Share this page
1 / 10
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels BISMILLAHIRRAHMANIR-RAHEEM INUWAR KADDARA (THE SHADOW OF DESTINY) BY moon🌚… Chapter 1: The weight of a false judgment. FEDERAL HIGH COURT, ABUJA NIGERIA…. Tsit Court din da ke cike da mutane yai, ba abinda kake ji sai sautin fitar numfashi, gabadaya mutanen gun sun kurawa judge din dake zaune yana en cike cikin sa a wasu takar du ido kamar zasu cinye sa, can gefe kuma in da aka tanada don me lefi wata matashiya ce wacce bata fi shekaru 21 a duniya ba sanye prisoner’s attire, idanun ta dake a bushe ba digon hawaye ko kadan na kafe a kasa , ita kadai ta san me take ji, ita kadai tasan kalar zafin da take ji a cikin ranta, tun tana kukan tana kuma a ambatan cewa she’s not guilty har ta gaji, a halin yanxu mutuwa ko azaba sun daina bata tsoro burin ta daya shine ta samu koda mutum daya ne da ko bayan ranta xe amice da cewa ba ita tai wannan kisan kan ba, ammah da alamu haka zata bar duniya batare da ta cika wannan burin nata ba. Bayan alƙali ya gyara takardun sa, ya kai hannu ya gyara sirin glasses din dake idon sa kafin cikin kakkausar muryar ya soma fadin “After carefully considering all the evidence placed before this court, the accused is found guilty of murder” “Accordingly, this court sentences YASMIN IBRAHIM life imprisonment.” yana gama fadin haka ya daki gavel din dake gaban sa. Nan take court din ya cike da maganganun mutane daban daban, gefe guda kuma sautin koke koke na tashi. har yanxu babu ko digin hawaye a cikin idonta, se dai jikin ta ya shiga rawa ba kakkauta wa, a hanakli take motsa lips dinta tana fadin “la haula wala quwata illah billah” a karo na biyu judge ya kara buga gavel din sa ayko nan take akai Shiru Sedai sautin kukan wasu da be kare ba, gangar jikinta ne kadai ke agun ammah xuciyar ta da tunanin ta baya tatare da ita, bata dawo cikin hankalin ta ba har se da taji ana saka mata handcuff gamida dragging din ta xuwa hanyar fita daga cikin court room din, duk da koke kokon da take ji amma besa ta juya ba, suna fita bakin court din mutane da kuma en jaridu suka zagaye su, kamar kullum zagi, tsinuwa da kuma tambayar mesa kika kashe ta shine ke dira cikin kunnan ta, rintse idanun ta tai saboda hasken camera da ke barazanar dauke mata ganin ta, can kuma ta bude a hanakali tana neman sa tana kuma addu’ar Allah ya sa ta ganshi, can ta hango sa cikin attire din lawyer, en jaridu sun zagaye sa, ammah baya iya cewa komai, Idanun sa ne suka haɗu da na ta, a idon sa akwai wani abu da ya fi kuka zafi wanda shine rashin ceton ta. Bai motsa ba amma shiru ya yi magana a madadin sa, Se a lokacin taji wasu hawaye na bin kwancin ta, daidai nan aka shiga kokarin tura ta cikin motar prison, ganin hakanne ya sanya shi saurin fadin “waittt!!” Cikin karaji, ganin kamar ba zasu saurare sa bane ba ya sanya shi saurin kutsawa cikin mutanen yana ture koma wa ya gani a gaban sa, Ammah Ina kafin yaje an datse kofar motar, amma duk da hakan ya kara saka karfi gun kutsawa cikin mutanen har se daya samu damar xuwa gun wasu hudoji da yake iya hango ta tanan kafin cikin wata kalar murya ya furta “i failed you.” Girgiza masa kai ta shiga yi hawaye na bin fuskar ta kafin cikin murya marar sauti tace da shi “na-na gode” ta fadi hakan hawaye na cigaba da bin fuskar ta, kamar jira ake ta gama fadin hakan ayko motar ta shiga tafiya, se a lokacin ta maida kallon ta kan waenda ke kuka gamida kiran sunan ta, daga haka ta lumshe idanun ta gamida jingina da kanta jikin seat wasu hawayen na bin gefen face din ta a lokaci daya kuma tana tuna kalar rayuwar da tai tun bayan tasowar ta…. Kusan 3 mins da daina hango motar ammah be dauke idon sa ba be kuma motsa ba, cikin ran sa ya shiga fadin “THIS ISN’T THE END, THIS IS WHERE THE BEGINNING STARTED….” FEW YEARS AGO…. ********* Innalillahi!! Ta fada a firgice saka makon ruwan sanyin da taji an kwara mata, da sauri ta mike tsaye tana me sharce ruwan dake sauka kan fuskar ta gamida kankame jikin tana rawar dari. kaff duniyar nan tasan ba wanda xe mata kalar wannan walakancin face “ammah” “Dan kaza kazan ki wa kike jira yai maiki aykin gidan ehh?? Don tsabar kin rena ma mutane hankali shine zaki saki baki da hanci kina bacci kamar wata sauna har karfe shidan safiya? To wallahi wannan ya zama na karshe don wlh duk sanda na kara shigowa dakin nan da sunan tashin ki wallahi ki kuka da kanki sakarya kawai” ammah na gama fadin hakan ta fice daga dakin, se a lokacin ta samu damar barin hawayen dake makale gefen idanun ta zubowa, tana Jin muryar ammah daga tsakar gida tana fadin “in kika kara minti 1 a dakin nan wallahi sena kakkarya kashin ki saura kuma kiyi bruntun daze tashar mun da yara daga bacci” Jin hakane ya sanya ta sauri daukar hijabin ta dake sakale jikin kofar langa langar dakin daga bisani ta kwashi kayan shimfidar ta tayi waje bayan ta janyo kofar dakin a hankali. ko ina na tsakar gidan da ya sha siminti a bushe yake gwanin ban sha’awa, slippers din ta dan madina ta xura ta nufi igiyar shanya ta shiga baza kayan shimfidar tata akai a ranta tana addua’r Allah ya sa ya bushe kafin lokacin futarta yayi. Sosai ko ina na jikinta ke mata ciwo don jiya se 1:30 na dare ta kwanta saboda wanki kayan kannen ta da ammah ta Saka ta yi guraren karfe 12 na dare, dauraye fuskarta ta shiga yi da ruwan da se mutum ya rantse daga fridge aka ciro sa, already tun da asuba da ta tashi ta wanke bakin ta don haka bata wani bata lokaci ba a bakin pipe din ta bar gun ta shiga kokarin kunna wuta don dora dumamen ruwan alkama da kunu. Karfe bakwai daidai tagama duk abunda ya dace ciki harda yima kannen ta twins mata wanka, juye ruwan data daura don ita ma ta samu tai wankan ta shiga yi, jiyo muryar ammah tai tana fadin “ke!me zan gani haka?” murya na rawa tace “ammah wanka zanyi” aje ruwan nan dan kaniyarki kafin inxo inda kike in gaggaura miki mari se ki fadan idan ke ce ko ubanki kuka sayo icen” ba musu ta aje ruwan ta dauki na sanyin da tai niyar yin surki dashi tai bandaki. wankan 5mins tai ta fito daga bandakin tai maza ta shige daki don kada sanyi yai mata lahani. Ballalen kofar wardrobe dinta ta jingina a gefe tana kallon en tsirarin kayan ta dake ciki wardrobe din ita kanta ta manta rabonda sabon kaya ya ziyarci cikin drower din nata, seda ta fara sanya kodaddiyar material dinta sannan ta dauko man shafawar ta na habiba ta milke sassan jikin ta dashi har ta dauki hijab dinta da niyar ficewa ta jiyo muryar kanwar ta me suna hafsa tana fadin yaya har kin shirya zaki fita? mesa baki tasheni ba? Murmushi taima kanwar tata wacce bazata wuce 15 years ba tace “ehh hafsa na gama yanxu zan tafi, in kin karya ki duba cikin wardrobe dina akwai 370 ki dauka 100 ki bawa umar 100 in ya tashi 70 din kuma ki sayawa en biyu alawa se ki aje mun 100” Sam hafsa bata saka ran cewa zata bata amsar tambayar da tai mata ba don haka tace ”mungode yaya allah ya kara budi ya taimaka ya bada saa” murmushi ta sakar wa hafsa tace “ameen” tana fadin haka ta fice daga dakin bayan ta shafa kan su twins dake ta faman shan koko. Tana fita ta ci karo da ammah dake rike da buta a hannu da alamun daga bandaki ta fito, ganin kallon da take mata ne kamar zata doke ta ya sanya ta tsayawa chak gamida rakubewa da jikin bango “Uban me kika tsaya yi har 7:23 baki tafi ba? Ni zaki tozar ta? toh wallahi kika sa aka koreki gidan aykin nan se kin bar gidan nan ki koma chan gun dangin babarki don ni ba asararriya bace ba da zan ringa samar miki gun ayki kina sulakanta ni ba sakarya kawai, bazaki dena kallo na da waennan idanun naki na mayun farkon zamani ba??” Da sauri tai kasa da idanun ta ta shige wani daki da sauri tana jiyo ammah tana fadin “saura kije ki kwace mata ýaýa ko miji bakar mayya kawai.” Yadda ta barsa daxu haka nan ta taddasa ba alamun ma ya sha kunun, yayi zugum yana kallon gu daya har ta shigo ma be Sani ba, “abby zan tafi aykin dan Allah kasha kunun ko ka samu kasha maganin” ta fada tana me duba ledar maganin nasa dake kan wani tsohon akwati wanda yaga duniya. Kallonta yake kawai ba ko kiftawa Daman bata sa ran xe bata amasa ba, don haka ta mike ta nufi hanyar fita daga dakin don kada Ammah ta xo ta kikkife ta, muryar sa da ta jiyo ne ya sanya ta dakata wa “nasan kin tsane ni ko YASMIN??” Da sauri ta jiyo ta kalleshi ya ciga ba da fadin “I wronged you, I failed u as a father, tabbas nasan cewa kina matukar Jin haushi na sbd gaza wa ta ne ya sanya kike fuskantar kuntata wa, nasan da ace mahaifiyar ki na raye…” bata bari ya kara sa fadin abinda yake son fadi ba tace “a’a abby ban tsaneka ka ba kuma bazan taba ba, a duniyar nan banida wani me sona sama da kai ni na sani dan haka ka daina fadin irin dai wannan maganar ko tunanin hakan ma banso ka ringa yi Kaji abby na??” ta Kara she maganar tana me sakar masa murmushin da ya sanya dimples dinta nunawa, kallon ta yai na en seconds kafin ya dauke idanun sa kasa, ha kika yayi babban kuskure a rayuwar sa, ya lalata rayuwar gidan sa da hannun sa, a koda yaushe ya kalli fuskar diyar tasa se yaga ta juye masa ta zama sak mahaifiyar ta marigayiya AISHATU saboda mugun Kamar da suke da diyar tata banbancin dake tsakanin su kadan ne. katse masa tunanin da yake yai da fadin “se anjima abby na tafi” tana fadin hakan ta bar dakin, da sauri ta nufi kofar gidan da tsatsa ta cinye ta tasss, bakin ta dauke da adduar fita gida ta fice, daidai nan er keypad din da yayar mahaifinta ta bata ya shiga vibrating zaro ta tai daga aljihun rigar tata, sosai wayar taga duniya, bakinta dauke da sallama ta kai wayar kunanen ta, daga daya bangaren taji ance “ina bakin titi ina jiranki kidan yi sauri don inada abun yi” yana fadin haka ya katse wayar sa, kara sauri tai don ta san yadda jira yake sammm ba dadi. Daidai bakin titin karshen waya ta tsaya tana waige waige Daman mota bazata shiga cikin Layin masu ba se da dabara, zaro waya tata tai daidai nan driver ya Kara Kiran ta, ko sallama be mata ba Ya ce “malama sauri fa nake wai kina Ina ne??” “Ka yah kuri bawan Allah gani bakin titin Ammah ban ganka ba” ta fada tanata faman waige waige, se a time din ta hango wata tsadaddiyar bakar mota kirar benza, ta gane motar don tabbas ranar da taje interview ta ganta kyan da yai mata ne ya sanya ta rike motar harda hadda ce plate number din motar, da sauri ta gangara bakin motar don ta kula deiven masifaffe ne. Harta karaso HABU driver besan ta karaso ba har se da tai knocking window din sannan hankalin sa ya kai kanta, sauke glass din motar yayi kafin daga bisani yace “fatabarakllahu-Ahsanul khaliqeen, kaiii Allah yayi hallitta anan gun” duk sambatun da yake bata kula sa ba don ba yau ta saba ji da ganin ganin kalar wannan reaction din gun mutane ba din wasu ma sunyi fin hakan. cikin muryar ta da tafi ruwan sanyi sanyi tace “Ina kwana nice wacce mukai waya yanxu” ta fadi hakan ba tare da ta kalle sa ba don she’s uncomfortable da kalan kallon sa yake mata, instead ya bata masa se taga yayi saurin fito wa daga cikin motar, “marhaban biki yake wannan kyakkyawar hallittar” ya fada yana me bude mata murfin motar, shiga tai a hankali tace “na gode” bakin sa kamar xe yage yace “girman ki ne ranki ya dade” daga haka ya shiga cikin motar suka nufi GOVERNMENT RESEVED AREA dake nan Kano. Tun da suka fara tafiya habu ke faman xuba ba kakkauta wa ita dai ko ci kanka bata ce masa ba shi kadai ke kidan sa kuma ke rawar sa. tafiyar 15mins sukai suka isa bakin tanfatsetsen gidan, gida ne me girman gaske wanda aka narka dukiya domin yin sa, iya gate din ma abun kallo ne, ba kowa a farfajiyar gidan se tarin motoci dake shake a parking lot. Habu ke gaba tana bin sa a baya, tunda ta sa kanta gaba bata kara waigawa ba sedai ta kasan ido take satar ko ina da suka sanya kafafun su da kallo. Daidai bakin kofar shiga parlon gidan suka dakata, habu ne ya danna door bell din after some minutes aka zo aka bude, wata matashiya ce wacce bazata wuce 23years ba ta bayyana bakin kofar kakkayawace ta bugawa a garida, fatar jikin ta har wani sheki yake tsabar hutu, bayyanar ta ke da wuya gabadaya ko ina da ko ina na gun ya gauraye da kamshin tsaddaden turarenta, farin hannun ta daya sha red henna ta kai gefen wuyan ta ta maida ponytail din ta dake nunawa. “Hajiya mun karaso” habu ya fada jiki na rawa, wani banzan kallo ta watsawa habu kafin tai amfani da gurbatacciyar hausar ta me kama da turanci tace “ayy ina da ido, and don’t hajiya me again, I noticed that your head is shaking, u better behave yourself” ta fada tana throwing ma habu dake ta faman bata hakuri bombastic side eye. Se a time din ta dubi yasmin, karaf suka hada ido da yasmin dake satar kallon ta, da sauri tai kasa da idanun ta tana fadin “ina kwana” bata bata amsa ba se fadin “come in” da tai ba yabo ba fallasa. Tsayawa fadin kyau da tsaruwar parlon bata bakine don duk wani morthen abu da ya dace ya kasance a parlor to akawai a nan Parlon. tun farkon shigowarsu gidan ta lura da cewa sam ba gidan da akai masu interview susu rai goma bane ba ammah tabbas a nan anguwar ne, “have a seat” ta ji matashiyar ta fada daga haka ta wuce upstairs. Anan kasan lallausan tsadadden carpet din parlon ta zauna se faman sake saken take yi. After 5mins ta ji alamar mutum na saukowa daga upstairs din, nan take ta maida attention dinta gun… A hankali take takowa cikin takun alfarma, hannu ta dauke da MacBook da alamu video call take, kaida ka ganta tabbas zaka gane cewa ba er nan nija bace ba, sam batada kiba kuma ba siririya bace ba, sanye take da light purple din abaya har kasa, idanun ta sanye da 4 Conner glasses da yai matukar yi mata kyau, a daya daga cikin cushion din parlon ta zauna ta ci gaba da wayar ta da take “alright oglum she here, we will continue talking latter in sha Allah, and please dont forget to call your dad coz I don’t want him to call you first abun will sound rude” ta fada tana me waving ma mutumin dake cikin screen din sannan ta cire earbuds din da ke kunnanen ta daura shi kan wani small royal table that was located slightly beside her’ ganin ta gama wayar ne yasa yasmin gaishe ta, a natse ta amasa gaisuwar tata kafin tace “masha Allah sannu en mata, nasan duk anmiki baya nin abun da ya kawo ki gidan nan right??” “ehh hajiya” Murmushi tai sannan ta ce “call me mami not hajiya understood?” Yasmin ta amsa mata da toh, cigaba da magana tai “ba abunda zance dake se ki rike gaskiya da amana a wannan zaman sa zamuyi dake, and neatness, wato tsafta coz banson kazanta, Amma by the way na ganki naga you are looking very good, sauran abubuwan kuma nasan duk kin sani so ba bukatar na kara maimaita wa, Allah dai ya bamu zaman lafiya, muje na nuna maki gidan” tana gama fadin haka ta mike itama ta mike ta bi bayan ta. sosai Yasmine tai mamaki matuka da Jin maganar da tai mata da hausa even though is not that clear kamar ta normal hausawa ammah still tayi kokari don bama ta taba zaton kalmar “zo” ze iya fita daga bakin ta ba. Tun da suka fara tafiya take ganin abubuwan mamaki kala kala don ita ko a tv bata taba ganin gida me tsari ba sama da wannan gidan, duk inda tasan ya ka mata ace ta nuna mata seda ta kaita tai mata bayani dalla dalla, in da suka shiga na karshe shine kitchen, “here we are, wannan shine kitchen, Amman bazaki ringa girki ba coz there’s my maid da zata zo from Turkey sunan ta BAHAR duk abun da ya shafi girki ita zatai, kedai se dai ki taya ta da kananan ayki” ta kare maganar tana kallon ta, ganin duk Yasmine din a takure ne ya sanya tace “ki saki jikin ki fa yamla…? Hakane sunanan?” girgiza kai yasmine taI cikin girmamawa tace “a’a yasmine ne” jinjina kai mami tayi tace “masha Allah jasmine Ashe flower ce me tsada a cikin gidan namu yau” ita dai yasmine bata ce komai ba se dan murmushin karfin hali da take yi don haka Allah yai ta da rashin sabo wanda hakan ya samo asali daga kiwar datai tun tana yarinya. “shekarun ki 20 right? Kuma kinyi secondary school koh?” Nan ma ta gyada mata Kai kamar wata lizard, a jiyar numfashi tai kafin tace toh “masha Allah haka ake so muje na nuna maki part din da zaki ringa zama in bakida ayki”. **INUWAR KADDARA (THE SHADOW OF DESTINY.) BY moon🌚…** Chapter 2: The mansion of unfamiliar kindness Ta wata kofa dake ta cikin parlon kasa suka bi se ga wasu rooms guda biyu sun bayyana, na biyun ta shiga da ita wanda ba abunda babu a ciki, dakin yayi mugun haduwa she couldn’t believe that wai nan ne dakin hutu, nan ta shiga tambayar kanta toh ya sauran rooms din en gidan ze kasance? “you will be staying here more especially if ba aykin da zakiyi, there’s a telephone if yayi ringing to u should pick coz tanan zamu ringa communicating if wani abun ya taso, dakin kusa da wannan da kika gani na bahar ne wanda nan da anjima jirgin su ze iso nigeria.”in Banda nodding head din ta ba abunda take yi, a haka ta ringa binta a baya har ta gama nuna mata abubuwan da suka dace. suna komawa parlor suka ci karo da wannan matashiyar da ta bude mata kofa dazu se faman frowning face din ta take, mami ta kalle ta tace “nazli I told you that I despise these attitudes de kike displaying lately, haka kawai ki ta hade rai kamar an dake ki? I had you shouting at the driver and Im very sure he did nothing wrong ammah kin sa Shi a gaba kina fada kamar danmi, what’s dis please??” Mami ta fadi hakan a kufule don ta tsani kalan attitude dinnan and ta kula tun ranar suka dawo nigeria take haka. Zama tai kan cushion sannan ta ma yasmine alamun ita ma ta zauna, can gefen kujera ta zauna, mami dake kallon nazli tace ”ina jinki” se da nazli tai raurau da eyes din ta kafin tace “anne ba big brother bane ba ya..” mami tai saurin tamabayar ta kan cewa me yai mata don tasan baya wasa da ita balle har yai mata wani abun Sedai in ita ta tabo sa. Se da nazli ta zauna sannan ta cigaba da fadin “bakiga abunda yai ma layla ba, yanxu muka gama video call da ita, she was crying about what he did to her, jiya ita da course mates dinta sunje shopping ta hadu dashi she talked to him buh ya nuna kamar he doesn’t know her and in front of her friends, har kokarin tuna masa inda ya santa tayi coz she thought ko ya manta tane Ammah he ended up shouting at her in front of lots of people, he even called her an attention seeker fa bakiga yadda yai embarrassing din ta ba, yanxu duk yadda muke da layla yace be santa ba?, da kansa fa yake kaini gidan su and ita ma she used to come over ammah ji abunda yai mata” Ta karasa maganar kamar zatai kuka. Duk abunda suke yasmine na zaune kasan lallausan carpet din da ke shinfide a tsakiyar tsararren parlon ta kurawa gu daya idanu tana sake sake daban daban,

Chapter 1 of 10