Gombe da ma
kauyikansu sai dai mu ce, Allah ya ji
kansa, halinsa na gari ya bishi, mutuwar
Alhaji Bawa da shekara Alhaji Mansir ya
tattaro ya dawo Kanon dabo mai mata
mai mota mai dala da gworon dutse.
saboda harkokinsa sun fi yawa a can kano
da Abuja, a inda ya kera gidansa a Zoo
road suka tare sai dai duk karshen wata
yake zuwa Gombe domin duba hajiyar,
sai da ya kaɗa ya raya ya ce, Hajya ta
dawo amma ta tubure ta ce, babu inda
zata saboda mutanan alhaji marigayi
saboda duk wani abu da ake yi da babu
100
IZGILI JAMILA MUHAMMED
wanda aka daina 'yan'yan ta maza sun
tsaya mata musamman Alhaji mansir dan
shi ne ya dauko kyauta irin ta
mahaifinsa, da son talakawa mararshi,
dan gaskiya yafi kannensa najib da
Isma’il taimako dan su da Hajjo tai musu
zancen duk wata ga abinda zasu kawo
cewa su kai kai a bari wanda Baffa ya yi
ya yi, ya isa, Allah ya bada lada.
Batai mamakin jin irin wannan
maganar daga bakinsu ba dan ta sansu ta
san halinsu suna kyamatar talaka sun ce
su da talaka ko a hanya, shi yasa
kwandalarsu ba zasu bayar ba, dama da
mahaifinsu yake yi ba asan ransu bane,
dan dai ba yanda zasu yi ne, kuma saboda
ba kudinsu bane, ko da yake shi najib sai
da ya taɓa gayawa Hajjo gaskiya ta
gayawa Baffa ya daina kashe musu kudi
haka.
101
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Ta kalle shi da alamar tambaya ta
ce, "Wana irin kudinku yake kashewa
aikuwa babu kun ya babu tsoon Allah ya
ce, Dukiyar Baffan nasu ai ta suce saboda
haka gaskiya Baffa ya daina raban kudi
da abinci ai sangarta su ake yi, su dinga
zaman banza, zuciyarsu ta ida mutuwa,
tunda suna da mai basu abinci har ma da
nace fane, dan kada ta Allah ta kasance
gadonsu ya zaru babu auki."
Hajjo sai ta saka salati tana
salallami fadi take oh ni Rahine yau naga.
abinda ya ishe ni najib Allah ya shiryeka
to ni dai ba za aji wannan maganar a
bakina ba, idan ka matsu kai ka same shi
sai kai masa maganar, shi yasa koda suka
ce su ficikarsu bazasu bayar ba bata damu
ba, ta gayawa Alhaji mansir ya ce, Dama
bata yi musu magana ba.
102
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Hajjo kin san dai kome ye kike
bukata zan yi miki su yarane daman niya
dace in yi ko meye Hajjo ta ce, "Duk da
haka kai ma ai zaka so su taimaka maka
tunda abinda ai da yawa, kuma kamar
yanda kudi suke zuwar maka suma haka
kawai dai su haka Allah ya yosu in dai
batu ne nasu bayar to fa ba za a ji bakinsu
ba, saboda Allah rayuwa kuwa zata yiwu.
a haka kana da shi ba zaka taimaki dan
uwanka marasa shi ba.
Alhaji Mansir ya ce, "Hajjo ki daina
ganin laifinsu suna fa da iyali ga yara da
wanne za su ji."
Hajjo ta ce, "Da yake kai baka da
iyalin ko haka dai ya dinga bata hakuri ya
ce, tunda ya ce, zai iya zai iya dinne
tunda mahaifinsu ya rasu, shi ya dauki
nauyin yin sadakar da aka sabayi, duk
safiya ana dama koko da kosan sadaka
103
IZGILI JAMILA MUHAMMED
kuma kokon da sukarinsa bajau, da rana
kuma ana yin wake da shinkafa da mai
mutum sai dai ya nemi ya ji, kuma ba sai
almajirai ba ko waye in dai yake ko ya
kai kwanansa, duk girmansa sai an take
masa shi abinci, duk ranar juma;a ana can
ja kalar girkin da safe ana yin kunun
tsamiya da fanke, da rana kuma ana yin
tuwon shinkafa da miyar taushe, kuma
gaba daya Alhaji mansir ne yake komai
hatta da 'yan aikin da suke wannan
aiyukan shi yake biyansu, kwandala babu
ta wani dan uwansa kuma duk karshen
Iwata yake zuwa ya saurari talakawan da
mahaifinsa yake taimaka musu, wasu
bikin 'ya zai yi babu gaba ba baya.
Wani matarsa ce ta haihu babu
Ragon suna wau rusaune ya rutsa da su,
da dai sauransu duk kuma wanda ya
kawowa Alhaji Mansir matsalarsa to sha
104
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Allahu sai ya taimaka masa sai mutumin
nan ya yi farin ciki ya saka masa albarka.
Hisham ya yi Primary dinsa wata
tsadaddiyar makaranta dake cikin birnin
na Kano mai suna Attaufeek Iliman an
tahafees yaro ranar da ya gama primary,
to ranar aka masa bikin sauka to shi ma
Hisham haka daga nan sai alhaji Mansir
ya kai shi Germany gidan kanwar Hajiya
Zalifan watan Nadiya da take aure a can
suke zaune a can ita da mijinta sai dai
basu haihu ba a can yai Secondry dinsa
yai kuma jami'a.
Hisham ya zaɓi ya gaji dadinsu
watan dai yana san zama controctor
aikuwa sai da ya zama Hisham tun yana
Secondry dinsa ya fara Harka da 'yan
mata kasancewar kyakkyawa gaskiya
Allah yai masa halitta gaskiya Hisham ya
gama haduwa Hundred percent to jinin
.105
IZGILI JAMILA MUHAMMED
larabawa fa, da kuma fulani ga kulawa
dole a ga kyau dan usuli duk inda kake
neman kyakyakyawa to kana samun
Hisam sai a shafa fatiha, saboda kyau ne
tsabarsa babu mide babu abinda yake
kara masa kyau irin wadannan kyawawan
idanuwansa masu firgita 'yan mata ko da
yaushe zaka gan su a lumshe.
Hisham dogone amma ba irin
zankalkal din nan ba ne yana da dan jiki
watan murjewajiki dan shi ba irin
ramammun nan bane sanna kuma shi ba
mai jiki ainun ba ne, fari ne tas irin farin
larabawa kana ganin sa zaka san shi din
balarabe ne ta yadda ga shin kansa yake
akananɗe mai kuma azabar santsi da
baki irin na larabawa.
Yana da dogon hanci, bakinsa dan
dai-dai mai fararan hakora tas, tamkar
kankara, idanunsa a lumshe tamkar mai
106
IZGILI JAMILA MUHAMMED
jin barci yana kassara dubun nan 'yan
mata da wannan kallon na shi mai ratsa
JINI DA JIJIYA.
Hisham Mansir Kwangila ke nan
miskili mai murdadɗan hali yana da
tsare gira ba shi da fara'a tunda yake shi
bai san so ba, bai taɓa yin shi ba kuma
baya son yasan shi bare ya yi shi, duk
'yan matan dayake yi bai taɓa cewa yana
san su ba sai dan shi suce suna son sa...
Ya yi 'yan mata 'ya'yan manya wadanda ba zai iya kirga su ba shi din
mane min mata ne na sosai amma ba ko
wacce kuci ku bamu ba shi din sai kin kai
kin doke kin haɗu koma ki na da abinda
ya yi masa shi ne zai ce miki bukatarsa
shi yasa matansu suke rububinsa suke
kuma son sa.
Hisham sai da yai shekara goma sha tara a duniya sannan ya samu kanwa mai
107
IZGILI JAMILA MUHAMMED
a sarar
sunan Hajjo kakarsu wato Rahina, ake
kiranta da Ummita, Hisham ko da ya
kammala karatunsa bai dawo Nigeria ba,
wani kamfanin zane zane ne suka dauke
shi aiki sai da Alhaji Mansir ya yi da
gaske sannan ya dawo gida amma duk da
aka yadawo da ɗabi'ar nasara
duniya ya koyi yadda ake daga kwalba mata kuma yanda suke sonsa duk inda ya
shiga in dai da mata sai sun so shi dan
Allah yai masa farin jini in dai ya shiga
guri sai an so shi to kuma daman an ta shi
garin ida suka dauki zina tamkar ado,
kuma akai dacen shi din mai farin jinin
matanne da kansu suke yi masa tallan
kansu, burinsu dai da fatansu ya yarda dasu batare da ko kwandalarshi ba, su
abin alfaharinsu ne kamarsa hadaɗden
saurayi ya kwasa sai dai alhaji Mansir yai masa jan ido kuma an kammala ginin
108
IZGILI JAMILA MUHAMMED
kamfaninsa na Abuja shi yasa ya matsu ya dawo domin ya kula da shi shi kuma
alhaji Mansir din ya kula da na nan Kano
din, ya kuma gaya masa ya siya masa fili
a nan cikin garin Abujan idan yana da
zanen gidan da yake sha'awa to ya turo
masa ta computer sai Ai masa kafin ya
dawo aikuwa har an kammala masa
hohoho dan da shi gaskiya gida ya tsaru tamkar wani shugaban kasa.
Gidan ya gama haduwa bada
dadewa ba ya diro Nigera kasarmu ta
gado, ya yinda ya kwashe tsayin shekaru
ba ya kasar dan tunda ya gama primary ya tafi sau biyu kawai ya zo shi yasa yaga
kasar ta canja masa, tamkar ba dan kasar
ba, dan duk komai ya canza masa, ‘yan
uwa ansha murnar dawowarsa, Ummita
kanwarsa ma sai murnar dawowar
yayanta take.
109.
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Bayan ya huta yai raban tsaraba
kowa aka bashi sai da yai wata biyu yana
hutawa sannan ya tattara ya koma Abuja
daman dawowarsa da sati akai
kasaitacciyar walimar dawowarsa, tare da
murnar bude kamfanin.
An sha shagali an kar kudi tunda ya
tare Abujan ya dada ci gaba da harka da
matansa giya tamkar ruwan roba ya
maida ta. Dan idan kuka ganta jejjere
cikin firji dinsa ka dauka lemo ne.
Gwani ne a harka da mata da kuma
wiwi, sai taba da ita ma ya kware gurin
shanta, to daga su baya karawa da komai
duk wani rashin tarbiya da ya koyo ya
kuma zubar da wanda iyayansa su kai
masa; to bai daina sallah ba, kuma yana.
yinta a kan lokaci, duk yanda ya kai da
sheke a yarsa to da zarar lokacin sallah ya
yi to zai watsar da koma mai yake, sai ya
110
IZGILI JAMILA MUHAMMED
sauke farali, Hisham yana da mutukar
tsafta ga
ya
shi kuma da tsantsani na jaraba.
Ba ko wanne abinci yake ci ba, sai
kina da maşifar tsafta shi a duk gidansu
idan ba Momi ce tai masa abinci ba ba
iya ci, da ba yacin girkin 'yan aikin
gidansu, dan haka ba kowane restaurant
yake cin abincinsu ba, sai irin kasaitattun
nan, wanda sai manyan garin na Abuja,
suke zuwa to irin su yake iya cin nasu,
koma sai ya bada tsaftar gurin da
ma'aikatansu zaka sha mamaki, mutuka
yadda ya dauki al'adun turawa, da
ɗabi'unsu to sai kuma bai dauki cimarsu
ba gaba daya ma ba zai iya cin irin
abincinsu ba, dan tunda yake bai taɓa
ɗanɗana irin abincin nasu ba, kuma ya
ɗauki tsawan shekaru goma sha tara
zuwa a shirin a turai amma bai taɓa gigin
dandanar cimarsu ba, don in har ya ce,
IZGILI JAMILA MUHAMMED
zai dandana to fa babu shakka sai ya
tanadi gadon a Asibiti, saboda yasan sai
ya kwanta ciwo dan shi a ganinsa babu
babban abin kazanta irin abincinsu, dan
shi ko gani ya yi suna wani jagulan girkin
to fa ranar yini zai yi zuciyarsa na ta shi,
sai ya yi amai, zai ji dadi.
Shi a rayuwarshi babu abincin da
zai ci ciki lafiya baka lafiya irin abincin
mu na Nigeria.
Aiko dole Anty Nadiya take yin
irinsu tun bata saba ba har ta koya dan shi
da kansa yake yi, tana ganin har ita ma ta
iya take yi musu ai fa sai ta ga gaskiyar
Hisham abincin Nigeria yafi na kowacce
kasa dadi, a ido, zaka ganshi da tsafta
hade da ban sha'awa, baki ga shi da dan
karan dadi ranar da Hisham yai musu dan
haka hohoho! Zo ka ga wawa su gurin Al
Mubrak mijin Nadiya shi ma Balarabe ne
112
IZGILI JAMILA MUHAMMED
aiki ne ya kawoshi Germany amma
haifaffen Misra ne, danwaken fulawa ya
yi musu, da man gyada ziryan da yajin da
yasha magi ya yanyanka dafaffen kwai a
ciki ai ji su tamkar kunnansu zai tsinke
saboda dadi duk wata Momi take aiko
musu da ka yayyakin amfani irin na
Nageria har fulawa take aiko musu da ita
su kuka, daddawa, karkashi, kuɓewa
bushashshiya, zogale, wake, gyaɗa, man
gyada, dakakken yaji, manja, kayan
kamshi, man shanu, bushahhen kifi,
ogun, ayodi, da dai sauran kayayyakin
girki irin na Nigeria.
Aikuwa Hisham ya zage ya danɗasa
musu girkin da wata macen ma ba za ta yi
test ɗn na shi ba, komai cikin tsafta
Tentable gare shi kullum ga kalar girkin`
da zai yi ya iya wainar fulawa, wadda
baya gajiya da cinta, wake da shinkafa,
IZGILI JAMILA MUHAMMED
jallof din shinkafa ko taliya alkubus ma
ya iya, arayuwa tuwo ne kawai bai iya ba, shi ma ba wai towanne bai san yanda ake
ba ya san yanda ake yi tuka tukenne bai iya ba, duk sanda zai musu tuwo sai dai
ya nunawa Nadiya ta tuka. To bata iya ba
har ya koya musu, ita da Mijinta.
Wai shi ma yana san ya iya saboda
watarana ko idan Nadiyan bata da lafiya aikuwa tunda kowa ya iya shi ke nan idan
daga Hisham ne ya riga dawowa
makaranta sai ya girka musu abinci, idan Nadiya ce, sai ta yi dan ita ma karatu take anan jami'a da Hisham din yake, amma ba departement dinsu da ya ba, idan kuma mijin tane ya riga ta dawowa to shi
zai musu abincin.
Haka yai rayuwarsa cikin jin dadi gidan Anty shi tamkar kaninsu haka suka dauke shi ba dan ba shi yasa yake yadda
IZGILI JAMILA MUHAMMED
ya ke so, a kuma lokacin da yake so
mahaifinsa ya shiga tashin hankali ne tun
randa ya kama kwalaben giya burjik a
dakinsa lokacin da ya dawo tun daga
sannan yake san ya yi aure ko ya rage
wani abun dan aure ni'ima gare shi yana
sa arage duk wani iya shegen da ake yi
tun daga lokacin yake tuntuɓarsa da
zancen amma shi Hisham din ya share
maganar a ganin sa me zai sa ya yi wani
aure idan banda takurawa kai da saka wa
kai tention to shi gara ya yi rayuwarsa a haka duk da ya san hakan da yake yi ba
dai-dai bane, ga tarin zunubin da yake ta
jibgawa kansa Zina ai babban laifi ne ko
da yaushe idan wannan tunanin ya faɗo
masa sai ya shiga ta shin hankalin irin
laifukan da yake aikatawa, ya yi ta tuba
gurin Allah amma ya kasa hana zuciyarsa
aikatawa, saboda shi din baya iya
'
IZGILI JAMILA MUHAMMED
daurewa ko ya ce ya daina da zarar wata
daga cikin 'yan matan nasa ta zo to fa shi
ke nan zai koma ruwa, saboda tsabar
sansa da 'yan mata suke yi ba shi yake
kiransu ba su suke zuwa har inda yake
kuma sai ya ga mai musu wulakanci
saboda shi din IZGILANCI halinshi ne,
ko dan jinin sarauta yana yawo a jininsa
ne, yasa yake da shariya, da tsare gida,
duk yanda kuke da shi karya ne ka ga
dariyarsa shi sam baya dariya sai dai
murmushi, shi ma mai gani daga Momy
dinsa sai Daddy dinsa sai fa idan ya yaba
da ke. Farkon haduwarku ba zai ce kin
masa ba, ko yai miki magana sai dai ya
dan yi miki murmushi, to har ku rabu da
shi ma, ba zaki kara ganin ya yi miki ba,
shi kuma duk yanda kika kai da nacinki
yawan lokacin da za ku yi ke da shi wata
ɗaya ne, da ga nan kuma sai wata, saboda
424116
IZGILI JAMILA MUHAMMED
yan matan su suke nuna masa kaunarsa su
suke kamar su ne namijin shi kuma shi ne
macen shi yasa yake ja musu aji yake yi
musu yadda yaga dama saboda su suke
binsa ba shi yake binsu ba.
Tir da wannan zamanin da 'yan
mata suke ganin cinye wace waye wace
dan kin buɗa baki kin cewa saurayi kina
san shi wannan ba ɗabi'ar kamun kai
bane, wai mai yasa mata muke wulakanta
darajar mu, muke banzartar da kimar mu
mace fa daraja gareta shi yasa Hisham bai
ɗauki mace wata tsiya ba, saboda ya cam
fasu duk matan waka suke basu da kintsi,
saboda bai taɓa haduwa da ta garin ta
kirki ba, wadda duk kyansa duk kuɗinsa
haka duk ajinsa kuma duk mukaminsa
karya yake ta bishi sai dai shi ya bita ko
da kuwa shi ne shugaban kasa, dan har
yau har gobe akwai na gari na kirki a
IZGILL JAMILA MUHAMMED
cikin 'yan matan masu kuma kima da
daraja, sannan kuma da yawa a duniya shi
din ne bai taba dacan haduwa da ta kirkin
ba yanzu watansa tara ke nan da dawowa
Nigeria.
Sanda ya dawo da sati biyu suka
'koma saban gidan da Alhaji Mansir din
ya tamfatsa a sultan road a ciki ma a kai
bude saban kasaitacciyar walimar
kamfanin na Abuja da kuma murna
dawowar ɗan lelan Alhaji wanda Alhajin
ya sangarta shi ya taɓarashi, su ka kuma barshi yake yadda ya ga dama ba kuma
tare da sun tsawatar masa ba.
AN DAWO LABARI
Hadiya ce sun kuye bakin murhu
tana faman hura wuta taki ta kama kasan
cewar icen ɗanye ne saboda yana yi na
damina ta ɗago da idanuwanta da suka yi
jajir saboda a tsabar hayaki tana amsawa
118
IZGILI JAMILA MUHAMMED
yaron da ya shigo sallamar da ya yi,
yaron ya ce, “Wai wani Awaje ya ce, na
sallama da Malam Usman.?'
Ta ce "Kace yana zuwa.
Ta mike daga durkson da ta yi tana
karkade jikin ta ta yi sallama kofar ɗakin.
Innar ta su, in da baban nasu yake
kishingide yana sauraren gidan radio
kano suna gabatar da zaɓan yamma Inna
kuma bata nan ta tafi dubiya, amma ta san
tana hanya tunda yamma ta yi, duk da dai
bata wani jima da tafiya ba, dan sai bayan
sallar la'asar sannan ta tafi.
Malam Usman yasa hannu ya rage
radio yana amsa mata sallamar ta durkusata ce, "Abbu ana sallama da kai'a waje."
Ya ce, "Wa ye.?"
Ta ce, "Ni ma ban sani ba."
Ya dauki hularsa dake ajiye a
gefensa yana kokarin sawa ya ce, "To
119
IZGILI JAMILA MUHAMMED
'yar gidan Abbunta maza je ki ci gaba da
aikinki."
wata
Ta saki wata dariya mai ban
sha'awa ta tafi ta ci gaba da aiyukanta
shi ma Abbun fitowa ya yi dan ya ga mai
sallamar yana fitowa yaga
tsadaddiyar mota ta dallare masa idanu,
saboda kyau sabunta tai shurum a kofar
gidan nasa, tana hutawarta daga gefe
kuma wasu kasaitattun Alhazawan birni
ne tsaye a jikinsu sanye da dakakkun
danyin shaddodi, sai zabga daddadan
kamshin turare suke irin nasu na manya,
ya dan ja turjiya ya tsaya turus, yana
tunanin ina mai sallamar yake dan shi ko
kusa bai yi tunanin wadannan hamshakan
mutanan sune masu sallamar ba dan ya
san shi dai shehu Usman mai faci duk
cikin mutanan daya sani yake kuma har
120
IZGILL JAMILA MUHAMMED
kar dasu ba shi da irin wadannan balle
har yai tunanin su ne suke sallamar...
Sallamar ya ji an yi masa yai saurin
dawowa daga tunanin da yake yi, ya amsa
sallamar shi ma cikin sakin fuskar tamkar
dai suma da suke ta sakar masa,
murmushin. Shi dai shiru ya yi yana
kallonsu daya ne ya farayin magana ya
ce, "Mu ne muke sallama."
Ya ce, “To madalla Alhaji Yakubu
babban na hannu daman Alhaji Mansir
dinne dai har yanzu yake maganar ya cc,
"Daman Mun zo gurin ka ne da wata
muhimmiyar magana wadda take bukatar
zama dan ni din ba gwanin tsaiwa banc.
Ya fadi hakan yana dariya, wadda
ta bayyanar da hakorin farin gwal din da
yake bakinsa.
Malam Usman ya kalli rugujajjen
kofar gidan nasa mai dauke da jarkasa
121
IZGILI JAMILA MUHAMMED
tumumu irin jajur din nan ya kai dubansa
gurgurarriyar kofar shiga gidan ta katako
mai barazanar rusowa. Ya dan saci
kallonsu dubi irin danyun shaddojin dake
jikinsu yanzu haka zasu dansu a cikin
jarkasar nan wata zuciyar ta ce, to ya za'a
ayi ai sun kallo yadda gurin yake kuma a
hakan suke san su zauna. Ya dubi Alhaji
Yakubu ya ce, "To bara in kawo abin
zama.
"
Suka ce babu damuwa ya juya da
sauri çikin gidan ya same ni ina kwasar
tuwon dare ya ce.
"Hadiya maza shiga daki ki dauko
sabuwar tabarmar ledar nan cikin
girmamawa ta ce, "To"
Ta dauko da sauri ya ce, "Yauwa ki
zubo ruwan sha ki kawowa baki."
Ta amsa cikin girmamawa ta saurin
karasa kwashe tuwan ta dauko saɓanin
122
IZGILI JAMILA MUHAMMED
kwanon sha sabo fil ta sake ɗauraye shi ta
tuttulo ruwan tulun Innar mai dan karen
sanyi ga shi ruwan dadi.
Farin fenti jikin kwanon shan sun
tai maka gurin fito da farin ruwan gami
da tsaftar sa tamkar irin ruwan da suka
saba amfani da shi, ta shiga ɗaki ta ɗauko
zumbulelen Hijab dinta da nikaf ta saka
ta ɗauki ruwan ta yi soro inda take jiyo
maganarsu duk da dai ba sosai ake jiyo
maganar ba ta yi sallama cikin siririyar
murya ta durukusa har kasa ta gaishe su
Alhaji Mansir da yake cike da fara'a gami
da wani matsanancin farin ciki ganinta a
zuciyarsa fadi yake tarbiya da dadi gami
da biyayya da sanin girman na gaba sai
gurin diyan talakawa dubi dai irin yadda
zube gwiwa bibbiyu saɓanin 'ya'yan
masu dà shi, wadda wata ma ko kallan
arziki abokanan babban nata basu isheta.
123
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Masu tarbiyar cikinsu ne zasu
gaishe su daga tsaye, ko kuma a ce,
sannunku.
Daddadar muryarta mai cike da
nutsuwa ce ta katse masa zancen zucin da
yake yi, ta ce, “Ga ruwa."
Alhaji Yakubu ya suri kwanan da ta
ajiye sanyin ruwan da ya ratsa kwannan
ya ratsa tafin hannunsa yayi saurin bude
murfin, ruwan garai-garai gwanin kyau
ya sha sanyin ruwan ya kwaranya a
tumbinsa yai hamdala Alhaji Mansir ma
ya sha su kai godiya ga Allah.
Alhaji Yakubu ya gyara murya ya
fara da gabatar da kansa ya ce "Ni suna
na Alhaji Yakubu Galadanci, ni haifaffen
garin nanne a galadanci iyayena suke
amman ni ina zauna ne a Alu Aɓenue sai
kuma abokina kuma aminina shi kuma
sunansa Alhaji Mansir kwangila haifaffin
124
IZGILI JAMILA MUHAMMED
garin Gombe ne amma anan garin shi
yake yana zauna ne a Sultan Road kuma
shi ne wanda yai dalilin zuwannmu nan.”
"
Malam Usman ya ce, "TO madalla
Allah dai yasa lafiya .?"
Alhaji Yakubu ya kuma sakin
dariya ya ce, "Lafiya kalau, alhaji Daman
dai yaga 'ya wajenka ne ya yaba da
hankalinta da nutsuwa gami da tarbiya
irin ta gidan nan shi ne ya yiwa dansa
kamu, in dai babu wanda akaiwa
* alkawarito yaran gurinsa yana son ta. "
Malam Usman ya ja shiru na lokaci
mai tsaho sai can ya ce, "To Alhaji
hakikanin gaskiya ban yi mata miji ba,
kasancewar ban bata damar sauraran
samari ba, saboda karatu, take duk da dai
ta kusa gamawa dan saura wata uku ne
kurum ya rage ta gama, to amma wani
hanzari ba gudu ba, kamar na so na ji
125
IZGILI JAMILA MUHAMMED
kace shi Alhajin ne yayaba da ita ba shi
yaron bane, ya ganta, ya ga yana son ta ba.
Alhaji Yakubu ya cc, “Haka nace to
mu din mu na yi ne kamar yanda shari'ar ta
tsara gurin neman aure kuma muna bin
yadda addini ya tanadar cewar idan zaku
aurar da 'yar ku, hakkin iyaye ne su
nemawa ‘yarsu miji na gari haka ma mijin
suna iya zaɓa masa mata ta gari shi yasa
muka zo da karfinmu saboda tarbiya irin ta
gidanka mu kai kwaɗayin hada zuri'a da
kai."
Malam Usman ya sauke ajiyar zuciya,
Gaskiya ya gamsu da duk wani bayani da
kuka yi kuma shi ma zai so hada zuri'a da
su dan ya fahinci su din dattawan kwarai ne,
kuma ya gane su din ba daya suke da sauran
,masu kudin wannan zamani ba, da karan
gidansu yafi ye musu talaka sau dubu, basu
talaka mutum ba, ba wai dan kuɗinsu ba
sai dan kamala da mutuncin da suka nuna ko
126
IZGILI JAMILA MUHAMMED
kusa ko alama bai ga wani wulakanci ko
tsantsanin da suka nuna masa ba tun
zuwansu lallai ku a cikin masu kudin su din
daban suke ya cc, su dan ba shi lokaci zai
tuntuɓi mahaifyar yarinya ko da wanda ita
yarinya take so suka cc to babu damuwa
kamar yaushe yake ganin zasu dawo dan su
ji yadda ake ciki ya ce idan Allah ya yarda
nan da kwan uku suna iya dawowa su kai
masa godiya ya ce, Ai babu komai ya rako
su har kofar gida gurin motarsu ya nayi
musu fatan alkhairi da addu'ar sauka lafiya.-
Suna karayin musabaha, Bintu ita da
dan Auta Aliyu suka dawo daga Tahfiz,
suka durkusa har kasa suna gaishe su, suka
amsa cikin fara'a gami da jin dadin yadda
aka karramasu.
Alhaji Yakubu ya fito da kuɗi a
aljihunsa har sun mike ya kira su, suka
farasa gabansa sosai suka kuma durkosawa
ya mifa musu sababbin ‘yan dubu dubun da
127
IZGILI JAMILA MUHAMMED
ya kirgo guda goma ya mika musu yaran
tamkar ashim film suka wani zabura a tare
gami da mikewa har suna hada baki gurin
cewar A'a mun gude su kai hanyar shiga
gida Alhaji Yakubu ya juyo da kallansa ga
Malam Usman ya ce, "Haba Alhaji ya za kai
min haka yanzu ba zaka sa baki su karɓa ba,
ni fa na niya ba wai rokona su ka yi ba,
cewa nake ka karanta babu mai mai da
hannun kyauta sai shadani, hakan yana da
kyau hana yaro amsar Abubuwa a hannun
mutane. Amma fa idan bai san su ba in dai
mutum ya san yaro ka ba shi abu bai karɓa
ba, sai ka ji babu dadi duk da yake karбar
ma ko da yaron ya san yanda ya ba shi to
hakan ma koyan kwadayi ne, cewa nake a
iya zaman da mu ka dan yi yanzu da kai ka
yarda damu din masoyanka ne, tunda har
muna son hada zuri'a da kai nan ba da
dadewa ba, insha Allahu, ai ina ganin mun
zama daya ko ba haka banc.?"
128
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Malan Usman ya cc, "Hakkun amman
ina ganin Alhaji kudin nan sun yi yawa."
Alhaji Yakubu ya ce "Ba wani yawa
da su ka yi in dai ka dauke mu da zuciya
daya, kuma 'yan uwa ka ɗaukcmu."
Malam Usuman ya cc, "Wallahi da
zuciya daya na dauke ku. "
Alhaji Yakubu ya ce, "To In dai haka
ne to ka sa su su karɓa tun da ni ma
babansu ne.
99
Malam Usman ya yi murmushi kawai
ya juya zuwa soran gidan inda yai kiransu
ya dawo gurin su Alhajin yana karayi musu
godiya su kuma suka ce babu komai sune da
godiya.
Bintu ita da Aliyu suka durkusa suka
ce, "Abbu gamu ya nuna su Alhaji ya ce,
"Alhaji ne yake kiranku.'
Suka karasa gurinsu ya mika musu
kudin ya ce, "Abbunku ya ce, ku karɓa.'
"
129
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Suka juyo suna kallon Abbun nasu.
Malam Usnam ya ce, "Ku yi musu godiya."
Ai fa yara suka dinga zararo godiya
sai da Alhaji Mansir ya ce, "ya isa ku je gida
ku sayi Buskit.'
"
Suka ta shi cikin nutsuwa suka shige
gida babu wata harguwa irinta sauran yara,
komai cikin nutsuwa suke yinsa nan dai
suka sake sallama sannan suka ja motar
suka tafi, da alkawarin za su dawo nan da
kwana ukun.
******
Da daddare bayan sun gama cin tuwon
dare sun baje suna shan iska suna kuma hira
Malam Usman yai gyaran murya ya ce,
"Lafiya baki tambaye ni in da dan autanki
ya samu kudi ba.?"
Inna ta yi dariya ta ce, "Malam ke nan
ai tunda Hadiya ta bani kudin ta ce su Binta
ne suka cc ka yi baki shi ne bakin suka basu
130
JAMILA MUHAMMED
na san za kai min bayani, idan ka mustu to
gajen hakurin na me ye, da zan tambayeka."
Malam Usman ya yi dariya ya cc, “Ai
daman tsokanarki na yi ni da na san halinki
na rashin bindiddigi da san jin kwakwaf ai
gaba daya suka saki dariya har da Bintu da
take kwance barci ya fara di banta.
Hadiya ta ce, zuciyarta gaskiya ina
san iyayena akwai su da barkwanci sai