Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 5
tura mata wata leda da ta ganta da ita ta ce, "Bisket da chacolate din nan, na Bintu ne da Aliyu shi kuma túraren naki ne. 32 IZGILI JAMILA MUHAMMED Sannan ta ɗauki post din ta ta ajiye "ta a kusa da ita ta bude ta fito da wata dalleliyar waya mai shegen kyau daga gani kuma zatai dan karan tsada sabida haduwarta, Nokia ce gaskiya ta hadu. Hadiya ta ce, "Gaskiya mutuniyata wannan wayar ta hadu karshe. Kuma daga wa?" Jana tana daga kwance sai ta lumshe idanta tana shafa dan gashinta, da gaba daya tattalin arzikinta yake karewa akansa tai wani wal da idanunta ta ce. "Daga wa kuwa? In ba daga Hubbina ba." Hadiya ta ce, "Gaskiya ya burgeki da waya, ana ji da wannan Salim din." Jana ta ce, "Wallahi kuwa ai duk cikin samarina babu wanda nake so kamarsa, wallahi Hadiya in har narasa shi ban san yadda zanyi ba na san sonsa IZGILI JAMILA MUHAMMED mahadin rayuwata ne kin ga in bashi ba babu rayuwa." Nan da nan Idanu Jana suka kawo kwalla ta ci gaba "Har tsoro zuciyata take bani ganin irin son da take masa ina sansa har ban san yadda zan kwatanta miki ba, jiya da ya zo tamkar zai yi kuka yake gaya min babanshi ya zaɓa mata 'yar abokin babansa wallahi tun jiyan har yanzu bana cikin nutsuwa hankalina a tashe yake dan idan narasa shi komai yana iya faruwa." ." masa Sai hawaye ya wanke mata fuska tamkar an bude famfo. Hadiya ta ji waii matsanancin tausayinta ya kamata, ita dai bata san so ba dan bata taɓa jinsa ba amma zama da Jana sarkin soyayya yasa ta fara fahintar so, abu ne mai dadi amma idan an dace kuma mai mutukar hadari idan anyi IZGILI JAMILA MUHAMMED rashin dace ta koma fahintar rabaka da abin son ka ba karamin tashin hankali bane. Ta matsa a hankali ta dafa kafadar Jana da take ta sharɓar kuka ji take tamkar ta tayata, ita ma kwallar ta tarar mata ta dai daure dan kada ta kara dagawa Janar hankali ta ce. "Dan Allah Jana ki dinga daukan lamarin da sauki kuka ko tunani ba zasu yi miki magani ba ki dage da addu'a a yanzu ita ce magani in dai Salim mijin ki ne to fa labudda sai kin aure shi, idan kuma ba mijinki bane Allah yasa hakan shi ne mafi alkhairi kin ji dan Allah Jana ki sassautawa kanki dan kada ki saka kanki a wata matsala. Jana ta ce, "Na ji in Allah ya yarda zan dage da addu'a har mu ga abinda Allah zai yi." t IZGILI JAMILA MUHAMMED Hadiya ta yi dariya ta cc, “Ko ke fa my sister tayi dariya. Ya yi nisa cikin tunaninsa har bai ji abinda uwar gida sarautar matan take fadi ba, ta shafa fuskarsa ta ce, “Wai ni Alhaji me ke damunka kwana biyu, duk ka canjamin kana yawan zama shiru kana dogon tunanin har baka jin me ake cewa dan Allah idan wani abunene yake damunka ka tai maka ka gayamin dan wallahi idan baka gaya min ba ni ma zaka sani a wani hali.” Alhaji Mansir Kwangila ya sauke ajiyar zuciya ya ce, "Babu abinda yake damuna Zalifa kawai dai ina wani ɗan nazari ne amma karki saka komai a ranki." Ta kalle shi kawai sai kuma ta mike da sauri zata bar falon, ya yi saurin IZGILI JAMILA MUHAMMED janyota da karfi ta fado jikinsa please Zalifa baki yarda da abinda nace ba ko, to ki kwantarmin da hankalinki ba wani abin tashin hankali bane amma ba zan gaya miki shi yanzu ba sai dai na miki alkawari da zarar na gama bincike zaki ji komai." Ta yi sauri sauke ajiyar zuciya ta ce, "To Allah ya mu ji alheri.' " Ya ce "Alherin ma za ku ji” Ta ce, "Shi muke fatan ji a duk inda muke" Ya ce, "To yanzu hankalinki sai ya kwanta da har za ai min fushi dan kawai ki sani a uku.” " Ta saki wata irin dariya mai kara mata kyau ta ce, "To Ai ban ji dalilin sauyawartaka ba a 'yan kwanan kin nan ka ga kuwa hankalin nawa bai kwanta ba zai dai kwanta. 37 IZGILI JAMILA MUHAMMED Ya ce, "Tun da na ce zan gaya miki to zan gaya miki da zarar lokaci ya yi ta cc, "Allah ya nuna mana lokacin nan. " Ya ce, "Amin" Ta ce, "To ta so mu je dinning dan abinci ya dade da kammaluwa kai kawai yake jira." Ya mika mata hannunsa wai ta tashe shi ta ce, “Kaima kasan ba zan iya ba in ba so kake ai haihuwar guzuma ba ɗa kwance uwa kwance yadda kake ɗinnan kace in dɗaga ka, kai ma kasan ba zan iya ba." Ya tashi yana dariya ya ce, "Laifinwa bake kike dirkamin abincin da zan karuba na zata santi kike tun da banji kina complai din ina sakar miki nauyi ba, ya karashe maganar yana daga mata gira. Ta yi dariya tana faɗin Alhaji Kafa girma." 38 IZGILI WHY JAMILA MUHAMMED Ya ce, To bara in gama cin abinci sai ki yi bayanin girman da na yi." Suka yi dariya. **** Yau kimanin sati uku ke nan yana yin zuwa na musamman domin ya san shin ita din wacece so yake ya wani abu game da ita yana so ya san gidansu, amma shiru kake ji babu ita babu labarinta jiya akan idansa aka shiga makarantartasu kuma yana nan aka ta shi ya dinga baza ido ko zai ganta amma komai irin hijabinta bai gani ba, gaba daya kansa ya dau chaji to me yasa bata zuwa makarantar a yan kwanakin nan ya rasa wanda zai tanbaya labarinta to yau din ma haka ya gama zagayanshi daga farkon titi na koki har karshensa, amma duka baba dantela dva va shiga damuwa. IZGILI JAMILA MUHAMMED To ko dai alhaji umar zai samu ne akan maganar gaskiya yana san sanin wani abu daya danganceta dai-dai nan ya ji wayarsa tana ringin ya dauka Alhaji Umar ne ya dauka bayan sun gaisa ya ce, "Kamar kasan yanzu nake tunanin kiranka sai kuma ga shi ka ri gani alhaji Umar mai akwai ya yi dariya ya ce, "Daman na san zaka neme ni dan ka ji ya muka yi da manajan ko?" Alhaji Mansir kwangila ya ce, "Ni ba dan wannan ba, muhimmiyar maganar ce dani kana gida ne? Zan zo 99 Alhaji Umar yai dariya ya ce, "Maganarce ta ruɗaka har ka manta ina Katsina. " Alhaji Mansir ya dafa kai gaba daya ya manta abokinnasa baya nan tun jiya yana ta dukko ɗakin kara. Ya ce, “Ka ga IZGILI JAMILA MUHAMMED naranta gaba daya yanzu dai sai ka dawo ke nan. " Alhaji Umar ya ce, "To ka gayamin mana ko bata waya ba ce maganar 53 . Alhaji mansir ya ce, "Bata waya bace sai dai kawai idan Allah ya dawo da kai lafiya, nan suka shiga maganar kwangilar da shi Alhaji Umar din yaje nemar musu a gurin gwammanan Katsi nan kuma da dukkan alamu zasu samu. ****** Kwance yake cikin bahon wanka kamshin turarukan wankan suna ratsa shi yana busa tabarsa cikin gwanancewa sai da yaji ruwan ya huce sannan ya zubar dashi ya sake sabo, ya daɗe yana cuɗa jikinsa tamkar mai shirin canja fata sannan ya dauko wani dan guntun tawul ya daura a kugunsa ya dau wani kuma yana goge kanshi hade da jikinsa. 41 IZGILI JAMILA MUHAMMED Ya tsaya gaban tangamemen madubin dake manne jikin bango toilet din wanda kake ganin tun daga kafafunka har kanka gefensa kuwa wata 'yar durowace wadda samanta yake sheke da turarukan wanka sabulan wanka dana hannu, dana kai, dana kafa, tamkar kantin sai dasu, su man baki turarukan baki gasu nan dai burjik ya rataya ɗan karamin tawul din gurin da suke jajjere tamkar akantin sai dasu yake gaban dirowar ya ɗauko wani mooth freshner ya kuskure bakinsa sai da yai amfani da wajen kala biyar kuma kowacce da kamfaninta da kuma kamaninta. Daga farshe kuma ya dauko wani dogon turare ya ware bakinsa ya dinga fesawa ya direshi ya dauko mansa na ka shi na dore ya shafa sannan ya ɗauko man tafin hann shi ma na kamfanin dore 42 IZGILI JAMILA MUHAMMED dinne ya shafa, ya ɗauko turaren gaɓa gaɓa duk set din dore dinne dan shi yana aiki da duk kayan kamfanin tun yana germany har kyauta kamfanin sukai masa, saboda aiki da kayansu da yake yi. Ya dauki kum ya yiwa sumarsa sannan ya ɗauko kalolin mangashi ya shafewa ya shafawa wannan kyakkyawar sumar ta shi irin ta asalin larabawa baka siɗik da ita mai taushi gami da santsi ya ɗauki wani turare wanda kuɗin turaren kawai jarin wani talakanne. Yana fesawa kan nan da nan ya kara kaɗannaɗewa tamkar yanda sloon suke cirewa mata waɗan nan rabubin haka gashin ya kanannade. Yana fitowa ya ji enter comm din gidan tana kara tabbacin yana da bako ya kalli agogon dake girke a saman durowar dake gefen lafiyayyan kuma kayataccen 43 IZGILI JAMILA MUHAMMED bed dinshi wanda ya ji wata irin lumtsumemiyar katifar leda da kuma wani datsetstsen bed sheet karfe biyar da minti ashirin to ko waye yake shirin shiga rayuwarsa ya dan saki gajeran tsaki gami da cewa koma waye sai na gama abinda nake yi ya karasa gurin wata irin wardrop wadda ba zaka taɓa cewa wardrop bace saboda tana like a a jikin bango kuma. kalarta ruwan madara ce sai ta saje da fentin dakin saboda shi ma ruwan madara ne, kuma a like take tamkar bangon yana budeta yai tsaye gaban jerin kayannashi wanda kowanne dá gurinsa gurin kananun kaya daban haka suit gasu nan ararrataye babu kalar da babu ya rike kugunsa da hanayansa biyu yana bin kayan da kallo dan ya rasa wanda zai saka, can dai ya dauko wata fitled din T shirt fara ce tas ya saka ta kamashi ya 44 L IZGILI JAMILA MUHAMMED fito masa kirarsa ta cikakken namiji a gaban rigar an subutu hand some guy, rubutun an yi shi da wata kala mai sheke tamkar ruwan kwai. Ya sa ka stripes brown ya dɗauko turaran jiki ya saka ya yi kala biyar ya dire ya dauko wayoyinsa tare da jaridar weekly trust ya fito kayatccen falon nashi har yanzu ma buga kofar bai gaji ba, bai kuma yi zuciya yatafi ba. Ya ajiye jaridar tare da wayoyin nashi kan center table ya nufi farij dinsa ya dauko coke ya ɓinci ni bakinsa ya daga sai da ya shanye sannan ya jefar da gwangwani. Sanyi ya ratsashi ya karasa bakin kofar ya bude kofar. Katum Farida Saraki ta baiyana fuskarta cike da takaicin irin wulakancin da wannan mutumin yake mata, ta kai minti hamsin a wurin nan kuma ta san yana jin 45 IZGILI JAMILA MUHAMMED knoking din da tun dazu take ta ſaman yi amma saboda dan karan wulakancinsa sai yanzu sannan zai buɗde mata, duk takaicinsa da haushinsa ya isheta fadi take a zuciyarta in dai ya bude sai ta núna masa damuwarta da ɓacin ranta na irin wulakancin da yai y mata amma abin mamakin shi ne yana budewa tana yin ido budu da shi sai ta ji wani irin farin ciki ya cika mata zuciya tai tsalle ta dane shi shi ma riketan ya yi yana kiss din bakinta ai take tamkar zata sume saboda santsen harshinsa da wani irin fitinannan kamshi da yake fita daga bakin mai saka mutum a wani yanayin. Sun kai kimanin minti a shirin atsaye abakin kofar suna ta ya mutsa junansu suna cakudawa, can da abin ya girmama sai ya maida kofar ya ya ɗan danna mata key ya rungumeta ya cika 46. IZGILI JAMILA MUHAMMED hannunsa da albarkatun kirjinta su kai bedroom dinsa. Inna Lariya ta shigo dakin da kofin silba a hannunta ta dire shi gami da zama ta ce, "Hadiya ki tashi ga fura malam ya shigo miki da ita." Hadiya da take kodundune akan yalolowar katifarta tai magana daga kudundunen da take tace, "Inna na koshi." Inna ta ce, "Ai kuwa baki isa ba kin taɓa jin inda aka warke daga cuta alhalin ba ashan magani, ba kuma a cin abinci saboda tsabar gardama da kafiya irin naki to tunda nadama furar sai kin shata, idan` ma zaki samawa kanki lafiya ki ta shi to ki tashi dan wallahi sai kin sha, kin kuma sha sha mu gani tunda ga shi an sami kudi an sayo miki." 47 IZGILI JAMILA MUHAMMED Hadiya ta ture abin rufarta ta tashi zaune ji take kanta tamkar zai tsage saboda ciwon da yake yi mata ga kuma matsanancin zazzabi. Ta dauki furar tunda ta ji Inna ta rantse ta san dole ne ta shata ta fara sha tana yamutse fuska duk santa da kaunarta da furar ji ta yi tamkar maɗaci take sha tana yin kurɓa ɗaya biyu ta dire kofin ji take tamkar zata yi amai, Inna ta saka mata manyan idanuwanta ai babu ariziki ta dauki kofin dan ta san ma'anar kallon. Haka ta dinga daurewa tana sha sai da ta sha rabi sannan ta kalli Innar dan taga a wana yanayi take, da taga bata nuna komai ba sai ta a jiye ta ɓare magungunan ta bata ta karɓa ta ce, “Dake wata ce, ai da sai ki bari sai maganin da furar da kika sha sun fada miki sannan ki kwanta." IZGILI JAMILA MUHAMMED Hadiya ta hadiye maganin nan da kyar ta dauki mayafinta ta dukunkune a cikinsa amma bata kwanta ba, dai-dai nan su ka ji sallama Jana Inna ta dauki kofin ta fita tana amsa mata sallama. Jana suka gaisa da Inna, jana tana tambayar mai jiki Inna ta ce, "Da sauki tana ciki ki karasa." meJana ta shiga ɗakin ta zauna ta kalli Hadiya cikin tausayawa ta ce, "Sannu Hadiya." Hadiya ta ce "Yauwa." Jana ta ce, "Ya jikin naki.?" Ta ce, "Da sauki. Jana ta ce, "Iya ta ce, a karayi miki sannu.' Hadiya ta ce, "Ina amsawa." Jana ta ce, "Habib ma yana duba ki ya ce, ya na miki sannu.' Ta ce, "Ina amsawa." 49 " IZGILI JAMILA MUHAMMED Haka suka dinga yin hirar yan makaranta Islamiya da boko da yake duk ajinsu daya tana gaya mata wadanda suka ce ai mata sannu, saboda basu sami damar zuwa dubata ba, dan gaskiya Hadiya tana da farin jinin mutane da wuya ta zauna a guri ba a so ta ba, ba dan komai za a so ta, dan kyanta dan can din din ita kyakkyawa ce ta ajin farko kuma tana da san mutane tana da mutukar fara'a in dai ta sanka in bata sanka bane tana da wuyar lamari. Alhaji Mansir ya dauki lemon Edotic din da mai dakinsa Hajiya Zalifa ta tsiyaya mai ya kurɓa gami da daukan remote control ya rage sautin tangamemiyar T. b plasman dake like jikin bango girmanta ya shahara tamkar mutanan jiki zasu fito ya kalli gefensa IZGILI JAMILA MUHAMMED inda Hajiya Zalifa take dan kishingiɗe kan tuntum tana cin Tufa suna kuma ‘yar hira. Ta zuba kwalliya tamkar mai zuwa fadar shugaban kasa, daman gata mai kyau duk mptsin da tai wani fitinan nan kamshi ne yake tashi, Alhaji Mansir ya ci gaba da kallanta. Gaskiya yana san matarsa yana kaunarta ko dan gayunta sam bata tsufa tamkar yanzu aka kawo masa ita gidansa shi yasa yai ta ganin bakin danginsa da suke damunsa da zancan aure yanzu sun daina, ya riga yasan Zalifa ta mallake zuciyarsa babu sauran gurin da zai saka wata ‘ya mace, ya san ba zai iya hada daki da wata macen ba dan yadda yake santa yake san farin cikinta ba zai so damuwarta ba ita kuma a duk duniya babu abinda ta tsana sama da kishiya bata santa kwata-kwata 51 IZGILI JAMILA MUHAMMED . tana kishi da abinda take so tana bashi kulawa sosai tamkar wani jariri haka take tattalinsa tun a farkon auransu har zuwa yanzu. Yau kimanin shekara talatin da takwas ke nàn da yin aurensu amma bata taɓa ɓata masa rai ba, tana sani ba, sai dai a ajizanci irin na dan adam, tana sonsa tana kyautata masa, tana san 'yan uwansa, tana kyautata musu, tana sansu. so na gaskiya, Allah mai hikima ne da ya ce, muddin mutum yai sa'ar mace ta gari lallai rabin imaninsa ya cika, sai ya kyautata aiyukansa, dan ya samu rabauta, ranar gobe kiyama, gaskiya mace ta gari jin dadin namijin duniya, mace tagari ita ce, silar wanzar da zaman lafiya gaba daya ya shagala da kallonta yana fasalto abubuwan alkhairinta gaskiya duk iya zamansa da ita bai taɓa ganin wani abun 52 IZGILI JAMILA MUHAMMED assha kona Allah wadai data taɓa yiwa wani, wani abun narashin kyautatawa ko zamanin da 'yan uwansa da mahaifiyarsa suka saka mata karan tsana. Can hajiya Zaliya ta kula da hankalin Alhajin baya kanta dan sai magana take yi masa amma hankalinsa yana wani wajen bai ji ta ba ta dago dan taga mai ya ke yi sai taga ya zuba mata ido ashe tun dazu ita yake kallo ta mike zaune daga kishingiɗar da ta yi ta kira sunansa, yai saurin sauke ajiyar zuciya ya ce, "Na'am' " Ta matso kusa da shi har sunajin numfashin juna, ta saisaita muryarta tana wasa da zagayayyen gashin bakinsa ta ce, "Alhajina wai ni lafiya? Duk fa 'yan kwanakin nan haka kake kafiya yawan shiru da tunani. " 53 IZGILL JAMILA MUHAMMED Ya sauke ajiyar zuciya ya ce, "Akan dai zancan nan da mu ka yi dake ne kwanaki, to wallahi yanzu abin ya dame ni sosai so nake in zaɓa masa kawai sai dai ince masa rana kaza dan nagaji da wannan shashancin banzar da yake yi. Dai dai nan wayarsa dake gefensa ta ɗauki ringin yana duba wayar yaga my son ya ce, “Kin ganshi ma ya danna ok ya fara maganar sosai da suka dan daɗe sannan ya mikawa mominsa tana yi masa fadan yaki zuwa ko ya makale Abuja. Ya ce, "Aiyuka ne Momi su kai min yawa amma insha Allahu zan zo karshen wannan satin. Ta ce, "Ka dai faɗa ne. 99 Sun dade suna magana sannan ta kashe wayar ta dubi Alhajin ta ce, "Dan Allah Alhaji ka sassautawa ranka ka daina yawan tunanin nan kar wani ciwo 54 IZGILI JAMILA MUHAMMED ya kamaka kabi komai a hankali dan Allah. Ya yi dariya ya ce, "To ranki ya dade za'a yi yanda kike so gaba daya suka yi dariya." NIGHT CLUB Club din cike yake makil da ‘yan kosassun Abuja ‘ya'yan manya Club din yai mutukar tsaruwa tamkar a turai, zaka yi mamaki ainun da man akwai club kamar wannan a Nigeria saboda yadda ake zuba lalata tamkar a garin nasara, asarar duniya babu abinda ketashi sai wani tattausan Music mai ratsa kwanya kowa sai harkokinsa yake kwanciyar hankali wasu gurin shaye shayensu su kafi kauri yayinda wasu gurin rawa suka karkata dai-dai nan Hisham Mansir kwangila ya baiyana gaba ɗaya samarin gurin suka ruɗe da ihu cikin 55 IZGILI JAMILA MUHAMMED wadanda suke kusa suka dinga rungumarsa ya yinda wadanda suke nesa suke yi masa fito suna fadin Hey hand some. Cikin takunsa na kasaita gami da shariya yake ɗaga musu yatsansa biyu bai saurari ko ina ba sai can wata kujera ta musamman yana zama Joh mai aiki gurin ya russuna cikin girmamawa ya ce, "Yallaai barka da zuwa.' Cikin kallon nasa na ka'ida ya kalle shi ya ce, Cikin wata daɗɗan muryarsa "Guiness masu sanyi zaka kawo." " Cikin sauri ya ce, "An gama oga. Ya kishingida ya daga daradaran kyawawan idanunsa yana bin club din da kallo ya ajiye wayoyinsa akan table ya fito da kwalin sigarinshi daga aljihun ya 56 IZGILI JAMILA MUHAMMED mannata abaki ya dauko lighter ya kunna yana bulbular da hayakin. Nan take ya haɗa dan karamin gajimare cikin kwarewa yake fesar da hayakin tun shigowarsa. Hankalin 'yan matan gurin ya yo kansa sai shawagi suke ta gabansa ko da Allah zaisa ya kyasa, kowacce so take taga ta burgeshi tana so ta samu shiga a ce yau ya yi mu'amala da ita koda sau daya ne, dan ta san kudin da zai shaka mata ba kaɗan bane, wasu kuwa so suke ya kula su ko bai basu komai ba, ai abun burgewarsu ne kyakkyawa na bugawa a media kamarsa ya kulasu, to su abin alfaharinsu ne musliki dan wulakancin tabar hannunsa ta fisu daraja, a gurinsa, dan shi ko da zai mutu saboda bukatar mace in ba kin isaba kin kai kin kawo wajen haɗuwa gami da aji ba, to ko kallanki ba zai yi ba, 57 IZGILL JAMILA MUHAMMED balle har ya hada jikinsa da na ki dan shi ko cikin mata ba kowace kwashi kwaraf yake kulawa ba, sai ya tabbatar kina da abin kallon sannan zai kalla shi yasa wasu mazan abokansa suke ce masa ba kai kake kallonsu ba, kai ake kallo. Ya lumshi idansa yana jin wani yanayi mai dadi can idanunsa suka kai filin, rawar nan idansa ya hasko masa wata yarinya sai juyi take mai ban sha’awa ya kura mata ido yana kallanta, sanye take cikin wite yar bingilar riga wadda gaba daya cillyoyinia, awaje suke rigar kuwa bata da hannu gaban rigar anyi mata gidan bireziya mamanta rabi duk a waje, suke tana sanye da wasu dogayen, takalma wanda suka dace dashigart kanta yasha wata mici micin kalaba gashin kanti, fara ce, tas, kunnuwanta sanye da dogayen yari gaba daya ta gama 58 IZGILI JAMILA MUHAMMED tsuma shi ta yanda take sarrafa hips dinta tana takawa cikin aji dai-ɗai nan Joh ya dire masa kwalaban sassanyar agabansa da ya jerosu akaǹ\ wani dan madaidaicin faranti, da kuma wasu kananan kofuna na karau, ya saka opener ya buɗe masa ya zuba masa gami da dan rusunawa ya ce, "Oga ga shi nan." Hisham ya dauko kofin batare da ya dauke idanuwansa a gurinba ya ci gaba da tultulawa tumbinsa ruwan barasar yana wani kasa-kasa da marayun idanuwansa yana kare mata kallo, tamkar ance mata juyo sai ta hango mai tsada sunan da yawancin 'yan matan suke faɗa masa ya wani dalalo mata waɗannan fitinannun idanuwannan nasa. Sai ta ji wani irin matsanancin farin ciki ya kamata ta san ma'anar kallon cak ta tsaya da juyin da " 59 IZGILI JAMILA MUHAMMED take yi kuma ta fito daga filin cikin taku mai jan hankali ta baro gurin rawar. Ta kara so gurinsa tana zuwa taja kujera dake gefensa ta zauna ta ce, cikin harshen turanci ta ce, “Barka da dare hand some cikin kallonsa na isgilanci ya dage gira yana dallareta da wani shi'umin kallo cikin muryar kasaita ya ce, “Ke ma haka." Ta dauki daya kofin ta zuba itama ta fara kwararawa 'yan hanjinta gaskiya gaskiya kyakkyawa ce duk da dai baba bahaushiya bace yare ce, ya ce, "Me sunanki.?" Ta danyi dariya ta ce, kudurat ya ce, "Amma yau kika fara zuwa nan dan ban sanki ba.' biyu." Ta ce, "Wannan shi ne zuwa nan na Ya ce, "Kina rakiya.?" IZGILI OFREADGES JAMILA MUHAMMED fara." Ta ce, "Kabana yi, ai akanka sai na 27 Ya ce, "OK" ya ci gaba da dadɗaar abarsa sai da ya shanye kwalabe uku ita kuma kwalaba tasha ya yafito Joh ya taho da sauri ya dantso kudi ya bashi ya ce, "Duk wanda yasha ga kudinsa nan idan kuma da ciko sai mun badu." 99 Joh ya dinga godiya tamkar zai ari bakin Hisham. Ya juya ga Kudurat da giyar ta fara bugarwa ya ware hannun nasa ya ce, "Come on my baby." Ckin wani irin hali slow ta karasa tana kicin kicin sabule 'yar guntuwar rigarta na wasu surutai irin na wadda giya ta fara aiki, yai saurin rungumeta gami da rike mata hannu, ya rada mata a kunne ba anan zaki cire ba sai mun je gida, kin ji baby ta Infe inse yo kwashe wayoyinsa yai hanyar barin club din IZGILI JAMILA MUHAMMED samari suka dinga cewa Good night handsome guy, ya kuma daga musu yatsansa biyu ya shiga rantsatstsiyar motarsa ya bar club din. ****** Hadiya ce ke kokarin saka safarta sauri take yi ta shirya kada uwar haiyatar ta zo ta haiyaceta. Sanye take da kayan makarantar ‘yammata ta saka kayan sun karɓeta komai ta saka sai sun karɓeta ta nannade himilin gashinta cikin wani tabkeken ribon sai ta yi ɗaurin mai tuntu sai kace mai acuci maza. Inna taɗaga labulen hannunta dauke da dankaramin kofi mai dauke da kunun tsamiya sai tururuwa yake, yasha lemon tsami ta mika mata ta ce, "Maza ki kurɓe Wannan ko aa tsaitsaya nene ke da arayuwarki baki san cin abinci da wuri IZGILI JAMILA MUHAMMED wai ku 'yan boko ko? To ko su ma 'yan - bokon ma wasu ne masu ka idoji wasu " kuwa sak suke." ' Hadiya ta karɓi kunun tana ta kukkurɓa. Jana ce, ta kwaɗo sallama Inna ta amsa ta shigo ita ma sanye take da kayan makarantar dan hijabin nan ɓigil iya kugu. Hadiya ta ce, "To uwar haiyata to ai kya jira ni in gama karyawa tu kunna.' " Jana ta samu gurin zama tana gaida Inna Inna ta ce, "Ya mutan gidan?" Jana ta ce, "Lafiya kalau." Inna ta fita jimawa kaɗan ta dawo hannunta dauke da wani kofi ta mika Jana. Jana ta amsa ta ce, “daman kuwa wallahi ban karya ba dan yau iya dumame kawai ta yi bata dama koko ba saboda jiya ba wanda ya ci tuwan shiyasa 63 IZGILI JAMILA MUHAMMED yau ta ce, baza ta dama kokon ba duk wanda baya cin tuwon ya barshi cikinsa. Jana ta shanye kunun tas gaskiya Inna Lariya ta iya girki gata da masifar tsafta 'ya'yanta ma agurinta suka dauko tsaftar ta dan Hadiya tasha karbar kyaututtuka ba daya ba ba biyu ba, na dalibar da tafi kowa ladabi da tsafta. Hadiya ta fita da kofunan ta ce, "Wai ni dan Allah Jana mai yasa bakya jin magana ne.?" Jana ta dallaro mata wata shegiyar harara ta ce, "Rashin jin maganar me na yi? Uwar iya yi. " A Hadiya ta kai kofin can gefen tsakar gidansu Inda Innar take yin girki ta dawo - ta sako hijabinta. Shi ma babbane da kadan ake hango kafarta sannan ta saka nikaf dinta, suka yiwa Inna Sallama tayi musu fatan dawowa lafiya suna fitowa 64 IZGILI JAMILA MUHAMMED Jana ta ce, “Uwar fi'ili fadi ina jinki ki gayan abin da na yi, na rasa jin maganar da na yi?' Ta cikin nikaf dinta take magana ta ce, "Ta yanda naga kinsha wannan make up din tamkar mai shirin zuwa party." Jana ta dallara mata harara ta ce, "Au! Ke ki na zatan wannan horan da suke na yiwa mutum bulala da cewar ka goge kwalliyar da farin hijibinka zai razana ni ne, har in daina kwalliya to in ma da kina tunanin haka to ki daina dan wallahi in dai ba adaina powder a duniya ba, to har tsofana sai kin ganni da kwalliya." Hadiya ta saki dariya ta ce, "NI ban taɓa ganin sahibul kwalliya ba kamar ki, ke ciwo indai ba wanda za a kwantar a tayar ba to bafa zai hanaki yin kwalliya ba." 65 = IZGILI JAMILA MUHAMMED Jana ta ce, "Ita ce cikar mace, ba ki zauna a kasa banbance fuskar namijin a kasa gane taki **** Wayarsa dake ajive kan yar durowar gefen gadance take a Taman burari bai sanya akai ya manta bai kashe ta ba, duk karar ta dame shi can ya dan dago ya dauka ya katse, ya maida kansa suka ci gaba da sheɗanar da suke yi, shi da ‘yammatansa. Ya yi nisa cikin abinda yake yi na sheke ayarsu kwatsam ya sake jin kiran ya shigo cikin magagi irin na wanda ya fita daga cikin duniyar mu ya suri wayarsa zai kashe can idanunsa ya hango masa tamkar daddy na ya gani da sauri ya ture Farida saraki ya mike ya yo falo yana amsa wayar. 66 IZGILI JAMILA MUHAMMED Alhaji Mansir kwangila ya ce; "Ka bude min kofa gani a bakin kofa." Cikin matsananciyar kidima ya ce, "Daddy kana bakin kofa fa kace? Yaushe ka shigo garin.?" Ya ce, "Yau ko in ce ma yanzu, idan kuma kana mamaki ne to ka bude mana. " Ai da sauri Hisham ya cillar da wayarsa yai bedroom dinsa da gudu Farida Saraki da Kudurat zaune 'yam matansa da yake ji dasu dan duk gaba dayansu ba baya ba, suna iyawa dashi. Suna kwance akan gado haihuwar uwarsu da sauri ya daka musu tsawa ya ce, “Maza ku barmin gidana ga Daddy na nan ya zo." Cikin sauri ya zurma

Chapter 2 of 5