bar wayarta da kuma jakar kudinta, kai da itama ta kile dan walahi tana ji tana gani zata ce itama saurayinta ya kawo mata iphone din, ai ba ita kadai take da damar yin saurayin ba dan wulakanci!
Tuki ne ya yi mai gaggawa, hankalinsa a kan Mahaifiyarsa dake ambaton sunnan yarinyar da yanzu yanzu ne ta ji sunnan ama kamar wata wace ta saka mata shi da kanta
Sunna karasowa ya fito dan sake daukan yarinyar ya kaita ciki kafin ma a kawo kujerar dora marar lafiya ko gadon, sai ya ga Mah ta cire mata hijabi ta cire mata ribom sai faman son tahsinta take yi tana jimke da hannunta da dayan hannun kuwa tana dan shafa gefen fuskarta a hankali tana fadin ta farka mana
Kansa ya dauke a kanta ya ja gefe har aka zo aka kamawa Mah aka dora yarinyar aka fita da ita aka yi ciki da ita
Wurin zama Mah ta samu ta zauna tana dafe kanta da hannayenta bibiyu
A nutse ya karaso ya duka gabanta ya saka nasa hannayen yana cire nata yana kallonta ya ce" kamar kin saka damuwar wace bakima sani ba da yawa a ranki Mama, Please ki sanyaya ba komai fa, zata farka ne yanzu sai mu maidata gidansu mu je gida ki huta"
Bayan zuba masa ido da ta yi sai ta samu kanta da cewa" Mu maidata? YUSUF mu maidata fa ka ce?"
Idannuwa ya zuba mata yana son gane me kennan
A sanyaye sosai Mah ta ce" matar da muka bari a gidan cen sam bata cencenci rikon yaro ba, ko nata ba zata iya ba tarbiyya ba bale wannan da take kishi da ita, Yusuf cewa fa take yi wai idan bai dawo ya kawo mata kudinta ba itace ajalinsa kuma itace ajalin yarinyar nan , Ni ban san tsakaninsu ba, ban san me ta yi mata da zafi har ta tsaneta haka ba, ban kuma san ko inada hurumin shiga wannan rigimar ba, abu daya na sani shine daga nan yarinyar nan zata je ne gidana kuma a gobe gobe zan shigar da karra dan kar matar ta rigayeni, Yusuf ai dadinta muna da sarakai masu adalci da hukuma tsayayiya, kuma a yannayin yarinyar cen ta yi shekarun da ta isa zabarwa kanta inda take son zama, Ni dai ina ji a raina kamar taimako ne zan yi, kuma kamar idan na yin Allah zai dubeni da idon rahama nima ya yafe min kura kuraina "
Idannuwansa ya lumshe a hankali , bai saki hannunta ba a sanyaye ya dora gefen fuskarsa a tafukan hannayenta yana jin dumin hannunta yana aukawa a tunani
Lokuta da dama idan ya zauna da mahaifiyarsa sai ya ji zuciyarsa tana girgiza , hankalinsa na tashi da nasa shima laifin
Mahaifiyarsa bata taba daina neman afuwar Ubangiji ba kan abu daya tal da ta aikata wanda bayan aikatashin ta rike abinta har ta haifi abinta kuma ta so ta raini abinta Allah ya amshi abinsa
Ama a haka a kulun idan ta budi baki zaka ji tana tsoron haduwarta da mai sama kan wannan abu, to ina ga shi jama'a?
Ya mayar da mace abin shigarsa dan samun nutsuwa
Yana yi yana hawayen bakin ciki da tashin hankali
Bai rasa abin ajiye hudu idan yana ra'ayi ba, ama ya kasa tsayawa waje daya bale ya ajiye din, ya yi nan ya yi cen da ransa
Kwarai shi din ya kasance mai aikata aiki mai munin gaske, wanda idan ta ji wa'azi wani lokacin yakan kasa rintsawa
A hankali ya sauke ajiyar zuciya ya dago idannuwansa yana kallon mahaifiyarsa
A ransa yake aiyana 'ni kuwa zan tsaya maki har sai kin kai ga cikar burinki dan samun nutsuwar zuciyarki Mah '
"Sir, ta farka, ama ta ki tsayawa mu mata allurar barci duba da bugun zuciyarta ya yi yawa ko ma samu ya dan daidaita mu yi mata gwaje gwajen da ya dace dan mu dorata kan traitment"
Mikewa ya yi , Mama ta bi bayansa suka nufi dakin
Budewa ya yi ama ya ki shiga sai Mama ce ta shiga sannan ya bi bayanta ya tsaya yana kallon Mama
Gadon Mama ta karasa da sauri ta zauna ta dago kan Rauda ta janyota ta rungumeta a jikinta da dan karfin da ya saka Rauda dawowa duniyar mutane har ta dan saurara daga rizgar kukan da take yi hancinta na shakar sansanyan turaran ruwan mama kunnayenta suka shiga jiyo mata kalamai a sanyaye kamar haka" me yasa zaki rikita kanki har haka ne? Kina son kamuwa da wata cutar ne? Waye ya fada maki ya rasu ne? Da ace sun kashe shi da wahala su kawo wayar nan, ina mai kyautata zaton yana raye sun yi haka ne dan su rikita mutane ya zamo da zarar sun yanke kudin da suke so a basu dan a amshe shi, kuma kin ga Honorable ya amshi wayar yanzu haka da ya ajiye mu ya tafi wajen commisiona na police dan ya masa maganar, Haba Rauda sai kace ba musulma ba? Koda rasuwar ya yi sai ki kasa yin tawakali ne? Allah baya barin wani dan wani ya ji dadi RAUDA, idan har Allah ya so zai dauke maki kowa ne ya barki ke kadai, saboda wannan sai ki kashe kanki kema? Hana Rauda ki yi hakuri kin ji?"
Tamkar wace Mama ta tuno mata da wani gibi, ko kuwa kalmar hakurin daga bakin uwa ne bata saba ji ba ta ji a yau? Ko rungumeta a rarasheta ne bata saba samu ba? Abin dai ya shige mata zuciya har ya saka ta dago idannuwanta ta zubawa fuskar Mama mai dauke da ni'ima da haske mai daraja kallo kafin a hankali ta fashe da kuka tana saka hannayenta a hankali ta rike na Mama ta kai kanta a hankali ta ɗora saman kirjin Maman tana sake riƙe maman tana kuka irin na cikin makogwaron nan mai zafi da ratsa zuciya muryarta na sarkewa ta ce" Dama iyayena da kanaina sun rasu, shine kawai gareni sai Abdul, shine kawai gareni , su ne kawai dalilin da yasa nake tafe da karfina, idan na rasa su Ni na san Bani da karfin dazan iya jurewa, innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, dan Allah Hajia ku taimakeni a samo min Abanmu, ko nawa suka yanka min zan biya su bani shi, ki nawa suke so zan basu Ni dai su bani shi"
Mama, tausayi, tashin hankali, mamaki duka sun hadu sun rufe mata zuciya, haba koda ta ji ta san wannan kam da wahala idan ta haɗa jinninda yarinyar irin yadda ta ringa jaza mata alkaba'i, haka kuma jin iyayen yarinyar duka sun rasu sai ya sake daga mata hankali, uwa uba kuma jin wai ko nawa ake so zata bada, aikin me take ne?
Shigowar docter da baban file a hannunta ya saka Mama bada hankalinta wajen docter, har zuwa lokacin kan Rauda a kirjinta tana dan dadabata a hankali, Yusuf kuwa yana tsaye ne yana sauraronsu
" wannan ba itace aka kawo jiya ba? " Docter ta tambaya
Mama ta tabbatar mata itace
Docter ya fita , jim kadan ya dawo tana sake bude takardar hannunta ta ce" To ai a jiya duka abinda ya dace na gwaji mun mata, sai dai idan kunna da bukatar a sake wasu to, dan jiya sir yace a mata komai dan lafiyarta"
Murya a shake sosai Rauda ta ce" Lafiyana kalau, gida nake so na je, Lafiyana kalau "
Mama ta dago daga kallonta ta kalli YUSUF dake tsaye bai ce masu komai ba, a tausashe ta ce" Eh yanzunma summa ne ta yi shi yasa muka dawo saboda wani abu da ya daga mata hankali, idan ba damuwa sai mu juya gida ?"
Likitar ta karaso ta fitar da abubuwan aune aunenta ta shiga auna RAUDA, wace lebenta ya yi Jajajir, hakama saman hancinta da wajen idannuwanta du sun kumbure sosai hakan ya sa da kyar take daga idannuwan , leben kuwa sai haske yake yi na abin kukan da ta ci
Da kula sosai likitar ta ce" kunna iya tafiya Madame, ama a sayi wannan maganin ta ringa shan daya idan zata kwonta na tsayin sati guda saboda bugawar zuciyar nan, kuma ta yi kokari ta cire damuwar dan yawan yanke jiki a fadin nan daga nan ake haduwa da mugun hawan jinni mai naci, Allah ya bada lafiya"
Daga nan ta yi gaba da kayan aikinta a hannunta
Mama ta dubi Rauda bayan ta dago kanta a tausashe ta ce" Kin ji abinda likita tace ko? Ki daina kukan hakanan, mu je gida ki huta za'a ganshi kin ji?"
Shi kam mamakin mama ya fi komai damunsa, su mata me yasa suke da saurin sabo? Haka kawai daga gannin yarinyar sai rungumeta take yi tana faman neman dagawa mutane hankali a kanta? Kai shi kam bai san me zai ce ba kam, ama Mama akoy rigima Allah kuwa, meye hadinta da wannan ne? Shi ba abinda ya bashi haushi sai jadadawa da take yi wai ko a je ko nawa ne zata biya? Shin aikin uban me yarinyar take yi da bata jin kunyar kowama ya ji? Kai subahanallah ashe rashin jin maganar mace haka yake da kayan haushi? Shi haushima take bashi kamar ya buge mata baki yake ji idan tace din nan ko nawa ne zata biya, aikin banza aikin wofi yarinya tunda ya santa cikin kaya kaya take? Shirme kawai!
Da kyar mama ta iya ganar da ita dalilinta na ta bita, sai da ta nuna mata ta ji furucin maman Farisa sannan ta yi gumm ta kasa cewa komai, sai alfarmar da ta nema kan zata je wajen kanninta gobe? Mamah kuwa ta nuna mata zata kaita ne da kanta dan haka ta samu yin shiru ta koma kukan zuci da addu'a ga wayarta a kirjinta wajen da za'a kaita kawai take jiran gani dan ta samu ta yi kira, ba zata iya rintsawa ba in har bata san inda uncle dinta yake ba, kuma ta san idan ta fadawa mutumen ta zai taso ko me yake yi ya zo ya nema mata shi, kuma ko nawa zasu yanka masa zai biya ne dan ta samu nutsuwa da kwonciyar hankali......
A lokacin da YUSUF ke tuki har ya dauki hanyar gidan Mama kira ya shigo wayarsa na Mahaifinsa
Dan rage tafiyar ya yi dan a tunaninsa ko ya zo asibitin ne bai gansu ba? Dan ya sanar masa sun taho gidan Mama
Yana dauka ya saurara yana jin Muryar mahaifinsa yana fadin" Yusuf, ka ganni na zo fada , ina tare da commitiona aka yi kirana cewar sarki ba lafiya, Hajia ce ta yi kiran nawa wai ba dama, shine na zo ka ganmu nan ance ba za'a kai shi asibiti ba, ama ana tsaye kansa ga likitoci nan, Ni ina ta lafiyarsa ne Hajia tace wai na yi kiranka in me kake yi, in a ina kake ka je maboyarka ku zauna har Allah ya tashe shi"
Tsai ya yi yana sauraron maganar ,.
Maboya?
Shi walahi ya manta cewar akoy maboya da aka masa wace abin ya bashi dariya a lokacin da akace a dukkan lokacin da wani abu ya taso ya je cen
Waje ne wanda zuwansama hatsari ne a yanzu dan dare ya shigo
Gashi sun ce idan suka ambata masa ya saki hanya kar ya bi cikin gari
Ikon Allah me kennan?
A tausashe ya ce" Abu, me ya hadani da wata maboya dan Allah? Gamu fa zamu je gidan Mah ne "
Mahaifinsa dake tsaye shi da Hajia wace ke zaune tana kallonsa ta masa alamun ya tirsasa shi, dan haka ya ce"
Sako zuwa gare ku masoya kuma mabiya wannan littafi nawa mai taken AZAL
*In sha Allah da zarar na gama free page zamu koma posting a telegram ne, dan haka wa'inda suka saye shi su yi kokarin sauke telegram, telegram, zamuna yin posting dinmu a cen ne, na gode*
🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶
*AZAL!*
🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶
*SAJIDA NIJAR*
*PAID BOOK*
_Bismillahir rahamanir-rahim._
*15*
*wannan littafin na kudi ne 300 Naira account details 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi Gt Bank ka turo shaidar biyan ta wannan layin +22793811618, yan nigar kuwa zaku turo katin airtel ko sahelcom ta 500 francs ta wannan layin sai a saka ku 93811618 sai kun zo my lovely reader 😍😍😍😍😍*
*TALLAH, TALLAH, TALKAH*
_*TOH TO TO!*_
🗣_*YEKUWA JAMA’AR NIGER 🇳🇪 DA KEWAYE KU MARMATSO KUJI👂🏼NESA TAZO KUSA SAI HAMDALLAH🙌🏻*_
_Muna matukar farin cikin sanar daku cewa wanan shaharraren kamfanin nan na kasar waje *{CHAINA🇨🇳}* wanda yayi suna duniya tasan dashi fagen hada ingatattu kuma tsaftattun maganguna wato kamfanin *GHT* 💃🏻 yanzu haka yazo kwacokam a *Niger* sunce muma kar abarmu abaya, ina kuke Mataye?_
Wanda suka ansa sunansu cikakkun Mata isassu yan kwalisa shalelen oga? Daku nake
_Amarya_Uwar gida_
_Zawarawa_kai harma da yan Mata kuma kar a baku labari👂🏼_
_Muna siyarda ingatattu kuma shararru magungunan mu kamar haka👇🏼_
INA MASU FAMA DA MATSALOLI KAMAR HAKA👇🏼
🦠*INFECTION*, *🦠 RASHIN HAIHUWA*, *🦠RAGE TUMBI DA KIBA*,🦠 *CIWON HAKORI*, *🦠MAGANIN GYARAN NONO DA MAZAUNAI*
*🦠 CUTAR CANCER*,*🦠 RASHIN KUZARI GA MAZA KO KARANCIN RUWAN MANIYI*,*🦠ULCER*,*🦠DIABÈTE*,🦠 *FIBROID*,*🦠ASMATIC**🦠SKINCARE TRAITEMENT DE LA PEAU*
_KURAGEN FUSKA KO DASU AKA HAIFEKI DA IZIN UBANGIJI MATSALARKI TAZO KARSHE🥳 TAREDA *{GHT}*_
_SIRRIN GYARAN JIKI SAIDA KAMFANIN *{GHT}* KARKU SAKE KUBARI ABAKU LABARI, HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKE SANIN NA KWARAI👍🏻_
💁🏽♀️MUNA SIYAR DA TURARE KOWANE IRI NA JIKI DANA DAKI AMARYA DA UWAR GIDA *KAMSHI SHINE MARTABAR Y’A MACE🙌🏻*
💁🏽♀️MUNA GYARAN AMARE DA UWAR GIDA DILKA DA SAURANSU, ABUN SAI WANDA YAGANI…
_MASU NEMAN KARIN BAYANI SAIKU TUNTUBI *HAJIYA FATIMA* WAKILIYAR *{GHT}* A WANAN LAMBAR KAMAR HAKA👇🏼_
*ADRESSE 94536935 94.53.69.35*
*Muna nan a unguwar Lazaret NIAMEY/NIGER*
KARKU BARI A BAKU LABARI🥳
Litattafan marubuciyar
Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Bak'a ce
Bani da zabi
Daga tafia daukar soja
Neman na kaina
Kutkale
Mage
Bani da zabi
Idan ka raina inda kake
Umughuluk itifal
Duk nisan jifa
Wata kokowar
Ni zan ladabi
Dakika biyar
Da ciwo a zuciyata
Aure yakin mata
Alkalamin Kadarata
Dutse
Daga tafiya daukar soja
Makauniyace
ND now *AZAL*
Mahaifinsa dake tsaye shi da Hajia ta masa alamun ya tirsasa shi, dan haka da yannayin nada umarni ya ce" Ka san idan akace ka je da dalili, ka je din sai na bukaci ka fito ka fahimta?"
Dan jim ya yi kafin ya bashi amsa da to
Hanyar ya dauka cikin tuki mai gagawa da kula, yana tafe yana kiran wa'inda ke ba wajen tsaro ya sanar masu shine zai shigo layin har ya karasa layin gidan da aka yi a cikin jeji wanda zaka dauka wani waje ne daban aka ware a cikin gari aka dankara wannan fasali da tsari na tsaro a wajen
Yana shigowa wasu maza hudu suka saka motar a tsakiya yana tukin a hankali su kuwa sunna biye da motar da gudu da kaffafuwansu har wajen get din gidan wanda aka yi shi tamkar garun gidan, dan in dai ba Sannin wajen ka yi ba ba zaka taba gane ga get din nan ba, domin a saje yake sosai da gidan kuma tsayin kofar a hade take da wani abu da aka saka da cen kasa ya hade da kasa, babu yar hudar da zata shaida maka ga wajen da zaka bude ka shiga sai masu tsaronta da suka san cikinta da wajenta
Da gagawa wasun dake kofar suka bude kofar wadinnan na ja gabar tafiyar, sunna shiga wasu hudun ne suka sake raba motar biyu gaba biyu baya ya zamo hudu gaba hudu baya , shi dai yana tuki a hankali ne, mahaifiyarsa kuwa kana kallonta hankalinta a tashe yake, dan ta san me hakan yake nufi ganninsu a wannan waje a irin wannan lokacin
Sunna tsayawa sojan daya ya bude masa motar ya sauko , lokaci daya suka saka gwuiwarsu daya a kasa dayar a dan dage suka dora hannayensu na hagu da dayar suka cire hulunan da suka yiwa fuskarsu katanga da gane su waye su sannan suka shiga masa sannu da zuwa hadi da gabatar da kansu daya bayan daya da kiransa da sunna *SARKI*
abinda ya tsaya gani daya ne, gabatar da kan nasu da zasu yi, sunna gamawa ya bude bayan ya mikawa mahaifiyarsa hannu yana kallonta a nutse ya ce" Mah sauko"
Mah ta sake zuba masa ido, a saman lebenta ta ce" Me yake faruwa ne?"
Da idannuwansa ya mata alamun bai sani ba, dan haka a dole ta kamo Rauda wace take ta kale kalen kowa da mamakin toh, ikon Allah, wannan mutumen kuwa wai wanene shi?
Rauda na fitowa sai ta ji tsoro ya fara kamata, saboda tana fitowa sai ta ga mutanen dake duduken nan kamar ba mutane ba? Gashi jikinsu gaba daya shigar baki ne, ga bindigogi a jikin nasu kamar wa'inda zasu je yaki? Da sauri ta dauke kanta daga bin su da kallo tana bin mama da ta rike hannunta sunna biye da ɗan maman har suka karasa kofar inda zasu shiga ya saka cod dinsa suka shiga Mama ta kaita cikin wani daki wanda Rauda ta kasa zama saman katifar dakin dan har ga Allah tsoro take ji da tunanin arzikin mutanen
Da sauri Mama ta dawo inda yake ta zauna tana fadin" YUSUF me yake faruwa a cen fadar?"
YUSUF dake son ya dauki hankalinta ya fice ya ce" Mama ban sani ba, an ce dai mu zo nan, Ni yanzu yinwa nake ji mama sosai fa"
Mama ta sauke ajiyar zuciya ta mike tana fadin" Bari in je kicin din naku, akoy komai ko?"
Kai ya gyada mata yana sakar mata murmushi yana kallonta har ta shige ciki
Wayarsa ya ciro ya ajiye nan da duk wani abinda ke cikin aljihunsa sannan ya juya da sauri ya fice
Yana fitowa ya samu baban mai ba gidan tsaro ya mika masa hannu
Baya ya ja kadan yana kallonsa da girmamawa ya ce" Sarki ina zaka je?"
Fuska ya hade sosai ya ce" Ka aike Ni ne? Bani ky!"
A dole ya bashi ky din daya daga cikin baburansu sannan ya bi bayan shi da gudu, dan walahi ba zai barshi ya je cikin gari shi daya ba, zai bi shi ne har inda zai je ko su mutu tare ko su yi rai tare, shi ya yarda ana neman ran bawan Allahn nan lokaci zuwa lokaci dan tare aka harbe su da bulet , ama shi sai kasada, sam baya ji idan aka ce ya yi biyayya kuwa kamar an ce baude!
Hanya suka dauka ta cikin jeji sunna keketawa da gudun gaske, bayan ya bar masu wasiyyar kar su saki su yarda a shiga a tarda mahaifiyarsa, in sha Allah zai dawo , koda shi bai dawo ba mahaifinsa zai dawo ko kuma RISLAN, domin ukun nan su kadai suke da damar shiga gidan nan bayan shi
Mah na fitowa dauke da plate wanda ta soya masa kwai kafin girkinta ya kare tana fadin" Yusuf wai yanzu baka da hakurin yinwa k.........?
Idannuwanta suka sauka saman kujerar da ya tashi da wayarsa da sauran abubuwasa nan zube
Da karfi ta ce" YUSUF! YUSUF!" Lokaci daya tana zubar da abinda ke hannunta ta saki plate din na kwalba ya fadi kasa,
Kararsa da ihun muryarta ya saka Rauda fitowa da gudu tana zarro ido ta zuba mata ido tana kallonta
A lokacin Mah ta je tana ta duduba shi bata ganshi ba, hakan ya bata tabbacin lalle Yusuf ya fita sai kawai ta nemi fita a hayacinta tana ta faman son saka cod dinsa a wayarsa ama ta kasa
Da sauri Rauda ta karaso tana kallonta, jiki ba karfi da kuma tashin hankalin menene wannan din kuma ta ce" Hajia, lafiya?"
Mah ta kalli Rauda ta sauri dan har ta fara manta tare suke tsabar tashin hankali
Da sauri ta mika mata wayar tana fadin" Dan Allah, cire min cod ki saka min numbobin nan da zan fada maki ki min kiransu, dan Allah yata"
Wayar ta amsa tana kallon yannayin Mah,
A hankali ya kamma hannun na Mah ta zaunar da ita saman kujera tana kallonta a sanyaye ta ce" Mama, ki yi hakuri, ki fada min numbar na bude maki, ama ki yi hakuri ko menene kin ji?"
Mah dai so take kawai ta bude mata ta kira mata numbar, dan haka ta shiga fada mata cod dinsa har ta cire mata sannan ta shiga fada mata numbar Honorable
Tana fara rubuta numbar sunnan ya nuna kansa da sunnan *UBANA* , ta karanta sunnan ta karra sannan ta danna kiran ta mikawa Mama ta zauna tana kallonta, dan sai ta ji anya kuwa zata iya tafiya ta barta a wannan yannayin?
Wayar ba fara ringin ya daga, muryarsa wata iri a sanyaye sosai ya ce" Yusuf kun karasa wajen?"
Muryarta na rawa ta ce" Aban YUSUF, Yusuf din baya nan ai, ban san ina ya je ba, gashi ya kawo mu gidan nan na jeji kuma ya fita, ya bar min wayarsa harda su katinsa na shedar dan kasa, ina ya je? Me yake faruwa a fadar dan girman Allah? Ka fada min walahi zuciyata bugawa zata yi"
Rauda ta kawar da kanta dan bata so ta maida hankali kan maganar Maman, ama kuma haka kawai ta samu kanta da maimaita FADA a cikin zuciyarta
"ya Salam, ya Salam, ya Salam" Honorable ya fada yana mikewa ya fice daga cikin mutane ya nufi cen bangaren matansa dan ba kowa a irin wannan lokacin , kowa yana ɓangaren Hajia tare da marar lafiyar
Yana zuwa ya sake rage muryarsa sosai ya ce" Sai fa da na fada masa ,kar ya saki ya fito, Allah kadai ya san gawar fari cikin mu da sarki da shi Yusuf, ama Hajia na gannin jikin sarki ta rikice ta ce in sanar da Yusuf in yana ina ya je gidan nan ya zauna har sai Allah ya yi yadda ya yi ji sarki ya mike ko akasinsa sai ta bada umarnin Yusuf ya fito zai fito, shine ya fito?"
A rikice Mah ta ce" Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, me yake damun Sarkin? Me yasa baka fada min ba Ni ai da ka san na rike Yusuf duk abinsa ba zai fita ba ko? Wayo na shiga uku yanzu yaya zan yi?"
Shi dinma hankalin nasa a tashen yake ya ce" kin ga ki kwontar da hankalin ki, in sha Allah ba komai, wai sarki bashi da lafiya tun shekaran jiya yake cikin gudawa da amai matan suka rufe suka ki fada min, sai da Hajia ta matsa kan ko ina yake a kira mata shi ne amaryarsa ta zo a sace ta fada mata walahi bashi da lafiya bakina san wanda yake kansa ba, Hajia baba ta hanna a sanarwa kowa sai magani ake didika masa a boye wai ko zai tashi ya zamto sai sun wanke shi sun cenza masa tufafi dan baya jin fitar gudawar daga jikinsa, shine fa Hajia ta yi kirana ta sanar min, da na zo ban nemi kowa ba na je bangaren nasa na bude na shiga da karfi dan kiri kiri Hajia baba ta nunan yana hutawa baya so a dame shi, da na shiga na tarda shi yana cikin wani hali, dan ko gudawar yanzu ba abinda ke fita sai ruwa tsululu, karshema malamai ne kansa ana ta addu'a, na yi na yi a je asibiti kowa ya wani nuna min wai me za'a kai"
Wani irin Gwauron numfashi Mah ta sauke kirjinta na dokawa
Ta rasa me zata ce,
Ya Salam wannan lamari na tsoratata yana kuma daga mata hankali
A me aka ɗauki sarauta ne?
Me suka dauki duniya ne?
A sanyaye hawaye na bale mata ta ce" Ai ba Yusuf ne abin a boye ba, kai ka san in dai abinda Hajia take nufi ne kaine abin a boye ba YUSUF dina ba, su cire Yusuf a duk wani abinda suke tunani, su fida d'ana daga rikicinsu, Aban Yusuf ka san ba zai taba yarda ya zauna kai kana cen din ba ko? Dan Allah ka fito Ku zo"
"Kar ki daga hankalinki, bari yanzu in fita in gani zan ganshi na dawo da shi, Ni sam bana son fitinar nan ta gidanmu, gashi dare ya yi ama kowa sai wani irin abu
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 11 Chapter of 12