jallabiyar da
yake sallah da ita ya bude dirowar gadon
ya dauko kudi kowacce ya bata ya ce,
67
IZGILI JAMILA MUHAMMED
“Sai na neme ku kada wadda tai gigin
zuwa idan ba na kirata ba, yana gama
fadar haka ya ce, Ku fito suka fito sai ya
bude kofar. Kudirat ta saki dariya ta ce,
"Handsome kalle kafa babu pant ana
ganinka a haka zaka je gurin Daddy."
Cikin sauri ya kalli jikinsa ai kuwa
ana ganin nasa kasan cewar rigar ruwan
madara ce kuma tana da yauki mannewa
mutum take da sauri ya fada dakin ya
sako gajeran wando ya fito dai-dai nan
ya sake jin karar wayar ya san mai kiran
batare da ya dauki wayar ba ya bude
kofar yana washe baki daddy ya ce, "Ai
ni da badan maigadinka ya ce, kana nan
ba kuma naga duk motocinka suna nan da
cewa zan yi baka gidan ko kuma ba ka yi
murnar gani na ba my son?"
Hisham ya ce, "Na yi murna mana
daddy.'
68
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Daidai nan suka shigo cikin falon
sosai Daddy ya kallu Kudurat da suke
zaune a falon ya mai da kanshi ga
Hisham din da yake tsaye da alamun
tambaya a fuskarsa, Hisman ya ce,
"Wadannan abokan aikinane wani aiki ne
ya kawosu yanzu.
Suka gaida daddy ya amsa musu
fuska babu walwala su kai waje Hisman
ya buɗe firij ya kawowa Daddy Ruwa da
lemo yana kuma tambayar Mominsa.
Daddy ya ce, "Tana lafiya.”
Daddy ya gyara zama ya ce, “Wai
ni shin Hisham sai yaushe za kai aure ne,
ko yaushe akai maka magana daga kace
wannan sai kace wan can kana ta faman
zille-zille.
Hisham ya ce, “Haba Daddy ni fa
ba girma na yi ba, just 33 year ne fa ka ga
da saura na. وو
69
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Daddy ya ce, "Da sauranka fa tunda
ba kai sittin ba,mana tunda shi ne dai-dai
lokacin ka ko?"
Hisham ya ɓata fuska tabbacin baya
son fadan nan ya ce, "Please Daddy ka
bar maganar nan daga zuwanka ko
hutawa ba ka yi ba, me ake da aure, aure
ai takura ne. "
Daddy ya saki baki yana kallan dan
nasa tun ba yau ba ya daɗe yanayin dana
sanin tura ɗan nashi kasar mai jan kunne
karatu, tun yana tatsitsinsa gaskiya ya
cuci kansa wannan Abu yana damunsa ya
rasa yadda zai yi bai isa yai masa faɗa
akan duk abinda yake yi ba sai ya ce, shi
dai ana san a takura masa, duk ya dauko
dabi'unsu na lalata.
Daddy da idanuwansa suka fara
canja launi saboda ɓacin rai ya ce, "To
wallahi bari in gaya maka in dai ba kai
70
IZGILI JAMILA MUHAMMED
wani abu kan maganar aure ba daga nan
zuwa karshen watan nan tuni zan yi wani
abu a kai, kuma sai na baka mamaki.'
"
Yana gama fadar hakan ya mike
dan yın Alwala dan ya ji masallacin kusa
da gidan suna kiran sallah.
Alhaji Mansir kwangila shi da
Alhaji Umar mai akwai suna zaune a
falon gidan Alhaji Umar din bayan
gaishe-gaishe irin na abokanai, Alhaji
mansir ya ce, "Gaskiya ina cikin
damuwa.?'
Alhaji Umar ya ce, "Ikon Allah
Alhaji me ke damunka Alhaji Mansir ya
furzar da huci mai zafi ya ce, "Akan
yaran wajena Hisham ne, wallahi ina
cikin ɓacin ran kaishi turai karatu banda
karatu har da shedana da duk wata lalata
ta turawa duk ya kwaso, to shi yasa nake
IZGILI JAMILA MUHAMMED
san in yi masa aure, tun lokacin dana
kama shi da giya a firji dinsa nake cikin
damuwa shi yasa nake san yi masa aure
kasan aure abu ne mai girma kuma yana
gyara mutum to gaba daya daya na rasa
yarinyar da zan zaɓa masa mai hankalin
wadda zata juri halinsa ta dinga tuna
masa idan taga yana abunda bai dace ba,
to na yi tunanin na yi tunanin na kasa
zaɓar masa to kawai sai sai
nana tattara
nabarwa Allah lamarinsa ya zaɓa masa
mafi alkhairi na kuma dukufa da addu'a
sosai.
Wani ikon Allah banyi sati da fara
tsaiwar daran nan ba na fara mafarkin
wata yarinya, to amma banga fuskarta
ba, tana sanye da dogon hijabi har kasa ta
juya bayanta da yaro a hannunta to tun
daga lokacin ya zama duk lokacin da na
kwanta sai na yi mafarki, to kwanaki da
72
IZGILI JAMILA MUHAMMED
na zo nan muna magana sai naga wata
yarinya zata wuce Islamiyar."
Alhaji Umar ya ce, Zawuya ke
nan.?"
Alhaji Mansir ya ce, “Ita, ya ci gaba
da cewa "Wato ranar da na ganta sai naga
nutsuwarta da hankalinta nasan ta fito
daga gidan tarbiya shi ne nake san in
tambayeka ko ka san 'yar inace tana saka
nikaf."
Alhaji Umar ya dan yi nazari ya ce,
"Gaskiya ban san ta ba, sai dai akwai
wani yarona kama sanshi dan Audu, to
zan sa shi ya binciko mana in da take da
kuma 'yar gidan waye."
"
Alhaji Mansir ya ce, "To shi ke nan
suka ci gaba da hirarsu akan harkokinsu
da kuma hirar duniya.
Cikin wulakanci ya kalli mai gidan
ya daka masa wata gigitacciyar tsawa ya
IZGILI JAMILA MUHAMMED
ce; "Saboda tsabar baka san aikinka ba ko
kuma dan ka koshi zaka nuna halin naku
na talakawa, daga kunci abinci sai ku
ɓollo da salo na rashin mutunci.
Baba Audu babu abinda yake in
banda makyarkyata yana durkushe yana
bawa ubangidan nashi hakuri tamkar
zugashi yake, sai faman tujara yake yi
masa da tozarci, kala-kala, tsohon zai
baka tausayi mutuka saboda a kalla ba a
kasara ba zai yi jika da shi, sai wulakanci
yake yi masa, irin na zafin naman nan.
Hisham ya ci gaba da yarfa ruwan
rashin mutunci yace, "Saboda tsabar ka
isa tun jiya abaka dakardu ka bani dan.
tsabar raini kaki bani har sai da mutumin
yayo min waya saboda ya ji shiru, sam
baka da niyar bani, saboda ka fara
farfaɗowa daga cutar talauci, data kama
ka, yanzu kana jin aljihunka da nauyi shi
74
IZGILI JAMILA MUHAMMED
ne kake ganin dai-dai kake da kowa tsiyar
talaka ke nan, a ɗaukeshi ranga ranga a
taimake shi daya fara koshi kai zai
farayiwa rashin mutunci, shi yasa ni da
talaka babu wani tausayi, ban ɗauki
talaka a bakin komai ba, face,
kaskantaccen bawa, wanda zai min bauta
in biya shi, a duniya babu wata rana da
talaka yake da ita, bashi kuma da wani
amfani daya wuce mai kudi ya bautar
dashi domin shi bawansa ne.'
"
Shi dai Baba Audu in ban da ban
hakuri babu abinda yake yi sai da ya ji ya
ɗan tsagaita sannan ya fara bayaninsa ya
ce, "Wallahi yallaɓai sanda mutumin nan
ya kawo takardun nan ka fita kuma baka
sake dawowa ba zuwa kuma sanda ka
shigo na manta sai yanzu na tuna, ina
shirin kawo maka sai kuma ga ka, amma
75
IZGILI JAMILA MUHAMMED
dan Allah dan Annabi ka yi hakuri hakan
ba zata sake-faruwa ba, in sha Allahu.'
"
Cikin Izgilanci gami da wulakanci
ya karɓi takardun ya ce, "Kuma daga yau
sai yau muddin haka ta kara faruwa to a
bakin aikinka, sake kwatanta abinda ka
yi, yana nufin ka koshi dai-dai kake da
kowa. Dan haka yarage ruwanka, ka
kiyaye, ko ka sake, aikatawa.
Cikin takunsa na isa hade da kasaita
ya bar wajen baba Audu ya dade
tsugunne a inda ya barshi saboda tunda
yake ba a taɓayi masa wulakanci da
kaskanci irin na yau ba, sai kawai ya ji
wani irin zazzafan hawaye suna zubo
masa ace kamar wannan da yayi jika
dashi a ce dan Allah ya yo shi talaka yana
aikin a karkashinsa kan ya yi masa laifin
da bai taka kara ya karya ba, zai zage
76
IZGILI JAMILA MUHAMMED
haka, yana gaya masa irin wadannan
maganganun.
Ya mike daga durkuson da ya yi
yana sharar kwalla cikin mutuwar jiki ya
koma kan benci da yake kai dai-dai nan
yaji sallama akansa ya dago da sauri yana
amsawa Malam Saleh ne direban
kamfanin ne ya zauna kusa dashi yana
bashi baki ya ce, "Baba ka yi hakuri da
abinda yallaɓai ya yi maka tunda Allah
ya haɗamu zama dashi babu yadda zamu
yi sai dai hakuri shi fa a duk duniya babu
wulakantacce a gurinsa kamar talaka,
babu wanda yake kyama yake tsangwama
hade da kyara irin talaka, gani yake
takalmin kafarshi yafi talaka, daraja, a
gurinsa ka gan ni nan Baba yallaɓai ba
jin kunyar na yi sa'an mahaifinsa baya
iya cire hannu ya wanke min fuska da
mari.
T
By lay mida on ideol
77
:
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Baba Audu ya ce, "Me yai zafi
malam Saleh?"
Malam Saleh ya ce, "Ranar kaddara
ce ta hau kaina ya aike ni ne to akan
hanyata ne karfan nasara da bashi da
tabbas sai kawai mota ta tsaya cak na yi
na yi taki ta shi na rasa inda zansa raina
dan yaja kunne na in yi sauri mutumin
sauri yake zai bar kasar ne, gaba ɗaya
hankalina ya gama ta shi kuskuran da na
yi na rashin kiransa in gaya masa tun a
lokacin kawai sai na fita ina ta 'yan
dabaruna ga mi da ‘yan jogane-jogane na,
na ma buɗe in jin motar ina ta
jagwalgwalawata na bar wayata a cikin
mota a she, shi mutumin da ya aike ni
gurinsa yana tai masa waya ya ce, ban fa
zo ba shi kuma zai yi missin din jirgin shi
dan haka shi ya tafi, sai kuma wani
lokacin, shi ne shima yallaɓai ya keta
78
IZGILI JAMILA MUHAMMED
kiran wayata ina ni ban sani ba, danni ina
waje ita wayar tana mota dan haka banji
kiran da yake tayimin ba.
Sai da akalla na yi kusan awa biyu
da wasu 'yan mintoci sannan cikin ikon
Allah sai ga shi ta tashi ai cikin sauri na
rufeta saboda sai da ya gargade ni da
lallai lallai in tabbatar duk yanda zan yi
nan da minti arba'in in kasance a gurin,
to gashi na kusanyin awa uku aikuwa
wanda na je domin sa yama daɗe da
tafiya cikin sanyi jiki naja motar na dawo
na riga na sani nashi ga wani hali, yau sai
Allah aikuwa tunda nai horn aka bude
min na ganshi yana ta zirga-zirga tamkar
mai nakuda na sanni kuma sai Allah,
aikuwa ina tsayawa na fito na durkusa
kafin ince wani abu sai jin wani
shahararren mari na yi akan kuncina ta
inda yake shiga ba tanan yake fita ba,
79
IZGILI JAMILA MUHAMMED
ashe takardun wata kwangila ce zan
karɓo masa da yake shirin shakar
makudan kudade bana wasa ba, shi ke
nan in ba wani ikon Allah ba ya rasa su.
A ranar na dandani bakin ciki bana
wasa ba wallahi da ina da yadda zan yi da
tun a lokacin zan baar aikin nan, to bani
da wata hanyar neman kudi, ga kuma
iyali, dan ba karamar wahala na sha ba
kafin Allah ya datar dani, na samu
wannan aikin dan haka dan Allah Baba ka
yi hakuri kuma ka dinga kiyayewa abinda
zai ja ya ci mutuncinka, tun da shi baya
ganin mutunci da kima hade da darajar
talaka ba.
Baba ya ce, "Kada ka damu insha
Allahu haka ba zata sake kasancewa ba,
zan kiyaye, tunda abin babu mutunci sai
kai ka alkinta girmanka dan kada a sake
ci maka mutunci.'
95
80
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Malam Sale ya ce, "Wannan
gaskiya ne dole ne ka dinga kiyaye
abinda zai sa a wulakanta ka."
******
Dan audu ne yake ta faman korawa
Alhaji Umar mai da akwai tare da abokin
nasa labari. Fuskar alhaji Mansir ta cika
da annuri ya godewa Allah tunda ya
taimaka aka samu gidan dashi har ya
shiga damuwa da yasa yaji shiru bai sake
ganinta ba, kuma ya ji dadin yadda Dan
Audu ya bincika ya gama cika shi haka
nan Allah yasa ka masa kaunarta tun
ganin daya ke ta mafarki yana yawan
ganinsa yana zaune a wani dokar daji ya
nata kuka shi kaɗai sai ya ganta ta zo
tana bashi hakuri tana lallashinsa duk da
baya ganin fuskarta wani sa in kuma sai
ya ganshi yana cikin fain ciki yana ta yin
mrmushin amma ita tana kuka shiya sa ta
81
IZGILI JAMILA MUHAMMED
tsananta da addu'a ya kuma sa'a taya shi
saukar karatu duk juma'a akan dai Allah
ya tabbatar da Alkhairi idan ita ce, mafi
alkhairi ya kuma kawo sauki ciki lamarin
ya kade fitina dake cikin al'amarin.
Dan Audu ganin irin tarin fara'ar
dake fuskar alhajin yasa ya kara kaimi
yana kara koro wasu kuskuren zancen
duk dai akokarinsa na ganin Alhaji yaga
kokarinsa
aikinnasa.
hade da kwazansa akan
Aikuwa kwalliya ta biya kudin
sabulu dan kuwa Alhaji ya yi masa
kyauta ta mu samman ya yinda Alhaji ya
ce, tukukaicin ka ka gobe ka jira zai a
kawo maka mashin shi ne tukuicin
binciko min gidansu, da ka yi ya kuma
dantso kudin da bai tsaya kirgawa ba ya
ce, "Wannan kuma kasha ruwa ka ji,
ladan kyakkyawan labarin.
82
IZGILI JAMILA MUHAMMED
Dan audu tamkar zai shiɗe saboda
murna godiya yake gami da jero dogayan
addu'o'in tamkar wani saban maroki,
yana karkawa yayi durkoso a gabansa
yana faman jinjina masa hannu tamkar
yanda akewa sarakai.
Alhaji Mansir ya ce, "To dan Audu
sai gobe ke nan. "
Ya ce, "To ya alhaj."
Alhaji ya fita yana kwararowa
‘ya'yan har jikoki dama tattaɓa kunnan
alhaji kasan zuciyarsa yana ta kakkabin
halin kwarai irin na wannan alhajin shi
sam ba matsolo bane tamkar uban gidan
nasa, da bai ajiye komai ba sai shegiyar
rowa ta bala'i duk yanda kake da shi
babbar kyautarsa ita ce, ya bawa mutum
gudar dubu ɗaya, to lallai wata dakwalar
budurwa ko bazawara ya kawo masa
labarinta to kuwa zai samu gudar dubu ko
83
1
IZGILI JAMILA MUHAMMED
kuma yinin ya yi yana wahalta masa, to
idan ba daya daga cikin wannan ba ne to
tsakaninsa da kai dari biyu ne sai kuwa
idan yasan kanai masa wata ranar ne.
Zai iya baka dari biyar shi ba abin
kunya bane ka zo neman taimako gurinsa
amatsayinka na yaransa ko kuma dan
uwansa ya tattakura ya fito da naira
hamsin ya ce, a sai wa yara garin rogo
(kwaki)
Duk unguwar Koki babu wanda bai
sanshi ba, koda karamin yaro ne, ka
tambaye shi gidan Alhaji Umar mai
akwai to zai nuna maka sai fa in mai shan
nono ne.
Kowa yasanshi saboda tsabar son
kudinsa da matsolancinsa uwa uba kin
talaka ya ce, talaka ba shi da wani alfanu
a gurin mai akwai. (Wato mai kudi) face,
hidim ta masa shi kuma ya biya shi shi ne
IZGILI JAMILA MUHAMMED
kawai amfanin talaka a gurin mai akwai,
alhaji Umar mai akwai ya yi mutukar
tsanar talaka gani yake tamkar shi
mutumin shi ya ɗorawa kansa talauci ba
Allah ba, Alhaji Umar mai akwai
shaharar ran mai auri saki ne gaba ɗaya
kudinsa suna tafiya ne aa gurin aure
aurensa mutane da dama sun ce auran
dandano yake ga shi kuma baya san
'ya'yan abin Allah sai ya yo shi daga
cikin masu rabon samun 'ya'ya, ko ya ya
taɓa mace, sai ta samu rabo da shi kuma
abinda yake ba kanta masa ke nan.
Shi fa gani yake a duk duniya babu
babbar matsalar irin zama da mace ɗaya
yasha yiwa abokansa fada idan yana jin
suna fadin matarsu daya ta ishe su ya
kance ba kuda hankali ba kusan ciwon
kanku ba, in banda rashin sanin me
duniya take ciki, ya za ka zauna da mace,
85
IZGILI JAMILA MUHAMMED
daya sai kace jaraba aini ko mata huɗu ba
zan iya zubewa ba in yi shekara dasu
batare da na yi can ji ba, ai gara adinga yi
ana sabuntawa, aikuwa Alhaji Umar mai
akwai ya auri mata kusan ashirin da uku,
a kun dade da shi kina iya masa so sai
shi ne zai barki ki yi shekara, to daga nan
zai ɗaga miki jan kati idan ciki ne dake
zai ce ya bar miki abinda yake cikinki
duniya da lahira kada ki kuskura ki doso
shi da wata matsala ta dan zai kuma yi
miki ba, razanar ranku daga ke har yaran
in dai kika kuskura kika danganta shi da
wata matsala ta yaran zai kuma gaya miki
zai fara rufawa yaran asiri, dan kada ai
masa gorin ko yaran shege ne zai kuma
gaya miki yana nan a amaṭsayinsa na
ubansa, sai dai fa baya so idan ke kina so
ya bar miki shi ke ka ɗai idan kema ba
kya so to ga gidan marayu nan kina iya
IZGILI JAMILA MUHAMMED
sadashi da can, idan kuwa ke din irin
barebarin nance, to uku ya yi yawa zai ce
waje road shi din bai dauki mace a bakin
komai ba face, ruwan kashe gobara, shi
yasa baya daukan raini, ko wulakanci
daga gurin kowa ce irin mace ba, da zaki
kawo masa shakiyancin banza zai gaya
miki ke din ba wata tsiya bace, agurinsa,
dan idan ya so ana fita da kayanki ana
shigo da na wata dan cewarsa mata sun
yi yawa, tamkar ledar pure water ne, ga
sunan burjik, duk inda ka zaga birni da
kauye, dan haka shi a gurinsa, canja mace
a gurinsa tamkar canja rigar jikinsa ne,
duk sanda ya bukaci yasha iska zai canza
ki da wadda ya ke so, shi yasa” yake
mutukar ganin bakin abokin nasa, ganin
tun wani shuɗadɗen zamani yake fama
da mata daya Aisha, wallahi ba zai iya
ba, sai wani ciwon ya shige shi, saboda
87
7
IZGILI JAMILA MUHAMMED
bakin ciki da takaicin kaɗaici,, kullum
babu wani canji sai kace masifa.
Alhaji Umar ya karkatar da kai,
yana kallon Abokin nasa ya ce, "Alhaji
Wai duk murnar wannan maganar ne,
yasa kake wannan rawar jikin hade da
wannan batun kudi, tamkar wani wanda
bai san ciwon su ba, akan wata can diyan
talaka, irin wannan kyautar ko ka manta
abinda dan Audu ya fada ne, ubanta ba
kowa bane, face, talaka, a cikin talakawan
ma na karshe a gun talauci ko baka ji
sosai bane cewa ya yi ubanta fa faci yake
yi, aini cewa nake daga jin baya nin Dan
Audu ko duban mai rin kamaninta ba
zaka sake yi ba, a matsayin Hisham na
dan mai kudi wayayye, kyakkyawa me
zai da wata Diyan talaka duk ‘ya'yan
manyan masu sukuni karasa wadda zata
zama sirikarka, matar danka, sai wata
IZGILI JAMILA MUHAMMED
‘yar mai faci, kai wannan abu da bakin
ciki yake, ina garin gami mai kuɗi da
talaka, da har za kai sha'awar hada
zuri'arka da ta shi.'
"
Alhaji Mansir Kwangila ya ce,
"Wai ni shin Alhaji Umar mai ka ɗauki
talaka ne, kaskantantacce, wulakantacce,
kuma mara 'yanci, wanda duk sanda mai
akwai (Mai kudi) ya mula yasha iska zai
ciwa zarafi, ciwa zarafi, ya tozarta shi dan
kawai Allah ya yishi mai shi, shi kuma ya
yo shi mara shi, to ba haka bane, talaka
mutum ne, tamkar kai, kuma ba'a bin
wulakantawa bane saboda dinbin daraja
da martabar da Allah yai wa bayinsa ‘yan
adam Allah da kansa yake faɗa a cikin
alkur'aninsa mai tsarki WALAKADI
KARRAMNA BANI ADAM!!! Hakika
ubangiji ya daraja ya girmama ɗan adam
sai kai dan kawai Allah ya huwace maka
89%
IZGILI JAMILA MUHAMMED
za ka wulakanta mutum talaka, waya sani
ma ko mutumin da kake wulakantawar ya
fika a gurin Allah dan haka wallahi
wallahi banga dalilin da zan kyamace
talaka ba, wai dan kawai ni me shi ne, shi
kuma mara shi, to haka Allah. ya nufin ya
ganshi, kuma ba zan taɓa kin saba, wai
dan yana faci, faci ai sana'ace, a gurin
kane da ka raina shi har kake kiransa da
al'amarin
duniya ba yadda ka zata bane. Dan kana
ganin kana da kudi to dare daya idan
Allah yai nufin nuna ikonsa da buwayarsa.
sai ya mai da shi kai da kake kiran
koma ya fika
sunan kaskantacce kuma
kaskantattace matsayinka kake kiran
kai kuma kadawo kamarsa, ko da yake ba
za kai jarumtakar da ya yi ba, tunda ance ya daɗe a nan anguwar amma baka san shi ba, kaga hakan yana nufin ya iya da talaucinsa, tunda bai taba takowa kofar
IZGILI JAMILA MUHAMMED
gidanka da sunan maulaba, ka ga hakan
yana nuni da cewar shi din mai
jajircewane, da kuma tsayawa iya
matsayin da Allah ya ajiye shi, kuma bai
yi bakin ciki da yadda Allah ya yoshi
marashi ba, bare ya dinga binbinin a
gurin masu akwai ba suna wulakanta shi,
kafin su dan watsa masa ‘yartsaba su nai
masa dagawa, suna hura hanci ka ga
kuwa akwai tarbiya a irin wannan gidan,
sakamako 'ya'yanmu da muke barinsu
babu tarbiya dan haka in dai ni Mansir ni
ne mahaifin Hisham to fa bashi da wata
matar aure idan ba 'yar gidan mai faci ba.
Alhaji Umar ya tsurawa abokin
nashi ido an ya kuwa kansa kalau, kai
anya kuwa ko da yake daman yasan
halinsa in dai akan talaka ne, yo mutumin
da zai zauna gurin mai gadi suna hira,
idan ka ganshi da ma aikatan gidansa
91
IZGILI JAMILA MUHAMMED
yana kwasar dariya tamkar ba mai
gidansu ba sai ka ga har wani share musu
bakin yake tamkar ba mai kuɗi ba, shi
yaga zai iya, shi yasa fa ko dariya baya
iya yi a gidansa, dan kar wata ta yi gigin
raina shi, in kaga dariyarsa, to yana
majalisar su ta masu akwai ne."
******
"
Shin wanene alhaji Mansir kwangila
Alhaji Mansir Asalinsa dan garin Gombe
ne mahaifinsa mai suna Alhaji Bawa,
shahararren mai arziki ne sannane a cikin
garin na Gombe, kai bama nan kadai ba,
har da sauran garuruwan da ke cikin
Nigeria ya shahara sosai dan kasuwa ne
babu irin kasuwanci da ba ya taɓawa, ya
kan sari Auduga ya sarrafa tata a
kamfaninsa yana fita da ita kasashen
duniya, idan ya ta shi dawowa shi kuma
sai ya saro shinkafa da wasu kayayyakin
92
IZGILI JAMILA MUHAMMED
da muke bukata buka, sannan yana da
kamfanin Tumaturin gwangwani sannan
yana da wani kamfani amma hadin
gwiwa ne, a jafan da suke kera takalma
masu shegen kyau, matar Alhaji Bawa,
daya mai suna Rahina, ana kiranta da
Hajjo Allah ya albarkace su da ‘ya'ya
bakwai uku maza hudu.
Mata ta farko mace ce mai suna
Binta da ake kiranta Batulu, sai na biyu
mai suna Mansir, daga mansir sai Barira
sannan Hindu, sai najib, sai Safiya, da
kuma dan autansu, Isma'il gaba dayansu,
sun ta so cikin kulawa hade da tarbiya
irinta addinin musulunci sam Alhaji
Bawa shi da Hajjo basu saki yaran sun
sangartasu ba, wai dan kasancewar
mahaifinsu, wani ne, sun basu tarbiya ta
gari dan gaba ɗayansu, sai da kowa ya
sauke sun yi karatunsu na boko amma
93
IZGILI JAMILA MUHAMMED
matan iyakar su secondry ake yi musu
aure Inna Batulu anan Gombe take aure
bata taɓa haihuwa ba.
.
Safiya Bauci take da yaranta Hindu
Abuja ita ma dana ta yaran Barira ma
anan Gomben take dan ita basu da nisa da
gidan iyayan nasu maza ne ya ce, su yi
karatu, duk anan gida Nigeria dan bai
yarda ya tura dansa wata uwa duniya da
sunan karatu ba, kuma garin da suka
daurewa sheɗana da duk wata lalata kugu
wanne karatun waɗannan makiya Allah
zasu koyawa yaran da suke son musulmi
ne su da a duk duniya basu da abokin
gabar da ya wuce, musulmi, to wanne
karatu zasu koya masa ban da su wayar
masa kai, ya san ilimin lalata ni wallahi
wannan abin yana damu na rashin sanin.
ciwon kanmu, Nigeria wani bature ko ka
taɓa ganin ya kawo dansa Nigeria ya ce,
94
IZGILI JAMILA MUHAMMED
ya yi karatu, sai mu da bama kishin kasar
mu zamu ringa jidar ‘ya'yanmu tamkar
gyada muna kaiwa makiyanmu masu
burin ganin sun karmu sun rusa mu, su zamu bawa yaranmu.
Ai wannan damar suke samu su
koyawa yaranmu duk wata sheɗana, sai
sun gama lalata musu tarbiya sannnan
zasu turo mana su dan su zame mana
annoba, su buwaye mu, dan haka Alhaji
Bawa yana daya daga cikin mutane masu
kyamatar tura yaransu karatu waje, gaba
dayansu mazan sun yi karatun su ne a nan
gida Nigeria.
Alhaji Mansir ya yi karatun sane a
Jima'ar A.B'U A.B'U Zariya inda ya yi
karatunsa akan kasuwanci wato Business.
Mansir ya dade bai yi aure ba, dan har sai
da dan Auta Isma'il ya fara haɓaka Alhaji
Mansir ya haɗu da Zalifa ne a Misra
95
:
IZGILL JAMILA MUHAMMED
lokacin ya ji kan wasu harkoki da suka
kai shi Zalifa balarabiya ce, gaba da baya
mahaifinta shi ne Wazirin Sarkin na
Misra.
Mansir ya haɗu da Zalifa ne ta
sanadiyar 'ya'yanta wanda Allah ya haɗa
su anan garin Kamfanin Babanta ya je,
domin gogewa da sanin makamar aiki,
domin ya fada har kar Kwangila to wata
rana ne shi ya yanta Alhaji bashir ya
gaiyace, shi cin abinci gidansa to sai Akai
sa'a Zalifan ta je gidan yayan nata ita da
kanwarta Nadiya, tun daga sannan
soyayya mai karfi ta shiga tsakaninsu
ansha fama kafin kasancewarsu
matsayin ma'aurata, saboda iyayanta
basa son tai musu nisa dagewarta ce, tasa
iyayen suka hakura suka aura mata
wanda take so batare da ɓata lokaci ba
aka sha biki amarya ta tare a Nigeriya
a
96
IZGILI JAMILA MUHAMMED
kuma a garin ‘iyayan mijinta watan
Gombe da farko iyayansa da yan uwansa
duk suna son ta amma daga baya duk sai
suka canja canja mata su ka bi suka
tsangwameta ta kuma rasa dalili sai daga
baya ta gane kan rashin haihuwar da bata
yi bane, a zuciyarta tai mamaki shekara
uku ne kawai da auran su shi ne har ake
gwada mata tsana irin wannan ta shiga
tsananin damuwa ta yadda dangin miji
suke tsangwamarta suka mai da ita
mujiya a cikinsu, duk ta bi ta rame, sai
hanci da manyan idanuwanta da suka
karayin manya idanuwanta da suka
karayin waje, gaskiya Zalifa kyakkyawa
ce dan ko cikin larabawan ma ita din mai
kyau ce, amma duk irin abinda suke mata
bata taɓa gayawa mijinta ba sai dai ko
yaushe ya nai mata korafin ramar da take
yi, ta yi yawa, to dole ne ta rame babu
97
IZGILI JAMILA MUHAMMED
'yan uwa akusa dangin mijin da take san
su zama 'yan uwanta sun tsaneta basa son
ta idan ta je inda suke suna kyararta ai
dole ta shiga wani yanayi to abin Allah
shekararsu biyar da aure Allah ya bawa
zalifa ciki wai murna a gurin Mansir da
Zalifa ba'a magana har ma da dangin
nasa da suke kinta sai duk suka saki aka
shiga tarairayarta, shi Alhaji mansir Bawa
ya yi mutukar murna da Allah ya nufeshi
da ganin jika, daga Mansir da yake
Mansir yaro ne mai hankali da biyayya ga
taimakon marasa karfi.
Akwana a tashi har Allah ya sauki
Zalifa lafiya ta haifi danta namiji
wowowo fadin kyau ɓata baki ne vare.
daka ganshi kasan jinin larabawa ne,
saboda tsantsar kyaunsa duk wanda ya zo
barka sai ya tafi da zancen yaron nan,
Hmm! Zo ka ga bakin Alhaji Mansir yaki
ng
IZGILI JAMILA MUHAMMED
rufawa sai Hidima yake ya kawo wannan
ya kawo wancan dangin Zalifa ma ba a
barsu a baya ba, ana igobe suna suma
suka diro nigeria dauke da kwaryakwaryar kayan arziki dan danginta sun zo
da dama, dan jirgi sukutum kakan yaro
mahaifin Zalifa watan Wazirin Sarki
Misra ya dira duk mai bukatar zuwa
Nigeria. To fa ga jirgi nan a kai ka a
dawo da kai, haka akai taron suna lafiya a
ka gama lafiya Jariri ya ci suna Hisham.
Hisham ya ta shi yaro mai-nutsuwa
gami da hankali amma fa miskili ne na
gasken gaske shekararsa biyu a duniya
Allah ya yiwa kakansa Alhaji Bawa
rasuwa, rasuwar da ta girgiza duk wani
mutum daya kwana ya ta shi a cikin garin
na Gombe jama'a sun ji mutuwar mutum
na mutane irin Alhaji Bawa, mai kirki
99
IZGILI JAMILA MUHAMMED
mai taimakon bayin Allah mai hidima a
gurin jadda kalmar Allah.
Ayyukan da yake gami da taimakon
da yake sai dai Allah ya biya shi
Islamiyyoyi da masallatai fanfuna
burtsatse babu wanda yasan adadin da ya
yi a cikin birnin na