fir ya kasa ganewa ya rabeta ko dan tsufanta?"
Kai HAJIA AMEERAh ta cire daga duban gefe ta maido kansa tana dubansa, a Nutse ta saki dan murmushi a tausashenta ta ce" Ka yi hakuri ka ringa duba furucinka a kansa, saboda mahaifi kake a wajensa , ko me yake aikatawa fatan shiriya shine ya dace ya fito daga harshenka, ka yi hakuri ka fi karfin zuciyarka domin baka sani ba abin ya fara fin karfin son ka ga ya dawo hanya ya koma abin birgewa wa zuciyarka yin daidaya da zuciyarsa"
A hankali ta ajiye maganar kafin ta dago ta saka idannuwanta tar cikin nasa ta ce" Me kake jira daga wajensa ? Ina ganin shi yana sara da duban bakin Gatari , da ace irin halayan da ake masa zai yi da an shiga uku, shin wani d'a za'a zagi mamansa yana tsaye bai dauki mataki ba? Fin karfin sa na yi shi yasa shi kuwa ya kaurace dan kar ya aikata aikin da za'a Dube shi da shi, me yasa bakwa masa adalci ne? Me yasa bakwa dora abinda yake iya ji a zuciyarsa kamar yadda kuke iya ji? , me yasa kuke gagawar yanke masa hukunci idan ya wulga koda bai yi tari ba?" Wannan karronma a hankalin ta ajiye maganarta sai dai dubanta na iya fasara daf take da tsinkewa
A Nutse ta dora da fadi " Yau da gobe nake guje maku, dan ba zan ware kowa ba, idan Ni na zamo takalmin takawarku shi a abu mafi daraja yake kallona, in ma me na aikatawa ahalinku wanda kai ake iya yafe maka Ni ake kallona a matsayin *AZAL* din da ta afko ahalinku da cikin da na ba kaina wace ba za'a iya hakuri a Dube Ni ba, shi yana dubana a mutun mafi daraja a duniyarsa, shin yaya kuke so yaron da kuke kiran uwarsa masifa shi ya zamo maku mai biyayya a gabansa? To ai koda ace shine shegen da muka yi Ni da kai ba zai taba fa......."
"AMEERAH!" Hon Bello Muctar Gali ya fada yana dagowa daga jinginar da ya yi hankalinsa na neman tashi zuciyarsa na bugawa, domin tunda suke da ita du irin abinda yake faruwa bata taɓa dubansa ta nuna bacin ranta ba, kai komai bata fadi bale har ta tado abinda shi ya birne yake kuma zaune da matarsa da zuciya daya da so da kauna Duda ita ya san ba lallai in ta iya manta baban abin da ya shiga tsakaninsu a zamanin samartaka ba, sai dai ga dukkan alamu abin na ranta har yau kunnayensa ke jiyo masa maganar dake daf da dauke nutsuwarsa
A hankali ta zuba masa ido kafin ta tari numfashinsa tana dan Bude lumsasun idannuwan da yaronta ya yi gado a wajenta tana kallonsa ido cikin ido a kausashe sosai ta ce " BELLO, idan maye ya manta uwar d'a ba zai yiwu ta manta ba, yayana da aka ciro a dakin tiyata aka nunan sun mutu ba zasu taba guguwa a zuciyata ba, ba zan taba mantawa ba!"
Sai kuma ta sasauta muryarta tana jingunuwa da jikin kujerar nan a hankali ta ce" Ina daukan zamana a ahali irin naku matsayin jarabawata ina kuma rokon Allah ya zamo silar yafewar laifin da na aikata, sai dai ka sani ina guje masu yau da gobe a kan D'ANA!, i love my love fiye da raina, ku kun san biyayar aure da shi ke rikeni ba dan bani da yadda zan yi ba!, Ni ce AMEERAH (GIMBIYA) ta DAMAGARAM, banbancin mai nisa ne!"
Daga nan ta yi shiru tana jin kanta na neman yi mata ciwo
Hon Bello kuwa sai ya rasa shin mamakinta yake ciki ko firgicin halin da take ciki? Lalle a yau an kaita bango, ashe itama tana iya nuna bacin rai a kan abinda ake yiwa Yusuf har haka?
Ajiyar zuciya ya sauke a sanyaye ya mike dan ya dauko mata maganinta da ya zamo kulun sai ta sha take kwonciya
Sai da ya je ya dauko ya kawo ama fir tace ba zata sha ba, wannan shi ya karra daga masa hankali domin idan ta yi fashin sha da wahala in bata KWONTA rashin lafiya ba, a hankali ya so sake fahimtar da ita ba zai taba iya kin gudan jinninsu ba, ama akace ka guji fushin wanda baya gagawar fushi, cikin wani bacin ran kafin ta mike ta nufi dakinta ta ce" Ka shiga tsakanina da A'isha!, ta fita a hanyata, abinda na hadiye na shekarun baya ba zan iya hadiyewa yanzu ba, kanwa take a wajenka , koda yaya ce ina iya dakatar da ita bale kanwa, ta guji budar bakina dan idan ta kirayi YUSUF mazinaci mashayi bata san me zan kirayi nata ya'yan ba wa'inda ba hasashe nake yi ba ko Kazafi, tana yawan kirana *AZAL!* idan aka bibiyi tarihi kalmar AZAL ta yiwa ahalinta kadan , a kan YUSUF babu abinda ba zan yi ba ciki harda rabuwa da UBANSA!"
Daga nan ta yi dakinta ta rufo ta saka ky ta murza da karfi sannan ta karasa wajen gadonta tana rike kanta ta KWONTA jiri na neman summar da ita daga kwoncenma
A falo kuwa da kyar Mahaifin Yusuf ya iya samun waje ya zauna yana dafe kansa da hannayensa bibiyu
A hankali ya bude idannuwansa sakamakon tuno ranar da yayansa ya fito da wani zannin gado a hannunsa rungume da jajirai biyu farare sal masu kama da shi tak tak Duda jajirtakarsu kamar ya yi kaki ya tofar kamanin har sun bace ko dan Allah ya nuna masu cewar ba gardama abinda suke gudu nasu ne? Yan jarirai sun yi fari fat na alamun ba rai a tare da su ya nuna masa, bai ko bashi damar runguma ba ya fice da su yana fadin abinda aka tsara za'a sanarwa duniya cewar ba kumburin cikin haihuwa bane ta yi dawainiya da shi, kumburi ne na kari dake girma tamkar cikin haihuwa yana ji yana gani bai san inda aka birne masa yayansa ba, haka uwarsu ko ganninsu bata yi ba aka yi rufa rufa ga zafin haihuwa na cs ga radadin rashin ƴaƴanta aka dawo gida aka daura masu aure a ranar tare da wasu matan biyu, wa'inda HAJIA ta zaba masa yana ji yana gani bashi da ikon furta ko kalma daya kuma aka nuna aurenta shine karshen daurawa kai fin karfi dai aka nuna ba zata tare a gidanta ba a kalla ta kusan shekarewa a tare da HAJIA , galazawa babu irin wace bata gani da Hajiar da kanwarsa A'isha, yayansa kuwa dama basa ko ga maciji da ita, shi dai bai nuna mata tsana ba ama kuma bai nuna mata kauna ba, a wajen su HAJIA kuwa nan ta ringa tsintar sababin sunnaye masu girgiza zuciya, gashi a lokacin ba damar ta je wajen Tata mahaifiyar saboda ta yi fushi da ita sosai, sai a rasuwar mahaifinta suka amsheta suka yafe mata har suka janyota jikinsu, ama Duda haka babu ruwansu da damuwar dake damunta na dakin mijin da a ganninsu ba gidan aurenta bane, gida ne mai hatsarin gaske , gida ne da jita jitar da ake yadawa a kansa ya sa da yawa ke masa wata irin fasara, su tasu sarautar mai hatsarin da baki ba zai iya misaltashi bane, wani abin ne a bine a ahalinsu ya sa haka ko Allah ne ya kadarto masu haka a rayuwarsu? Allah shine masani, ama yannayin matarsa na yau ya girgiza shi fiye da tunanin bawa
Menene bata gani ba? Bata taba nuna masa ba
Idan yana fada ma Yusuf takan kauda kai ta yi murmushi ne ta ce" Sai addu'a Aban Yusuf"
Ama a yau ta fadi abinda yake gannin shi dai bata yi masa adalci ba
Shin yaya take tunanin zata haifo masa d'a tsatsonsa ya tsana? Yau ko ba nasa bane in dai daga jikinta ya fito ba zai taba tsanarsa ba, bale nasa ya Allah yaya zai iya tankwasa zuciyar wace bata cika fushi ba?.......
🤔🤔🤔🤔🤔🤔🤔
Asalamu alaikum jama'a....mun zo maku da nagartacen ingantaccen maganin Ulcer, magani ne na Hausa jikake wanda Dubai suka gwada suka ji dadinsa, nagartatun tsatatatun itaciyoyin da suka bamu sasake masu anfani ne ake anfani da su, a nan jamhuriyar Nijar a garin Damagaran a farashi mai rahusa dubu biyu yan naija , yan nijer kuwa 1500francs mai bukata ga numbar +227 96897192 , HAJIA RAHAMA
🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶
*AZAL!*
🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶🫶
*SAJIDA NIJAR*
*PAID BOOK*
_Bismillahir rahamanir-rahim._
*7*
*wannan littafin na kudi ne 300 Naira account details 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi Gt Bank ka turo shaidar biyan ta wannan layin +22793811618, yan nigar kuwa zaku turo katin airtel ko sahelcom ta 500 francs ta wannan layin sai a saka ku 93811618 sai kun zo my lovely reader 😍😍😍😍😍*
*TALLAH, TALLAH, TALKAH*
_*TOH TO TO!*_
🗣_*YEKUWA JAMA’AR NIGER 🇳🇪 DA KEWAYE KU MARMATSO KUJI👂🏼NESA TAZO KUSA SAI HAMDALLAH🙌🏻*_
_Muna matukar farin cikin sanar daku cewa wanan shaharraren kamfanin nan na kasar waje *{CHAINA🇨🇳}* wanda yayi suna duniya tasan dashi fagen hada ingatattu kuma tsaftattun maganguna wato kamfanin *GHT* 💃🏻 yanzu haka yazo kwacokam a *Niger* sunce muma kar abarmu abaya, ina kuke Mataye?_
Wanda suka ansa sunansu cikakkun Mata isassu yan kwalisa shalelen oga? Daku nake
_Amarya_Uwar gida_
_Zawarawa_kai harma da yan Mata kuma kar a baku labari👂🏼_
_Muna siyarda ingatattu kuma shararru magungunan mu kamar haka👇🏼_
INA MASU FAMA DA MATSALOLI KAMAR HAKA👇🏼
🦠*INFECTION*, *🦠 RASHIN HAIHUWA*, *🦠RAGE TUMBI DA KIBA*,🦠 *CIWON HAKORI*, *🦠MAGANIN GYARAN NONO DA MAZAUNAI*
*🦠 CUTAR CANCER*,*🦠 RASHIN KUZARI GA MAZA KO KARANCIN RUWAN MANIYI*,*🦠ULCER*,*🦠DIABÈTE*,🦠 *FIBROID*,*🦠ASMATIC**🦠SKINCARE TRAITEMENT DE LA PEAU*
_KURAGEN FUSKA KO DASU AKA HAIFEKI DA IZIN UBANGIJI MATSALARKI TAZO KARSHE🥳 TAREDA *{GHT}*_
_SIRRIN GYARAN JIKI SAIDA KAMFANIN *{GHT}* KARKU SAKE KUBARI ABAKU LABARI, HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKE SANIN NA KWARAI👍🏻_
💁🏽♀️MUNA SIYAR DA TURARE KOWANE IRI NA JIKI DANA DAKI AMARYA DA UWAR GIDA *KAMSHI SHINE MARTABAR Y’A MACE🙌🏻*
💁🏽♀️MUNA GYARAN AMARE DA UWAR GIDA DILKA DA SAURANSU, ABUN SAI WANDA YAGANI…
_MASU NEMAN KARIN BAYANI SAIKU TUNTUBI *HAJIYA FATIMA* WAKILIYAR *{GHT}* A WANAN LAMBAR KAMAR HAKA👇🏼_
*ADRESSE 94536935 94.53.69.35*
*Muna nan a unguwar Lazaret NIAMEY/NIGER*
KARKU BARI A BAKU LABARI🥳
Litattafan marubuciyar
Duk karyar kada
Yar mahaukaciya
Bak'a ce
Bani da zabi
Daga tafia daukar soja
Neman na kaina
Kutkale
Mage
Bani da zabi
Idan ka raina inda kake
Umughuluk itifal
Duk nisan jifa
Wata kokowar
Ni zan ladabi
Dakika biyar
Da ciwo a zuciyata
Aure yakin mata
Alkalamin Kadarata
Dutse
Daga tafiya daukar soja
Makauniyace
ND now *AZAL*
A gidan su RAUDA
Tun karfe shida na safe hayaniya ta kaure a tsakar gidan, wace ta hannata mikewa bale ta je ta samu ta dauro alwallah ta gabatar da sallar asubahi, rikici ne wanda yake tashi sama sama, fada ne irin na matar mashayi da mashayi, fadan da farkonsa aka sani ba'a san karshensa ba, fadan da du tsiya da zarar ya nuna zai rabu da ita take komawa ta yi mikis kamar ba ita ba, du gorin da take yi, du masifar da take yi cewar an hadata da balaki an aurota ba'a ciyar da ita, ba'a shayar da ita, an kawo mata rikon ya'ya an zuba mata irin tsiya gayar tsiya ba zata iya ba fatanta Allah ya rabata da masifa da BALAKI, domin auren Umar masifa ne da BALAKI ba komi na, ba karuwa sai raguwa , babu farin ciki sai bakin cikin rayuwa, na kulun hauhawa yake yi ba raguwa ba, da zarar ya nuna wai su saki hannun junna mana sai ta shige daki ya labe ba zaka kuma jinta ba sai ya fita ta fito ta wulakanci su RAUDA da dan uwanta wanda tsoron maman nasu ya saka ko muryarta ya ji sai jikinsa ya kama rawa ya shiga neman wajen buya
Ido Rauda ta rintse sakamakon wata ashariya da Mama ta kyatsa tana fadin" WALAHI baka isa ba, baka isa ba Umaru, kudin da nake binka ai sun fi haka, a kan me zaka ce zaka siyawa RAUDA kayan makaranta da kudina? Kar ta yi karatun mana, karatun nata da ba anfanar uban kowa zai yi ba, yawon banzan da take fita ne kake kira karatu ko me kake so ka daukeni? Yau da ace wannan yarinyar ba y'ar zumunka bace har na yi maka wata fasarar, ama Duda haka zan zuba ido sosai dan WALAHI karya ne ba'a yi y'ar da zan gogi arzunzumi ta goga ba.... ba z........."
Wani irin karan duka da ya shiga kunnayensu ya saka su duka biyun rintse idannuwa, hawayen da RAUDA ke rikewa suka samu damar fita da gurbin idannuwanta shar masu zafi da radadi, shi kuwa kannin nata ya rarafa ya boye a jikinta jikinsa na rawa kirjinsa na dokawa kamar zai summa
Ihun kukan Mama da y'arta ke tashi sama sama tana fadin " Allah ya isa tsakanina da kai, dan na fadi gaskiya zaka dakeni? Menene ba'a yi a duniya yanzu? Ni dai da RAUDA da iyayenta sai Allah ya mana hisabi, tunda suka fadi suka mutu ka zama mashayi ka kawo min ƙatuwar budurwa ka saka min ga wani dama da nake riko, ba zan yafe masu ba kuma kaima ba zan yafe maka ba dukana da ka yi, kuma na fada sai na saka ido a kanku dan ban yarda da mashayi ba, in kuka sha kun san abinda kuke yi ne? Ba zan kyaleka ka wulakantani ba Umaru!"
Shi din da kansa a tsayen da yake yana haki zuciyarsa tamkar zata balo kirjinsa ta fito hawayen ke wanke masa fuskarsa
Gannin idan ya zauna yana iya kasheta ya saka kansa a uku ya saka ya juya kansa na sarawa ya nufi hanyar fita
A lokacin da ya fito waje idannuwansa suka sauka a kan makocinsa da kuma limamin anguwarsu sunna tsaye daga nesa da gidan kadan ama ga dukkan alamun gidan hankalinsu yake
Yana yin ido hudu da su kunya da tsananin takaicin kansa suka rufe shi, a hankali ya dakata ya so juyawa sai dai makocinsa ya ki bashi wannan damar ya karaso inda yake tsaye ya mika masa hannu yana masa Salama
Hannun nasa ya kalla, sai ya ringa jin dari darin bashi nasa dan na makocin nasa a wanke tasss ga tabjinsa a hannunsa yana ja har wani kanshi yake, shi kuwa nasa harta miyar da ya ci jiya da dare bai wanke ba, sai kunya ta saka shi kallon nasa hannun ya nemi nokewa
Karasowar liman ya riko hannun nasa suka yi musabahar dole yana kallonsa shima a tausashe ya ce" Shin ka yi sallar asubahi?"
Wata kunyar ce ta sake kama shi, to rabonsa da yin Sallar asubah a kan lokaci ai har ya manta, dan haka ya sada kai yana cike da jin da kunya
Ajiyar zuciya liman din ya sauke a tausashe ya ce" Mu je ka gabatar da sallah, itace abinda take gaba da komai a yanzu, bismillah"
Kamar kanninsu ko dan gidansu suka saka shi gaba, ba da niyar tozarci ba, a'a da niyar taimakonsa, dan kuwa kasancewarsa mutum dake rayuwa cikin halin maye bai Hanna masa girmama duk wani mutumen Anguwar ba, datijawan Anguwar na binsa da Adu'ar shiriya, da kuma fatan Allah ya shiryi matarsa, dan babu wanda bai san wacece ita ba, dabi'unta a bayyane suke ba a boye ba, irin yadda take yiwa Rauda kuwa da kanninta ya zamo kowa na yi mata wani kallo, gashi dai kiri kiri tana son mayar da yarinyar kamar wata mai zaman kanta, a koda yaushe cikin zance da masu motoci a kofar gida, a koda yaushe tana karbar baki a kofar gida
Makocinsa na hannun dama ne da liman din suka zauna sai da ya gabatar da sallar asubahi har karfe bakwai na safiya ta gota sannan suka zauna tare da shi, cikin nutsuwa da kula suka ringa yi masa nasiha da nuna masa irin illar wannan rayuwar, abinda ya riga da ya sani, ya kasa zaunawa ya yiwa kansa fada ne saboda bashi da mai tunatar da shi
A tausashe Liman ya ce" 300Babu yadda rayuwa bata zuwarwa bawa, kuma komai girman laifinka idan ka tuba Allah mai karbar tuban bawansa ne, babu abu mafi hatsari irin maye, maye bashi da anfani Malan Umar, mai yin maye bashi da daraja kuma bai san abinda yake yi ba , kana da ya'ya yan mata, ga namiji masu bukatar taimakonka, dan Allah ka ceci kanka ka daina wannan halaya, ka rufawa kanka asiri kar ka samu matsala a wajen aikinka, domin rayuwa yau kana gannin idan mutun bashi da aikin yi damuwa ce, gashi kai din nan uba ne kuma Magidanci ne malam Umar"
Makocinsa Elhaji ashiru, mutun ne mai abin hannunsa daidai gwargwado kuma mai kyauta da taimako, ya jima yana da burin gannin sun samu kusanci da makocin nasa dake gaishe shi idan ya ganshi ko a ina ne Allah bai yi ba sai yau, ya Dube shi da kula sosai ya ce" Kowani bawa da irin tasa jarabawar makan Umar, kuma kowa lalube yake yi , babu abin tsoratarwa da wannan duniyar sai irin yadda babu wanda ya san ranar mutuwarsa, idanma babu mutuwa malam Umar Akoy tsufa wanda ke yiwa mutuwa fadan garaje gareta ta bar bawa da shi ta gani, malam Umar duniyar nan mutun ya yiwa kansa abin kirkima yaya ya kareta bale yana wasa da damar da Allah ya bashi? Bama kamar sallah da kiyaye hakokin ubangiji, ga nauyi a wuyanka a rataye, kaine uba kuma uwar ya'yan nan, ka yi kokari ka fi karfin zuciyarka ka fuskanci rayuwarka ka daidaita abinda ya dace ka daidaita, idan kana bukatar taimako ko na menene ka same ni in sha Allah Ni zan kawo dukkan talafin da ya dace, kana da halaya masu kyau, domin kaf Anguwar nan babu wanda zai ce ga abokin gabarka ko wani abin ya haɗaka da wani saboda dukiya ko ya'ya, hakan kuwa baban ALKHAIRI ne shi yasa yanzu na zo shiga gidana daga masallaci na ringa jin hayaniyar nan na kasa hakura na tabo liman muka yi jiranka, ba dan mun saka maka ido a shige da ficen gidanka bane, a'a, damuwa muka yi da dan uwanmu musulmi muka kasa hakura sai mun sauke nauyin hakin makotaka "
Sosai uncle din Rauda ya karra jin zuciyarsa ta yi sanyi, hakan ya sa shima ya gyara zamansa yana sauraron nasiharsu da kuma tunatarwa a kan gobe kiyama da kiyamarsa, ya shiga halin tunanin idan mai kasancewa ta same shi a irin wannan halin? Me zai cewa ubangijinsa? Tsoro ya kama shi ainun hakan ya sa ya zauna tare da su sunna ta zamtawa
A cikin gida bai san ya fita ya balowa RAUDA gagarumin rikici bane
A lokacin da ya fita Mama ta gama kukanta ta mike ta nufi dakin su RAUDA ta bankada kasarin dake kofar dakin ta shiga rai bace ta mika mata hannu ta ce" Bani!"
Gaban Rauda ya yanke ya fadi, dama ta san a rina wai an ari zanin mahaukaciya
A hankali bayan ta sake riƙe hannun kanninta dake ta rawa ta ce" Mama jiyan dare na yi gudun kar ya min shi yasa na dawo gida dan kar na yi dare ki kasa barci ba'a rufe gida ba"
Sai da maman ta dan kankance ido tana kallonta kafin ta shigo gaba dayanta ta ja yar kujerar tayani tsegumin da ita ta sanyota dakin ta zauna tana kallon Rauda ta ce" Ama ban taba gannin yar bakin ciki, marar mutunci irinki ba, ban taba gannin munafuka algunguma irinki ba, dan ubanki na taba zaman jiranki idan kika fita ne? Nan ko zance kike yi sai ki kai karfe goma sha biyu na dare a waje kina yi na taba zaman jiranki ne? Ko saurareni da kyau na rantse Miki karya kike yi, kin ga a yau idan har baki bani abin kirki ba sai na maku horon yinwa ta wata guda cir kuma sai kun bar min gidana , tunda kin san ba ubanku ke biyan haya ba, ke in banda raini da wulakanci da bakin ciki har nice zaki kawowa wannan maganar? Ai ba ubanki ya kawoni duniya ya tafi ya barni da wahala ba bale na zauna ina ciyar da gandamemiyar kamarki a banza ba, na fada maki kirarki ta ki nemo min kudi ce, ba ruwana da wa ta yaya! Matsalata kudi, idan kuwa tsiyar da iyayenki suka mutu cikinta zaki nuna min ba matsala, dama ke kin san har ki mutu ba zaki mallaki abin kanki ba, ama Ni WALAHI sai kin nemo min in ba haka ba......."
Da karfi ta janyo Abdul Hakim ta rike hannayensa ta kashe shi da marin da ya saka RAUDA saurin mikewa ta janye shi jikinta na rawa ta kafe fuskar Mama da kallo Maman kuwa ta mike tana kallonta itama ta ce" Dukana zaki yi yar mararsa mutunci? To WALAHI na fada maki idan baki nemo min kudi ba sai na halaka wannan kafin na halaka uban baki kema na halaka ki, ba kin fada min saboda su nake taka ko ba? Zan ci gaba da taka ki ko bayan na halaka su in dai kika yarda kika yi wasa da umarnina y'ar matsiyata mai shegun idannu kawai, ki miko min shi ya je ya kai surfen masara tunda ba ubana dake kabari zan taso ya kai ba!"
A hankali RAUDA ta sake tare hannunta tana kallonta a tausashe da yannayin tsarin halitarta ta ce" Ki ba almajiri ya kai zan biya, ki bi Ni bashi zan kawo maki"
Dan tsura mata ido ta yi kafin ta juya ta fita tana sababi da aibata RAUDA, da yawan lokuta takan so ta kai hannunta jikin RAUDA sai dai tun ranar da RAUDA ta riki y'arta ta yi mata wani tsinanen duka dan ta ga Maman na zagin iyayen Rauda ana zama lafiya itama ta kalleta ta zageta ita kuma ta nuna mata bata da hankali Maman ta yi ta yi ta kwaceta ta gaza karshema da Raudar ta yi kukan kura ta hankade Maman da y'ar Tata sai da Maman ta fi wata tana zuwa ana murza mata bayanta dan ta baya ta je ta fada ta ji rauni sosai, shi yasa idan Raudar ta mike tana huci sai Maman ta ringa kiyaye abinda ke saurin sakata fita a hayacinta wato zagin iyayenta
Mama na fita Abdul Hakim ya rukunkume Rauda yana fashewa da kuka ya ce" Aunty tsoronta nake ji, kasheni zata yi"
Itama zuciyyarta ce ta karye ama ta ki nuna masa a hankali ta zaunar da shi ta zauna ta dora kansa saman cinyarta tana shafawa a tausashe ta ce" Dama Akoy wanda ya isa ya karar da kwanan wani in ba lokacin mutun ne ya yi ba? Haba boy din aunty, ka daina fadar haka ka ji? In sha Allah babu abinda zai sameka sai abinda Allah ya kadarta maka ka ji? Fada minda me zaka karya yau? Zaka je ka siyo ne ko na je na siyo maka? Yau zaka je makaranta kuwa an kanena?"
Ajiyar zuciya ya ringa saukewa a jejere da sauri ya gyada mata kai ya ce" aunty zan je, kin ga Malamin mu na islamiyya yace ko me aka yiwa bawa ya barwa Allah, sakayar Allah ta fi ta kowa, Allah zai saka masa ya saka shi a aljanna ama kuma yace bawa ya kasance mai yafiya, na yafewa Mama aunty kin ji?"
A hankali ta dauke hawayen gurbin idannuwanta ta lalubo kudin dake cikin rigar Mamanta ta mika masa dan idan bata saka kudi a nan ba tana kwonce za'a lalubeta a kwashe Abinda ta ajiye, gashi nauyinta da na Abdul Hakim a wuyanta yake, Mama na ikirarin hana masu abinci dama ba basu take yi ba ai
a tausashe ta ce" Maza karbi je siyo mana abinda ranka ke so bari in zuba maka ruwan wanka idan ka dawo ka yi sai mu je na kaika makarantar daga nan na kaika wajen inna kaka zaka je?"
Cike da farin ciki ya amsata kan zai je kafin ya mike ya tafi da gudu
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 12