ne a farko, sai sashen Fulani Halima, Sashen Fulani Hauwa kulu na ƙarshe shi ne sashen Fulani Asiya. Da yake a jere kamar yadda suke uwargida da mabiyarta har zuwa amaryarsa Fulani Asiya.
Duk a tsammaninsu zai leƙa sashensu ya fara ganim lafiyarsu, amma ga mamakinsu sai suka ga ya wuce wurin Fulani Asiya.
Fulani Hauwa kulu tana daga ɗaki ta ga giftawarsa, mamaki da takaici ya kamata. Tana nan zaune ta ga ya fito har zai fita ta yunƙura ta fita wurinsa.
"Ranka shi daɗe barka da hutawa."
"Barka!"
Ya amsa mata a daƙile, duk da bata ji daɗin abin da ya yi mata ba. Amma sai ta saki murmushi ta ce.
"Ranka shi daɗe idan ba za ka damu ba mu shiga daga ciki..."
"Duk abin da za ku faɗa, muna sauraronku ba sai mun shiga ba."
Ya furta fuska a haɗe, ajiyar zuciya ta sauke tana haɗiyar yawu mai ɗaci ta ce.
"Ranka shi daɗe haihuwa fa na yi, na aika Jakadiya ta sanar da kai ɗan babu rai, amma har aka binne shi ba ka zo ba. Kuma ba ka ga jaririn ba, sannan yanzu ka shigo ba ka leƙo ka ga lafiyata ba. Amma idan na yi kuskure ka yi haƙuri ranka shi daɗe."
"Tun da muka ji shiru ai kuna cikin ƙoshin lafiya, haihuwa kuma tun da babu rai mene ne amfanin ganinsa? Muna da magada masu yawa, don haka ku yi haƙuri idan ma kun haifa sun mutu. Domin tun asali mun fi son jinin Fulani Asiya ya gaje mu, kuma hakan ce ta faru tun da kwalliya ta biya kuɗin sabulu."
Cikin murmushi mai ɗauke da manufa ta ce, "Amma muna fatan waɗannan tagwayen su lafiyayyu ne da za su iya kula da sha'anin mulki?"
Da mamaki Sarki Dikko ya dube ta, sai Fulani Hauwa kulu ta cigaba da cewa.
"Amma kada ka sa a ranka su ne kaɗai za su iya zartar da mulkin masarautar nan. Wataƙila akwai wani jinin naka da zai shammaci magadan da ake tsammani."
Tana gama faɗar haka ta faɗa ɗaki, cikin ƙasa da murya ta ce.
"Sarki Dikko ka yi kuskure da kake tsammanin ni Karima zan lamumce maka, kuma ka yi ganganci da kake tsammanin tagwayenka za su mulki masarautar nan. Batul! Ita kaɗai ce za ta gaji karagar nan, ni kuma zan cigaba da yaƙi har na samu nasarar fitar da Babagana daga ƙangim bautarka."
Tana rufe baki Sarki Dikko ya ɗaga labulen ɗakin ya ce, "Me kuke faɗa haka?"
Fulani Hauwa kulu ta saki murmushin ƙeta ta ce. "A sauka lafiya ranka shi daɗe."
Masarautar Kajjura
Ɗan ɗagowa Sarki Gambo ya yi, ya zuba wa Fulani Sadiya idanu ya ce. "Matsalar da zan sanar da ke a kan su Hasana ne."
"Ni ma matsalarsu ce take tafe da ni, Sarkina akwai gagarumar matsala. Ka gafarce ni ranka shi daɗe, amma a yadda na lura da su Hasana kamar ba su da wadatacciyar lafiya."
"Ba kama ba ce Fulani..."
Nan take Sarki Gambo ya zayyane mata duk abin da ya faru, Fulani Sadiya ta kawar da kai gefe tana sakin murmushim ƙeta. Amma sai ta danne ta ce.
"Mene ne mafita Sakina, domin ba na son magauta su fahimci rauninmu. Ko kuma Malami ya kawo maka wata mafitar?"
Gyaɗa mata kai ya yi sannan ya sanar mata da bayanin Malami, sun jima suna tattaunawa. Sai da Fulani Sadiya ta kwantar da kai ta gama jin sirrin Sarki Gambo, sannan ta shiga nuna masa kulawa cike da soyayya.
Fulani Zainaba
A bayan ɗakunan bayi suka keɓe suna tattauna, cikin shigar ɓadda kama ta ce.
"Wanzam na kira ka ne domin na sanar da kai na san duk wani tuggu da kuke kitsa wa kai da Ciroma, kuma kai ka sani idan har na buɗe baki a wurin Takawa taka ta ƙare."
Wanzam da cikinsa yake kaɗawa ya ce, "Tuba nake ranki shi daɗe."
Murmushin cin nasara ta yi ta ce, "Idan ka ga wannan maganar ta mutu, to tabbas ka samar mini da jinin Sarki Gambo a gobe Alhamis idan za ka yi masa aski. Idan ba haka ba kuwa, tabbas zan bankaɗa masa sirrinka. Sannan na sanar da shi tuggun da kuka binne a cikin turakarsa."
Cikin sauri ya zube a ƙasa ya ce.
"Tuba make uwar ɗakina, zan yi duk abin da kike buƙata."
'A Gobe war haka na tabbata na samu nasarar ganawa da tsoro Sulaimanu tare da Kursum.'
Zainaba ta raya a ranta, daga can bayan bishiya Jakadiya da ke laɓe ta gyaɗa kai ta ce.
"Ƙarshenki ya zo Fulani Zainaba, na rantse da girman Allah sai na yi sanadin da Sarki Gambo zai tarfa ki a ɗakin."
A nan na zo ƙarshen book 1 na KUNDI UKU mai son karanta 2&3 zai tura 700 zuwa ga Aisha Adam 3090957579 shaidar biya ta nan 07062062624 idan littafi ya kammala zuwa doc 1k
Sarki Giɗaɗo ga shi da jaririya Batul, Sarki Gambo da Fulani Zainaba ga Jakadiya a gefe. Sarki Dikko ga Babagan ga Fulani Hauwa kulu/ Karima. Ba sai na ce komai ba, kun san dai akwai ƙura.👌🏻
Ummou Aslam Bint Adam🌚
07062062624
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels