sa tsantsar ƙarfin hali a tare da ita domin babu da na sani a fuskarta, don ta ji an zo ceton ta gabaɗaya sai ma ya ga rawar kanta ya dawo.
Baki ya damƙe ya ce
"Ka san dai babu wanda zai ɗauki maƙudan kuɗi ya sayi rigar shadda kaɗai ko? Ta cuceni ta taƙaitani ai dai ba zan je wajen ɗaurin aure da gajeran wandon ba, wallahi babu mai cewa ma gajeran wando ne tun da ba a iya hango wandon sai zallar ƙwanrin ƙafata, kalli yadda ta mayar da wandon nan iya cinyata dab da tsantsa ta fa yake, banbancinsa da ɗan kamfai(Pant) Kaɗan ne"Ya faɗa yana saka hannu ya kama wandon yana nunawa Hudu. Hudu ya danne dariyarsa saboda arziƙin da Malam Nuran yake da shi ya wuce ya yi wannan abun a kan shaddar da bata kai dubu talatin ba har kuɗin ɗinkin, amma duk ya saka damuwa a ransa.
Hudu ya ce
"Ka bar batun wanna shaddar tata ta ƙare, don ko a Kano shagon da na siyo ita kaɗai ta rage a bandir ɗin ni na saye gabaɗaya, ka ga kuwa ko da an sake kawowa ba lallai a samu mai zanenta sak ba da sai a yanko a yi wandon ka siyar da ita tun da asarar kake hangowa" Kasa magana ya yi harara kawai yake aikawa Kuluwa ji yake tamkar ya zama ƙuda ya shiga ɗakin ta windown ya aiwatar da nufinsa ko ya samu sauƙi.
Maimakon ya yi wa Hudu magana sai ya juya wajen Kuluwa ya ce
"Kuluwa baki da zanen shadda kalar wannan?" ,Da mamaki take kallonsa har dariya ta so kuɓuce mata amma gudun masifarsa ta danne, saboda ta san tana darawa zai ce bata damu da halin da yake ciki ba, muryarta da alamar dariya domin sai da ta danne, yau ne ta tabbatar da cewar idan mutum yana neman mafita komai ma gani yake zai dace tana karkata kai cike da nuna damuwar da yake ciki ta ce
"Haba Malam ina ni ina shadda irin wannan mai tsada, kai ma ina jin a kaf rayuwarka wannan ne karon farko da ka ɗinka kuma kananganin siyar da ita za ka yi ba za ka ci gaba da sakawa ba bare ni... Kamar zai kai mata duka ya ce
"To na ji abun da na tambaye ki da ban amsar da kike bani da ban... Hudu ya ce
"Ba fa ita ta kai zomon ba rataya aka bata, ga wacce ta yi abun can tana ɗaki baka da damar hukuntata kawai don ita ce kuka mai daɗin hawa... Malam yana masifa ya ce
"Ya isheka matarka ce ko tawa?" ,Hudu ya ce
"Allah ya baka haƙuri, wai kana nufin zanin shaddar za ka ɗaura idan tana da akwai?" Ya faɗa yana haɗiye dariyarsa don har ya hango gogan nasa ɗauri da zani.
Malam Nura ya yi shiru yana tuno da yanzu fa yana can a cikin jama,a ana masa Allah sanya alkairi, ana ta musu hoto shi da Hadiza wataƙila ma har hannunsa dai ta kama, tana masa murmushi, da yanzu ta zama mallakinsa amma Kuluwar nan ta kawo masa tsaiko a lamarin auren nan.
Kamar ya kai wa Hudu duka ya ce
",Kamar wani bayerabe zan ɗaura zani, ka san dai na ɗaura zani na je wajen nan wallahi kwanan ɗaurin aurena da Hadiza ya ƙarw don ba za ta aureni ba, daman nufina a je a samu wani tela mai saurin ɗinki ya ɗinka mini wandon, ko zanin ba zai isa ba sai ya mini ƙafafun in ya so daga saman ko atamfa ce ya saka a mini kwanbileshin (Combination) ka ga idan na saka babu mai cewa zanin atamfa ne daga sama tun da rigar shaddar za ta rufe wajen.
Idanun Hudu gabaɗaya sun kawo kwalla, amma ba ta kuka ba sai ta tsabar dariyar da take cinsa yake dannewa, ba komai yake bashi dariya ba illa idan ya kalli Malam Nura da wannan ƙonannan wandon, abu na biyu idan ya tuna yadda ido ya juye da mujiya, wato Malam Nura ya je wajen Hadiza ne da soyayyar ƙarya saboda an ce mijin ta da suka rabu mai kuɗi ne, kuma ita ma tana da kuɗi shi ne ya je da nufin ya aure ta ya wanki banza, ya tatiƙe kuɗaɗen ya sake ta, ya tsakuri wani abu daga abin da ya mora daga gare ta ya auro wata, amma da yake Allah ya ga mugun ƙudirinsa aai ya jarabce shi da son ta na gaskiya, sannan sai gashi shi take wanka a maimakon ya wanke ta, ita take cin kuɗinsa har yanzu yana ganin idan ya aure ta, zai ci kuɗin ta ne. Abu na uku yana mamakin yadda Kuluwa ta shammace shi ta ƙona wandon shaddar, ya san ba komai ba ne yake faruwa da abokinsa sai irin tijarar da yake yi wa mata, da ɗaukan haƙƙinsu ya aure ki ya wulakanta ki ya sake ki, shi a lamarinsa ma bai san mene ne so ba, don kowacce ba yana auren ta don so ba ne, kawai son zuciya ne.
Hudu ya ce
"Kawai ka haƙura da shaddar nan ka samu wani kayan ka saka" Yana masa kallon ka janyo ruwa ya ce
"Haba Hudu ka hana ni sakat da maganganun da ka san amsar su, yanzu a kaf suturuna ina na ga wanda zan shiga taron jama,a, babu wani kayan kirki fa ka sani, a ce kamar aurena da Hadiza amma ban saka kaya na kirki ba, ni wallahi damuwata ma idan har ba da shaddar nan na je wajen Hadiza ba wallahi ba za ta ɗauki hoto da ni ba, har fa cewa ta yi za ta kafe hotonmu a ɗakin ta, wallahi Kuluwa idan muka yi gaba da gaba ni da ke ina ga ba wai ƙafafu kawai zan datse miki ba, gunduwa-gunduwa kawai zan yi da ke" ,Ya faɗa kamar an caka masa wani abu ya zabura ya koma ya buga taɓaryar hannunsa da ƙarfi a jikin ƙofar ɗakin nata, da yake ta san ƙofar tana da ƙwari ta ce
"Lokacin da zan fito ma baka gidan nan, kuma dole ka aika mini takardar sakina... A masifance ya ce
"Ƙarya kike mai mugun hali, ai wallahi ba zan yi asarar kuɗina ba da aka ɗaura mini aure da ke, ba yanzu zan sake ki, bare ma ke da kika mini aika-aika ai ko a gurguce kike sai na ci gaba da gana miki azaba a gidan nan, ke Hadiza ma a kan bayanji za take zaunawa tana tuƙa tuwo, kuma dole ki sunkuya ai sai kin karɓi ukuba...
Saboda ta sake cusa masa haushi ta ce
"Haule miƙe mini wannan rigar shaddar da ya cire, miƙo min ita ta window in ƙarasa babbake ta, in ya so sai ki ara masa riga da zani na atamfa tun da neman aron zani yake" Da sauri ya kalli igiya ya ga rigar tana nan a rataye. Bai ce komai ba domin shi kaɗai ya san irin haushin da yake ji a kan Kuluwa baki ba zai misalta ba.
Wayarsa da take ta neman ɗauki Haule ta tafi ta ɗakko tare da hularsa da Hudu ya take ta lotse, ta haɗo kan takalmansa, wayar ta miƙo masa ya karɓa ya kalli sunan Hadiza ne ɓaro -ɓaro a jiki ya rasa ma ya zai yi Hudu ya ce
"Ka ɗaga wayar mana, wai ni yaushe ka zama matsoraci ne wai? A ce kana tsoron mace haba abokina" Malam Nura kamar zai yi kuka ya ce
"Baka san so ba ne Hudu, so ne ya mini raga-raga da zuciya ni ban san ma akwai so ba sai wannan karon, ni dai na san masoyina kuɗi amma ban san ana son ɗan adam ba... Hudu ya ce
"Taɓɗi ai daman idan mutum ya ƙi sharar masallaci ta kasuwa yake yi, yanzu ai ga ta inda jarabawarka ta fito, idan ka saki mata ba har kuka suke ba ka mayar da su saboda suna sonka amma ka ce musu son banza... Kiran da ya shigo ne ya datse maganar haka ya yi ta maza ya ɗaga yana ɗauka ta balbale shi da masifa kamar uwarsa ta ce
"Nura ni za ka wulaƙanta a idon duniya? Tun ɗazu lokacin ɗaura aurenmu ya cika, amma dai baka duba lokaci ko? Tun daɗewa sha ɗayan ta wuce yanzu Babana ne ya ƙara awa ɗaya ɗaya, idan har awa ɗaya ta cika akwai mazan da zan sa su hau layi duk wanda na ga wankansa ya mini shi zan zaɓa...
Sai da ya gyara muryarsa ya ce
"Haba masoyiyata gani nan fa ai kaf garin nan babu wanda zai kai ni ɗaukan wanka, in kin ga yadda shaddar nan ta karɓe ni zaki yi mamaki su Hudu ma sai yabawa suke, abin da ya tsayarmu abinci ne da naman da aka dafa na ɗaurin aure ake zubawa a kwanuka za a raba in mun dawo, shi ne ya tsayar da mu amma gamu nan" Hudu da yake jin ƙaryar da Malam Nura yake shararawa ya kalli kan murhu ya hangi wata tukunya ce da alama ma ruwa ne kawai yake dahuwa babu wata alamar za a yi girki barw har a samu nama, shi da ya tambaye shi mai za a ba abokai ma cewa ya yi daga wajen ɗaurin aure kowa ya kama gabansa shi babu kuɗin da zai kashe, ya maido da dubansa zuwa jikinsa da babu kaya sai ƙonan nan gajeran wando, shi da wandon ma babu wanda zai saka amma yana batun wai ya yi kyau.
Hadiza daga ɗaya ɓangaren ta ce
"Yawwa nawan, ai shi ya sa ina nan ina faɗawa ƙawaye da ƴan uwa cewar su jirayi zuwanka, domin kowa idan ya ce mini kin yi kyau sai na ce masa ai iri ɗaya muka ɗinka da angon shi har ya fini yin kyau ma" Hudu da Haule da Kuluwa duk sun jin abin da take cewa kasancewar a handsfree wayar take, kamar zai yi kuka ya juya ya kalli rigar shaddar ya daure ya ce
"Abin ba a cewa komai sai ma kin ganni hula ta zauna daram" Haule ta yi saurin kallon hularsa da karin da aka mata ma ya ɓaci saboda taka hular da Hudu ya yi.
Hadiza ta ce
"Shi ya sa nake son miji kerewa sa,a shi ya sa ɗazu da aka ce baban su Zainaba ya zo ya ce in yarda a ɗaura da shi... Gaban Malam Nura ne ya buga da ƙarfi, inda Kuluwa ta carara guɗa. Malam Nura da sauri ya ce
"Ki ce ba za a ɗaura da shi ba" Ta yi karaf ta ce
"Ina ni ai sai sabon aure da Nurana, wai burgar kuɗi zai yi wa mutane bai san ba cewar kuɗi suna wajenka in na aureka ma babu abin da zan rasa gidanka ma sai ya fi nashi sau dubu" Yana gyaɗa kai kamar tana ganinsa ya ce
"Shakka babu gamu na zuwa" Kafin ta amsa tashin hankali ya sa Malam Nura katse kiran da sauri ya juya yana kallon Haule ya ce
"Haule dan Allah ki samo mini hayar zanin shadda ko nawa ne kuɗin hayar zan biya, ko siket ne ma, in dai za a samu kalar shadda ta wacce bata ji jiki ba, ko zanen ba ɗaya ba ne, ki samo mini, bari na saka wuƙa na yanka miki gefen wandon nan da Kuluwa ta yi wa lahani, ki tafi da shi ki nuna musu kalar shaddar ko Allah zai taimakeni a samu, a yadda nake jin Hadiza ta ɗauki lamarin saka shaddar nan ta kai shi ƙololuwa, ga hoton nan da take ta ambata idan har babu shaddar nan tana iya fasa auren, gwara ki samo zanin in tsargashi da reza ya yi kamar wando in ɗinke da zare da allura ya fiye mini" Haule da Hudu kawai dariya suka ƙyalƙyale da ita ganin yau ɗaya Malan ya zama kamar wani sauna a kan mace
Malam Nura kuwa harara yake aika musu, a inda Haule ta yi ɗiff kawai sai ji suka yi Kuluwa ta carara guɗa ta ce
"Duniya juyi -juyi kwaɗo ya faɗa ruwan zafi" Wannan kalaman ya yi wa Malam ciwo, hakan ya sa ya ƙara ƙudurtar duk lokacin da ya kama Kuluwa mai ƙwatar ta sai Allah.
Hudu ne ya ce
"Yanzu ka bar batub hayar zani ko siket, don ba samu za a yi ba, bari na je gida a cikin kayana na samo maka wanda za ka samu ka saka mu tafi ɗaurin auren nan" Buɗar bakin Malam Nura ya ce
"Akwai sabbi dal wanda baka taɓa sakawa ba?" Yana masa wani kallo cike da gatse ya ce
"A,a akwai sabbi wanda na kawo daga kasuwa yanzu" Malam Nura ya ce
"Ka san dai ai ba zan saka tsoho na je wajen ɗaurin auren Hadiza ba"
Hudu ya ce
"Idan ka je da shi a koro ka"
Malam Nura ya ce
"Da in saka tsohon kaya gwara a samo mini aro a wajen wanki da guga"
Hudu ya ce
"Wallahi ka sake ka karɓi kayan wanjen ƴan wanki da guga, za a tsinka ka a wajen ɗaurin aure, wajen ɗaurin aure ai wajen taron jama,a ne ka sani ko mai kaya ya je wurin? Ai wanda kake ara ma saboda hira kake zuwa da daddare shi ya sa asirinka yake rufuwa" Hannu ya sa yana dafe fuska don takaicin Kuluwa ne kawai yake shaƙa.
Haka Hudun ya lallaɓa shi ya tafi gida ya samo masa kayan, Hudun yana kuyawa Malam Nura ya bi bayansa da kallo yana ganin kayan jikinsa saboda kyaun da Hudun ya yi shi tsoronsa ma ɗaya kar abokin ango ya fi ango kyau.
Hudu yana fita ran Malam ya ɓaci ganin ya kashe kuɗi amma zai ƙare a kayan aro, kuma tsohon kaya, a zuciye ya yi wurgi da taɓaryar hannunsa ya fara tafiya da baya-da baya sai kuma ya tafi da gudu ya yi tsalle ya doka ƙofar ɗakin Kuluwa cikin sa,a ƙofar ta ɓalle don ta ya bugu. Kuluwa da take cikin nishaɗi babu zato da tsammani ta ji ya bugo sai ta ga wayam ƙofa ta buɗe, idanu ta zaro domin har ta fara hango tsayawar alƙiyamarta.
Malam Nura wanda ya buga ƙofar jirif ya faɗi a reran saboda tsallan da ya yi amma bai ji ciwon faɗuwar ba saboda ya ga kwalliya ta biya kuɗin sabulu. Kuluwa ganin ya faɗi ta fara ƙoƙarin tserewa don ta tabbatar ya kamata kashin ta ya bushe sai dai idan tana da sauran kwana ne za ta kai labari, a kiɗime ta kai kallon ta kan ƙafafunta da ya ce zai sare, da gudu ta taho, bai ankara ba ya ji ta taka cinyarsa, ya ji saukar ƙafarta a ƙirjinsa yana ƙoƙari tashi daga kwancen ya ga wulgawarta ta samansa fittt kamar walƙiya. A sukwane ya muskuta, cikin sa,a ya cafko ƙafarta ɗaya, jan ciki ya yi ya janyo addarsa. Kuluwa wacce nufinta ta fice daga gidan amma a lokacin da take dab da cim ma nasara sai ji ta yi an riƙe mata ƙafa ɗaya da ƙarfi irin riƙon da ba za ta iya ƙwacewa ba.
Fisgar ƙafar ta yi, amma ta kasa ƙwatar kanta, jan ƙafar ta yi da ƙarfi ta zube ta fara rarrafawa da ƙarfin ta na gaske, ƙiii ta fara janyo Malan da addarsa, ganin tana neman kufce masa ya yi ta maza ya miƙe zaune, har lokacin yana riƙe da ƙafarta, wani uban ihu ta saka tana faɗin
"Jama,a ku taimakeni ƙafata, Haule kirawo jama,a a awaje su kawo ɗauki" Malam ya ce
"Ai ba ƙafarki ba yau hatfa wuyanki yankan saniya zan miki kamar yadda kika raba wandon ɗaurin auren Hadiza da ƙafafunsa ta ƙarfi da yaji" Haule ta hau faɗin
"
"Innalillahi wa inna ilaihi raji,un Malam kar ka yi haka" Ta faɗa ba tare da jiran komai ba ta yi hanyar wajen, har lokacin mutane suna nan hango Hudu ta yi da ya kama hanyar gidansa ta tura wani yawo ya bi shi da gudu ya taɓo mata shi, ta ɗaga masa hannu, da ɗan gudu ya taho, tun kafin ya ƙaraso ta juya da sauri ta shige gidan, yana shigowa karaɗin Kuluwa ta fara masa sallama a kunne.
Yana shigowa ya hau ƙoƙarin ceton ta don Malam ya fara saita ƙafar, a kwance suka same ta tana fisge-fisge ya haɗe ƙafafun ta waje guda da alama sare su zai yi da gaske. Hudu ya shigo da gudu yana faɗin
"Kar ka yi haka Nura mene ne hakan" Yana zare ido yana faɗin
"Ka barni na gurgunta ta, daga yau ba za ta sake wa wani haka ba" Hudu ya tafi bayansa ya shiga janshi, suka shiga kokawa, ai kuwa Kuluwa ta samu sa,ar ƙwace riƙon da ya mata, tana tashi ta zabga da gudu ta ƙanƙame Haule, Malam Nura ya fishe riƙon da Hudu ya masa, ya nufo wajen Kuluwa da Haule, Kuluwa da gudu ta saki Haule ta yi wajen Hudu, a rikice ta kai masa cafka za ta ƙanƙame shi.
Haule ta dage ƙarfin ta faɗi take
"Kuluwa Hudu ne ba ni ba ce, Kuluwa kar ki rungumi na miji ba muharraminki ba ne" Amma Kuluwa bata ma fahimtar abin da Haule take faɗa ta ga mutuwa muraran. Hudu ganin ta taho za ta cakume shi ya sunkuya, yana faɗin
"Kuluwa alharam giya a gidan liman.
Shigowar wasu mata kusan guda bakwai shi ya dakatar da kowa da abin da yake da wata maroƙiya tana faɗin
"Gamu mun zo cin arziƙi, unguwa ta cika, ɓangaren mata ma yana can ya cika ana ta hidima ango kawai ake jira a ɗaura aure" Malam Nura da sauri ya warci rigarsa siyam siyam ya wuce ɗaki babu wanda ya lura da shi cikin mutanen da suka shigo. Wata nannauyar ajiyar zuciya Kuluwa ta sauke gani ta tsallake rijiya da baya. Haule ta hau yi wa matan sannu da zuwa.
Kuluwa ta fara neman takalmin ta za ta tafi gida, amma shigowar ƙannenta su Mariya ya hana ta tafiya ta wayince tana musu yaƙe, nan ta shiga faɗa musu abin da yake faruwa bayan fitar Hudu. Suka shiga zuga ta a kan ta murje idanunta tw zauna duk kurin banza ne babu abin da zai iya mata kawai burga ce amma ba zai cire mata ƙafafu ba tun da ya san shi ma sai an ɗauki fansar abin da ya yi, da wannan ta ɗan saki ranta.
Hudu ya dawo da wani yadi a goge tass a kawowa Malam ya ce ya saka don ya jima ma bai saka ba, ba lallai a gane cewar na Hudun ba ne amma dai ana iya ganin ba sabo ba ne. Haka ya saka ransa duk ba daɗi ya wanko ƙafafunsa da suka sha ƙasa ya shafa mai ya saka hula da turare suka fito da Hudu. Hudun ne yake raɗa masa a kan ya saki ransa saboda kar hankalin jama,a ya koma kansa. Haka ya shiga washe baki yana yaƙe duk da fargabarsa haɗuwarsa da Hadiza ne, yana tsoron ta gan shi da wannan kayana ta ce masa ta fasa, gashi ma ba ya jin ko ta yarda an ɗaura za ta amince a ta yi hoto da shi.
Hadiza tun suka gama waya da Malam Nura take jin wani daɗi a ranta saboda ta san zai zo da kwalliyar kece rainin da kowa ya ganshi ya san bata yi zaɓen tumun dare ba, shi ya sa ma za ta saka su yi hoto ta kafe a ɗaki ta ko da baya nan ta yi baƙi za su ga miji na nunawa sa,a ta aura ɗan gayu mai saka kaya masu tsada.Shi ya sa ma ta yi gyara na musamman Hadiza ta yi amfani da Packages na bazawara wanda na musamman ne ƙawarta ta kawo aiko mata, da kuma cicciɓin garari, tightening set wanda yake haɗe mace, ga wani sanyi fllusher da yake wanko gabaɗaya sanyin mara, sanyin mahaifa, da sanyin jijiya, Hadiza gyaran da ta yi ita kaɗai ta san Malam Nura zai san ya yi sabon aure ba lallai ya bambance cewa ba bazawara ya aura ba saboda ta dawo tamkar sabuwar budurwa, duk abubuwan nan za a same su a wajen surayya halin yau ta wannan lambar 08032773332
[4/12, 7:04 PM] MOM MASHKR & AFRAH: *UWAR AGOLA*
🅿️7️⃣
*Bojuwa herbs*
*By*
*Surayya Dee.*
*08032773332.*
*Sanyi flusher!*
*Yana wanko dukkan sanyin mara, mahaifa Har ma da jijiya.*
*Tasirin da karfin maganin sanyinmu ya wuce misali don kuwa duk wacce ta siya Slsai ta dawo ko ta turo wasu*.
*Alhamdulillahi Allah ne ya yi mana.*
*Tightening set na hade mace ta dawo Zamzam tamkar yar budurwa.*
*Tasirin magani Idan andafa tamkar yankan wuka ne shiyasa kazar sababi da ciccibin garari na surayya halin yau suke da kyau da tasirin gaske a jikin mace.*
*Muna da gimbiyar zabuwa da tattabarun alheri.*
*Akwia packages na mussaman ga Amare, uwargida ,zawarawa da masu jego.*
*Tuntubeta a wannan lambar*
*08032773332*
*Don samun ingantattun kayan gyara da babu algush.*
*UWAR AGOLA*
NA
MAMAN AFRAH
*Daga marubuciyar*
*Ruwa cikin cokali, ci ma zaune, malamin bogi, ƙazamin miji, Bonono ƴar zaman wanka, ruɓaɓɓiyar igiya ƴan adaidaita sahu, ƙara,in inna delu, jalli joga, Beelal, ungozoma da sauransu.*
09025576222
🅿️7️⃣
Hudu ne a gaba lokacin da za su fito daga cikin gidan Malam yana biye da shi, gabaɗaya idanunsa kafe a jikin kayan Hudu ba don kar Hudu ya ce bashi da godiyar Allah ba, kuma bai gode ƙoƙarinsa ba kawo masa yadin da ya yi ba da sai ya ce ya tuɓe kayan jikinsa ya bashi ya saka, don ya hango tsantsae tazara mai yawa tsakanin kyan da ya yi da kuma kyan da Hudun ya yi. A zahiri ma dai sai dai a ce kyan da Hudu ya yi amma Malam Nura ba za a ce ya yi kyau ba za dai a kira abin da ya yi da suna, ba yabo ba fallasa.
Suna fitowa ƙofar gidan inda jama,a suke jiransu, saboda Malam ya yi gayya sosai, ga kuma wanda Hudu ma ya gayyato, tun da ya ga Malam yana ji da auren nan nasa da Hadiza.
Kunya ce ta kama Malam Nura ganin duk kamar ma ido ba ya kansa, sai hannu ake ba Hudu ana gaisawa da shi, sai sun fara bashi hannu sannan ake ba Malam, wannan wai wanda ma suka san shi ne angon bare baƙi kamar makaɗa da maroƙa da suke ta wasa Malam Nura amma kuma Hudu suke kallo alamu sun nuna cewa sun ɗauka shi ne angon. Hudu ganin wannan kara da ake musu ya sanya hannu a aljihu ya ciro yan naira ashirin sabbi yake liƙawa maroƙan kamar wanda suke jira suka shiga ƙara ƙaimi wajen ƙarawa kiɗan nasu da wasawar armashi, shi kuma sai gyaɗa kai yake alamar yana taya Malam Nura farinciki. Malam Nura da bai fito da ko sisi ba, takaici ya hana shi magana sai hannu yake sakawa a kai- a kai yana gyara zaman hularsa, wacce tun lotsewar da ta yi lokacin da Hudu ya bi ta kanta bata dawo daidai ba sai yake jin kamar an kifa masa kwano a kan. Wato ta ƙi zama daidai.
Kabiru da Lawwali ƴaƴan Malam Nura ne suke musu da wasu yara abokansu wanda musun ya sauka a kunnen Malam Nura inda abokin nasu yake cewa.
"Ashe daman ƙarya kuke da kuka ce babanku ne ango, ashe bashi ba ne baban su Ya,u ne(Hudu) Kallu shi ne ya sanya sabon kaya amma babanku tsoho ya saka, ai ango ba ya saka tsohon kaya"
Kabiru ne ya ce
"Wallahi muna babanmu ranar nan ya siyo sabon kaya mai kyau aka masa ɗinki, kayan sun fi na baban su Ya,u kyau"
Yaron ya ce
"Ai dai tun da bai saka ba bashi ne ango ba" Malan da yake jin tamkar ya kwaɗawa yaron nan
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 6 Chapter of 12