ita ce ta fita tana zabga ihu daga ɗakin Rakiya ba. Bai amsa mata ba, sai gefen gado da ya zauna yana haɗe fuska. Ganinsa hannuwa suna dukan cinya ya sa ta wurga masa tambaya, kwata-kwata ya manta da sayen wani naman kazar amarci. Don wannan auren ya yi ne kawai da zummar ko Rakiya za ta samu salama a wurin Inna. Abincin da Inna ta girka Zuwaira ta miƙa masa, kamar ba zai karɓa ba sai kuma ya ci loma biyu ya ce ya ƙoshi. Zuwaira da kanta ta dinga jan Malam Hasan cikin kissa da kisisina har mai afkuwa ta afku a tsakaninsu. Don haka koda gari ya waye ko ƙofar ɗaki Zuwaira ƙin fitowa ta yi, wai ba ta jin daɗin jikinta don a dole ta nuna wa Rakiya wani abu ya gifta a tsakaninsu. Da safe koda Malam Hasan ya fito zai shiga ɗakin Rakiya fir Inna ta hana shi, a cewarta ba kwananta ba ne don haka ba ta da haƙƙi a kansa ranar. Yana ji yana gani ya tafi tallan turaren, don kwandon turarensa ma sai Inna ce ta ɗauko masa.
Sannu a hankali zaman Rakiya da Zuwaira ya fara sauya salo duk da dama ba zaman daɗi suke yi ba. Sai Zuwaira ta ɓullo da duk ranar girkin Rakiya tun rana za ta fara kwanciya ta ce ba ta da lafiya, idan yamma ta yi sai ta haye gado ta rufa da bargo. A kan dole idan Malam Hasan ya dawo Inna take tilasta masa kwana a wurin Zuwaira. Saboda wani lokacin cewa take ana tsorata ta, ko ta ce motsi da giftawar mutum take gani. Tun yana ɗaukar abin kamar gaske har ya fara fahimtar makirci ne, damuwarsa ta ninku musamman da yake buƙace da matarsa Rakiya. Don a ƙalla ya kai sati uku ƙwarara bai kwana a ɗakin Rakiya ba, ko da rana bai isa ya shiga ɗakinta ba sai Inna ta fara yi musu masifa. Watarana Inna ta fita unguwa, yana zaune a bakin kasuwa ya ga wucewarta. Farinciki ne ya lulluɓe shi, don haka cikin sauri ya ɗauki kwandon turarensa ya wuce gida. Ya ci sa'a Zuwaira ba ta tsakar gida, don haka ya faɗa ɗakin Rakiya. A kwance ya same ta idanunta suna kan silin, da yake ta yi zurfi a duniyar tunani ko motsinsa ba ta ji ba. Sai da ya kira sunanta sannan ta kalle shi, da sauri ta miƙe tsaye kamar ta ga sabuwar hallita. Malam Hasan ya zuba mata idanu ganin lokaci ɗaya ta zabge duk ta rame, a hankali ya fara takawa wurinta Rakiya ta matsa da sauri ta faɗa jikinsa sai ta ji kuka ya ƙwace mata. Kukan da ta ɗauki kwanaki tana son zubar da hawayensa ba ta samu sukuni ba, tausayinta ya ji har cikin ransa. Ya saka hannu yana bubbuga bayanta, cikin so, ƙauna da tausaya ya ce.
"Ki yi haƙuri farincikina."
Sai da ta share hawayenta ta ce, "Ka fita kada Inna ta dawo."
Bai iya amsa mata ba, sai janyo ta da ya yi ya sake riƙe ta tsam. Tana son ƙwace kanta amma ta kasa, ya sunkuya saitin fuskarta ya furta.
"Na yi kewarki, kullum da tunaninki nake kwana nake tashi. Ban san ya zan ɓullo wa Inna ba."
"Mu cigaba da haƙuri, watarana sai labari."
Rakiya ta furta a sanyaye, don shi kansa ba ƙaramin tausayinsa take ba. Girgiza mata kai ya yi ya ɗago da fuskarta ya ce.
"Ba zan iya ba Rakiya, saboda ina shiga haƙƙinki. Ya zama dole na nemar mana mafita."Ba ta amsa masa ba, ya cigaba da aika mata kalaman soyayya masu kassara jiki, a hankali yake aika mata da saƙon soyayya mai cike da kewarta. Rakiya mace ce da ta san kanta, don haka ta shiga mayar masa da martani. Kowannensu sai da ya nuna wa ɗan'uwansa ya yi matuƙar kewarsa, don yadda ta ga Malam Hasan ya birkice mata sai ka yi tsammanin babu mace a kusa da shi duk tsawon kwanakin da suka ɗauka.
"Ka tashi ka gyara jikinka ka fita lokaci yana tafiya."
Rakiya ta furta masa, ga mamakinta sai ji ta yi hawaye ya gangaro daga idonsa.
"Me ya faru kuma?"
Ta tambaye shi muryarta tana rawa, don ta fahimci dalilin hawayensa.
"Ina sonki matata, ina ƙaunarki farincikina. Idan na fita yanzu ban san lokacin da zan sake jin ɗuminki ba, a cike nake da kewarki zuciyata ina jin kamar kada na matsa daga kusa da ke."
Yadda yake magana ne ya kashe mata jiki, amma gudun kada a samu matsala ya sa ta shiga tausarsa. Suna nan maƙale da juna suka ji sallamar Inna, tamkar waɗanda suka ga mala'ikan ɗaukan rai haka suka firgice lokaci ɗaya kowannensu gabansa ya shiga faɗuwa.
Tun shigowar Inna gidan ta hango takalmin Malam Hasan a ƙofar ɗakin Rakiya, don haka rai a ɓace ta ƙarasa ɗakin cikin masifa ta bankaɗa labulen ɗakin. Ta windon uwar ɗakin ta hango su da yake a gadon Rakiya a saitin windon yake. A kunyace su Rakiya suka ja zanen gado suka rufe jikinsu. Inna ta ja dogon tsaki cikin masifa ta ce.
."Ke dai wannan an yi jarabaiyar yarinya, yanzu don masifa da rana tsaka ma sai da kika yaudaro mini ɗa? Ki bar shi ya tafi nema amma kin kanainaye shi a ɗaki, wato kin samu dama na fita ko? To ka tashi ka fito ka je ka yi wanka ka fita nema, shashasha sai kace ba shi da wata matar don jarabar tsiya."
Inna ta yi furucin da ƙarfi, jin Hasan ya amsa ciki-ciki ya sa ta ce.
"Za ka fito ko sai na fito da kai da kaina?"
A kunyace Malam Hasan ya zura wata doguwar rigarsa ya fito, ya nufi banɗaki yana jin ɗacin ɓacin rai a zuciyatsa.
Ummou Aslam Bint Adam🌚
07062062624
[15/05, 18:55] Ameerah Adam: *GAMMON RAMA*
©AMEERA ADAM
*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*
Gargaɗi: Ban amince a sarrafa mini littafi ta kowacce siga, ba tare da izina ba.
Tsokaci: Ƙirƙirarran labari ne bai faru a gaske ba, idan ya yi daidai da yanayin labarinki/ka arashi ne.
SHAFI NA SHIDA
ABBAN FAUWAZ
Da sauri mutanen da ke ƙofar gidan suka ƙarasa wurinsa suka shiga kiran sunansa, sai dai ganin ba ya numfashi ya sa aka yi gaggawar ɗaukarsa zuwa asibiti. Tun da Tani ta ji abin da ya faru ta saki sabon kuka da kururuwa, da farko abokan Abba cewa suka yi ta bari su je asibiti su ga yadda yanayin jikinsa zai kasance tukunna. Amma ganin yadda Tani ta ɗaga wa mutane hankali ya sa a kan tilas aka bar ta ta tafi asibiti. A lokacin da ta ƙarasa bacci yake yi ana ƙara masa ruwa, tana nan zaune bayan wani lokaci ya buɗe idonsa ya zuba wa fankar da ke wulwulawa ido kamar yana ƙidaya adadin gudun da take yi.
"Sannu Abban Fauwaz!"
Tani ta furta tana matsawa gabansa, a hankali ya dube ta cikin sanyayyar murya ya ce.
"Tani ina cikin tashin hankali."
Lumshe idonta ta yi cikin nuna damuwa ta ce, "Bari na fara kiran likita ya duba jikinka Alhaji. Saboda jininka ya hau, don haka suka ce idan ka farka a sanar da su."
"Tani babu buƙatar kiran likitoci, don lalurar da ta afko mini babu likitan da ya isa magance mini ita."
Abba ya furta da muryar damuwa, riƙo hannunsa Tani ta yi ta ce.
"Komai ya yi tsanani maganinsa Allah."
Abba ya jinjina kai sannan ya ce, "Wannan haka yake, amma abin da nake so ki fahimta. Irin wannan guguwar da ta taso mini, irinta ce wacce ake cewa gobara daga teku maganinta sai Allah."
"Alhaji har yanzu riga kake ɗinka mini babu wuya, ban fahimci inda maganganunka suka sa gaba ba." Tani ta furta masa tana tsare shi da ido. Sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya ce.
"Kuɗin da na ara kwanaki, waɗanda na zuba a kayan da aka tafi da su kwatano da Ghana ne suka halaka."
"Innalillahi wa inna'ilahir raji'un!"
Ta furta a hargitse cike da tashin hankali ta ce, "Ban fahimci sun halaka ba Alhaji?"
Abba ya furzar da iska mai zafi ya ce, "Kayanmu ne aka kama su, sakamakon an samu ƙwayoyin hodar iblis a cikin wasu daga cikinsu, Alhaji Ɗan gaske ya ce mu yi ta addu'a idan ba a nemi masu kayan ba domin hukunta su."
"Hasbunallahu wa ni'imal wakeel! Alhaji wannan wacce irin jarrabawa ce? Yanzu ya za ka yi da kuɗin wurin Alhaji Dikko?"
Tani ta furta masa, jim ya yi yana nazari sai ya ɗago ya ce. "Wallahi ban sani ba Tani, ban san yadda za mu kwashe da shi ba." Zumbur! Ta ga ya miƙe, cikin sauri ta riƙo shi ta ce.
"Yi a hankali Alhaji, ko a kira likitan ne?" Girgiza mata kai ya yi ya sauka a kan ƙafafuwansa sannan ya ce.
"Gida zan tafi."
Duk yadda Tani ta so hana shi fir ya ƙi amincewa, sai da ya fita harabar asibitin ya ci karo da abokansa waɗanda suka kawo shi asibitin. Bayan an gama biyan kuɗaɗen da aka kashe suka wuce gida.
A washegarin abin da ya faru, sai da ta tabbatar da Abba ya fita, saboda tun a ranar Alhaji Dikko ya fara doka masa waya don ya ji makamar wurin da kuɗinsa za su ɓullo. Saboda ya ji labarin abin da ya faru da Abba a wurin mutane da dama. Abba ya tafi wurinsa ne domin ya ba shi haƙuri, ya kuma nemi alfarmar ya ɗaga masa ƙafa zuwa wani lokacin kaɗan.
Uwar ɗaki Tani ta shiga ta ciro wata lamba a takarda, sai da ta kwafe lambar a wayar sannan ta latsa kiransa. Daga can ɓangaren ta ji an ce, "Kunama mugunyar ƙwaro, ga ki da harbi mai kai mutum ƙasa." Murmushin jin daɗi ta yi, kanta ta ji ya ƙara girma. Cike da isa ta ce, "Kuma ko a yanzu kasuwa ta tashi ɗan koli ya ci gwagwgwaɓar riba." Shi da ita duka suka bushe da dariya. Yadda Tani ta shagala ne ta manta da Fauwaz yana cikin gidan, Fauwaz ya fito zai fita ya ji tana cewa.
"Amma ya aka yi wannan tarkon namu ya kama shi yanzu? Ni fa na ɗauka sai tura ta kai bango. Ka san fa duka kuɗin da ya ranto na saka shi ya zuba a waɗannan kayan da yake shi mahaukaci ne." Daga can ɓangaren ya ce, "Ki ce ya ɓallo wa kansa ruwa. Yanzu kusan nawa ya ranto?"
Shiru Tani ta yi tana nazari sannan ta ce, "A ƙalla za su kai miliyan uku, kuma daɗin da na ji maganin wurin malamin nan da ka karɓo mini bai karye a jikinsa ba."
"Ke fa bala'i ce Tani, amma ki ɗan ɗaga masa ƙafa mana." Mutumin ya furta yana sakin murmushi, ita ma murmushin ta saki ta ce. "Wallahi tallahi ko Alhaji zai yi yawo tsirara ba zan rangwanta masa ba, don tun kafin yarinyar nan ta mutu tuni na yi masa farraƙu da su. Tsakaninsa da su sai tswangama, kuma duk abin da na faɗa ta zauna."
"Sai da ke 'yar kunama."
Ya furta cikin kanbabawa, jin haka ya sa ita ma ta amsa suka kwashe da dariya sai ta ce.
"Lighter ka ƙara riƙe wuta fa, saboda daga wurin Alhaji Dikko kai tsaye tashar jirgin ruwa zai nufa." Amsa mata yi sannan ta ce za ta kira shi gada baya.
Fauwaz da ke jin duk tattaunawar da Tani ta yi, duk sai ya ji tausayin mahaifinsu ya kama shi. Duk wani haushi da ƙullatar da ya yi masa ya saɓe, sai ya sake jin tsoron Tani ya sake mamaye shi. Duk yadda yake fasalta rashin imanin Tani sai ya ga ashe ta doke harsashensa.
'Yanzu ta ina zan fara nusar da Abba wace ce Tani?'
Fauwaz ya raya a ransa, ganin ba shi da tsayayyar mafita ya sa shi barin wurin ya shiga ɗakinsa yana tunanin yadda zai ɓullo wa al'amarin.
Tun daga wannan ranar kwanciyar hankali ta yi ƙaura a wurin Abba, ban da Tani da a zahiri take nuna masa tana cikin damuwa amma a baɗini ta fi kowa farinciki da al'amarin da ya same shi. Sai dai kuma ba ta so al'amarin ya faɗo a daidai wannan gaɓar ba, don tana gudun kada kwaɓarta ta yi ruwa tsululu asirinsu ya tonu.
A ɓangaren Fauwaz ya samu sauƙin tsauwalawarta da ta Abba sosai, saboda kusan kullum mahaifin nasa ba ya zama a gida. Yau yana tashar jirgin ruwa yana fafutukar a saki kayansa, gobe yana ƙofar gidan Alhaji Dikko. Ita kuma Tani ya rasa abin da take ƙullawa kusan kullum da mahaifinsa ya fita take shurar takalminta ta fita.
Ana cikin haka ne wani a cikin tashar jirgin ya ce zai yi masa hanyar da kayansa za su fito, amma sai ya biya kuɗi kusan dubu ɗari biyar. Jin haka ya sa Abba ya kasa zaune ya kasa tsaye, haka ya dinga buga-buga tsakanin abokan kasuwacinsa na goro ya ranto kuɗi dubu ɗari biyar. Tun da Abba ya byar da kuɗin, mutumin yake yi masa yawo da hankali. Yau yace ba ya nan gobe ya ce an tura shi wani gari, daga ƙarshe ma har ya daina ɗaukar wayarsa. Ana cikin haka Alhaji Dikko ya tayar masa da ɓalli, don har hukuma ce ta shiga tsakaninsu. Don haka Tani ta shawarce shi da ya sayar da gonakin da ya saya idan ya so sai ya biya kuɗaɗen da suke kansa.
Kai tsaye lambar Gambo dillali ya nema, amma sai ya ji ta a kashe ba ta shiga. Da yake a buƙace yake da kuɗi kai tsaye 'yan dillalai ya nufa yana nemansa. A nan mutanen wurin suka jaddada masa cewar ya bar garin, sakamakon dama can asali ba ɗan jihar Kano ba ne. Buƙatar da ke tafe da shi ya sanar da su, a nan Shamsu dillali ya shige masa gaba wurin tallata ƙaton gonakin nasa. Ko sati guda ba a rufa ba cikin hukuncin Ubangiji aka yi dace da samun mai saya, bayan da suka je aka duba gonakin suka yi ciniki ya ɗebo takardu ya miƙa masa. Da yake sun ga a buƙace yake da kuɗi bai wani ci riba da gonar ba, don kusan yadda ya saye su haka ya sayar da su. Yana karɓar kuɗin kai tsaye ya kai wa Alhaji Dikko ko gida bai koma ba, ya kuma nemi alfarmar ya ɗaga masa ƙafar sauran zuwa wani lokacin. Sai da suka yi rubutu a gaban wani ɗansanda kowa ya saka hannu sannan Abba ya wuce gida.
Tun bayan fitarsa Tani ta cika fam da farinciki, a lokacin Fauwaz yana ɗebo ruwa yana zubawa a drump. A wani zuwa da ya yi zai juye ruwan ya ji muryarta can ƙasa tana cewa.
"To yanzu me ya rage? Ai ƙarshen tuka-tuka tik, mun yi waya da shi ya sayar da gonar. A tsammaninsa sayar da wannan gonar shi ne rufin asirinsa, bai san ɗaya daga cikin manyan ƙofofin tashin hankalinsa ne suka buɗe ba." Amsa mata aka yi daga can ɓangaren sai ta cigaba, "Wai ka san waye Alhaji Dikko a kan kuɗi kuwa? Kai dai ka zuba ido ka sha kallo."
Fauwaz ji ya yi zuciyarsa ba za ta iya ɗauka ba, don haka ya sauke bokitin kansa ya ƙarasa cikin ɗakin ya ce.
"Ke wacce irin mace ce da ba ta tsoron Allah?"
"Irin wacce mahaifinka yake muradin rayuwa da ita."
Tani ta ba shi amsa tana tsare shi da ido, wata irin tsanarta ta sake mamaye shi. Ya dube ta ido cikin ido ya ce. "In Shaa Allahu yau zan sanar da Abba wace ce ke, da irin cutarwar da kike yi masa." Wata irin dariyar izgilanci ta saki ta ce.
"Ai babban kuskuren da ka tafka a rayuwarka shi ne gangancin sauraron kalaman da nake yi yanzu. Waɗanda suka ingiza ƙeyarka har ka tsoma mini baki, kana tsammanin furucinka zai yi tasiri a wurin mahaifinka?"
Ta wurga masa tambaya tana tsare shi da ido, shi ma ita yake kallo babu ƙiftawa. Yana jin kamar ya yi tsalle ya maƙure wuyanta, yana nan tsaye ya ji ta cigaba.
"Da ace kalamanka suna da tasiri, da a daren da ƙanwarka za ta yi mushe sun ratsa jikin mahaifinka."
Dum! Ya ji a tsakiyar kansa tamkar an buga masa guduma, ya runtse idonsa da sauri yana hasko fuskar Abida cikin mawuyacin hali. Tani ta nuna shi da yatsa cikin wata irin murya mai cike da zallar rashin imani ta ce.
"Ka jira mummunan saƙon da zai iso gare ka..."
Ba ta kai ga dire kalamanta ba, ta ji sallamar Abba ya shigo gidan. Haka ya sa ta saki murmushin ƙeta sannan ta rushe da kuka.
ƊANBATTA
Duk abin da yake faruwa Zuwaira tana daga ɗaki laɓe a jikin labule tana kallo. Farincii ne ya mamaye ta, don ita kanta ba ta san ya shigo ba sai hayaniyar Inna ce ta tashe ta. Sai da ta ga Malam Hasan ya shige banɗaki sannan ya fito tana yamutsa fuska, kan tabarmar da Inna ta shimfiɗa ta hau ta zauna. Cike da kissa da makirci ta ce.
"Inna lafiya kike ta faɗa? Ni ma bacci ne ya kwashe ni da yake ba ni da lafiya, na kira Yaya kuma ya ce mini ya yi nesa da mu ya gangara sabon titi."
Sakin baki Inna ta yi sannan ta ce, "Wato bayan cin amana har ƙarya Hasan ya koya kenan? Dole ya ce miki haka mana tun da yana liƙe a ɗakin baƙar munafukar nan." Zuwaira ta sake narke fuska ta ce, "Ai shi kenan, amma magani fa na ce ya kawo mini ɗazun."
"To idan kika mutu ai ba asara ya yi ba, tun da ba 'yar gaban goshinsa ce babu lafiya ba. Bari ya fito zai zo ya same ni..."
"A'a ki rabu da shi Inna, ni zan yi masa maganar. Idan kika masa zancan muna shiga ɗaki a kaina zai huce." Zuwaira ta tari numfashi Inna, Takaici ya sake rufe Inna ta ce.
"Oh ni Kulu na haɗu da ƙaddara, wallahi da na san kalar asirin da uban yarinyar nan ya yi wa Hasan da tuni na ba wa almajiran soro sadaka sun ba yara zikiri an karya shi."
Suna nan zaune Malam Hasan ya fito ya wuce ɗaki, a lokacin da ya shiga Rakiya tana duƙunƙune a cikin zanen gado tana kuka. Sosai ta ba shi tausayi, don har a ransa yana ji su suke cutar da ita a zamantakewar da suke yi. Sannan abin da Inna ta yi masa ba don mahaifiyarsa ba ce, da babu abin da zai hana shi ɗaukar mataki a kanta. Wanne irin abin ne yake damun Inna da za ta shigar masa ɗaki a lokacin da yake keɓewa da iyalinsa? Me ya sa duk cikin 'yan'uwansa babu wanda Inna take yi wa cin kashin da ake yi masa? Me ya sa ba zai samu farinciki ba? Waɗannan tambayoyin ya shiga jefa wa kansa. Shasshekar kukan Rakiya ne ta dawo da shi daga duniyar tunani, ya zauna a kusa da ita ya riƙo hannunta. Da sauri ta fisge ta sake cusa kanta a tsakanin cinyoyinta.
A yadda yake jin tausayin Rakiya, da ace zai iya rabuwa da ita da a take zai ba ta takardarta domin ta samu salamar rayuwa. 'Idan na sake ta ina za ta je? Da su wa za ta fara rayuwa? Shin na yi mata adalci idan na rabu da ita? Ko kuwa na riƙe amanar da mahaifinta ya damƙa mini?' Tambayoyin da ya dinga ƙissimawa a zuciyarsa kenan.
'Koda babu alaƙar aure a tsakaninku, kuma koda mahaifinta bai damƙa maka amanarta ba. Kai mai zame mata uwa da uba ne, domin mahaifinta ya yi maka gatan da iyaye suke yi wa 'ya'yansu.
"Ba zai yiwu ba."
Ya furta a fili cikin suɓutar baki ba tare da ya yi tsammanin zancan zai fito ba. Sake riƙo hannunta ya yi, tana niyyar ƙwacewa ya riƙe ta tsam a jikinsa. Ya kai bakinsa saitin kunnenta cikin tattausan lafazi ya ce.
"Ba zan hana ki kuka ba, ki yi kukan idan har shi zai sanyaya abin da yake cikin zuciyarki."
Kamar Rakiya tana jira, ta sake sakin sabon kukan da kana ji ka san daga ƙasan zuciyarta yake fitowa. Bubbuga bayanta ya shiga yi, har sai da ta ci kukanta mai isarta ya ce.
"Ki yi haƙuri Rakiya, komai ya yi tsanani maganinsa Allah. In Shaa Allahu da jarina ya ƙara ƙwari za mu koma cikin gari, na sani ba a kyauta miki. Ana zalintarki kuma ana, shiga haƙƙinki, amma In Shaa Allahu zan yi bakin ƙoƙarin gyara wasu abubuwan koda ba a daina yi miki duka ba."
Muryarta a dashe ta dube shi ta ce, "Ba na son ka yi abin da zai sa ka saɓa wa mahaifiyarka, ina son ka cigaba da yi mata biyayya. Kamar yadda ka faɗa ne watarana sai labari..."
"Wai ba za ka yi ka fito daga ɗakin ba ne Hasan? Ka saka mace a gaba idan ba ka fita nema ba me za a ci?"
Kalaman Inna suka katse maganarta, murya babu walwala Malam Hasan ya ce.
"Yanzu zan fito."
Daga haka ya shiga kintsa kansa sannan ya ɗauki kwandon turarensa ya fita. Bayan fitarsa sai da Rakiya ta sake shan sabon kukanta, ta ɗauki hijabi ta saka sannan ta fita banɗaki domin ta gyara jikinta. Tana fita kuwa Inna ta dasa zaginta Zuwaira ta shiga zuga ta, bayan ta fito har ta kusa shiga ɗaki Inna ta ce.
"Ki sako kaya ki fito ga surfen gerona nan kwano uku yana jiranki." Cikin biyayya Rakiya ta amsa sannan ta shiga ɗaki. Kamar yadda ta amsa tana gamawa ta fita ta karɓi geron, tana surfawa Inna tana wanke ta da baƙaƙen maganganu.
A wannan ranar Malam Hasan tun da ya shiga ɗakin Zuwaira ta sha jinin jikinta, amma sai ta nuna kamar ba ta fahimci yanayin da yake ciki ba. Don ko abincinta bai ci ba, dama kuma tun da ta tsiri rashin lafiyar ƙarya ta saka Inna ta sa shi kwana kullum a ɗakinta ya daina cin abincin kirki. Bai fi ya ci cokali ɗaya ya ce ya koshi, a wannan ranar da ta tambaye shi ko kula ta bai yi ba. Yana nan kwance ya ji ta ɗora hannu a jikinsa, cikin zafin zuciya ya fuske ta gefe. Da yake ya san halinta sarai, Zuwaira irin jarababbun matan nan ne da ba su da haƙuri.
"Wai me ya sa kake yi mini haka ne, ko don ka ga na damu da kai? Kusan kullum kafin ka ba ni haƙƙina sai ka wulaƙanta ni."
Zuwaira ta furta a narke cikin damuwa, tashi zaune Malam Hasan ya yi. Ya ji tsanarta ta sake mamaye shi. Da sauri ta ɗan ja baya, don ta yi tsammanin mari zai kai mata. Cikin tsana ya nuna ta ya ce.
"Ke wacce irin mai son kanta ce? Ashe kin san halin da kike shiga amma kika sa nake danne haƙƙin Rakiya? Shin kina lissafin yau kwana nawa rabon da na kwana a ɗakinta? Kullum da kalar ciwon da kike tashi da shi, saboda kin san Inna ta tsaya miki ko? To bari ki ji, tun da abin na ki haka ne ni ma daga yau babu wani abu da zai sake shiga tsakanina da ke."
Da sauri ta ɗago ta dube shi, ganin babu alamar wasa a fuskarsa ya ta miƙe ta ce.
"Ai kuwa dole Inna ta ji, don wallahi ba zan yarda ba."
Tana gama faɗa ta ɗaga labulen ɗakin, cikin ɓacin rai ya nuna ta da yatsa ya ce.
"Wallahi tallahi kin ji na rantse miki, idan har kika sake kika fita daga ɗakin nan sai na sauke igiyar aurena uku da suke kanki. Sakarai wacce ba ta san sirrinta ba, ballantana na mijinta. Wai ganin ina yi wa Inna biyayya gani kike ba zan iya rabuwa da ke ba? Bari ki ji,