ga datti a jiki domin so yake ya je ya cire ya haɗa da na jiya ya mayar inda ya karɓo, saboda tsabar maƙo ba ya iya ɗinka sutura ta kirki amma yanzu da yake neman auren Hadiza shi ne yake arowa yana sakawa dan gudun kar a raina shi.
Da sallama ya shiga gidan babu kowa a tsakar gidan sai Kuluwa, ita Haule tana ɗaki ita da yara tana musu tatsuniya, Kuluwa jin muryarsa sai ta ji tamkar ya caka mata mashi a maƙoshi, ta yi banza da shi ta buɗe randa ta ɗakko ruwa a kofi, tahowa ta yi lokacin ya zo daidai saitin ta zai tafi ɗakinsa, buguzum-buguzum ta zo wucewa kaɗan ya rage ta bangaje shi. Tana shiga ɗaki ya tsaya gyaran murya ya yi a saita bakinsa yadda amon muryar zai isa ga kunnen ta ya ce
"Kai gaskiya mace ƴar duma-duma mai diri ta yi, ko tafiya take sai ka ga ɗagwas-ɗagwas, ,gwanin sha,awa na yarda mata suna suka tara, amma wata macen idan ta taho yadda aka san motar tantan za ta wuce... Kuluwa wacce tun da ya fara magana ta tsaya tana huci kamar zakanya domin a take zuciyarta ta raya mata cewa da ita yake wato amaryarsa wacce ya kira da suna mai jiran gado ita ce ta iya tafiya, tun da dai ta san duk wanda ya yi zagi a kasuwa ya san da wanda yake, rai a ɓace ta dangwarar da kofin hannunta wanda ta ɗauki ruwa, ta taho a sukwane don zuwa a yi wacce za a yi ita da Malam Nura don ba za ta bar wannan maganar ba, ta sanya a ranta ita da amaryarsa shege ka fasa domin za a yi zaman doya da manja!.
MAMAN AFRA
09025576222
[4/6, 5:18 PM] MOM MASHKR & AFRAH: https://chat.whatsapp.com/CoSIFObGSJeG4TLAuJwo3J?mode=gi_t
*UWAR AGOLA*
NA
MAMAN AFRAH
*Daga marubuciyar*
*Ruwa cikin cokali, ci ma zaune, malamin bogi, ƙazamin miji, Bonono ƴar zaman wanka, ruɓaɓɓiyar igiya ƴan adaidaita sahu, ƙara,in inna delu, jalli joga, Beelal, ungozoma da sauransu.*
09025576222
🅿️2️⃣
Malam yana tsaye sai ganinta ya yi kamar an jefo ta, ta fito ta tsaya tana huci kamar zakanya, da kallo ya bita yana aro jarumta ya tsuke fuska amma alamu sun nuna Kuluwa bata lura da tamke fuskar da Malam Nura ya yi ba don idanunta sun rufe da kishi hakan ya sanya ya zuba mata na mujiya. Sai da ta tsare shi da ido tq ce
"Nura wace ce take tafiya kamar motar tantan ɗin? "Ta faɗa yana kallon yanayin ta ya gama gane ta haɗa kanta da baƙar wahala don baƙin kishi mugun ciwo ne musamman na mijin da bai damu da kai ba, kuma ba ya ɗaukar duka ɗawainiyarka.
Sai da ya danne dariyar da ta so ƙwace masa ya sassauta murya ya ce
"Haba Kuluwata, ni a wa zan kira ki da motar tantan ki duba kanki da kyau ai idan diri ake nema da iya tafiya sai dai mata su take miki baya, amma ai ke tafiyarki kamar ƙirga sawun ki kike" ,Shiru ta yi tana binsa da kallo amma ƙwaƙwalwarta tana raya mata avubuwa da dama ciki kuwa har da nuna mata raina mata hankali ya yi hakan ya sa ta ce
"Ka ji da shi ciwon ajali a ɗan yatsa, ai ni na san ba a sakewa tuwo suna, mai hali ba ya canjawa, ai duk wannan maganganun naka ba ganewa zan yi ba wai an yi yamma da kare, tun ba yau ba na san cewa kai munafukin mata ne k... Hannu ya ɗaga mata a ƙufule cike da faɗa ya ce
"Dakata! Kuluwa, ni nan da kike ganina na fiki hawa tamfar ɓacin rai don haka ki taka a sannu ko na shuka miki rashin mutunci, ni yanzu hankalina a kan sabuwar amaryata yake dan haka a halin da ake ciki yanzu ina kan bakana na cewa mata suna suka tara! Kuma Hadiza ita ce zara a cikin matan" Yana faɗar hakan ya juya ya yi hanyar ɗakinsa ya barta a tsaye tana jin tamkar ya watsa mata wuta da ya ce Hadiza amaryarsa ce Zara kenan su duk suna suka tara wato ba mata ba ne su.
Har ta kama hanyar ɗakinsa ta fasa ta juya ta shige ɗakinta tana jin tamkar ana hura wuta a zuciyarta, tana shiga ta kwanta tana saƙa da warwarar yadda za ta ɓullowa lamarin ta yadda za a fasa wannan auren domin ita bata fatan Malam Nura ya ƙara auro kowace mace har duniya ta naɗe!.
Yana shiga ɗakinsa ya cire kayan jikinsa ya mayar da linkin ya ajiye ya saka wasu kayan, cikinsa ne yake ƙugi yunwa yake ji tamkar ƴaƴan hanjin cikinsa za su fito su nemi abinci da kansu haka yake ji. Tunanin inda zai samu abin da zai saka a cikinsa ya yi jim kaɗan ya fito ya je ya rufe ƙofar gidan, ɗakin Haule ya nufa yana shiga ya same ta a zaune tana lissafa ƴan kuɗaɗen ta lokacin duk yaran sun yi bacci, daman yaran uku ne nata biyu ɗayan kuma wata mai rabon haihuwar ce a cikin matan da ya aura ta haifa ta kawo masa ita ta karɓa take riƙewa.
Kasancewar basu samu haihuwa da wuri ba tun da babbar ƴarsa Alawiyya tana da shekara tara, sai Kabiru mai shekara shida, su ne ƴaƴan Haule, da kuma Lauwali mai shekara huɗu shi ne ba ɗan Haule ba. Allah da ya taimake shi duk yawan aure-auren sa matan ba sa samun ciki da yanzu ƴaƴan sun kusa ashirin. Yanzu yana da shekara talatin da bakwai a duniya, inda Haule take da shekara talatin da ɗaya, Kuluwa kuwa ashirin da tara.
Haule mace ce mai haƙuri da kawaici abin duniya da duniyar ma basu dame ta ba, inda Kuluwa take masifaffiya da baƙin kishi tana da masifa sannan bata barin ta kwana. Shi kuma Malam Nura mutum ne mai son mata sannan yana da maƙo ba ya ɓanɓaruwa ta daɗin rai kuma mutum ne shi da ba ya sauke haƙƙin iyalansa bayan yana da hali tun da manomi ne sannan yana neman kuɗi amma kulluɓ cikin tarawa da kuma ambaton babu yake.
Yana shiga ta yi saurin ɓoye kuɗin nata duk da bata san cewa ya gani ba, tun da ya san halinsa mutum ne mai son abin wani yanzu yana iya cewa ta ara masa kuɗin. Yana washe baki ya samu bakin gadon ya zauna ya ce
"Haulatuwa uwar gidan ran gida, uwar gida sarautar mata, ke ce ta farko kuma kowacce bayanki take bi" Ɗan kauda kai gefe ta yi tana rayawa a ranta cewa sai yaushe zai daina zambaɗa ƙarya da kuma daɗin baki, ta ɗan saki murmushin irin ta ji daɗin nan a fili ta ce
"Wannan haka yake, kana fasa min kai fa amma" A zuciyarta kuma ta ce
'A haka za ka ƙare kullum cikin daɗin baki abin da za ka faɗawa wannan daban wanda za ka faɗawa wacccan ma daban shi ya sa duk lokacin da gidanka aka ce akwai mace fiye da ɗaya kai kake haddasa fitina amma a guji zuwa rafi wata rana tulu zai fashe!'
Yana ɗan washe bakin samun nasara ya ce
"Kin cancanta ne" Dariya kawai ta yi ya ɗan sauke numfashi ya ce
"Za a samu wani abu a nan ne?" Tana kallon sa ta ce
"Kamar me?"
Ya ce
"Abin da zan saka a bakin salati yunwa nake ji" Sai da ta karkata kai gefe ta ce
"Ayya daman gayan tuwon da Kuluwa ta bamu na yi miya su kansu yaran bai ishe su ba sai da na siya musu awara suka ƙara" Shiru ya yi yana nazari ya san shi ya bada hatsi kaɗan wanda ba zai isa a ci a ƙoshi ba sannan bai bada kuɗin kayan miya ba ya san kuwa Kuluwa ko da danginsa zai zo bai isa ta bashi miya ba.
Ya ɗan yi jim ya ce
"Kuma babu sauran miyar?" Ta ce
"Wallahi babu" Miƙewa tsaye ya yi ya fito ta taɓe baki ta bi bayansa da kallo. Yana fitowa ya nufi ɗakin Kuluwa ya shiga tana zaune ta doka uban tagumi ita kaɗai ta san tunanin da take kusa da ita ya je yw zauna sai da ya zauna ma ta lura ya shigo ɗakin. Wata harara take zabga masa kamar idanunta za su faɗo ya rausayar da kai irin nn ƴan duniya ya ce
"Kuluwa tawa, ni kuwa na Allah" Wani gajeran tsaki ta ja ta ce
"Kanka ake ji mahaukaci ya faɗa rijiya" Basarwa ya yi ya ce
"Ki bani tuwo ina jin yunwa" Tana masa kallon tsaf ta ce
"Inda ka je ba a baka ba?"
Yana kawar da maganar ya ce
"Bani da inda ya fi nan, wallahi yunwa nake ji kamar in ci babu" Dariya ta yi mai haɗe da shewa ta ce
"Da za ka ci babun ma da ya fi" Ganin abin nata ba na ƙare ba ne ya ce
"Ke Kuluwa abin naki ya isa ba fa tsoronki ake ba, ki ɗakko tuwo ki bani tun da ba ke kika noma mini hatsin ba" Kamar jira take ta tashi da sauri ta janyo wata roba da tuwon yake ciki ta turo gabansa ta ce
"Inda wannan gayan tuwon ne gashi nan"
Yana kallon tuwon ya ce
"Ina miyar?"
Ta ce
"Wacce ka bani kuɗin cefanen na yi?" Yana zare ido ya ce
"Idan ma ban baki ba ke ba a cin arziƙin ki ne, wata shegiya miya ba za ki nema ki yi ba a miki ciki a miki goyo, wato na nemi hatsin tuwo na baki na miyar ma ni kike so na nemo" Hannu ta saka da buga ƙasa ta ce
"Wannan ne baka isa ba wallahi, ni ba wahalalliyar mace ba ce, idan kanka zafi yake to ni nawa hayaƙi yake, masifa wane shege ta kashe, miya ce baka bada kayan yi ba ni kuma wacce na yo billahillazi ba zan bada ba, ɗumamen tuwo zan yi da ita gobe, nima gari na siya nasha da daren dan haka ka ɗauki tuwon ka fita min a ɗaki" Ganin ba zai iya masifarta ba ya miƙe tsaye ya saka ƙafa ya buge robar tuwon ya ce
",Aikin banza gayyar na ayya gayyar tsiya, ɗanyen tuwon, abin da har yau baki iya tuwo ba sia ɗanye, kana ci yana maka dariya, ai an kusa yin ta ta ƙare wato zan auro galleliyar amarya Hadiza mai iya girki da iya tafiya ta zo ta kawo sauyi a gidan nan" Yana kaiwa nan ya juya ya fita daga ɗakin.
Cikin ɗaga murya take faɗin
"Idan har tusa tana hura wuta za mu gani, lokaci zai nuna ai daman duk wanda ya ce bai iya kuka ba uwarsa ce bata mutu ba za mu jira zuwan amarya mu ga yadda za ku ƙare! Daman yanzu za a yi amarya mu za a shuka mu kamar dusa" Yana jin ta ya yi dogon tsaki har zai shige ɗakinsa ya dawo da baya ya zo ya ɗaya labulen ya ce
"Kin ba kanki amsa" Yana faɗar hakan tafi ya shige ɗakinsa.
Tun da ya kwanta yake juyi yunwa ta hana shi ya runtsa ya ɗakko waya ya kira Hadiza suka yi hira suka yi sallama yana jin suna hira tana tauna, alamar tana cin abu kuma yana jiyo muryar Zainaba tana batun akwai daɗi ya san kuwa nama da lemon da ya saya ne suke ci, shi an bar shi da ciki yana masa ƙugi.
Bayan sun gama wayar ya buɗe wani jug, gayan fura ne a ciki haka ya ɗakko ya ci ya sha ruwa ya kwanta bacci ya yi awon gaba da shi da mafarkin an kawo amarya Hadiza gidansa.
Washe gari da safe yana fitowa ya ga yaran suna shan koko da waina, gaban Kabiru ya je yana faɗin
"Kabiru ina kuka samu waina?" Yaran suka haɗa baki wajen cewa
"Iyarmu ce ta saya mana" Baki ya washe ya kalli Haule da take gyaran wake ya ce
"Ku dai mata sai kuke kukan babu kuɗi alhalin kuɗi suna wajenku a nannage, ban san mai ya sa kuka fi kula da ƴaƴanku sama da mazan ku ba, yanzu maimakon ki cika kwanon samira da wainar nan ki cika dogon kofi(Jug) Da koko ki kai mini ɗaki in saka miki albarka amma kika yi mirsisi tusar ango" Kallo ɗaya ta masa ta ɗauke kai ta mayar da hankali wajen yin abin da take yi.
Yana tsaye ya ce
"Haule ba magana nake miki ba?" Kuluwa wacce take wajen murhu tana iza wuta ta ce
"Shiru ma ai amsa ce ga mai hankali" Cike da jin haushin ta ya ce
"Ni dai Kuluwa kin zame mini ƙarfen ƙafa wallahi, ina dalili ana magana da kishiyarki amma kina tare mata faɗa" Banza ta masa ta fara waƙa tana faɗin
"Wani mijin namiji ne wani kuma sauna ne" Kasaƙe ya yi yana cika yana batsewa ya ce
"Da wa kike?"
Tana ɗan ɗaga kai alamar mai jiran faɗa ta ce
"Wanda yake tsoron ta mutu... Kafin ta ƙarasa maganar fuuuu ya yi hanyar ɗakinsa ya fito da ledar kayan aron da ya je hira da su jiya ya zo a fita daga gidan.
Bayan ya mayar da kayan ya wuce wajen mai shayi ya sha shayi da biredi ya ƙoshi. Yana shigowa gida ya ce kira su ya ce
"Yau saura kwana shida ɗaurin auren nan, ina so in faɗa muku bakin ku ya ƙare" Haule ta kalle shi da mamaki ta ce
"Ban gane ba?" Ita daman Kuluwa kai ta ɗauke gefe bata ce komai ba.
Ƴar dariya ya yi ya ce
"Ina nufin na sallame ku zuwa turaka!. Wato duk wani tanadi da zan yi nan gaba na amarya Hadiza ne" Su duka cike da rashin fahimta suke kallonsa yana tsaye hannayensa a cikin aljihunsa yana murmushin jin daɗi shi kaɗai ya san irin amarcin da zai kwasa.
Kuluwa a harzuƙe ta ce
"Kamar ya wai?"
Ya nuna ɗakinsa da hannunsa ya ce
"Ina nufin daga yau duk wacce take da girki to iya girki za ta yi babu ruwanta da zuwa turakar miji da daddare, yanzu lokacin amarya ne!"
Haule ta ce
"Sabon salo kiran sallah da usur, wannan amaryar da abin da za ta zo kenan?" Yana kaɗa kai ya ce
,
"Eh akwai wasu ƴan magungunan gyara da zan fara sha to bana so maganin ya salwanta" Kallon -kallo aka shiga yi tsakanin Kuluwa da Haule Haule tana ƴar dariya ta ce
"Toh Malam ai abin wannan ba komai ba ne, idan ka ce a baka wata biyu ma sai mu baka ka gama cin amarcin...
Kuluwa ta bugi ƙirji ta ce
",Sannu Haule dami sarkin haƙuri, wallahi ba zan yarda ba, idan na yarda Allah ya tsine mini, wato ke saboda baki san ƴancin ki na mace ba za ki bar kwananki tun amarya bata tare ba namiji yake mata tanadin jikinsa, to ni dai ba zan yarda ba, tun da yau ma baki kwanana ne kuma bani da wani wajen kwana da ya wuce turakar Malam a yau, haka idan kwanan ya zagayo ma sai na je... Wani haushi da tsanar Kuluwa ce ya cika Malam daman ita take kawo masa cikas a kowane abu shi ya rasa wannan jaraba da ya je ya kwasowa kansa biyan bashin auren ta gashi ta addabe shi.
Ganin tana masifa shi ma ya ce
"Haule Allah miki albarka ai shi ya sa kika daɗe a gidan nan kika yi ƙarko"
Kuluwa ta yi karaf ta ce
"Ai ciwon kanta ne bata sani ba shi ya s... Haule ta haɗe rai ta ce
"Kuluwa ki taka a sannu fa, shiru -shiru ba yana nufin gudun magana ba, kawai kyalewa ce da son zaman lafiya, kuma na san ciwon kaina kawai biyayyar aure ce da bin maganar miji, ni nan da kika ganni ina iya sadaukar da duk wani abu don farincikin mijina, ina iya haƙura da jin daɗina don in faranta masa" Baki sake Kuluwa take kallonta ba tare da ta ce komai ba ta ɗauke idanunta daga kallon ta ta mayar kan Malam, don ita idan ta tsaya maimaita magana da Haule hawan ruwa ne zai kamata.
Tana kallon Malam ta ce
"Na faɗa maka ba zan yarda ba, kuma da ka saka mata albarka nima ai ba tsine mini aka yi ba"
Da yatsa ya nuna ta ya ce
"Ai duk ƙwawarki kwanan turakar miji ya barki Kuluwa ki ɗauki na annabawa... Tana tafa hannuwa ta ce
"Wallahi yau ma kwanana ne a ɗakinka zan kwan...
Ya katse ta da faɗin
"Ga fili ga mai doki, in dai za ki je ɗakin ki kwanta ga wurin nan, ni dai sunna ce ba zan aikata ba tun da na faɗa miki tanadin amarya Hadiza ne, ban da neman jaraba ma ke da kika kwana jiya a ɗakin ki amma yau shi ne don na nemi ku bani lokaci shi ne kika hau dokin zuciya kike sukuwa" Banza ta masa ta juya ta ci gaba da aikin ta.
Hannu ya saka a aljihu ya ciro naira ɗari ya miƙawa Haule ya ce
"Ungo nan Haule, ai ke kam kina cin ribar zaman aure daman mai haƙuri shi yake cin ribar zaman duniya, kin ga jiya ga ɗari biyar ɗinki ta faɗar kishiya, yanzu ga naira ɗari ta haƙurin bin maganar miji ɗari shida me kika manta" Tana dariya ta ce
"Allah amfana, Allah barka da Hadiza amarya"
Ya washe baki kamar gonar auduga ya ce
"Amiiiiiin Haulen arziƙi"
Kuluwa ta ɗago daga sharar da take ta ce
"Ina tsiya ina wata ɗari shida, kamar wata matar kyankyaso zan ke karɓar wannan kuɗin ai wallahi sa,a ka yi da sai na ɓare maka kai a biyu"
Tsaki ya yi ya ce
"Ai duk namijin da ya auri mace mai baƙin kishi bai yi dace ba, gashi nan bakya cin ribar zaman auren kina zaune miji yana yi wa kishiya kyautar kuɗi"
Ta ce
"Ai ko ni zan iya kyautar sama da naira dubu ba wai naira ɗari ba" Ita dai Haule bata tanka musu ba, haka ya shige ɗaki ya bar ta tana ta kumfar baki, sai ta yi shiru kamar an tsikare ta sai ta ci gaba da masifa ita kaɗai.
Da yamma Kuluwa ta shirya ta nufi gidan Baba Ramma mahaifiyar Malam Nura da sallama ta shiga bayan an amsa ta same ta tana tuƙa tuwo, tabarma ta shimfiɗa mata suka gaisa Baba Ramma ganin ran Kuluwa a ɓace ta ce
"Kuluwa ina fatan dai kuna lafiya kuma kuna zaune lafiya" Kamar mai jira ta ce
"Ina fa zaman lafiya gidan kamar filin yaƙi"
Baba Ramma ta ce
"Ya subhanallahi mai ya yi zafi shi ba wuta ba?"
Kuluwa ta ce
"A kan wannan neman auren da yake yj ne sai tauro da abubuwa yake yana kafa mana dokoki a gidan duk sai kambama amarya yake yana nuna ta fimu matsayi"
Baki sake Baba Ramma take kallon Kuluwa cike da kasa ɓoye mamakin ta ta ce
"Ke yanzu Kuluwa a kan ƙarin auren ne kika kawo ƙaran mijinki?In ce dai ba ke kaɗai ba ce ita Haulen fa?"
Kuluwa ta ce
"Ita bata san inda yake mata ciwo ba"
Baba Ramma ta ce
"Ni dai tun da Nura yake aure-aurensa Haule bata taɓa kawo ƙaransa ba amma ke kin zo kina ba kanki wahala, shin baki san cewa shi namiji idan zai ƙara aure sai mace ta kawar da kai ba, sannan duk wani rawar kai da wulaƙancinsa sai a lokacin yake tsurowa, duk da ba kowane namiji bane yake haka amma yawanci mazan duk haka suke"
Kuluwa takaici ne ya cika ta hakan ya sa ta ce
"Ni dai Baba dan Allah ki bashi umarni ya fasa auren nan ji nake kamar zuciyata ,a ta buga... Baba Ramma ta ce
"Inyeee lallai fa, sannu Kuluwa, wato in hana shi rawar gaban hantsi bayan da ransa da lafiyarsa da ƙarfinsa a jikinsa ai daga nan in aure hamsin zai ƙara ba zan hana shi ba, komai lokaci ne wataran ko an ce ya yi ma ba zai yi ba"
Kuluwa ji ta yi tamkar ta shaƙe Baba Ramma har sai ta bar numfashi, duk da ba wannan ne auren ta na fari ba amma bata san mai ya sa ko mijinta na fari bata son sa kamar yadda take son Malam Nura ga wani kishi da ta ɗorawa ka ta yake ɗawainiya da ita. Tana so ta faɗa mata har ƙairace musu ya ce zai yi wai tanadin amarya zai yj amma kunya ta hana ta magana haka ta taso ta baro gidan tana da na sanin zuwa tun da babu biyan buƙata!.
Yau wani yadinsa da yake ganin ya fi kowane yadi kyan gani a cikin kayansa duk da shekara ta uku kenan da ɗinkawa ya gyara tass ya saka saboda ya gaji ya biyan kuɗin aro kaya.
Hadiza ko da ya zo yau ta ga hannunsa babu komai hakan ya sa ta ƙi sakin jiki take wani kumbure-kumbure shi ma yana ganin yanayin ta ya san dalilin fushin amma haka ya basar don shi a nashi ganin ya gaji da nomawa jaki ciyawa yana kawo kayan daɗi don su ji daɗin hirar soyayya amma tana ba ƴaƴanta ita cw kaza uwar son ƴaƴa a zuciyarsa ya ce
'Idan aka ɗaura auren ai na huta sai su koma gidan ubansu, ko ki bar su a gidan kakannin nasu ina dalili'
Hira yake jan ta da ita tana basarwa ya gaji ya ce
"Hadiza yau ko bakya jin daɗi ne?"
Ta yatsina fuska ta ce
"Ƙalau" Fitowar Zainaba daga gidan tana riƙe da hannun Shafi,i shi ya katse musu maganar. Zainaba ce ta tsaya shi ma ya tsaya kasancewar hannunsa cikin nata, ta sunkuyo ta masa raɗa a kunne. Kai ya gyaɗa ta saki hannunsa ya taho da gudu yana cewa
"Oyoyo baba" Yana zuwa ya haye cinyar Malam Nura ya ƙanƙame shi, kasancewar yana cin tuwo Zainaba ta je ta kamo shi suka fito. Dariyarta ta shiga dannewa ganin haƙarta ta cim ma ruwa, daman tun da ta ga Innarsu ta fito, ta saka a ranta yau ma sai ta masa abun da zai masa ciwo, hakan ya sa ta saka luda ta kwalfo miyar kuka ta ƙara a kwanon da Shafi,i yake in tuwo da yake miyar ta huce, ta ringa ɗaukan miyar da ludan ta zuba masa a jikin kayansa da duka hannuwansa har bayan hannun. Shi ne da suka fito ta raɗa masa cewar ya je ya haye cinyar Malam Nura duk ya ƙanƙame shi.
Malam Nura gabaɗaya ya rasa ma ya zai yi, jikinsa jaga-jaga da miya gashi kuma miyar manja ce yadda fari yadin ya sha miyar tamkar ya saki kuka.
Cikin yaƙe don kar ta ga kamar ba ya son ɗanta ya ce
"Oyoyo Shafi,i ɗana na kaina" Ya faɗa yana ƙoƙarin ɓanɓare yaron don ya maƙalƙale shi, hannuwansa suna maƙale a wuyansa hatta wuyansa da gefen fuskarsa sun san Shafi,i ya ci tuwo. Dakyae ya ciro shi yana faɗin
"Duk ka ɓata ni da miya" Ya faɗa yana kallon jikinsa. Hadiza ta haɗe rai ta ce
"Haba Malam Nura to mene ne don ya goga maka miya kai baka san yaro ba" Gudun ɓacin ranta ya sa ya washe baki ya ce
"Haba Hadiza amaryata ai da kai da kaya duk mallakar wuya ne, ina ni ina masa faɗa ai ba miya ba ko kashi ne ya goga mini ba zan ji komai ba ai ɗana ne" Dariya ta yi tana faɗin
"Shafi,i jeka gida ka wanke hannunka" Don ita ba ta san duk shirin Zainaba ba ne, Zainaba kuma ta ce
"Kake kamshin miya a maimakon ƙamshin turare " Ta faɗa
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 2 Chapter of 12