyar taka."
Kanti ya juya baya. Bashi ya saki
dariya ya ce, "Wallahi Allah ya suturu
bakui in ji kishiyar mai dorina ina zan
iya."
Kanti ya juya baya "Ai ba zan iya
koyaushe dan cinikin da nayi akasuwa su
kare akantin nan mutane ba.
Nura ya ce, "Yanzu ina jin ta daina
tunda yai mata illa."
29
Bashi ya ce, "Ta daina me? Kallo
kafarta ka gani mana malam tamkar ta
turawa saboda tsahar mankanti fuskarce
dai dai ta ga ji da man shi yasa ta lalace
take rufeta yarinya sai shegen jiji da kai
18
IZGILI JAMILA MUHAMMED
ke da fuska ta riga tai dameji har kece me
wani ɗagawa mutane kai."
Su ka sake dariya suka tafa Alhaji
Mansir ya ce, "To me ye ma'anar Kanti.
Ya juya baya sun santa ne ko̟ ku ma
dai ita ma bata da nutsuwa tamkar su, dan
kallo daya za kai musu ka san su din
kwararrun 'yan duniya ne, haka zuciyar
Alhaji mansir ta dinga masa tambayoyi
barkatai wanda ba shi da amsar su, dai
dai nan Alhaji Umar mai Akwai ya fito
hannunsa dauke da wasu takardu ya
karaso inda Alhaji mansir yake tsaye
jikin motarsa, ya mika masa hannu gami
da cewa “Ga_su_nan ka duba su, jibi
jibin nan nake son tafiya Kaduna akan
aikin makarantun nan.
"
Ya ce, "Insha Allahu zan yi
kokarin ganin na gama su jibin su kai
sallama ya shiga motarsa ya tafi.
19
IZGILI JAMILA MUHAMMED
BAYAN SATI UKU
Hadiya ta duba agogon dake daure a
tsintsiyar hannunta ta kai dubanta ga Jana
data ke ta faman baza powder Hadiya ta
ce, "Dan Allah Jana kibar saka powder
nan haka kin ga yamma ta yi kada Abbu
ya dawo ya tarar bamu dawo ba gobe ba
zai sake barina fita ba."
Jana ta dan dauke idonta daga
kallon Mirrow ta ce, "Dan Allah kada ki
takuramin ki barni in yi kwalliyata cikin
nutsuwa dan na sanki da shegiyar
hayyata in ke bakya abu sai ki hana masu
yi suyi."
Hadiya ta ce, "Yanzu duk wannan
baza eye shadow da wannan jam bakin da
kika gabza ba ki yi minti sha biyar kina yi
ba, ai ban miki magana ba, to sanin ki da
nayi naga ko kin gama fentefenten naki
ba gama kwalliyar bace dan sai ki kara
20
IZGILI JAMILA MUHAMMED PROSTY
wani minti sha biyar din kawai kina
kallon madubi kina kara baza powder ja
na ta ajiye sosan da take shafa powder ta
kara gyara zaman ɗaurin ɗankwalinta ta
ce, "To da zaki ishe ni da Ina ta shafa
powder ca nake ke ma kin shafa ko ke
naki ba sai ni zaki hurawa wuta.'
"
baki gaAnty Meena ta shigo tana fadin ita
ai shafawar masu hankali ta yi ba irin taki
ba da sai a kusan karar da ita ashafawa
daya, ke in dai zakiyi kwalliya sai ki
shafa powder wajen sau goma. "
Jana ta cuno baki tana kunkuni ita
kuwa Hadiya dariya take mota ta ɗauki
Hijabinta ta saka gami da ɗaura nikaf
dinta ta ce, "To fi'ili madi ai sai mu tafi
ko?'
Jana ta kalleta wani takaicinta ya
kamata tace dan Allah dubeta haka kawai
kisa kanki a Uku ki dinga yawo cikin
21
IZGILI JAMILA MUHAMMED
wannen zirmemen Hijah ki wani rufe
fuska ke ba matar Liman ba zafi duk ya
damc ki, dan Allah dubeki duba kayan
dake jikin ki Hadiya tai saurin daga Nikaf
dinta tana kallon Jana ta ce "Mc kayan
nawa su ka yi.?"
Jana ta ce, "Riga da siket ne ajikinki
sun yi miki bala'in kyau sun yi cif-cif a
jikinki tamkar ajikinki a ka dinka su
saboda kyan da kayan su kai miki amma
zaki kassara rayuwarki ki rufewa mutane,
to ba a haka bane zaka samu mai son ka
wanda zai ganka ya ga ka yi masa amma
ke kullum zurum-zurum cikin hijab har
da su nikaf shi yasa har yanzu baki da
saurayi ko daya, to yaushe mutum zai ce
yana sanki alhalin bai ga abinda yai masa
a jikinki ba bare ya ce, yana son ki.
Ta cije gefen danyatsanta ta ce,
"Wayyo Allah garin dadina nesa in ji
22
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Angulu da ta lefa masai ai wallahi da ni
Allah ya bawa farin ki gashinki, dirinki
idanunki muryarki, wallahi ba karamin
yaki zan yi ba don sai na saka samari
runtsċ ido sai na daga musu ganye da duk
wankan da nai sai na sumar da samari
warwas Allah yai miki kira ba ta Allah
Sarki ba ya yi miki halitta ba wadda miji
zai ce shiga daka na yi ba, Amma kina
cutar da masu sanki ni na tabbatar ko sau
daya kika cire Hijab din nan da wannan
Nikaf din na tabbatar sai kin saka maza
karo."
Anty Meena ta kaiwa bakin Jana
duka ta ce, "To taki yin yadda kike so ke
ganin fito da tsiraici waje shine wayewa
to wallahi ba wayewa bace, sai ci baya
wanne namijin ne kin gama tallar Nono
da kugu awaje zai kwashe ki sai kace
mara mafadi to bara in baki misali ke ce
23
IZGILI JAMILA MUHAMMED
kika ga a titi ana sai da cincin ga wani
abude kura da iska duk sun koɗashi ga
kuma wani a cikin glass a rufe sai mai
cincin zai baki nawajen nan wanda
saboda kura da ta badeshi har ya fara
canja kamannin shi, "Ai na san babu ta
yanda za'ayi ki yarda ya baki
wannanAlhalin kina ganin yarda yake sai
dai ki ce na rufen nan kike so, saboda yafi
mutunci to haka ma maza suke kallan duk
wata mace mai bayyanar da jikinta mazan
titi suna gani haka suke kallanta tamkar
wannan buɗaddan cincin din da dattin
duniya ya gama badeshi..
Hattara dai mata masu irin wannan
hali masu gani cinyewarke nan to wallahi
ci baya ne ba cinyewa bane bar ganin a
nayi miki layi a gidan ku dan kina irin
wannan shigar to ina mai tabbatar miki
duk cikin masu zuwą gun naki babu
24
IZGILI JAMILA MUHAMMED
wanda yake zuwa da zummar aure sai
dai da niyar wata bukata ta shi, kuma da
bukatarsa tabiya ba zai kara ko kallon
inda kike ba to talla ki kai shi kuma ya
taya kika sallama to kin ga kuwa taya zai
kai ki gidansa harki zama uwar ‘ya'yansa,
ke ma kin san (Impossible)
Jana ta dauki ɗan yalolon
mayafinta daya dace da atamfar jikinta
da akaiwa dinkin riga da siket sun kamata
dan-dam ta dauko post dinta ita ma kalar
kayanta. Ta ce, "Sai mu tafi Sayyada."
Anty Meena ta ce, “Ko baki faɗa ba
mutane zasu fada su ce ita din Sayyada
ce ke ko kunyar jerowa da ita baki ji ba,
ita ta yi shigarta ta kirki mutum duk na
cinsa ba zai ga ko ina nata ba, amma ke
dubeki dan Allah wallahi Jana ki yiwa
kanki faɗa, ki yi koyi da Hadiya ki dinga
komai na ki da nutsuwa."
25
e.
2
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Jana ta figi ledar da Anty Meena ta
shigo musu da ita, turaren wuta ne da
Humra da take siyar da su ta basu turaren
wutar ta kaiwa Iya mahaifiyarsu da kuma
Inna mahaifiyar Hadiya Humrar ta suce ta
basu sannan ta mikawa Hadiya dari biyu
ta ce su hau adaidaita sahu.
Hadiya ta ce, "Wallahi ki barshi
Anty muna da kudin Mota."
Anty Menna ta dan zare mata ido ta
ce, "Karбi mana ai na san kuna da kudin
motar na baku.”
Hadiya kasancewarta mai da'a
kuma ba a ai musu tarbiyar jayayya dana
gaba, yasa ta karɓa tai mata godiya ta
rakota har soro. A kokafar suka ga Jana ta
cuge tana ta faman kumbure-kumbure.
Anty Meena ta ce, "Ku gaishesu."
Hadiya ta ce, "Za su ji."
26
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Ta gangara inda Jana take suka jera
zuwa titi Anty Meena yayar Jana ce uwa
daya uba daya ita cc a biyu a gidansu
tana aure a Yalwa bata taɓa haihuwa ba.
Jana suna tsaye abakin titin,suna
jiran adai-daita sahu kasancewar duk
wanda ya taho zaka same shi da mutane
saboda yamma ta yi tun daga nesa ya
hangota ya ganeta ita ce zuciyarshi ta
gaya masa ya tsura musu ido yau ma dai
irin shigar da ya ganta da ita ce sai dai
wannan ba hijabin Islamiyar bane shi
wannan kalarsa maron ne kalar flat din
takalminta ne kuma sanye take da Nikaf
dinta babu abinda kake gani sai kafarta
kasancewar Hijabin dogo ne sosai.
Idonsa ya kai ga wadda take kusa da
ita ya kalleta yaga irin shigar da ta yi
gaskiya ya yaba da nutsuwarta da
hankalinta yana. kallo sai tsaida abin hawa
27
IZGILI JAMILA MUHAMMED
suke amma ba su samu ba ya wuce ta
gabansu yana ci gaba da fadin kamun
kanta to shi dai duk ganin da yake yi
mata cikin nutsuwa yake ganinta bai ma
taɓa ganin fuskarta bato me yasa ya ji
wannan samarin suna fada mata wani
suna wai kanti ya juya baya mai hakan ke
nufi? Wata zuciyar ta ce, masa kawai dan
sunga ba kalarsu bace shi yasa suke jin
haushinta har suke Igaya mata wani suna
haka ya dinga tunani harya isa gida.
**
.
Hadiya tana sharar tsakar gida ta ji
sallamar babbar kawarta tata Jana. Jana
kawar Hadiya ce tun suna yara sun yi
mutukar shakuwa ta yadda babu wadda
za tai kwana biyu batare da ta nemi 'yar
uwarta ba duk da babu ta yanda za ai su
hadu batare da sun kafsa ba anan dai na
yi musu da maganar Malam bahaushe da
28
IZGILI JAMILA MUHAMMED
ya ce, sai hali yazo daya ake abota to
waɗannan aminan junan su sam ba haka
bane dan ko wace da inda ta dosa inda
hakan halaiyace inda Jana ta kasance mai
san gayu da kece raini tana da rawar kai
mutuka ga saurin fushi amma bata da
wuyar saukowa.
Tana da kirki bata kuma da kyashi
ko hassada ita in dai dan uwanta ya samu
to ji take tamkar ita ta samu sannan bata
da rufi duk abinda ya dameta kai tsaye
zata gayawa babbar aminiyarta bban
abinda yasa suke samun matsala da
kawartata shine ita dai Jana Allah ya yo
ta mai san saka kananun dinkuna ce
kuma idan tasa ba zata sami mayafi mai
yalwa ta rufe jikinta ba, sai dai irin na
'yammatan zamani ita tana jin bakin ciki
ganin yadda kullum Hadiya take faman
jibgawa jikinta dogayan hijab har da su
29
IZGILI JAMILA MUHAMMED
nikaf, sai kace a zamanin jahiliya ga dai
kyau dan asali kyau zalla amma bashi da
amfani tunda kullum ana rufcwa masu so
basu gani ba bare su yi sha'awa yayinda
Hadiya tata kasance kasance. marasan magana
sannan bata san raini ko wulakancin sam
bata da saurin fushi amma kuma bata da
wuyar saukowa tana da shagaɓa mutuka
da sangarta in dai a gaban Abbunta ne da
Innarta tana da tausayi ita abu kankani sai
ya sata kuka shi yasa Jana take ce mata
mai arhar hawaye, ita abu kaɗan sai ya
sata kuka.
Ta dago da sauri tana dariya Jana ta
kalleta ta dauke kanta ta karasa gefen
tabarman dake shinfide suna gaisawa da
Inna Hadiya tana sharar tana dariya dan ta
san lefinta ta san kuma shi yasa Jana ta zo
tana karasa sharar ta wanke hannuwanta
30
IZGILI JAMILA MUHAMMED.
ta karaso kusa da ita tana fadin "Kawata
ya dai.?"
Tana dauke kanta Hadiya ta guntse
dariyar da ta cika mata ciki ta ce, "To ta
so mu shiga ciki sai ingaya miki uzurina
da abinda yasa ban aiko miki da wuri ba."
Jana ta bita ɗakinsu ta zauna kan
'yar yalolowar katifar Hadiya wadda
saboda sidewa ta dawo tamkar tabarma,
ta kalleta ta ce, "Uhm Ina jinki faɗa min
dalilin da yasa da kika san ba zaki je ba
me yasa baki aiko min da wuri ba.?"
Hadiya ta zauna kusa da ita ta ce,
"Ai ya kawata ni ma ba haka na so ba na
san Bilkisu Ibrahim ba zata ji dadi ba,
babu daya daga cikin mu daya je."
Jana ta harareta ta ce, "Waya ja?
Idan bake ba da kika san ba za ki je
waliman nan ba tunda wuri ba sai ki
aikomin ba in sami abokin tafiya kawai
31
IZGILI JAMILA MUHAMMED
sai dana shirya ina ta jiranki sannan zaki
wani ce min Inna bata nan, shi yasa ni ma
Faina ya ɓaci kawai nace to nima na fasa
zuwa.
"
Hadiya ta ce, "Haba sister me yasa
kika fasa ai Amiru ɗazu ya gayamin dana
ce ya je ya gaya miki ki bani kayan
walimar ya ce ke ma ba ki je ba.
Jana tana faɗin ‘yar rainin hankali
bayan sai da kika bari duk 'yan tafiyar
sụn tafi sannan kika wani aikomin ai na ji
haushinki sai kuma daga baya na ji
daɗima da bamu je ba.
Hadiya ta ce, "Saboda me? Yanda
kika kwallafa ranki akan walimar nan. "
Jana ta