Share this page
6 / 9
alfarma wayarshi yadauka bayan yadebi kudi masu yawa excode dinshi yakira awaya akan sushirya gashinan fitowa zashi anguwa su kansu excode din seda sukayi mamaki dan rabonshi da fita anguwa kusan shekara guda kenan Dan haka cikin sauri suka shirya komai yana fitowa suka budemishi mota yashiga basu zarce ko inaba se airport yana zuwa jirgi is ready dayake jirgin na shugaban kasane Kai tsaye wayarshi yaciro yakira gomnan Kano yashaida mishi yana zuwa nanda 40 minutes [3/13, 07:09] Ussaina: *ALLAH GATAN BAWA*✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨ Salam masoyana kuyimin afuwa asakamakon rashin jina dakukayi nagode *page 59-60* *RANA BATA KARYA* Tun kafin jirgin su ilham ya iso airport tuni su daddy sunzo tararsu Ko ina inka Kai dubanka yan jarida ne suna jiran isowar jirgin Anwar kuwa ji yake kamar yatashi sama yataro jirgin Basu jimaba jirgin yasauka dauke da ilham da twince dinta da Inna da Adnan da Abban Adnan Su twince ne suka fara saukowa wohoho jamaa naso ace kuna gurin yayinda ilham tabiyo bayansu shigace ta alfarma ajikinta fuskarta sanye cikin bakin glass kayan jikinta Jane da green Swiss less sauran kwalliya nabarwa masu karatu kuyi mata da kanku Anwar numfashinshine yadauke yayinda yake tunanin Anya wannan ilham ce kuwa tunaninshine yakatse lokacin da daddy yataboshi yana cemishi to anwar gafa ilham kobaka ganetabane kallon daddy yakeyi kamar wani wawa dan tuni yagama raina kansa dan koda hadi ilham tawuce tunaninsa Ameera ma tagane ilham but tana mamakin yadda ilham din tacanja one time haka binta kawai takeyi da kallo Itako ihsan dama harga Allah bata ganetaba Babu abinda yakara firgita anwar seda ilham tafara takowa zuwa gurinsu ganin yadda hips dinda ke rawa cikin wani yanayi tafiya take kamar tarwada yayin da su twins suka rugo da gudu suka rungume daddy domin sun ganeshi Mommy ce takarasa ta taryo ilham yayin da yan jarida suka fara aykinsu tamvaya suka shiga Jerawa mommy agame da farin cikin datake ciki sakamakon dawowar surukar tata Dariya mommy tayi sannan tayi godiya ga Allah daya dawo da ita Lfy Juyawa sukayi kan ilham inda tashiga bayani cikin harshen turanci wayyo duniya💃💃naso ace kunga irin firgitar da anwar yayi dayaji zazzakar muryarta hmm abin baacewa komai godiya tayi ga Allah sannan tagodewa daddy da mommy da inna Dakyar suka barsu suka karaso gurin daddy shima seda security suka dakatar dasu Idon ilham ne yasauka kan anwar gavantane yafadi ganin kamannin dayakeyi da twins Wanda ko baa fada mataba tagane shine mahaifinsu tsananin kiyayyarsace taziyarci zuciyarta Dan ita da Tana da hankali lokacin da zaa auramatashi bazata yardaba sabida har ga Allah bata kaunarsa tsarinshi Sam beyimata ba amatsayin miji tofa!!! Tana cikin wannan tunanin ne taji anrungumeta dasauri takai dubanta gurin ameerace kuma tabbas taganeta sabida jini daya bawasa bane ita ma rungumeta tayi Tana kiran sunanta tambayarta tashiga Yi ina mahaifansu kukan ameerane yakaru ganin hakane yasa daddy yace sushiga mota suwuce gida dasauri aka budemusu motoci sukai tashiga Wanda se alokacin daddy yasamu damar gaisawa da amininsa wato daddyn Adnan Wanda shi tunda yaga ameera yakara rikecewa Anwar yana zaune ne kurum Dan gama yagama firgita da kallon da ilham take masa Wanda yayi imani kallon kiyayyane wasu zafafan hawayene suka zubo masa na danasani 😭gashi su twince dinsa ko kallo be ishesuba kaichonshi koda suka isa gida gabadaya part din daddy suka nufa abinci sukaci Wanda har yanzu ilham na makale da ameera yayin da shikuma anwar yasamu damar daukar twins dinsa basumishi kiwa ba sabida bahalinsubane sonsune ke Kara shiga zuciyarsa yana danasanin wulakanta mahaifiyarsu falo suka dawo gaba dayansu domin daddyn Adnan yace yanada mgn farawa yayi da basu tarihin bacewar Dan uwansa har zuwa sanda Adnan yahadashi da ilham a London kuma yanzu bayan yazo Nigeria kuma seyaga ameera Dan hakan yana bukatar Karin haske daddy ne yafara bashi lbr iyakar abinda yasani sannan itama ameera tafadi Nata tun bayan rabuwarsu da ilham har zuwa yanzu ilham yanke jiki tayi tafadi kasa sumammiya dagudu anwar yayo kanta yanakiran sunanta ruwa ameera ta dauko aka yayyafamata koda tafarka wani kuka takeyi metsuma zuciya Wanda har yanzu Tana jikin anwar dago kanta tayi taganta ajikinshi dasauri takwace kanta daddyn Anwar ma kuka yakeyi Kamar yaro yayinda kowa na falon seda yatayasu dakyar akasamu duka sukayi shuru yayinda Alh Imam yayiwa daddy godiya abisa nemawa ilham magani dayayi Adnan ma godiya yataya daddy nsa alfarma yanema agurin anwar da daddy akan yanaso yatafi dasu ilham gidansa Dan yanaso yakaisu meduguri suka ragowar danginsu daya gano bayan komai yalafa daddy yaamince batare da damuwaba yayinda anwar beso hakaba amma bashida zabi tunda daddy yagama mgn washe Gari dasafe suka dau hanyar kaduna yayinda har yanzu ilham kukan mutuwar iyayenta takeyi Adnan ne ke rarrashinta yana bata baki dangama daddy yagaza mgn Don shima kukan yakeyi ahaka har suka isa kaduna yayinda su twince se tsalle tsallensu sukeyi ajikin daddy maman yusuf [3/13, 07:09] Ussaina: *ALLAH GATAN BAWA*✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨ Zahra Muhammad mahmud *page 57-58* Suna isa Kano motocine birjik na Security da gwamna yatanadar masa Kai tsaye yabasu umarnin sukaishi wudil gidan me gari Se alokacin yakira moneer yashaida mishi gashinan zuwa garin dan tuni ya iso Kano ba moneer ba harsu megari seda zuwanshi yabasu mamaki Sunanan zaune suka fara jiyo jiniya takoina acikin garin hakanne yabasu tabbacin ya iso Hankalin yan garinne yatashi sabida jin jiniyar alhalin sunsan bakasafai masu mulki suke zuwa garinsuba Akofar gidan megarin motocin suka faka Wanda tuni megari da moneer sunfito domin tararsa iso suka masa zuwa cikin gidan adakin megari suka saukeshi yayin da security nsa suke jiransa akofar gida Bayan gaisuwa aka gabatarmasa da abinci Amma anwar ko kallon abincin beyiba illa tambayarsu ina ameeran take dasauri megari yakirata Shigowa tayi jiki asanyaye tasamu guri tazauna sannan tagaisheshi Yaamsa fuska cike da walwala danji yakeyi kamar yaga ilham Tambayarta yashiga Yi dangane da aynihin tarihinsu kuma yabukaci data sanar dashi gaskiya Batare data boye mishi komaiba tasanardashi tarihinsu seda kwalla tazubo a idon anwar ashe spouse dinsa marainiyace yadunga azabtar da ita kuma yayi imani batasan iyayentasun rasu ba share hawayensa yayi sannan yayiwa ameera taaziyya Sumasu megari duk sunmasa bayani agame da abunda suka sani akansu ameera Besheda musu halin dayake ciki ba na rashin ilham Illa kawai yanemi izinin megari nason yatafi da ameera Abuja sabida komai dare yau ze wuce Megari beji dadin rabuwa da ameera ba amma bashida yadda zeyi shiyasa yaamince Anwar ne yafahinci megarin ranshi besoba shiyasa yace wata guda kawai zatayi tadawo kayi hkr Special number dinsa yabasu Wanda in akira Kai tsaye zaa sameshi sannan yamike domin tafiya bayan yaajiyewa megari kudi wanda suke dollars ne Wanda shikanshi besan adadinsuba megari kusan suma yayi azaune sabida ganin yawan kudin Wanda tunda uwarsa ta haifeshi betaba ganiba😀 kofar gida yawuce yayin da ameera tashiga hada kayanta bata bata lokaciba tagama Hadawa tayi sallama da matan gidan tanata kuka Moneer ma dakyar sukayi sallama dayar wayarshi yadauko Yabata sannan yace zasu dunga waya kuma kafin tadawo zezo yasameta ahaka suka rabu taje tasamu Anwar dayan bangaren yasa aka budemata tashiga suka dau hanya tana ta kukan rabuwa da gidan megari dan tanaji ajikinta kamar tabar gidan kenan har abada ahaka suka dau hanyar Kano Kai tsaye gidan gomna suka wuce bayan gaisuwa tsakanin anwar da gwamna se gwamna yake cemishi tun dazu akace ka iso amma najika shuru murmushi yayi sannan yace wlh dady wani uzuri ne yakawoni me muhimmanci kuma harna kammala yanzu haka Abuja zankoma sekace ana korarka anwar inji gwamna murmushi yasakeyi sannan yace bahakabane daddy Amin afuwa zan wuce yanxu gwamna beso anwar yatafi ba amma bashida yadda zeyi yahanasa Dan yaso ace su gana da nafeesa kozeji tausayinta har airport gwamna yarakoshi se anan yaga ameera yayi zaton ilham ce Dan Tsananin kamarsu yace amma anwar baka da Kirkikazo da iyalinnaka amma baka kawota mugaisaba murmushi yayi sannan yakalli shashin da ameera take wacce tayi firifiri sabida rashin sabo sannan yace daddy wannan ba ilham bace kanwartace murmushi gwamna yayi Dan se alokacin yalura ilham tafi wannan kilewa sannan yalura wannan Kamar akwai duhun Kai atattare daita sallama suka masa suka shiga jirgi suka daga zuwa abuja Wanda ameera jitake kamar zata sume sabida tsoro yayinda azuciyarta godiya takewa Allah sabida adalilin yaruwarta you tayi ido biyu da gwamna Wanda da sede taganshi a hoto ko TV nabiyu gata ga Dan shugaban kasa duk adalilin ilham nakarshen shine yafi mata dadi wato jirgin datashiga godiya tasake yiwa Allah yayin da dokin ganin ilham da yaranta yacika zuciyarta *10:00pm* suka isa gida bayan andaukosu daga airport kaitsaye part din su mommy yawuce da ita suna zaune dukansu afalon suna jimamin me anwar yajeyi a kano sabida lokacin daya fita basanan security nsane suke shaidamusu sunkaishi airport yatafi Kano sallamarshi ce takatsemusu hirar ganin wacce kebinshi abayane yasasu hada baki gurin kiran sunanta ilham!!!! harda daddy ba itabace yabasu amsa se alokacin suka kureta da ido sannan suka gane ba itabace kamace kawai bama kamar daddy da mommy sabida sunsan ilham tadade dawuce wannan matsayin ameera zubewa tayi akasa jiki nabari wai yau itace gaban shugaban kasa da matarsa lalle iko se Allah gaishesu tayi sannan duka suka sami guri suka zauna daddy ne yafara mgn tabbas Anwar duk daga inda wannan take tahada jini da ilham Diyata Dan haka kuyi saurin sanar Dani wacece ita anwar umartar ameera yayi data sake basu labarinta batare da bata lokaciba tasake basu tunda tafara bada lbrn babu Wanda beyi kukaba afalon harda daddy sabida tausayinsu ihsan ce taje tarungume ameera Tana kuka kamin daga baya mommy tabi bayanta dadyne yaci gaba da mgn kallonsa yamaida kan Anwar sannan yacigaba anwar matarka ilham Tana kasar London kuma sati mezuwa zata dawo Nigeria iyaabinda zan shaida maka kenan game da matarka dagudu anwar yamike yaje yarungume daddy yanamasa kiss afuska fadi yakeyi thanks you daddy ngd da wannan albisheer dakamin daddy ne yakatseshi nafada makane badan komaiba sedan ameera sabida nasan zata bukaci ganin yar uwarta kaga dole inmata bayani inda take amma wlh dabadan hakanba se in tadawo zaka ganta shide godiya yacigaba dayi ihsan daddy yama umarnin takai ameera dakinta tashi tayi taja trolley din ameera sannan tarike mata hannu suka wuce anwar ne yasake yiwa su daddy bayanin yadda akayi yasamo ameera mamaki sukayi daga baya suka jinjinawa social media daddy da mommy ne suka wuce dakinsu yayin da anwar shima yawuce nasa part din farin ciki duk yabi ya isheshi jiyake kamar yabita London Dan yakosa satin yacika yadawo abar kaunarsa abangaren ilham zuwa yanxu takammala karatunta se shirin dawowa gida takeyi murna duk sukeyi ita da inna su twince ko zuwa yanxu sun iya fadin mommy da daddy dan wayone dasu (kamar yusuf dina) yaune doctor Adnan yasanar da daddy nsa labarin ilham danhaka be bata lokaciba yace yakaishi yaganta dayake daddy yazo London din Kuma shima Adnan yazo kaitsaye gidan su ilham suka je koda daddy yaga ilham jikinshine yafara rawa daauri Adnan yazaunar dashi itama ilham Tana ganinshi ta tuno da mahaifinta dagudu taje tarungumeshi tana cewa abba Dan ita azatonta mahaifintane dakyar inna ta banbareta ajikinshi sannan dukansu suka zauna tambayar inna daddy yayi game da alakarta da ilham bata boye mishi kmaiba tafadamishi dubansa yakai ga ilham wacce har yanzu Tana rike da hannunsa ta kwantar da kanta akan kafarsa tambayarta yajuya zeyi Adnan yakatseshi daddy ko katambayeta baabinda zata iya sanar dakai sabida yawancin abubuwa tamantasu inaga kahakura har zuwa lokacin dazata koma Nigeria semu bisu Dan musamu Karin bayani idon daddy ne yasauka akan sarkar dake daure awuyan ilham dasauri yakai hannunsa kan kwadon sarkar yana dubawa wlh wannan kodaga ina take jinin Dan uwanace ita shine abinda yafito abakin daddy sannan yacigaba sabida wannan sarkar tamahaifiyarmuce iri biyu gareta tabani daya taba Dan uwana daya tace inmuka haifi yaya mata semu basu Dan haka tabbas wannan jininace innane yadaure dan haka Adnan yabasu shawarar abar maganar zuwa dawowarsu Nigeria shine zasu sami Karin bayani amma anan babu abinda zasu gane hakan akayi domin dukansu sun amince da shawarar da Adnan yakawo su twince ne suka shigo falon suna gujegujensu idon daddy ne yasauka akansu dasauri yadaukesu yadora acinyarsa tabbas dayake basu da kwuiya wasansu suka cigaba dayi cikin wasanne sukayi arba da gemun daddy habawa ay basu Yi sanyaba suka shiga Dan sundauka wani nauin kayan wasanne love you all maman yusuf [3/13, 07:09] Ussaina: *ALLAH GATAN BAWA*✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨ Zahra Muhammad mahmud *Page 61-62* Suna isa gida momyn Adnan kamar zata cinyesu se rungumesu takeyi basuba basu twins ba Bayan sunci abinci kowa wanka yayi yayi sallah yabi lafiyar katifa Shakuwace me tsanani tashiga tsakaninsu dukansu mutanan gidan ilham ko da ameera kamar zasu maida junansu ciki sabida tattalin juna yayinda kullum ameera namakale da waya tana waya da moneer soyayyace sukeyi bata wasaba abun har mamaki yakeba ilham sabida gani take gaba daya ma nawa ameera take Satinsu guda akaduna suka daga zuwa meduguri Sunga tarba agurin danginsukowa jiyake dasu se godiya akewa Allah da ganinnasu yayin da aketayiwa iyayensu addua Sosai suke samun kulawa agurin danginsu allabasshi su twins iyayen farin jini Satinsu biyu suka koma kaduna bayan komawarsune Daddy yace ilham tashirya ta koma gidan mijinta kuka tarushe mishi dashi akan ita don Allah yamata rai yakyaleta itafa batason anwar kokadan azuciyarta Kan daddy ne yashiga charge sabida jiya sukayi waya da daddyn anwar yashaida mishi jibi ilham zata dawo amma yanzu ga abinda ilham take fadi dankari Kasa yayi da muryarshi ta sigar rarrashi yafara bata baki akan tayi hkr takoma Itako ilham ina ko sauraronshi batayi sabida kukan datakeyi mommyn Adnan ce tasa baki akan daddy yakyale ilham yanzu ita zata mata mgn hakan akayi kuwa domin mommy har daki tasamu ilham tafara rarrashinta gami da nuna mata illar dake cikin rabuwar aure inda hartake cemata yanzu inkinki kikoma dakinki mijinki aure zeyi Sannanyazo ya amshi yaransa ahannunki yaba matarsa itakuma inba ta Allah bace azabtardasu zatayi kinfison yaranki sutashi suga iyayensu basa tare kinasone yaranki su tashi cikin rashin syy mahaifiyarsu kiyi tunani ilham nibanga laifin anwar ba yakai matsayin dayakamata kowacce mace tasoshi ko wani laifin yamiki ne dasauri tadaga kanta sannan tace tunda aka fita dani waje betaba zuwa inda Mukeba ko awaya betaba kiranmuba har zuwa nasamu Lfy ko murna betayani murmushi mommy tayi sannan tace kimasa uzuri sabida bakisan meya hanashi zuwaba Dakyar mommy tashawo kan ilham tayarda zata koma sabida yaranta amma tayi alwashin anwar se ya gwammace mutuwa akan zama da ita😳 *ABUJA* mommy da ameerane suka dawo da ilham dakinta a falon mommy suka sauka su twins naganin mommy suka je gurinta da gudunsu suna dariya waisu sunganeta Anwar ne yashigo da sallamarsa fuskarsa dauke da faraa gaida su mommy yayi yayin da yakai dubansa kan gimbiyarsa akayi ko saa suka hada ido wata uwar harara ta wurga masayayinda shiko jikinshine yakama rawa dangama harga Allah yanxu yana shakkar ilham Dan kwarjini take masa baya iya jure kallonta ballantana yanzu data wurga masa harara guri yasamu yazauna Bajimawa daddy yashigo nanma gaisuwa akai tayi tsakaninshi dasu ilham naseeha sosai daddy yamusu yayinda daddy yakara Jan kunnan anwar akan takiyaye kar yakuma maimaita abinda yafaru tsakaninshi da ilham ita kuma hkr daddy yasake bata akan abinda anwar yamata kan ilham ne yadaure Tana tambayar kanta me anwar yamata abaya har ake sake jamishi kunne ita kuma ake bata hkr shuru tayi Tana tunani tabbas akwai abinda Yamata kuma tasha alwashin seta binciko ko menene mommy da ameera ne sukace ta tashi suje da ita part dinta in Dan sunaso su wuce da wuri dan daddy yace karsu kwana mikewa tayi jiki ba kwari Tama su daddy sallama tabisu suka nufi part dinnata Wanda rabonta dashi tun ranar daaka kawota komai nanan fes kamar yanzu akasakasu sede yanzu hotunan su twince ne takoina agidan fada sosai mommy tasake yimata inda daga karshe sukamata sallama suka wuce kuka takeyi sosai yayinda ameera ketayata ahaka suka tafi suka barta part din su daddy suka koma sukayimusu sallama yayinda daddy yabada excode mota goma su rakasu gida gadiya suka musu sosai sannan suka dauki hanyar kaduna anwar yana ganin sun tafi mikewa yayi Yamasu mommy sallama yanufi partydinsu hannunshi rike dasu twins yayinda zuciyarshi keta bugawa kamar zata fito addua kawai yakeyi akan Allah yasa hukuncin da ilham zata masa yazamo me saukine agareshi gashi inna ladi tun bayan tafiyarsu ilham kaduna itama tawuce gida dan taga yan uwanta da seyaje gareta yayi kamun kafa kozata shawo masa kan gimbiyar mata wato ilham itako ilham tun dasu ameera suka wuce wanka tashiga tayi yayinda tsantsara kwalliya afuskarta kamar me shirin zuwa party wasu arnayen English wears tasaka rigar bata rufe mata cibiyaba yayinda daga saman rigar nonuwanta Duksunfito gasu Masha Allah daga bayan rigar kuma wasu igiyoyine akayimusu style kamar yadda ake daure igiyar kambus rigar maroon color ce yayinda wandon shikuma fari ne jeans kuma irin pensur dinnanne amma kuma duk an yayyagahi alamun kwalliyarnan da ake cewa crazy jeans gashinta sakinshi tayi a gadon bayanta tura ruka tashiga pesawa kamar bagobe dama gashi dataje meduguri tasiyo wasu masu kyau falo tadawo tazauna tadora kafa daya kan daya Tana dan girgizasu yayinda bakinta kuma tana taunar ciwingum agaskiya bakarya ilham tahadu musamman rigar jikinta bame hannu bace shine yakara fito mata kyanta abunka da farar mace iya kyau ilham tayi kyau ba namijiba ko mace kika Kalli ilham alokacin sekin maimaita to inaga anwar Kuma jiran shigowar anwar kawai takeyi shiko yana waje yana ta adduoi Akan Allah yataimakeshi to masu karatu gade ilham tayi kwalliya tadaukar hankali waito hakan na nufin Anwar tayiwa kwalliyar Dan yaji dadine ko kuwa [3/13, 07:09] Ussaina: *ALLAH GATAN BAWA*✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨ Zahra Muhammad mahmud *Page 63-64* Tura kofar anwar yayi yashiga jiki asanyaye bata falon kasa Dan haka Kai tsaye yahaura sama Gabanshine yafadi saura kadan ya yarda su twins dake hannunshi Sabida arba dayayi da ilham Cikin shigar da ko amafarki bezaci zata iyaba Sauke su twins yayi suka ruga gurin mamansu shikuma yaci gaba da tsayuwa agurin kamar andasashi Ilham ko se ayko mishi take da sakon harara mikewa tayi taja hannun su twins suka shige daki tafiya take tana juya masa uku Wanda yananyin datake juyasu ko namiji ladifine inyagani seya koka balle anwar cikakken namiji Wanda tuni hankalinsa yakai kololuwa gurin tashi .binta yayi da kallo harsuka shige daki zama yayi yadafe kansa yana tunanin menene mafita. Yana zaune agurin har aka Kira sallar magrib Mikewa yayi yashiga bayi yayi alwala yawuce masallaci Bedawo gidanba se takwas koda yashigo suna zaune afalo suna kallo gefenta yaje yazauna ko kallonshi ilham batayiba tamaida hankalinta kan kallo Mgn yafarayi cikin muryar tausayi da neman gafara Ilham Don girman Allah ki ajiye duk abinda ke ranki muzauna Lfy wlh nime kaunarmine kitausayamin Don Allah Tsakine amsar data bashi bata bata lokaciba tanufi dakinta Dan har ga Allah ita haka kawai anwar bemataba amatsayin miji shiyasa ta tsaneshi sosai .koda tabar gurin anwar kasa daurewa yayi beyi auneba Kawaiseji yayi hawaye nabin fuskarsa yarasa gane meyasa baya iya daure damuwa daga ilham one time take sashi kuka Itako ilham tana shiga daki wanka tayi tasauya kayanta dawata arniyar night gown Turare tafesa akowanne lungu najikinta sannan tafito falo domin daukar su twins nide nace tafito tsokanane Anwar naganinta zumbur yamike sabida bemasan meyakeyiba dukawa tayi Wanda hakan yasa har Dan fant din dake jikinta yana hangowa tuni miyaun bakinshi yakafe soyake yayi mgn amma ba kalma abakinnasa duk sun gudu Ranar kwana yayi wanka da ruwan sanyi sabida muguwar shaawar data taso mishi gashi ba fuska agurin ilham dan kulle dakinta tayi *Bayan shekara daya* Zuwa yanzu anwar iya horuwa yahoru agurin ilham gashi abinda yafi bashi takaici tsawon lokacinnan Kala ilham batacedashiba sede yagama bata hakuri ta tashi tabashi guri Gabadaya yarasa ina zesa kansa koda yakaima su daddy Kara ko kulashi basuyiba bare yasa ran zasu taimaka masa zuwa yanzu jiyake kamar zeyi hauka gashi yanzu ilham mkrt take zuwa Dan tuni daddy yasamomata admission a Abuja Turkish university Inda take karantar medicine su twins. ma tuni ansasu amkrt suna play class shikadai suke bari sutafi Abubuwa da dama sunfaru aciki harda zuwa nemanwa moneer auran ameera inda daddy yawakilta megari ne yafi cancanta daya aurar daita duk da yanzu bata gidan megari takoma hannun daddy da zama inda ahalin yanzu Tana kasar India Tana Karasa secondary school dinta Adnan tabi shike kula da ita inda adaya bangaren soyayyace takullu me tsanani tsakanin Adnan da ihsan inda akasa rana auransu dazaran ameera takarasa mkrnt kuma duka family sunyi farinciki da auran Ilham ce zaune adakinta Tana rage kayan jikinta dawowarta daga makranta kenan anwar ne yafado daki da sallamarsa aykinshi Dan kullum yashiga Yi wato bata hkr ran ilham ne yagama baci Dan haka taga yadace ta taka masa burki tsawa ta dakamasa tahanyarcewa dalla malam dakata anwar Kake kowa wlh kadami rayuwata tsawon shekara guda kana bani hkr ban hakuraba Kai jakine dabaza ka gane hakurinne bazanyiba dasauri anwar yakalleta sabida kalmar jaki data kirashi da ita ranshi ne yasoma baci sabida tunda yazo duniya babu wani Mahalukin daya taba cimishi mutunci kamar ita ayau tunaninshi ne yakatse lokacin dayaji tacigaba da mgn koda yake ay Kare dama bashida zuciya Dan haka inaso kajini da kyau wlh anwar bana sonka bana kaunarka natsaneka tsanar da ko mutuwata banayiwa ita Kuma wlh bazantaba sonkaba har abada duk ranar dakaji bakina yafurta yana sonka wlh karya nakeyi karka yadda inkokayarda inasonka toko tabbas harka mutu sunanka jaki a idon duniya tarine yaturnuke anwar tunyanayi atsaye har yadurkusa itako ilham tana gama fada masa mgn tawuce toilet ta kyaleshi shikuma yaci gaba da tarin yana rike da gefen zuciyarshi zuwacan yafara aman jini mikewa yayi Dan yafita adakin ahankali yafara bin step zuwa kasa ko rabi beyiba ya yanke jiki yafadi yafara gangarowa Wanda hakanne yayi Dede da shigowar ihsan rike dasu twins andawo dasu daga mkrt sakinsu tayi dasauri ta isa gurinshi aman jini yakeyi sosai juyo dashi tayi abinda taganine yasata kwalla wata gigitacciyar kara kamannin anwar gabadaya Sun sauya maana fuskarsa tadan karkace harda bakinsa ga jini nazuba abakin Wanda ko baa fadamataba tabbas tasan anwar yasamu paralyse😳 maman yusuf [3/13, 07:09] Ussaina: *ALLAH GATAN BAWA*✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨ Zahra Muhammad mahmud Nagaisheku masoyana baride indan taka💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃 *page 65-66* Agigice ihsan tajuya da gudu domin kiran mommy Suko su twins kuka Sukasa sabida ihun ameera yafirgitasu Kukannasu yayi dede da fitowar ilham daga wanka dasauri tazura doguwar Riga tafito folon dan ganin meyasasu kuka Tahowa take dasauri danhaka bata lura da anwar dake kwance akasaba seji tayi tayi tuntube da Abu tuni tafara tambul akasa bakinta ne yabugu da center table tuni yafara jini Dakyar tamike takai dubanta inda taji tuntuben gabantane yafadi ganin mutum akwance dasauri tamike taleka fuskar nakwance ido taware sosai ganin anwar akwance cikin jini gashi halittarshi tasauya Tunani tafarayi akan to anwar kasheshi akayi tahanya caka masa wuka koko fuskarshi aka watsawa wani abun dayasa ta karkace wani sanyine yaratsa zuciyarta gami da adduar Allah de yasa mutuwa yayi Kai dako naji dadi kalar dadin data tuno zatajine yasata fara taka rawa hartana juyawa harsu Mommy da ihsan suka shigo agigice batasan sunshigoba se rawarta kawai take takawa Jin salatin mommy ne yadawo da ita daga tunaninta dasauri tawaiga inda suke kallon tuhuma mommy takemata Dasauri suka karasa kan anwar ganin halin dayake cikine yasa mommy faduwa kasa sumammiya ihsan dawani arnen gudu tanufi security din gidan dasauri suka shigo falon lokacin ilham nakan mommy hankalinta atashe nace kuji rashin kunya gurin ilham Daukarsu security din sukayi gaba daya sukasa amota yayinda ihsan da ilham suka rufamusu baya akabarwa security su twins agida Wani katafaren asibiti suka nufa Wanda tunkafin su ISO tuni anyi waya asibitin danhaka koda zuwansu ilahirin maaikatan gurin suna waje suna jiran akawosu kai tsaye emergency akawuce dasu akahana su ilham shiga awaje suka tsaya suda securities dinsu Tuni akayi waya office din daddy akasanar dashi cewa yazo fa gida balfy yanxu haka suna asibiti Hankalin daddy ne yatashi matuka yana tunanin meyafaru da family dinsa dawannan tunanin yakaraso asubiti shida makarrabansa dasu ilham yaci Karo akofar emergency ward Ihsan dagudu tafada jikin daddy Tana kuka cikin kukantane take fadamasa abinda kefaruwa jikinshine yafara rawa alamun zefadi dasauri security dinsa yazaunar dashi doctor ne yafito daga dakin yayinda abayansa wasu nurse ne guda hudu suke gunguro mommy akan gado hannunta daure da drip agigice sukayi kanta wani daki aka kaita na musamman bayan ankwantar da ita doctor yafarayiwa daddy bayanin abinda ke faruwa Dan durkusawa yayi sannan yafara mgn Kamar haKa ranka yadade madam bawani abubane yasameta illa frgita datayi asakamakon ganin abinda yafirgitata wanda insha Allahu nanda wasu lokuta zata farka dan tuni mukashawao kan matsalar shikuma yallabai anwar am sorry to say to say what!!!! Inji daddy afirgice doctor yace am Sorry sir but anwar yana cikin halin mutuwa ko

Chapter 6 of 9