yin tsaye.
“Ranki shi daɗe ga ni na samu saƙonki ne a yanzu” ta faɗa cike da ladabi,sai kuma na ji babu daɗi yadda ta zubar da duk wata dangantaka da ke tsakaninmu ta bani matsayin shugabarta.
Da ido na yi mata nuni da ta zauna,ta cire takalminta na fata ta zauna tare da maida hankalinta a gare ni.
“A cikin tarihi wace ce aljana zaƙuma?”
“Aljana ce mai matuƙar santsi da farin fata,tana ɗauke da kambun Maitar shan jini.Lokutan da ta fitowa shi ne dare musamman wuraren jeji ko kusa da rijiya.Tana jan hankalin mazaje musamman maharba don su ne suka fi shiga jeji,tana fitowa cikin siffar barewa haka za ta yi ta wasa da hankalin maharbi har sai ya faɗa tarkonta sai ta ja shi izuwa duniyarta” Deborah ta faɗa tana mai buɗe littafinta sai ta nuno mini hotonta,kallo ɗaya na yi masa na kawar da kai.Sosai ta fito a siffar mayyar shan jinin kuwa don bakinta kaca-kaca yake da jini.
“Kika ce maharba sun fi shiga tarkonta ?” na tambaya.
“Eh haka tarihi ya zo da shi”
“Meke faruwa bayan ta kama mutum?”
“Tana kai shi wani kogo ne,sai ta basa zaɓi biyu.Na farko zai bauta mata,in kuma ya ƙi zaɓi na biyu shi ne za ta kashe shi”
Ummilo na duba ina mai cewa “dukkan alamu sun nuna ita ce ta zo yau don har yayyafin jini aka yi”
“Hakan na nufin tana son jan ra'ayin wasu mazajen ne ,don haka mu zama cikin shiri” Ummilo ta faɗa .
Deborah ta girgiza kai tana mai cewa “ Aljana ZAƘUMA ba ta taɓa bayyana a wurin da ba a ambace ba ko kuma sunan ɗaya daga cikin waɗanda ke baƙin tsafi da ita.Tun da kuka ga ta zo to tabbas a garin nan akwai mai yin aiki da ita”
Da wani mugun sauri na dube ta,a cikin ƙwayar idonta na hango tana zargin mijina Banah da wannan ɗanyen aikin.Ban san me ta gani ba ita a nawa idon sai ci gaba ta yi da cewa “ta yiyu kuma wucewa ne kawai ta zo yi,don haka za ki iya yin watsi da lamarin mu gani in za ta sake dawowa”
Numfashi na furzar tare da jinjina kai,Ummilo ta karɓi littafin tarihin tana mai cewa “ina mugun son labarun tarihin ƙarnin da ya wuce musamman a kan maita,shin a page lamba ta nawa ce zan samu tarihin Mayu da kuma yadda suke rikiɗa daga bil'adama zuwa dabbobi?”
Deborah na shirin yin magana Banah ya shigo hannunsa riƙe da manyan kifaye,da dukkan alamu kuma ya ji tambayar da Ummilo ta yi duba da yanayin yadda fuskarsa ta cika da tsantsar mamaki.
“Jira na zo na fayyace miki komai Ummilo ” ya faɗa yana mai miƙawa wata hadima kifin ya zo kusa da ni ya zauna sannan ya karɓi littafin tarihin ya mayar wa Deborah da kayanta sannan ya kamo dukkan hannuwan Ummilo ya ce “a duk lokacin da mutum yake son rikiɗa zuwa dabba da farko zai ɗan rage tsayi sannan ya furta kalaman tsafi yana mai tsayar da ƙwayar idonsa wuri guda ba tare da ya ƙyafta ba.Bari na nuna miki ta yadda za ki gane sosai” sai ya saki hannuwanta tare da yin tsugunne ya soma magana a hankali amma duk muna iya jiyo sautin.Cak kuwa ya tsayar da idonsa suka bar motsi,babu jimawa ya koma narkeken kare baƙi ƙirin yana wani fito da harshe waje.
Duk da ni ma yau ne karon farko da na ga canjin siffa sam ban ji wani tsoro ba sai ma burge ni da lamarin ya yi na soma yin murmushi.
Cikin firhici Ummilo ta furta “ Ya Ubangijin Ka'aba ka tseratar da ni daga sharrin wannan halittar” sai kuma ta soma yin ihu tare da tashi za ta zuba a guje,ni da Deborah muka yi saurin taro ta yayin da Banah ya yi baya yana haushi cikin hassala.
Hakan da yake ba ƙaramin ƙara firgita ta ya yi ba,ni kuma lura da hakan yasa na juya na yi masa tsawa sai a lokacin kawai ya dawo cikin siffar bil'adama.
Ummilo ta soma furzo wani zance “kar ki cutar da ni Ummu A'ishah ki sani ban taɓa aikata maita ba,wacce ke maƙale a ruhina ba sayenta na yi ba kyauta ce daga wasu ruhikan da ke zuwa mini cikin MAFARKI (MRS SADAUKI akwai littafin nan na MAFARKI complet mai so zan barsa shi a 700 maimakon 1k) .Ban so ki bari in ba haka ba zan tona miki asiri na faɗa kowa ya sani ke ce mai yin Maitar dare” tana kawowa nan sai numfashinta ya tsaya cak sai da muka tallabe ta tare da shimfiɗe ta.
Deborah ta ce “ da dukkan alamu ita ma ta fito a yanki da ke maita duk da dai a yadda take furuci Maitar ba ta yi ƙarfi ba.Sannan ita wannan Ummu A'ishar tana ɗaukar siffar kare ne a duk lokacin da za ta yi maita ”
Banah ya matso yana cewa “ai da na san haka ne da na ɗauki wata siffar,amma sam ban yi haka da wata manufa ba”
Na ce “kar ka damu na fahimta,daga yau sai ka kiyaye” ya jinjina kai.
Deborah ta ce “ni zan koma,in ta farka ki ce ina yi mata sannu da jiki” haka muka rabu.
★
Yarima NASLAM ne kwance yana yin bacci yayinda tantabarsa ke tsaye ƙiƙam tana kallonsa sai da ta gaji don kanta kafin ta ɗaga fukafukinta ta je ta sa ƙafafunta ta ciro shi sama tare bi ta window da shi ta fita.Haka ta dinga zaga duniyar ɓoye da shi yana cikin wani yanayi wanda shi ba bacci yake yi ba kuma idonsa ba a farke ba.
Cikin wani jeji mai cike da dragon ta sake shi ,shuuu yayi kamar zai faɗi amma sam jegaran ba su bari hakan ta faru ba haka suka buɗe fukafukinsu wuri ɗaya ya faɗo a sama. Kafin kuma su kai shi kan wata lafiyayar shimfiɗa da aka yi da ganyen furen floris.
Yarima NASLAM ya ja wani dogon numfashi tare da ɗan ware idonsa,nan ne ya yi arba da sarauniya Naomi cikin shigar ganye,ta rufe ƙirjinta da fatar lemun zaƙi kugunta kuma ta suturta shi da bayan albasa.Gashin kanta kuwa ya ci ado da ganyen lemu,tafiya take yi cikin yanga da jan hankali har ta zo gare shi.Kan shikinsa ta kwanta tare da yi masa rumfa kafin wasu lamurra su biyo baya waɗanda suka kusan sheƙa shi lahira.Yana gama samun nutsuwa ya farka daga baccin,a kan shimfiɗarsa ta asali ya samu kansa ƴar tantabarsa na can gefe tana bacci.
Ya dafe kansa yana jin wani irin takaici na rufe shi,saboda shi babu wacce ya tsana irin aljanar mafarkinsa.A gajiye kamar wanda yayi mu'amalar a gaske ya ƙoƙarta ya tashi tare da shiga toilet,sai dai fa babu ruwa ba ciki babban bokitin ruwan ba.Ya ja tsuki ya fito kafin ya soma ƙwala kiran sunan jakariya Ali,dama ɗakinsa yana kusa da nasa babu jimawa kuwa ya shigo hannunsa riƙe da sharɓeɓiyar takobi duk a tunaninsa farmaki ne aka kawo musu.
Turus yayi ganin iya yariman ne kawai a ɗakin,ya yi saurin ajiye takobin yana mai cewa “ranka shi daɗe me kake buƙata?”
“Babu ruwa a banɗaki” yarima ya faɗa yana jin ƙyanƙyamin kansa,da sauri jakariya Ali ya fita babu jimawa ya dawo jaye da baro an lodo ruwa a ciki.Banɗakin ya shiga ya juye ruwan kafin ya fito,sai a lokacin yarima ya shiga sai ya ga hatta bahon wankan Ali ya cika masa shi da ruwan.
Kwanon da ake zuba ruwa a ciki domin yin alwala ya ɗauka ya soma wanke hannunsa sau uku bayan ya ɗauki niyyar wankan.Daga nan yayi ɗahara sai ya wanke kansa tasss kafin ya game jikinsa duka,daga ƙarshe ya kurkure bakinsa ya kuma yi shaƙar hanci.Sai a lokacin kawai ya ji nutsuwa ta ratsa shi sai ya shiga bahon wankan ya kwanta a ciki,tunanin gimbiya A'ishah yake son yi amma da zarar ya fara cankar surarta sai fuskar Naomi ta zo ta yi fakan-fakan a dole ya haƙura ya fito ya ɗaura alwala ya zo ya fara yin sallar nafila.
A ɓangaren gimbiya A'ishah kuwa tsakiyar dare Dadda ta tashe ta,tana shirin yin magana amma Dadda ta toshe mata baki tare da janta suka je bakin window suka yi tsaye suna fuskantar farin wata da ke wasar ɓuya cikin giza-gizai.
Dadda ta soma yin magana a hankali tana cewa “a wurin Mayu dare shi ne lokaci mafi tsaro domin farauta,duk da cewa ana iya sarrafa maita safe ko rana amma irin wannan lokutan an fi yinta a cikin siffar bil'adama yayin da ita kuma ta dare ake ɗaukar ɓoyayyar siffa.Yau zan nuna miki romon da muke sha duk dare ni da sauran Mayu na wannan Daular ”
Cike da mamaki gimbiya A'ishah ta ce “dama bayan ke akwai wasu Mayu a cikin daular nan?”
Dadda ta yi wani irin murmushi kafin ta ce “idonki za su yi matuƙar mamaki in ki ka ga wasu mutanen” tana gama faɗar haka sai ta jimƙe hannun gimbiya A'ishah tana furta wasu surkulle nan take suka sama wasu ƴan ƙananu kamar sauro tare da tashi sama suka bi ta window.....
Za ku iya fara yin payment domin shiga paid group . 500 ta wannan account:
2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank
Shaidar biya ta WhatsApp +22795045822
[12/04 19:22] MRS SADAUKI: *TIF DA TAYA*🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐
"""""""""""""""""""""""
LoVe aNd HoRrOr StOry☠️
```MRS SADAUKI```💫✍️
FCWA☀️
____________________________________________
09
Yana ɗaya daga cikin tabi'un Mayu yin yawon dare a lokacin da mutane ke yin bacci,saboda babu dare yana ƙunshe da sirrika dayawa.Gimbiya A'ishah baki da hanci ta buɗe tana kallon duniyar ƙasa,cike kuma da burge wa da ban sha'awa take ware idonta tana kallon gidajen da aka rufe babu bismillah.Kamar misalin tukunya ce babu murfi,haka idon Mayu ke gane gidajen da ba a ambaci sunan Allah ba a lokacin da ƙafa ta tsana za a kwanta.
Suna cikin shawagin suka yi ta haɗuwa da jiragen dare na Mayu, waɗanda suka kasance na tsafi ba wai zahiri ba.
“Duk ina za su je Dadda? Ya na ga mutane cikin gwangwanin kifi?” gimbiya A'ishah ta tambayi mahaifiyarta sai dai kafin ma ta bata amsa wani jirgin na tsintsiyar tsaye ya bi ta gabansu shuuu yana ɗauke da wata tsohuwa da kuma ƙaramin yaro.
Dadda ta yi murmushi tana mai cewa “A'ishah a duniyar ɓoye abubuwan da ba za su taɓa faruwa ba ne a duniyar zahiri suke gudana a nan ɗin.Muna amfani da duk wani abu da kika sani matsayin jirgin farauta,kamar irinsu turmi,jan zanen isimi,tsintsiyar tsaye da sauransu.Ke ma in kina sha'awa ai za ki iya hawa madadin ki yi yawo kamar leda”
“To mene ne banbancinsu Dadda?”
“Sauri! In kin hau jirgi kin fi saurin zuwa inda kike so,ko ba ki lura yadda mutane ke ta wuce mu ba?”
“Na gani,amma me yasa mu ba mu shiga ba?”
“Dama ina son fayyace miki komai ne,amma yanzu da zarar wata tawagar mayun za ta wuce zan tsayar da su don rage mana hanya”
Ai kuwa babu jimawa sai ga wata tsohuwa zaune kan baƙar akuya mai ƙahonni dogaye.Dadda ta tsayar da ita tare da neman alfarma,tsohuwar ta ƙara matsawa gaba gimbiya A'ishah ta fara hawa sannan Dadda daga ƙarshe.Kamar wani babur haka akuyar tsafin ke keta hazo da su.
Gimbiya A'ishah wacce duniyar ɓoye take sabuwa a wurinta sai cewa ta yi “ita ma akuya tana cikin jerin jiragen yawo?”
Wannan karon tsohuwar ce ta bata amsa bayan ta yi ƴar dariya mai fitar da zallar tsufanta,ta ce “ jikata ita akuyar nan protector ɗina ce,suna da banbanci da jirgin dare saboda ita tana numfashi sannan kuma tana kare ni daga dukkan sharri” gimbiya A'ishah ba ta kai ga cewa wani abu ba tsohuwar ta yi ƙasa da ƙahonnin akuyar sai ta yi shuuu ta fara yin ƙasa har ta sauka a wani babban gawo wanda ya cika tanƙam da Mayu da kuma matsafa.
Girki ake yi kan wata tunkunya wacce ke da zanen ƙwarangwal ta buɗe baki.Gimbiya A'ishah ta sauko daga kan akuyar tana wani riƙe Dadda ,ita kuwa sai cewa ta yi “ wannan ita ce TUKUNYAR MAYU ( ga mai son complete na Tukunyar Mayu yayi mini magana zan yi masa discount) duk dare muna haɗuwa a nan mu ci abin da wasu daga cikinmu suka yo farauta”
Sai kuma Dadda ta ja ta suka ƙarasa,hannu ta saka cikin tukunyar da ke ta faman tiriri ta tsamo wani abu mai kamar zare amma su a wurinsu nama ne,bakin gimbiya A'ishah ta kai ita kuwa ta buɗe ta saka mata sai ta soma ci tana jin wani irin yanayi na ratsa ta.
Dadda ta saki murmushi tana jin wani sanyi na luluɓe ta,a yanzu shirye take tsaf wurin tursasa ƴarta ta auri yarima Naslam ba don komai ba don ta san a cikin tabi'ar Mayu babu kara babu jin kunya,hatta uwar da ta kawo su duniya suna iya damƙewa ita kuma babban burinta shi ne ta bayar da yarima NASLAM a dafa shi kowa ci kamar yadda yasa aka yanke wa Ummarta hukunci kisa daga kawai asirinta ya tonu ta damƙe kurwar iyayen jakariya Ali.
Bayan sun gama cin naman sai idanun gimbiya A'ishah suka ƙara buɗewa ta soma gani tarau ,babu abin da ba ta iya gani da ke jikin mutum ko dabba.Rawa suka soma yi suna zagayen wuta,duk da mutane sosai hakan bai hana ta gane wasu fuskokin ba sosai kuma ta yi mamaki kamar yadda Dadda ta ce mata tun kafin zuwansu.
Alfijir na dab da ketowa suka koma gida,ta inda suka fita ta nan suka shigo.A gajiye duk suka zube suka ta yin rankon baccin da ba su yi ba.
A ɓangaren yarima Naslam kuwa tun bayan sallar asubah ya je ya samu sarki da maganar aurensa da gimbiya A'ishah.Ya yi haka ne duk don ya bar mafarkin Naomi,ba tare da ya san alƙaluman ƙaddara sam ba su rubuta masa auren wata mace ba bayan maƙiyiyarsa.
Gari na yin haske sosai sarki ya bada shelar baikon yarima zai kasance a yau bayan sallar asar in sha Allah.
Jakariya Ali ne ya dinga taimaka masa wurin shiryawa,yana daidaita masa hullar sarauta a kai ya ce “kana ganin kun dace kai da gimbiya A'ishah?”
“Me ya ja ra'ayinka wurin yin wannan tambayar?” cewar Yarima yana kallon mai tsaron lafiyarsa Ali .
Shi kuwa kai tsaye ya ce “na ga ba sonta kake yi ba”
“Haka kuma ban ƙinta“
“Duk da haka dai ya kamata a ce ka yi dogon nazari,na fi yi maka sha'awar auren soyayya gaskiya”
“Ita ma ina sonta tun da har na damu da ita” yarima ya faɗa yana mai zuwa bakin gado ya yi zaune,jakariya Ali ya duƙa ya soma saka masa takalmi yana mai cewa “in kana son mutum bai kai sai ka faɗa ba,ayyukanka ne za su bayyana hakan”
“Ko ma dai mene ne na yanke shawarar zan aure ta,kuma ta dace da ni tun da tana da addini sosai iya wannan ya wadatar” yarima ya faɗa yana tsayar da idonsa kan tantabarsa wacce ta yi wani saƙo kamar mai sauraren hirar da suke yi.
Jakariya Ali ya juya ya dubi inda yake kallo,sai ya saki ɗan murmushi kafin ya je ya ɗauko ta ya miƙawa yarima.Ya karɓa tare da soma shafar kanta,“zan je na duba na gani in sun gama shirya wurin taron” Ali ya faɗa tare da ficewa.
Yarima ya miƙe tsaye tare da zuwa bakin window yana kallon yadda ake ta kai komo cikin masarautar.Ko ina yayi kyau,hatta dawakai an yi musu ado na sarauta .Dokinsa wanda yake hawa a duk lokacin da zai fita yayi wani irin kuka,tantabarar hannunsa ta fizge tare da fita a guje tana kaɗawa yarima iskan fukafukinta da sauri ya lumshe ido kafin kuma ya ware su yana kallon yadda ta je ta hau kan dokin,duk wannan ɗin ma bai sa ya zargi wani abu ba kawai murmushi ya yi tare da fita.
Masjid ya fara zuwa,bayan an gama sallah ne duk aka dugunzuma zuwa wurin da aka ware domin gudanar da shagalin bikin baikon.
Zinare sarki ya ware masu yawa ya bayar matsayin kyautar mun gani muna so.Ayyub wanda ya kasance mahaifin gimbiya A'ishah da matuƙar farin ciki ya shaida wa dukkan taron jama'ar ya bai wa yarima damar auren ƴarsa,duk sai aka yi kabbara tare kuma da yin addu'o'i kafin a fita zuwa can inda za a yi wasar dawakai.
Ta madubin tsafi Dadda ke kallon komai,tun lokacin da aka yi shelar yin baikon ta shirya baƙin tsafi mai ƙarfi ta tura domin hallaka yarima.Ita dai gimbiya A'ishah cike take da farin ciki duk gajiyar nan ta jiya sai ta neme ta duk ta rasa,duk da cewa kuwa ta sha bacci sosai sai wuraren goma na safe ta farka.A bakin mahaifiyarta kuma ta ji abin da ke faruwa,sosai ta so a ce ta fita ta ga yadda komai ya wakana sai dai hakan haramun ne a masarautarsu zuwan mata a irin wannan taron.
Cikin rangaji ta ƙaraso ta zo ta yi tsaye ita ma tana kallon yadda ake wasar tseren .Wani irin murmushi ya suɓuce mata lokacin da ta ga yarima Naslam ya je kusa da dokinsa za su yi wasar tseren shi da wanda ya yi nasara akan dukkan dakarun da aka tsara wasar da su.Ita ma Dadda nata murmushin ta saki tana jin cewa saura ƙiris burinta ya fara cika don ta jefa kibiyar tsafi akan dokin yarima saboda in ya hau shi sai ya masakance.
Yarima ya hau kan doki yana mai ambaton sunan Allah tare da yin kabbara,Dadda ta ɓata fuska tana mai ɗan satar kallon gimbiya A'ishah wacce har yanzu murmushi ya ƙi barin fuskarta.
“Dadda dube shi ki ga yadda yake da ƙwarjini da cikar zati, wannan shi ne mijin A'ishah ”
“Haka ne ki yi fatan Allah yasa ya ci gasar kar ya kwabsa abin ya zama abin goranta miki” Dadda ta faɗa tana mai shafar madubin haɗi da yin wani surkulle daidai nan su yarima suka fara gudun.Ƙafar dokin ta ƙure da ido ta na shirin aika masa wata gubar tsafin kawai sai ganin bakin tsuntsuwa ta yi ya caki madubin ya tarwatse.
A tare suka ja ba,kafin su kalli juna.Da wani irin gudu kuma gimbiya A'ishah ta fita don jikinta ya bata babu lafiya,mayafinta ta ja ta rufe fuskarta lokacin da ta isa filin sukuwar.
Yarima NASLAM wanda ya lashe wasar tseren dokin ya juyo yana kallon inda take a tsaye,suka haɗa ido da sauri ta sunne kai tana wani murmushi kafin ta juya da sauri ta koma.Ya ja numfashi yana jin a ransa ya yi dacen mata.
★
An ɗauki tsawon lokaci kafin Ummilo ta farfaɗo wannan karon ma tana yin wasu kalamai a cikin Yaren da ban fahimci me take nufi.
“Alhamdulillahi lazhi ahayana ba'ada ma'amattana wa'ileyhi nushur” ta furta tare da ware idonta a kaina,na sakar mata murmushi na ce “sannu Ummilo” ba ta amsa ba sai martanin murmushin da ta maido mini tana mai shafar gefen fuskata kafin kuma ta miƙe ta fita.Haka na take mata baya sai na ga ta shiga banɗaki,can kuma ta fito ta soma wanke hannuwa da baki da fuska da hannuwanta hatta kai da kunne sai da ta shafa haɗi kuma da wanke ƙafafu.
Mayafinta ta gyara kafin ta zo ta fara yin wata irin bauta da ban san ta mece ce ba,ni dai ido kawai na tsura mata da na ga ba ta da niyyar idawa kawai na je gun baby Mila na ɗauke ta dama tun ɗazu ta tashi.Madara na soma bata tana sha tana kallona cikin ido, murmushi na saki ina jin sonta na ratsa ni.
Banah wanda tun bayan abin da ya faru ya koma can ƙofar gida yayi tsaye,sai yanzu ya shigo yana mai tambayata “mene ne can Ummilo ke yi?”
“Ina kifin har yanzu ba a gama dafawa ba?” na tambaye shi ,don sau tari in yayi mini tambayar da raina bai so ba nuna masa nake yi kamar ban ji ba sai na ɗauko masa wani zancen.
Fita ya yi ba tare da ya ce mini komai ba,can kuma sai ya dawo riƙe da kwano yana tiriri.Kamshin kifin ya daki hancina,nan take yawuna ya tsinke sai na shimfiɗe Mila na karɓa na soma ci shi kuma Banah yana aukin kallona.Ina gama ci na ji wata kasala ta rufe ni,sai na kwanta ni ma sai a lokacin kuma Ummilo ta shigo.
Banah ya ce “ga kifi nan da Naomi ta rage ki ci”
Da fara'a kuwa ta karɓa tare da gyara zama ta sa hannunta,sai dai fa ta gagara ci sai yamutsa fuska take haɗi da yunƙurin kai shi bakinta.Can dai ta haƙura tare da ajiye kwanon tana mai girgiza kai ta ce “in na ci wannan ai tamkar na cinye kaina ne,a'a sam maita ai ba hauka ba ce da zan ci jinsina ”
Banah ya ƙanƙance ido yana kallonta kafin kuma ya fice ya bar mu.Maƙoshina ne na ji yana wani irin zafi kamar ana hura wuta,murya kamar ta mai koyon magana na ce “Ummilo sanyi nake ji ki rufe ni” sai kuwa ta miƙe ta ɗauko bargo ta luluɓa mini.Daga wannan kwanciyar ban ƙara farkawa ba sai washegari da zakara ya fara cara,na buɗe idona da suka yi mini nauyi kafin na yunƙura zan tashi sai dai na kasa sakamakon bayana da na ji ya riƙe kafaɗata ta ƙara nauyi.
“Banah?” na kira sunansa kasancewar ni da shi ke kwana a ɗaki ɗaya,Ummilo kuwa cikin jerin ɗakunan da aka yi daga baya take kwana ita da Mila.
Shiru ban ji motsinsa ba,sai na ƙara yunƙurin tashi a wannan karon gangar jikina ta baro shimfiɗar sai dai na gagara tsayuwa kan ƙafafuna na faɗi kwacaaa.Jeren kwanukan da ke ɗakin duk ya baje,ƙarar ta jawo hankalin Ummilo ta shigo tana tambayar lafiya sai dai muna haɗa ido da ita ta ɗau haske.Da sauri ta zo ta taimaka mini na miƙe tsaye tare da riƙe ta gam,murya na ɗan rawa na ce “ki kai ni banɗaki na yi wanka” ita ce ta kai ni,sannan kuma ba ta fito ba sai da ta yi mini wanka.Bayan ta saka mini kaya sai ta miƙo mini wani icce ta ce na riƙe,na karɓa ina jin ƙusumbina da ya ƙara girma ya rinjaye ni na yi mini wani motsi.....
My book is only 500 via
2670215530
ZULFAU YAHAYA
Ecobank
DM +22795045822
[13/04 09:45] MRS SADAUKI: *TIF DA TAYA*🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐🪐
"""""""""""""""""""""""
LoVe aNd HoRrOr StOry☠️
```MRS SADAUKI```💫✍️
FCWA☀️
____________________________________________
Daga yau discount ya ida.
Last free page
10
Wata rusunawar dole ce ta zo mini saboda girman ƙusumbina ya wuce a yi kwatance sam tsayuwa ko tafiya babu sanda ba zai yiyu a gare ni ba.A haka na fito daga banɗakin ina jin wasu canje-canje na daɗa ƙaruwa a jikina,ban zame ko ina ba sai a ƙofar gida inda mutane birjit ke a wurin dukkansu kuma a ƙarƙashin ikona suke.Tamkar sun ga ubangijinsu haka duk suka tsaya da abin da suke yi suka zube ƙasa tare da yin kwanciya suna yi mini wani irin kirari da ba a taɓa yi mini shi ba.Idona na ƙanƙance ina kallon Banah da ke can ɗan nesa da ni yana wani irin murmushi da ban san mene ne ma'anarsa ba,don ko kaɗan ban zargi cewa a cikin kifin da ya bani na ci ba ne wannan girman ƙusumbin ya ƙaru.
“Sabbin dokoki sun sauka,don haka al'ummar gari ku kasance cikin shiri ga dukkan abin da shugaba za ta zartar” Banah ya faɗa yana mai takowa yana doso inda nake hannunsa riƙe da kwari da baka.
Sai da ya zo dab da ni sannan ya saita kibiyarsa a sama yana mai furta ɗalasiman tsafi,ji kake shuuu kafin wata wuta ta baje a sama.Babu kuma jimawa sauran jama'ar gari suka fara ɓullowa ta kowace kusurwa,tuni wurin ya ɗauki harama ya cika tanƙam.Sai kuma a lokacin ne na soma yin magana,“daga yau an zartar da yin hadaya duk ƙarshen mako,ruhikan ruwa su ne ke da alhakin zaɓar wanda suke so ko dai mu ɗauke shi mu bayar ko kuma su da kansu su kira mutum zuwa can domin ɗaukar ransa.Abu na gaba shi ne duk wani jinjiri da za a haifa sai an kai shi bakin kogo uwa gijiya ta saka masa albarka tare da ƙa'ide masa adadin shekaru ko watannin da zai yi a duniya”
Yanayin fuskokinsu duk sun nuna ba su ji daɗin wannan sabon tsarin ba,sai dai babu wani mai zarrar yi mini magana duba da irin ƙarfin ikon da ya ƙara hawa kaina ba tare da ni kaina na shirya masa ba.
A haka aka watse na koma ciki na tarar da Ummilo a zaune ta yi uban tagumi.Tana ganina ta miƙe tsaye tare da nufo