tana dariya, don ita Hadiza ba ta son a kwaɓi ƴaƴanta bata ganin laifinsu. Ta kalle su ta ce
"Innata yau ba a kawo nama ba?"
Malam Nura a fili ya ce
"Yau ba a kawo ba a yj haƙuri ƴar baba"
A zuciyarsa ya ce
'Aikin banza shafa lalle a mazaunai kamar ubanki ne yake nema mini kuɗin'
Idanun uwar ta faka ta galla masa harara tare da yatsina fuska ta juya ta nufi cikon gidan Shafi,i kuwa ya ja tunga ya tsaya ya ce
"Alewa" Babu yadda Malam Nura ya iya haka ya ciro 200 ya bashi ya ce ya saya. Bai wani jima ba ya bata dubu biyun ta ta karyawa a zuciyarsa yana faɗin
'An kusa ɗaura aure ki tare in huta da wannan jigilar bada dubu biyu ki je can ki haɗu da su Kuluwa, ba kina kyashin cin tuwo a gidanku ba, idan kika je gidana tuwon ma gaya za ki samu sai kin nemawa kanki miya, kafin na gama cin moriyar ganga na hankaɗa ƙeyarki'
Sun yi sallama ya kamo hanya ya tafi gida yana ta jera tsakin wankan miyar da Shafi,i ya masa.
A can gida kuwa Kuluwa ta samu maganin matan ta bita zai-zai ta sha don ita tun da ya ce su bar kwanan turaka ta saka a ranta yanzu ta fara kwanan turaka. Ko da ya zo wanka ya yi ya cire wannan kayan. Tana sane da shi, don biredi da lemo ya siyo ya ci iyalinsa kuwa ko oho. Sai da ta daidaici ya gama komai ta nufi ɗakin tana zuwa ta ji ƙofa a rufe ta tura amma ƙofa bata buɗu ba. Daga waje ta bubbuga tana faɗin
"Ka buɗe mini in shigo" Haule tana jinta a zuciyarta ta ce
'Kin haɗu da wahala'
Daga cikin ɗaki ya ce
"Wallahi sai dai ki kwana a waje amma na haramtw muku kwanan turaka" Tun tana magiya har ta lura abin ba na wasa ba ne. Haka ta raba dare tana zaune a ƙofar ɗakin da ta gaji ta ringa masifa ta koma ɗakinta. Washe gari ta yi ta masifa amma ko kallo bata ishe shi ba.
Zaune suke a kan benci shi da abokinsa Malam Hudu, Malam Nura ya ce
"Wannan dubu ashirin ɗon ka siyo mini shadda yadi huɗu yar dubu biyar biyar, wannan dubu biyar ɗin ka haɗo mini magani"
Ya kalle shi da mamaki ya ce
"Maganin mai?"
Yana masa hararar wasa ya ce
"Haba kai ma, maganin maza mana, gyara zan yi fa, ai shi ya sa ma na dakatar da su Haule daga zuwa turaka, saboda gyaran tarɓar amarya zan yi, ka ga kuwa tun da ba su na yi wa gyaran ba babu dalilin da zai sa suke zuwa mini turaka,sai dai wacce aka yi gyaran dan ita idan ta zo ta mora" Da dariya ya fashe ya ce
"Wallahi kaima abokina da wani abu to ina kai ina wani gyara" Yana masa wani kallo ya ce
",Naka wasa ne, ka san dai mata suna gyara to mu maza mai yasa ba za mu yi gyara ba? Gwara ka siyo mini ka ga ai ba raini" Karɓa ya yi yana faɗin
"Gaskiya na yarda amaryar nan ta musamman ce kana son ta, wato shadda ma sabuwa gal aleda mai kyau za ka yi ga magani," ,Shi ma dariya ya yi yana tuna irin son kuɗinsa sai dai ya samu yadika masu araha amma wannan karon dai ya yi ƙuri zai yi mai tsada.
Malam Hudu yana irga kuɗin ya ce
",Gobe ai da sassafe zan tafi kanon saboda na kammala abun da zan yi in gama, ni anya wannan Hadizar za ka iya sakin ta kuwa kamar yadda kake sakin sauran matan? Na ga fa ka kamu da sonta"
Ya yi tsaki ya ce
",Ita wa ta fi, ka san ai mace kamar riga na ɗauke ta in saka wannan in cire wannan"
Haka suka yi ta tattaunawa abin su suna tsara yadda abubuwa za su kasance, daman ita Hadiza ya sallame ta kuɗin da ta yanka masa yanzu kawai ɗaurin aure ne za a yi da tarewa
Mu je zuwa ba a fara wasan ba akwai ƙura mai tsakuwa ma kuwa🤔😹
MAMAN AFRAH
09025576222
[4/7, 5:00 PM] MOM MASHKR & AFRAH: https://chat.whatsapp.com/Bu295Z6iGnL3SoKYtgqnbZ?mode=gi_t
*UWAR AGOLA*
🅿️3️⃣
*Bojuwa herbs*
*By*
*Surayya Dee.*
*08032773332.*
*Sanyi flusher!*
*Yana wanko dukkan sanyin mara, mahaifa Har ma da jijiya.*
*Tasirin da karfin maganin sanyinmu ya wuce misali don kuwa duk wacce ta siya Slsai ta dawo ko ta turo wasu*.
*Alhamdulillahi Allah ne ya yi mana.*
*Tightening set na hade mace ta dawo Zamzam tamkar yar budurwa.*
*Tasirin magani Idan andafa tamkar yankan wuka ne shiyasa kazar sababi da ciccibin garari na surayya halin yau suke da kyau da tasirin gaske a jikin mace.*
*Muna da gimbiyar zabuwa da tattabarun alheri.*
*Akwia packages na mussaman ga Amare, uwargida ,zawarawa da masu jego.*
*Tuntubeta a wannan lambar*
*08032773332*
*Don samun ingantattun kayan gyara da babu algush.*
*UWAR AGOLA*
NA
MAMAN AFRAH
Labarin mai cike da abin dariya
*Daga marubuciyar*
*Ruwa cikin cokali, ci ma zaune, malamin bogi, ƙazamin miji, Bonono ƴar zaman wanka, ruɓaɓɓiyar igiya ƴan adaidaita sahu, ƙara,in inna delu, jalli joga, Beelal, ungozoma da sauransu.*
09025576222
🅿️3️⃣
Tun da ya kama hanyar zuwa gidansa yake jin farinciki don yana son ba marar ɗa kunya a wannan ƙarin auren da zai yi, musamman da Kuluwa take son hana shi rawar gaban hantsi tana son shige masa hanci da ƙudundune. Shi kuma bata san hakan ƙara rura masa wuta take ba tana ƙara zuga shi domin ya saka a ransa cewar zai yi abin da zai shallake mata tunani abib da bata zata ba, sai ya cusa mata takaici tun da shi bai saba idan zai yi ƙarin aure mace ta takura masa ba ko ta nuna rashin amincewar ko ta ɗaga masa hankali sai a kanta, don ita Haule in don ta ita ne duniya ta zauna lafiya.
Ko da ya ƙarasa gidan tsaye ya tarar da ita tamkar tana jiran dawowarsa. Yana sallama amma bata amsa ba sai Haule ce ta amsa masa daga cikin ɗaki. Zai wuce ta sha gabansa ya ƙara ratsewa ta sake shan gabansa a ƙufule ya ce
"Mene ne kuma?" Tana masa kallon raini ta ce
"Duk abin da ka zata shi ne, ko in ce duk abin da kake ji da shi ni ɗin ma shi nake ji" Kallon ta ya yi ya a ransa ya fara tunanin anya wannan za ta bari ya ci amarcin nan a kwanciyar hankali kuwa? Zuciyarsa ta fara raya masa cewa ko dai ya aikata gidansu amma ba da zummar saki ba, tun da ya saka a ransa ba zai sake ta ba sai ya gama amfanar kuɗinsa amma dai yanzu tun da tana son kawo masa cikas gwara ya ce ta tafi gidan, sai dai ya ƙudiri cewa ba zai dawo da ita ba sai bayan wata biyu wataƙila ma lokacin ya saki Hadiza ya fara neman wani auren.
Gyaran murya ya yi ya ce
"Kuluwa abin naki ya fara yawa, ke baki san mace mai kishi fita take daga zuciyar miji ba?" Ta kama ƙugu da hannu ɗaya tana jijjiga jiki ta ce
"To na nawa kuma? Ai na san wannan bazawarar da kake kira mai jiran gado ta daɗe da yin fatali da ƙaunata daga zuciyarka, shi ya sa baka ganin kaina da gashi"
Haule da ta fito daga ɗaki ta mata kallon ɗaya saura kwata ta ce
"Kuluwa ya kamata ki wa kanki faɗa, ki yi karatun ta nutsu, shi mijin da ya damu da kai shi kake kishi a kanka, kuma wa ya ce miki akwai ɓurɓushin ƙaunarki a zuciyar Malam da har kike ikirarin wata ta tunkuɗe son naki, idan baki sani ba in faɗaa miki, daga lokacin da mace ta sako ƙafarta a cikin gidan Malam Nura daga ranar duk wata ƙaunarta take bankwana daga zuciyarsa shi ya sa zaman ba ya iya zuwa ko ina ake rabuwa domin daga ya hango wata zancen ta cikin gida ya ƙare amma kin ɗauki kishi kin hana rai da zuciyarki sakat ki kafa faɗin wai mai jiran gado shin ke idan ta jira gadon sai me? Kafin ta jira gadon mata nawa ne suka jira dan Allah ki sauƙaƙawa kan ki amma shawara....
Cike da masifa da kallon raini ta ce
"Haule ki kama girmanki idan ke bakya son Malam ni ina son shi, dan haka babu ruwanki da ni ki riƙe shawarar ki"
Haule tana kwashe kayan shanya ta ce
"Allah baki haƙuri" Daga haka ta kama kanta bata ƙara cewa komai ba ta ci gaba da sabgar gabanta.
Malam Nura ya ce
"Matsa in wuce" Ta yi ƙememe ko gizau bata yi ba. Hannu ya sanya ƙiii ya yi gefe da ita, da fisge ta sake shan gabansa cike da ƙosawa ya ce
"Mai kike so ne wai?"
A zuciyarta tunaninta masifar da ta addabe shi da ita ce ta yi tasiri dan haka ta sake tamke rai ta ce
"So nake ka fasa auren wannan amaryar taka" Baki sake yake kallonta sai kuma ya fashe da dariya ya ce
"Tambaya ɗaya zan miki idan bar kin amsa to"
Ta ce
"Ina jinka"
Ya ce
"Kin taɓa ganin wanda ya mutu ya dawo?" Tana masa kallon rashin fahimta ta ce
"Ban gane ba"
Ya ce
"Idan har wanda ya mutu yana dawowa to haka za a fasa auren" Kallon ƙurilla ta masa don ta san kawai raina mata wayo ya yi hakan ya sa ta ce
"Mai kake nufi?"
Ya ce
"Ba zai taɓa iyuwa ba ke ni da a ce auren nan an fasa to gwara aurenki da ni ya mutu" Yana faɗar haka ya juya zai tafi ta kamo rigarsa daga baya ta janyo shi ƙiiii tamkar wanda daman tigar tasa take jiran a ja haka ta shiga yagewa domin daman kayan sun ga yau sun ga jiya sun gaji fa shiga ruwa. A ƙufule ya juyo ya kai mata mari ta sunkuye ya mari iska yana zare ido ya ce
"Kama hanya ki tafi gidanku" Gabanta yana bugun uku-uku ta zaro ido don tunanin ta sakin ta ya yi hakan ya sa ta ce
"Ban gane in tafi gidanmu ba"
Cike da ɗaga murya ya ce
"Eh ki tafi sai na neme ki"
Ɗan sanyi ta ji a ranta a ƙalla ba sakin ta ya yi ba.
Cike da cika baki ta ce
"Ai da ba a kawo ni gidanka ba sai da aka ɗaura mana igiyoyi uku dan haka yanzu idan baka warware ba babu inda zan je"
Faɗa aka shiga zabgawa ita da shi amma ta ƙi tafi shi kuma so yake ta tafi ko ya sake idan amarya ta zo don ya lura lamarin Kuluwa babu sauƙi wai ciwon arne.
Kiran Hadiza ya yi a waya ya ce yau ba zai samu zuwa ba, dan haka ta ce ya aiko a kawo mata kuɗin kari, haka ya ba wani dubu biyu ya kai mata, shi kuma ya ƙuduri aniyar kai Kuluwa gidansu tun da ita ta ƙi tafiya, ya kore ta amma ta ƙi saboda naci.
Tana banɗaki ya je ɗakinta ya ɗakko kaya kala goma ya kai ɗakinsa ya zuba a zani ɗaya ya ƙulle, ya fita ya ba wani saurayi yw ce ya ajiye masa zai kira shi, haka ya karɓi kayan shi kuma ya dawo gida.
Ɗakinsa ya shiga sai da ya ji fitowar ta daga banɗakin ya fito, yana fitowa ya washe baki ya ce
"Ina gwanar wani ga tawa, Kuluwa ta Malam Nura bada kanki a sarw ki je gida ki ce ya faɗi, ni da ke amana ce babu rabuwa kowace mace sawu take, take miki" Kuluwa tana dab da shiga ɗakinta ta fara jin wannan batu hakan ya sa ta dakata tare da saurin jiyowa don ganewa idanunta. Rass idanunta suka yi tozali da Malam Nura har ta shuga ƙarewa tsakar gidan kallo tunanin ta ko da wata yake, sai dai ambaton sunanta da ya yi a maganar hakan ya bata tabbacin da ita yake. Wani irin washe baki ta yi tana tunano cewar ɗazu da ta yi salaar magriba ta yi ta addu,ar Allah sa ya fasa auren Hadiza Allah sa ya daina ganin kowace mace sai ita, hakan ya sa ta fara tunanin tabbas addu,ar da ta yi ce ta karɓu.
Haule tana jin su a ɗaki ita da su Kabiru duk da yaran suna hayaniya amma hakan bai hana ta jin abin da Malam ya faɗa ba, sai dai hausawa suka ce sanin hali ya fi sanin kama, shi ya sa aka ce duk daren daɗewa idan ka daɗe baka tare da mutum to ka tambayi komai nasa amma ban da hali domin halinsa yana nan shi hali zanen dutse ne!. Ta san halinsa kamar yunwar cikin ta, kuma ta san ruwa ba ya tsami banza, dole akwai wata maƙarƙashiyar da yake shiryawa Kuluwar amma da yake idanunta a rufe suke ba za ta gane waye Malam Nura ba, shi ya sa har yau tana fata da kuma jiran ranar da Allah zai fitar da haƙƙin matan da yake kansa wanda ya ɗauka tun da ta san matuƙar ana kwana ana tashi zai auro daidai da shi wacce za ta zame masa ƙarfen ƙafa ta ganar da shi shayi ruwa ne!.
Kuluwa ta wani gyara tsayuwa haɗe da gyara ɗaurin ƙirjin da yake jikinta, daman ruwa ta watsa tana ƴar dariya ta zumbura baki ta ce
"Kamar gaske" Danne dariyarsa yake don ya lura har ta bada kai bori zai hau, hakan ya sa ya ce
"To da wasa ne?"
Tana kallonsa don yanzu ta fara takowa zuwa gare ta ta.ce
"Ai ka ce babu kowace mace a gabana amaryar taka mai jiran gado fa?"
Ya ƙyalƙyale da dariya irin ta ƴan duniya ya ce
"Rabu da ita ai da tsohuwar zuma ake magani, ai ni yau babu abin da zai sa ma in je wajenta hira, kin san dai tun da na fara neman auren na kullum sai na je hira ko? To yau ba zan je ba yau ranar ki ce, kuma ina miki albishir da cewa maganar auren ma janyewa zan yi" Ta masa tsuru da ido sai dai da ta tuna cewa addu,a ta yi kuma babu abin da ya gagari ubangiji sai ta yarda da maganarsa.
Ganin hakan ya ɗora da faɗin
"Yau gidanku za mu je mu gaishe da babanku sannan mu je duk inda kike so a tare daga haka mu dawo gida" Kanta ne ta ji ya yi wani gingirim ta fara tuno irin tsiyar da za ta shuka hakan ya sa ta ce
"Yau fa bakin girkin Haule ne"
Sai da ya ɗan kalli ɗakin Haulen ya yatsina fuska lokacin Haulen ta taso ta leƙo ta window inda ta ɗaga labule ya taɓe baki ya ce
"Rabu da ita, kin manta daman na ce bakin girki kawai za kuke yi sannan ma ita fa babu ruwanta, to ma ya za a yi ta haɗa kanta da ke, ai ke ce ta gaban goshi" Bakin ta har kunne ta washe, Haule ta saki labulen tana danne dariyarta don ta san wata tsiyar zai shuka amma da yake ita Kuluwa dukan iska ce har yau bata gane inda ya saka gaba ba, bata taɓa tantance waye namiji sai ya shuka mata tsiyar ta zo tana tagumi da balbalin bala,i.
Ɗaki ta shiga ya bi bayanta, rigarta da zani na kan gado da ta ajiye ta ɗauka ta saka, yana zaune a bakin gadon yana mata daɗin baki, ta ɗauki mayafi ta yafa kasancewar ko drower kayanta bata buɗe ba shi ya sa bata san ya kwashi kayan ta ba.
Sai washe baki take suka fito ta rufe ɗakinta, shi ma ya rufe nashi ɗakin suka fita ko sallama ba su yi wa Haule ba, Kuluwa jin ta take a sama don miji yana yayin ta.
A jere suke suna tafiya sun kama hanyar gidansu Kuluwar, suna tafiya suna hira Kuluwa ta ce
"Nurana na kaina"
A fili ya ce
"Ke kaɗai kuwa"
A zuciya ya ce
'Sakarya za ki gani shayi ruwa ne, banbancin suga ne kawai da lipton'
Tana washe baki haɗe da kafe shi da ido ta ce
"Haulen fa?" Hararar wasa ya mata ya ce
"Ke wai sai kike maganar gawa shin gawa tana da amfani bayan san cire mata rai?" Ta yi shiru don bata gane ba ta ce
"Gawa dai kake nufi" Haushi ya kama shi don Haule ta fita saurin gane zance ita kamar kidahuma sai an mata ɓaro -ɓaro.
Cike da ƙosawa ya ce
"Ina nufin ita bata da amfani ne a gidan" Ta ƙyalƙyale da dariya har wasu ƴanmata guda uku da za su wuce ta kusa da su suka bita da kallo.
A sake kallonsa ta ce
"Hadizar fa?"
Ya yi tsaki irin na gajiyawa da maganr wasu matan da take masa ya ce
"Na ce Haule ma bata da amfani bare wata Hadiza da bata zama matata ba"
Allah ne kaɗai ya san daɗin da take ji a ranta ta washe baki ta ce
"Zan iya zaginta baka ji komai ba?" Kafin ta yi zagin shi ya fara kama sunan Hadizar ya zaga yana faɗin
"Ƙarewa ma ai kin ji na zage ta da kaina, ni fa bana ganin kowa sai ke"
A zuciya ya ce
'In dai zan ci amarci bakya gidan nan gwara ko me zan yi in faɗa ' Ƙaran wayarsa ce ta katse musu maganar ya dakata da tafiya bayan ya fito da wayar daga aljihu ya ga sunan Hadizar ya ce
"Hudu ne yake kirana" Ya faɗa yana ja gefe ya ɗaga wayar haɗe da ƙasa da murya ya ce
"Amarya bakya laifi ko kin kashe ɗan masu gida, amarya mai maganar zuma" Bata amsa masa ba ta ce
"Maganar kayan da zan yj fitar biki ne, na ga yau baka zo ba yau na so mu yi maganar, ka ga lokaci yana wucewa saboda ɗinki ga kuma su Zainaba ba kai kuma uban nasu baka ce komai ba kan kayan namu" Shiru ya yi kansa yana juyawa shi ya ma rasa abin faɗa, abu na farko yana tunanin shi da ya cake kuɗi ya bata dubu ɗari biyu bayan kaf kauyen nasu dubu ɗari biyu da hamsin ne kuɗin budurwa ma bazawara dubu ɗari amma ta matsa masa ya bata dubu ɗari biyu kuma yanzu take masa maganar kayan fitar biki? Har tana ambaton wasu agololi shi ina ruwansa da kayan da ƴaƴanta za su saka shi da burinsa bai wuce a ɗaura aure ya ɗauke ta ta koma gidansa ya daina ganin ƴaƴan nata ba don ko gidansa ba zai ke basu fuskar suke masa difdiftu ba.
Sai da ta sake magana ya dawo hankalinsa ya ce
"Yanzu ina gidan Baba Ramma muna magana zan kira ki in na koma gida" Ta amsa masa tana yanke kiran, ya kara wayar ya taho yana ɗaga murya yana cewa
"Haba kaima Hudu na faɗa maka ni da rabin raina ne Kuluwa za mu je gidansu mu gaishe da su, to sai na dawo ma ƙarasa" Kuluwa sai wani washe baki take, haka ya ƙaraso suka ci gaba da tafiya tana masa magana ta ji ya ce
"To kayan uban me zan saya kuma" Kuluwa ta tambaye shi sai lokacin ya gane ɓaranɓaramar da ya yi, don ya gane maganar zuci ce ta fito fili ya ce
"A,a daman Hudu ne yake cewa na fasa sayan kayan amaryar na ce kayan uban me zan saya ni da na fasa auren" Dariya ta yi ta ce
"Ai ni so nake idan muka dawo daga gidanmu mu biya gidansu Hadizar nan a kira ta ta fito in zage ta tassss in faɗa mata daman bakin rijiya ba wajen wasa makaho ba ne, in ce a bi wani sarkin amma ba wannan ba" Gabansa ne ya faɗi amma da ya tuna cewa a gidansu zai barta shi kaɗai zai dawo sai ya yi dariya ya ce
"Nima zan taya ki" Dariya suka yi su duka, lokacin sun ƙaraso gidansu Kuluwar.
Dakatar da ita ya yi ya ce
"Na saya klin da sabulai na wanka da wanki da za ki kai musu, bari na kira a kawo mana sai mu shiga da ƙwarin gwiwa" Sosai ta ji daɗi, wayarsa ya ɗauka ya kira wanda ya ba ƙullin kayan Kuluwa, ya ce ya kawo masa gidansu Kuluwa yana ƙofar gidan. Amsa masa ya yi da to gashi na zuwa.
Saboda ya san halinta matuƙar ta ga kayan ba lallai ta shiga gidan ba, hakan ya sa ya ce ta shiga gidan ta faɗa musu zai shigo, da murna ta shige gidan shi kuma a take ya kira Hudu abokinsa yana labarta masa maganar da Hadiza ta faɗa masa yana ta kumfar bakin cewa son samun ta ya yi yawa kar fa ta fara tunanin za ta wanki aljihunsa ne, Hudu yana ta bashi haƙuri domin ya bi komai a sannu haka ya kashe wayar ransa yana ƙuna ya tsani duk wani batu da za a yi na taɓa kuɗi amma ya ga Hadiza idanunta idon kuɗi.
Kashe wayar ya yi daidai da zuwan mai kawo kayan haka ya karɓa ya kutsa kai cikin gidan ya tsaya a zaure wani ƙaninta ya zo ya ce an ce ya shigo. Kuluwa tana zaune a kan tabarma kusa da mahaifiyarta mahaifinta yana kan tashi tabarmar yana sauraren rediyo sai ƙannenta mata guda biyu suna cin tuwo. Da sallama ta shigo aka amsa masa ana masa faram-faram mahaifinta zai iya cewa tun da aka ɗaura auren bai sake ido huɗu da Malam Nura a gidansa ba, sai dai su haɗu a hanya haka ma mahaifiyarta sai dai idan ta je gidansa amma yau gashi dan badangarci har cikin gida ya zo, kuma tare da ƴarsu wannan abin farinciki ne musamman da Kuluwar ta ƙyanƙyasa musu cewar klin da sabulai ya tsaya a wajen za a kawo masa wanda za a basu tsaraba, ta faɗawa mahaifiyarta hatta auren ma ya fasa, daɗi sosai uwar ta ji domin a tarihin aure-auren Nura kowa ya sani a ƙauyen Shabaru bai taɓa nemab aure ya fasa ba!.
Maimakon su ganshi da leda riƙi-riƙe sai suka ganshi da ƙullin kaya, ita dai mahaifiyar Kuluwa saboda son samu tunaninta ɗinkuna ne ya musu aka ɗauro a zani, amma Kuluwa da ta yi wa zanin da aka ɗaure kayan ƙuru tabbas ta gane kamar dai atamfarta!.
Malam Nura ya zauna a kan tabarmar da aka shimfiɗa masa daga gefe kusa da ta mahaifin Kuluwa duk da daman babu wani ganin girman juna tsakaninsu tun da akan biyan bashi suka yi ta ɗauki babu daɗi har dai ya bashi auren ƴarsa a kan hakan. Ƙullin ya ajiye a gabansa ya shiga gaishe da su suna amsawa, amma Kuluwa ta yi mutuwar tsaye sai dai hasashenta bai kai kan gaɓa ba, domin iya tunaninta bata taɓa kawo cewa zai ɗakko kayanta ya kawo ta gida ba, da a ce ta yi wannan tunanin da ta tabbatar cewa Malam Nura ba ƙaramin ɗan duniya ba ne, sannan da hankalin ta ya fahimtar da ita cewar maganganun da Haule take faɗa masa gaskiya ne sun ishe ta ɗaukan darasi sai dai ba haka ba ne, ranta ya kissima mata cewar ko dai ɗakkowa ya yi ya kawo a bayar zai ɗinka mata wasu, amma mai ya sa bata ga kayan ba sai yanzu, sannan ina ledar sabulan, wannan tambayoyin take ta yi a zuciyarta.
Mahaifin Kuluwa ne ya ja shi da zance yana tambayar Baba Ramma inda mahaifiyarta ta yi ƙasa da murya ta ce
"Kuluwa ko dai ɗinkuna mijin naki ya iyo mana? Gaskiya yarinyar nan kin samu mazaunan zama a gidan miji" Daɗi
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 3 Chapter of 12