san ita Zaliha sam ba ta damu da
soyayya ba." ya yi dan murmushi "Ai kuwa ta huta da wahalar duniya." Ya fada yana satar kallon Asma'u.
Itama ta yi masa wani irin kallo da gefen ido
"Masu yi ma ai wahalar ba kashesu ta yi ba." Ya yi shiru bai tamka mata ba, sannan ya ce
"Muma muna da biki Yola Karshen wannan watan, zan
fi so ace. dake bikin domin ni ba 7an halacci bikin ba
zamu yi tafiya da Daddy, kuma na tabbatar Mina za ta
zo wurin bikin, kin ga in kin je za ki samo min rahoto."
"Gaskiya nima zan so zuwa bikin nan in dai bai zo
lokaci daya da bikin mutuniyar
tawa ba, dan nima ina
son ganin Mina amma dai ko mun hadu ba Jallai ne ta
gane magana ta ba, tun da ka ce ba ta jin Hausa sosai." "Duk da haka za ta fahimce ki, bare ma an ce inda
ta yi aure garin Hausawa ne." wannan lokacin ne suka Karaso gate din makarantar, Salim ya tsinkayo wani
(lecturer) dinsu ya danno hancin motarsa, ya yiwa Asma'u nuni "Ga fa mutumin na ki." Ta dan tsuke fuska "Ina ruwana da shi ka manta da
shi Kawai shirmensa yake. Ran nan ma ya bi ni har gida amma ina ganin abin da na gaya maza zai yi tasiri." "Me ki ka gaya masa?" Salim ya yi tambayar yana dubanta.
hakun kai zan aura." Ya Kura mata ido sannan ya dan girgiza kai yana dariya "Ki daina yi min Karya dan ni na fara gajiya da
iin wannan Karyar da kikewa samarinki, shi ya sa mutane suke dauka soyayya ce tsakaninmu. Ya kamata ki daina Karya, tunda kin san ba hakan bane."
"A'aha da so kake su dauka Kiyayya muke?"
"Haba Malama ba haka nake nufi ba." daidai
lokacin da suka isa harabar wurin da aka tanada' musamman dan ajiye motoci ta yi fakin. Tana shirin fita daga motar wayarta ta yi Kara, ta dan ja tsaki saboda
Ta dan kanne ido tana dariya "Cewa na yi ya yi
ganin ta kusan makara, yatsine ta zuge jakatacirokan wayar, amma ganin mahaifiyarta ce sai ta fadada
fara'arta gami da kara kan wayar kunnenta, sannan ta dan rusuna tana gzyar da ita tamkar gabanta
take.
"Momy ina kwana nima ina nan tafe da mun
sami hutu. Salim zai kawo ni Kaduna....Mommy ina Abbana? Jina na nemeshi waya amma na ji rufe." Sai da suka gama surutai akan abinda ya shafesu
sannan ta mikKawa Salim kan wayar suka gaisa da Mommy daga nan ta rufe ta nufi aji hanzarce, saboda makarar da ta yi, dan tun kan ta Karasa ciki ta tsinkayi malamin nasu tuni ya fara lecture tana shiga ta nemi wurin zama ta bi sahun dalibai, 'yan uwanta ta nutsu ta
fara sauraren bayanan lecture din. Gaba daya ta maida
66
hankali akan lecture da yake yi musu ko baa fada ba an
san karatun likitanci karatune mai wabala, wanda yake
Lakcar su ta yau dai ta debesu tsawon awanni biyu
sannan suka tashi suna fitow aba ta tsaya galsawa da dalibai ba kai tsaye ta nufi gindin motarsu, inda Salim
ke zaman jiranta, babu abin da ya dameshi ya
saka kida
ya nutsu sosai yana sauraren sauti, tun daga nesa ya
zubawa Asma'u ido yana yaba kyan
halittar da Allah ya
yi mata tana Karasowa ya bude mata Kofar motar sai da
ta fara cilla jakarta cikin motar sannan ta shiga
ta zauna.
"Wash! Na gaji wallahi." Ta fada wahalce gami da dan lumshe ido. Ya dan rage sautin kidan sai da ya
tada motar
sannan ya jeho mata tambaya gami da watsa mata
iadanu Surfe ki ka yi ko sussuka?" "Ba daya." Ta bashi amsa ba tare da ta dubeshi ba.
"Haba Malama mene ne na gajiya daukar lecture daya? kai kake ganin haka." Suna fita daga harabarjami'ar ya dauke kan motar
suka nufi titin da zai kai su asibiti, tafiyar da ba ta wuce minti goma ba ta sadasu da asibiti da yake nan ne asibitin da iyalan gidansu Salim suke zuwa basu sha wata wahala ba suka ga babban likita, bayan bincike da
'yan gwaje-gwaje Doctor Hashim ya rubutawa Asma'u magunguna da kuma shawarwari da wasu dokoki da ya
kafa mata daga bisani kuma ya dan nuna ra'ayinsa
kanta ganin zai dameta sai cewa ta yi. "Lah, Doctor ina fa da miji."
buKatar nutsuwa.
67
"Kai ban yarda ke matar aure ce ba." Ya dan dubi Salim "Ya abokina ina fa ciki,
ina fata za ka bani Kanwar taka." Asma'u ta ce "Doctor ka yi kuskure, ai wannan shi me Mal cidan nawa."
razane likitan ya kai dubansa ga Salim "Ka yi aure ne?" Ya yi dan murmushi "Kwarai ita ce amarya ta." Murmushi kawai likitan ya yi amma sam bai yarda
ba. saboda ya lura da lokacin da suka hada ido suna dariya. Suka fito jere likitan ya taka musu har gindin mota, da kansa ya budewa Asma'u motar shige, ta
zauna, sannan suka yi sallama ya koma bakin aikinsa. Salim ya bar Asma'u cikin mota ya koma gefe ya kunna
Sigarinsa ya gama zuka, bayan ya sha tabarsa ta isheshi sannan ya dawo cikin motar. Asma'u ta kama yi masa dariya, ya kalleta kawai ba tare da ya yi magana ba, sai da ya laluba wurin da
yake ajiye alawar tom-tom dinsa, ya ji ba ko daya ashe Asma'u ta shanye, girgiza kai kawai ya yi gami da dan murmushi sannan ya tayar da mota suka tafi bai nufi
igida da ita ba sai ya dauki hanyar gidansu. Ta dan watsa masa fararen idanunta "A'aha haka muta yi da kai?" Ya ce "Wai da ina nufin mu je gidanmu ki dan
huta in kin gaida su Mommy da yamma sai na maidaki gida, kin ga yau Daddy ma yana gida sai ku gaisa." Da yake bata son yi masa musu sai ta yarda, suna
isa yaran gidansu Salim suka tarbeta da murna da komai duk suka rirriKe mata hannu, ta isa falon Mommy ta
68
gaida ita ta dan zauna suka fara hira, ta dubeta cikin murmushi.
"Asma'u kin yi wuyar gani yanzu sam ba kya son
zuwa gidanmu, ba kamar da da kike yawan zuwa ba?" "Lah Mommy wallahi karatu ne ya Boye ni, amma
tun da zamu sami hutu sai kun gaji da ganina." "In ce dai wannan yaron ya gaya miki maganar bikin diyar yayata da za mu yi Yola?" "E Salim ya fada min kuma in sha Allahu zan je." daidai wannan lokaci ya shigo, ya dan dubi Asma'u "Ki taso mu je ki gaida Daddy." Ta mike cikin nutsuwa ta bi bayansa har falon mahaifinsa ta dan rusuna ta gayar dashi. Daddy ya dan
fadada faza'arsa "A'a diyata Asma'u yau ke ce gidan
namu? Ya ya karatu? Ya mutanen gida, duk lafiya?
In ce dai ana maida hankali karatu?" Salim ya ce "Daddy ka yi mata fada tana yawan sa
tunani ranta, gashi nan yanzu damuwa ta haifar mata da ciwo." Ya dan dubeta cikin murmushi "Wai haka ne diyata?" Ta sunkuyar da kai tana amsawa kunya ce "Dadd
ba haka bane kawia fa Kirjina ne yake ciwo, kuma mun
je asibiti." Ya dan fadada murmushinsa "To shi kenan Allah
ya sawwake dinga maida hankali akan karatu, kun dai sani karatunku na buKatar nutsuwa." Daga nan suka yi sallama da Daddy suka fito daga
sashensa. Salim ya cewa Asma'u "Ki jirani zan je na yi wanka." 69
Ta tabe baki "Kai ka &walisa da yawa, ni zan
shiga ciki in ka gama ka iskoni (study room) akwai abin da nake son dubawa computer." Tana zuwa study room ta janyo kujera ta kai gaban
computer ta shiga danne -danne ta kwashi tsawon lokaci ciki, sannan Salim ya shigo ya duba rubutun da take
cikin computer, ya yi 'yar dariya
"Malama likitan nan fa da gaske yake yi ya bugo min waya yanzu ya jaddada min bafatarsa. Ta dan kada ido gami da harararshi "To inda gaske
yake sai me?" "Kai gaskiya yarinyar nan masha Allahu akwai ki da dankaren farin jini, gashi nan maza sai kawo caffa
suke.*
"Haba da Allah sai ka ce ni ce kai ga ka nan 'yan
gusta sai rububinka suke ka tsaya kana yanga sai faman
yankwanasu kake. Cikin murmushi ya ce "Haba yarinya kin dau bashi na data yi miki uzuri daga yanzu duk wanda ya ce yana
sonki zan bashi dama." Ta dan marerece "Haba Yaya Salim mijin Mina, ai hama haka da kai. wannan lokacin Shema'u Kanwar Salim ta shigo
"Anti Asma'y ki zo ki ci abinci in ji Mommy." Salim ya ce "Je ki ki kawo mata nan." Asma'u ta ce "Anya zan ci abincin nan, lemo
kawai za ki kawo min." Salim ya ce "Dame-dame aka yi kicin?" Shema'u ta ce "An tuKa tuwon shinkafa da miyar agushi, kuma akwai shinkafa da salad sannan akwai
70
ragowar farfesu," "Shi kenan abin da aka girka
kicin din?"
"Ina jin shi kenan amma bari dai na tambayo masu
aikin kicin din ko akwai wani abin bayan wannan. Har ta kai bakin Kofar "Ji nan Shema'u." Salim ya
ce da ita "Je ki sa hado mata salad ki taho kuma da
lemo saboda Antin taki ba ta fiye
son cin abinci mai
nauyiba." Asma'u yini guda ta yi gidansu
Salim, sannan da marece ya maida ta gida.
"Yan makarantun jami'a
sun sami hutun Karshen
zangon karatu wanda shi ne Salim ya
kammala
karatunsa fannin likitanci,
ita kuma Asma'u tana shirin
shiga (level three) Kwamishina baban Salim ya
shiryawa dan nashi Kasaitacciyar liyafa
saboda murnar
taya babban dan shi nasarar kammala karatu lafiya, ya
gayyaci manyan mutane da dama. Bayan an gama komai, ya shirya musv tafiya Kasar
Jamus (Germany). Bayan tafiyar su ne Asma'u ta raka su Momi biki can garin Yola burin Asma'u bai wuce ta ga Mina ido da ido ba, ai kuwa suna isa da kwana daya Mina ta zo lokacin da Mommy ta nunawa Asma'u ita ba Karamin firgita ta yi da ganin yarinyar ba, muguwar kyakkyawa ce, sai ka ce aljana, tsananin kyanta ya zarce duk yanda kake zato ita kam duk yanda Salim ya
siffanta mata ita yanzu da ta ganta sai ta ga ta wuce
nan, abin sha'awa Mina tana da fara'a da son jama'a
gashi kuma ta waye, saboda zaman birni da take yi. Hausarta tana fita sosai, amma kuma Asma'u ta ji
labanin wai Mina har yanzu ba ta daina yiwa mijinta
tawaye ba, kullum ita kenan guje-guje gidajen 'yan uwa. Asma'u ba ta fi mako daya da dawowa daga bikin
Yola ba ta yi shirin tafiya Kano wurin bikin Zaliha
Kawarta, tare da gudunmawarta mai tsoka. Lokacin da ta
isa Kano ba gidansu amaryar
ta sauka ba, dan
girmamawa sai ta sauka gidan dan uwan mahaifinta dayake shi kadai ne dan uwansu wanda ya rage garin
Kano, wato mahaifin Yusuf mijin da aka aura mata da
farko, lokacin da aka sanar da Yusuf zuwan Asma'u da
saurinsa ya ZO yi mata sannu da zuwa ganinta ke da wuya duk sai ya rude, saboda irin canje-canjen da ya
gani tare da ita. Asma'un da aka yi musu aure tana Karamar yarinya har yana raina shekarunta, amma yau
gata ta ama munzalin mace sosai, ta goge ta dada wayewa, boko ya ratsata sosai, gashi
idonta ya bude
saboda cudanya da masu ilimi, rayuwar
ta gaba daya ta.
sauya ta samu ci gaba kowanne fanni ta dada kyau
sosai, jikinta ya murje, ta yi haske fatarjikinta sai sheki
take yi. Kuma abin mamaki ta bashi hadin kai suka
gaisa faran-faran cikin mutunci, babu wani alamar raini ko tsiwa. Sai ma girmamashi da ta dinga yi matsayinsa na dan uwanta, sam ta nuna kamar auren dole bai taba
shiga tsakaninsu ba, shi kuma ganin haka sai ya fara bullo mata da maganar kome, wai ta yi hakuri su maida
aurensu tunda yanzu su ba yara bane, sun mallaki hankalinsu. Dariya kawai ta yi ta shareshi, duk yanda ya
so ya shisshige mata ta ki yarda. Da ya matsa mata da
zancen soyayya sai ta ce ya yi haKuri dan yanzu shi
72
Yayanta ne, zai fi kyau su rike matsayinsu na 'yan
uwantaka amma ya fidda batun komai. Ya kada ya raya ta ki bashi goyan baya, ita abin ma dariya ya bata, sai dai kuma ta yi mamakin
shiryuwar da Yusuf ya yi ya
zama nutsattsen mutum, ba
kamar shekarun baya da yake harkar sharholiya ba da alama yanzu duk ya tuba ya daina shaye-shaye
amma
koda ta
tambayeshi labarin abokinsa Bashir, sai ya
shaida mata bashi da lafiya yana nan yana jinya, duk ya
fita daga kamanninsa sakamakon kamuwa da cutar Kanjamau (AIDS) da ya yi. Allah ya kyauta abinda ta ce kenan tun da Asma'u
ta zo biki Yusuf na tare da ita, duk wata zirga-zirgar zuwa gidan biki shi ne ya ke dawainiyar kaita da daukota, fir ta Ki yarda direba ya kaita bayan haka ta
ziyarci mutane da dama har gidan Sunusi abokin Yusuf sai da ta je ya yi aure har da 'ya'yanshi biyu sannan ta je
gidan Ahmed abokin Aminu, babu yanda bai yi da ita
akan ta daure su gaisa da abokinsa waya amma fir ta Ki yarda ta kawo uzirin wei tana da miji, kuma ta Ki yarda
ta kar6i lambar Aminun. Bayan nan ma har. gidan Babar Aminu ta je ta gaisheta, ta kai mata kaya sha tara ta arziki, amma ta Ki
fadin garin da take da zama da mahaifiyar Aminu ta matsa mata da tambaya sai cewa ta yi Sudan take aure. Asma'u dai tana cikin kacaniyar bikin Zaliha, Salim ya yi mata waya ya shaida mata sun dawo shima
yana nan zai biyota Kanon don haka ana sauran kwana daya gama bikin Zaliha, Salim ya iso sai da ya kama daki Tropicana Hotel ya biya sannan ya yiwa Asma'u
waya suka yo suka daukeshi. Zaliha ta yi farin ciki da Salim, ya halacci gurin bikinta koda yake party daya
kawai ya samu da yake duk shagulgulan da za yi an yi an gama. Tua da Yusuf ya Kyalla
ido ya ga Salim kishi ya masa tsakaninta da Salim dan haka Yusuf sai ya yi zaton
saurayinta ne, kishinsa Kin boyuwa ya yi, hankalinsa bai kwanta ba sai loakcin da Salim ya gabatar da kansa ga Yusuf, ya ce shi abokin karatun Asma'u ne kuma shi ne amininta na hannun dama, tun daga nan Yusuf ya saki
jiki da Salim duk shi ya kaishi yawace-yawace cikin
gari, ya nuna masa gurare da dama cikin Kano. hirarrakin da suka yi da Salim sai da Yusuf ya bashi labarin irin zaman da suka yi da Asma'u lokacin. da ya aureta, da yanda har suka rabu ba tare da ta bashi
kamashi duk iya bincikar da yayiwa Asma'u ta Ki gaya
hadm kai ba. Sam Salim bai yi mamaki ba, domin ya Za
rina wai an saci 7anin mahaukaciya dan yanda Asma'u
take son Aminu baya jin akwai wani da namiji da za ta
amincewa har ta bashi hadin kai su yi zaman aure. Sai da aka gaba bikin Zaliha da kwana biyu sannan
suka tafi, amma abin mamaki tunda Asma'u ta je Kano
ta tafi sai Yusuf ya kasa samun sukuni domin ji ya yi duk duniya babu wata 'ya mace da yake so illa Asma'u matarsa ta da. Bayan sun koma Sokoto Salim ya
ce "Ya ya ki ka
Asma'u ta ce "Gaskiya na ji dadin ganin Mina, domin yarinyar
tana da kyau, tana da hankali, kuma tana
ga Mina?"
If
da nutsuwa."
yaba da halayenta?" "Kwarai ni ka ta burgeni." "To ko akwai-Wani alamu da kika fahimta wanda
za ki yi min albis gashi?"" Ta gyada kai tana murmushi cike da
zolaya, sannan ta ce "Na fahimci Mina tana cikin Koshin lafiya
kuma tana jin dadin zaman aurenta domin mijinta yana masifar sonta. albishir kuma Mina dai tana da Karamin
ciki..."
"What?!" Ya fada da sauri gami da Kura mata ido. Ta dan dake gami da tsagaita dariya
"To me ye
aibi? Ai Raruwa ce, ko kuma kana nufin kun yi yarjejeniya ba za ta haihu ba?" "No, ba mu yi haka da ita ba." "To tun da ka san ba ku yi haka da ita ba sai ka yi
Ya yi dan murthushin jin dadi "Kenan kema kin S14addu'a Allah ya sauketa lafiya." Ya sake dubanta razane "Please tell me the true
am not
joking" (Don Allah ki gaya min gaskiya, ba wasa
Ganin rudewar da ya yi ya sa ta dan kanne ido
gami da sakin 'yar dariya, "Kai yarinyar nan kin
ke ba)
shammace ni, amma zan rama bashi kika dauka kin
gane?"
Yusuf ya rinfa zaryatsakanin Kano da Sokoto shi ala dole so yake Asma'u ta koma amma duk lya Dacinsa
kallo ma bai isheta ba, da ya matsawa Goggo cewa ta yi "Ba ruwana ka je can ku Karata ka manta lokacin da ake
ik
bin ka ana ro€onka kana iya shege?" \.
Ya ce "Haba Goggo ki yi hakuri ki manta da wancan maganar ba wai hankalina na yi ta ba na furta
furucin ne cikin 6acin rai amma yanzu na fahimci Asmna'u ce kadai matar da nake so dan haka tunda muka
rabu kasa yin aure, ita kadai zuciyata ke Kauna." Goggo ta ce "To ni mene ne nawa ciki? Ai ko
yaa Asma'u ta amince da kai sai in yi rakiya....." Sai da hutu ya zo Karshe sannan Salim ya kai Asma'u Kaduna wurin Mamanta bayan ya dawo ya fara
sturye-shiryen tafiya bautar Kasa, inda zai yi service
jibsr Delta. Koda hutu ya Kare Asma'u ta koma makaranta ba
karamin kewar Salim ta yi ba, kwata-kwata ji
ta yi karatun ma ya gundireta, saboda babu Salim, da yake
bata frye shiga cikin Kawaye ba, dama shi ne abokin
brrarta, koda yaushe suna tare haduwarjini kenan, Allah
ne ya hadasu matsayin aminan juna.
Shekarun Aminu hudu da barin Nijeriya.zuwa
karatu Kasar Rasha ko sau daya bai taba zuwa ganin
gida ba, tun farkon tafiyar shi ya yi alkawarin ya yiwa Niyaeriya adabo dan tunaninsa zai iya zama na dindindin Kasar Turai, to amma ga mamakinsa tun da
ya dira aKasar sai ya kasa samun sukuni,saboda kawai
fimanin yarinya daya, dan gaskiya rayuwarsa ta gigita
saboda soyayyar yarinya daya da ta dinga wahalar dashi ya yi kuka da idonsa ya shiga damuwa iri-iri, ya yi jinya
sosai, duk dalilin Kaunar Asma'u bayan ya kammala
karatunsa laftya tare da dimbin nasarori sai da ya dan
dakata ya fara aiki da wani kamfani na zitga-zirgar
jiragen sama. Kwatsam lokaci daya
sai ya
tsinci kansa
da rikicewar dukkan al'amura domin abokinsa Ahmed
ya warware masa abubuwan da ya boye masa tsawon
shekaru hudu game da masoyiyarsa Asma'u dan shi Aminu duk tunaninsa Asma'u na gidan aure, Kila ma ta hayayyafa dan duk san da ya tamkbayi Ahmed labarin Asma'u cewa ya ke yi tana can gidan mijinta. Amma abin mamaki lokaci daya
sai Ahmed ya
bashi labarin abubuwan da suka faru da Asma'u bayan
tafiyarsa duk dai da Ahmed din ya
tabbatar masa amma
yanzu bai san garin da take ba, gaba daya hankalinsa
ya ji ya tashi komai ya kwance masa, ji ya yi tamkar ya
yi tsuntsuwa ya taho Najeriya, yanzu kam zaman Turai ya gundireshi in band ya ganshi Kasar shi ta haihuwa babu abin da yake buKata. Gaba daya hankalinshi ya tafi ga
auren Asma'u, shi dai ya ganshi yau gashi ga Asma'u, matsayin ma'aurata shi ne cikar burin rayuwarshi. Nan da nan ya
ajiye aikinshi dan ba zai
jure zama wata Kasa ba, alhali Asma'u na Can Najeriya ba ta da aure, in ya yi haka ma
al ya ci amanar Kaunar da ta nuna masa, dan haka &aggauce ya yi shirin baro Kasar Rasha, ya dire Najeriya Kasarshi. ta gado da zummar neman masoyiyarsa Asma'u duk inda take fadin Najeriya. Kwananshi biyu Kano suka zauna shi da abokinsa Ahmed suka tsara yadda zasu fara neman Asma'u da yake lokacin da ta zo gidan Ahmed ta Ki
fadin takamaiman garin da tek da zama. Aminu ya sanar da mahaifiyarshi zasu je neman
fi
Asma'u. Mamaki ya kama babarshi. "Shin Abba har yanzu yarinyar nan tana ranka?" Ya dan shafa kai yana murmushi "To Mama ya ya
zan yi tun da Allah ya jarrabi zuciyata da Kaunar yarinyar, kawai dai ki yi min addu'a Allah ya yi min
katarin ganinta.
Itama ta yi murmushi "To Abba Allah ya bada
sa'a. Koda yake ina ganin Kila fa yarinyar nan duk inda
take tana da aure, domin lokacin da ta zo gaisheni cewa
ta yi mijinta ne ya kawota. oF
"Kai haba Karya take an gaya min tuni aurenta ya mutu."To ku yanzu ina kuke zaton za ku sameta?" "E to zamu fara zuwa nemanta garin Sokoto idan
bamu sameta ba sai mu nufi Kaduna, inda Mamanta take
"To Allah ya taimakeku ku sameta." "Amin Mama, addu'ar da nake so ki yi mana
kenan. Gobe ne zamu tafi Sokoton." Washe gari sammako suka yi shi da Ahmed suka nufi birnin na Shehu, suna shiga cikin garin Sokoto sai
suka dauki hanyar da za ta kaisu Kauyen (Shodi) da
yake babu wani taKamaiman wurin da zasu nemi Asma'u garin Sokoto, dan haka stka yanke shawarar
zuwa wannan Kauye dan suna zaton akwai wasu
Kakanin Asma'v wannan gari, amma koda suka shiga
sai suka yi ta faman bilinbituwa sam gidan da suke nema
ya Bace musu, suka yi ta yawo cikin Kauyen suna
tambaye-tambaye
sai da suka gaji da yawo duk sun
karade ko ina sannan Allah ya taimakesu suka sami
aure
has wani dattijo ya ce ya san gidan da suke nema. Nan take
ya
rakasu gidan Dudu Kanwar Kakar Asma'u, bayan sun
sami gidan sai suka yi rashin sa'a she ita dai Dudu Allah
ya yi mata rasuwa, tun tuni kuma duk iya kokarinsu
nasu sami koda daya daga cikin ya'yan marigayiyar duk abin ya ci tura, domin dukkansu sun tafi cirani sai da damina suke dawowa gida. Amma koda su Aminu suka matsa da bincike sai aka yi musu kwatancen wani tsoho wani dan Kauye
gaba
kadan aka tabbatar musu in dai suka je gurinsa
zai
gano yarinyar da suke nema, domin shima dan uwan Dudu ne. ~Su Aminu suka yi mura, suka nufi garin da
tsohon yake har da dan rakiyarsu. Bayan sun isa garin
suka je-gidan mutumin suka ggaisa
sannan suka
zayyanewa wannan
tsoho abin da yake tafe dasu, suka
kwatantama masa Asma'u suke nema. nutse suka gabatar da kansu sai da tsohon ya
gama fahimtarsu tsaf kuma ya riga ya gano ko su su waye nan take ya raya ransa wato masifar da ta tafi tun
shekarun baya ita ce take so ta sake dawowa, haka
kawai muna zaune cikin kwanciyar hankali wannan
kafirin yaro ya Zo ya tayar mana da hankali,w ato kenan
so suke duk su karkashemu da wannan shegiyar soyayya
yanda suka kashe uban yarinyar nan. To wallahr ba zai yiwu ba, yanda suka zo haka zasu koma amma ni ba zan
gaya musu inda jikar Yalwa take ba. Su dai su Aminu da suka yi shiru suna jiran amsar da tsoho zai basu amma abin mamaki duk Bata lokacin
da suka yi wajen kwatanta masa Asma'u tashi daya sai
te
ya birkice musu wai shi sam bai gano yarinyar da suke nufi ba, babu mai sunanta cikin danginsu daga Rarshe da suka matsa masa sai ya ce "Ayyo na tuno yarinyar da ku ke nufi, ko ba Ma'u 'yar gidan Marigayi Alhaji Masa''ud na Kano ba?" Da sauri Ahmed ya ce "Yauwa ita muke nufi Baba." Yayin da Aminu muma ta kamashi Allah-Allah
yake ya ji abin da tsohon zai fada, shi dai kawai burinsa ya ji garin da Asma'un take amma budar bakin tsohon nan Sal Cewa ya yi. "Allahu Akbar kaico duniya, ai in dai wannan
yarinyar kuke nufi ta rasu tun tuni wjaen haihuwar
jikar Yalwa ta riga ta mutu da dadewa. Nan da nan Aminu ya dafe kai da hannu biyu cikin
Karaji ya ce "Shi kenan ta faru ta Kare, rayuwata ta
ruguje.Ya tsuguna gaban tsohon yana rasgar kuka sal ka ce Karamin yaro. Tsohon ya ce "Haba samari hakuri za ku yi ai duk mai rai mamaci ne, mu ai tuni muka yi kukanmu muka "FE hakura. Ahmed duk ya riga ya Kule da haushin tsohon nan, ya dafa Aminu "Ka yi hakuri abokina tashi mu tafi kar ka damu duk inda Asma'y take zamu nemota. Aminu ya dan harareshi "Haba Ahmed ya kake
abu kamar wani yaro, kana ji
fa bawan Allahn nan ya ce' mana Asma'u ta mutu, in haka ne ina zamu nemota?" Ahmed ya janyo hannunsa "Ni dai kawai ka tashi mw tafi." Ya juya ga tsohon nan "To Baba dattijo mun
gode Allah ya ji Kan Asma'u, mun tafi, sai wata rana." Tun da suka shiga motar Aminu babu abi da yake
80
sai Zub da hawayc duk yanda Ahmed ya yi kokari ya ga
ya shawo kan Aminu ya yarda Asma'u ba ta mutu ba abin ya ci tura, saboda shi kawai ya
da abin da
tsohon nan ya fada, tunda an ce dan uwansu ne. Ahmed ya ce "Haba mutumina ka daina kka haka nan ni fa na san Asma'u tana nan da ranta bata mutu ba. Garin da take ne kurum ban sani ba, amma tana yawan
kirana waya muna paisawa." Aminu ya ce "Mutuwa fa aka ce ai ka san baya ba
ta da kadan komai yana iya faruwa ba mamaki Asma'u
ta rigamu gidan gaskiya, kuma gashi ma har an ce
gurin haihuwa ta mutu." Ahmed ya tausasa murya cikin KoKarin sa na
rarrashin abokinsa 'Amma in ba ka manta ba shi wannan
tsoho ya nuna mana wai ta mutu da dadewa har ma an y1
shekaru alhali