na aura ba, duk tsanani Hubbi ba zai taɓa juya min baya ba, ba zai taɓa cin zarafina ta irin wannan hanyar ba, matsayin da nake da shi a zuciyarsa ya wuci gaban yaci mutuncina ta irin haka, yana tsanin sona na sani, kowa kuma shaida ne.
Kaman daga sama na jiyo ana kwaɗa sallama a parlo, na miƙe da sauri ina saita natsuwata na fita da sassarfa, da zumuɗin da na fita inci karo da Hubbi nah a asalin Hubbin da mu kayi aure cike da so da ƙauna gami da kwanciyar hankali a zamanmu na baya.
Sai dai me! Ina isa falo gabana ya faɗi ras sakamakon tozalin da nayi, duk sai na daburce ina neman rasa ina zanyi kuma mai ya kamata inyi. Yayar Hubbi ce ta zo Maijidda wadda muke cewa Yaya, daga ƙanne har ƴaƴa da ƴan uwa kowa Yaya yake ce mata, ita ce babbar su wadda ta zamar musu tamkar uwa, kowa na sonta haka kuma kowa na tsoronta, sai abin da tace ayi haka kuma idan ta faɗa ta zauna, ko mahaifiyarsu bata fiya yanke hukunci ba sai dai ta bata wuƙa da nama, haka duk abin da za'a yi sai da shawararta, ba'a taɓa yin abu ba tare da masaniyarta ba, ana girmamata sosai da mata biyayya, kuma itama tana mutunta kowa, ba zan ce bata da kirki ba idan na faɗi haka na zalunceta, macece mai ƙaunar nata, duk abin da ta tattaro na ahalinta ne, burinta taga kowa cikin farin ciki, haka kuma kowa ya tashi kai kukansa ita yake kaiwa, kowa Yaya komai Yaya, sai dai tana da zafi, bata ɗaukar raini, idan ta tashi faɗanta da masifarta shafar kowa yake yi, shisa kowa ke kiyaye abin da zai haɗosa da ita.
Kaf cikin matan ƙannenta tafi sona babu ya ni a wurinta, ba wai don su ɗin bata son su ba, a'a nima albarkacin tsananin soyayyar da take ma Hubbi ne yasa na zama ta gaban goshinta, yanda take nan nan da ni kamar ƴarta Shatu wacce mubke sa'anni, amma duk wannan tarin soyayyar tata da kulawarta gareni sun rushe cikin ƴan watanni, halinta da ɗabi'unta sun sauya, ban san laifin me na mata ba haka kawai ta ɗora dukkan fushinta da karan tsanarta a kaina, ko bikin da aka yi watan da ya wuce cewa tayi kowa ya zauna ya huta ni a tattara min duka ayyuka, haka na zama kamar wata ƴar aiki ko baiwa, nayi ta fama da uban wanke wanken kwanukan taron biki, shara kuwa har sai da na ranƙwafa saboda mugun riƙewar da bayana yay, da an tashi rabon abincin zata kira sunana ta yarfo min zagi tace in ɗauka in bi mutane in raba musu, ban da damar zama ko na sakanni, hatta kashin ƴaƴa da wankan yaran baƙin kunya duk ni ce, haka tasa aka wareni a gefe wai banda amfani, ta mayarni kaman wata jaɓa, na sha baƙin ciki da takaici a bikin nan, har sai da na dinƙa jin kaman in gudu gidanmu, sai dai ban isa ba YaShaik tsab zai takeni idan yaji cewar nayi yaji.
Su kan su ƴan bikin sai da suka ɗinka tausaya min wasu na cewa ya kamata a barni in huta, in huta tunda surukan gidan gamu nan fal, to amma ban isa ba, zaman hutawata daidai yake da zaman hutu a gidan iyayena tun da har Yaya na fushi da ni. To ni kam yanzu mugun tsoron Yaya nake yi, Wallahi a baya da zarar ta ganni take washe baki ta buɗe min hannaye in tafi jikinta ta rungume ni, amma yanzu har gwara naga hukuma su ce kamani suka zo yi akan ganinta, ganin ma ace a gidana.
Harar da ta banka min ita tasa na razana na ƙarasa gaban kujera cike da furgicin ganin fuskarta babu annuri. haka na rakuɓe tsugune kamar an jijjiga ɓera a buta, ji nayi gaba ɗaya ta cika falon saboda irin matan nan ne zabga zabga masu ƙiba, duk da idona a ƙasa yake amma ina jin irin banzan kallon da take jifana da shi, tana aikin kyaɓe baki kamar taga amai, ganin na buɗe baki cikin fusata ta katse ni.
"Lumɓu-lumɓu wutar ƙaiƙayi, tsiga tsiyau kazar matsiyata, wato saboda ba ki da mutunci, ba ki da tarbiya, ba ki da ɗa'a, ba ki san darajar na gaba da ke ba, ni kike jira in gaishe ki...me kika taka da har kike ganinki daidai da ni?, ko saboda an ɗauko ki daga tsiya an rufa asirinki cikin daula shiyasa kike ganin kinfi kowa?, aikin banza shafa lalle a ɗuwawu uban me ma kika aje a gidan da har za ki gadara. to ko shi me gidan yayi kaɗan in zo gidansa ya wulaƙanta ni wallahi, ke ga ƴar iska kina so ki nuna min dangin mijinki mutanen banza ne a wurinki, shiyasa har kina ji ina kwaɗa sallama ki ka barni a shanye, wato in gaji in bushe in kama gabana, to idan ba ki sani ba ki sani, ni mai sakawa ya sallameki ne kuma kin sallamu wallahi, ko idan danginki ne za ki wulaƙanta su har haka?, wato sai ni Yayar mijinki ƴar banza tazo miki gida ba za ki amsa sallamarta ba ko?".
Jiki na rawa na girgiza mata kai alamar a'a ina faɗin,"duk ba haka ba ne Yaya, don Allah don Annabi kiyi haƙuri, wallahi sam banji sallamar ba ina aiki...".
Daka min tsawa tayi tana katse sauran maganata, cikin faɗa sosai take cewa,"dalla rufe min baki munafuka algunguma makira mara tsoron Allah, aikin uban me kike yi a gidan nan banda kici ki kwanta, to idan ma aikin ne fina yayi da ba za ki iya katse kome ne ba, ballantana babu aikin da kike kina kwance sharaf kaman kayan tsinuwa, rashin mutunci dai irin na matan yau shi ya hanaki fitowa".
Na haɗiye abin da ke tokare a maƙoshina ina karanto hasbunallahu, cikin sadda kai ƙasa nace,"don Allah kiyi haƙuri hakan ba zai ƙara faruwa ba in sha Allahu, ki yafe min Yaya don Allah".
Sai na miƙe tsaye jiki babu ƙwarin kirki na shiga gyara kan kujerar da yake a gyaransa nace,"Bismilla Yaya ki zauna".
Ta maimaita,"in zauna?...Sa'ida saboda raini da cin fuska ni kike kallo kina ce min in zauna saboda ga jarababba ta isheki da hayaniya, Yo Sa'ida har wacece ke a gidan nan da sai kin ban izini akan abu, ko tunaninki umarninki nake jira shiyasa nake tsaye har wa yanzu?, Ehh lallai yarinyar nan kin riƙa, wuyanki ya isa a yanka, raini da cin fuska mai muni har haka?, ina Yayar mijinki za ki wulaƙanta ni?, to uwar me kike gadara da shi a cikin gidan nan?, tun da aka auro ki wacce tsiyar kika aje?, shekara takwas babu ɓatan wata balle ɓari, kin kasa ajiye ko tsinke sai aikin ci da kasayarwa, kuma a hakan kike neman gadara da gida, to ke a wa?".
Sai tayi shiru tana bin ko ina na cikin falon da kallo,"ina Nazifin yake?".
"Ya fita".
"Ya fita ina?, Ƙarya za ki min, shi dama yana fita ne ya wannan lokacin?"
Nace,"ai in ya fita magriba sai anyi isha'i yake dawowa, kuma yauma da mota ya fita ba lallai nan kusa zai dawo ba".
Zagayowa tayi ta zauna kan kujera, ta ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya tana girgiza su, tana ta kaɗa kai. Na wuce kitchen na ɗauko ruwa da lemu na kawo mata, a kofi na tsiyaya ina ce mata ga shi, na duƙa gefen ƙafafunta, cikin taushin murya nace da ita.
"Yaya don Allah ina neman afuwar laifin da nayi".
Ba ta dai ce min komai ba har wucewar wasu sakanni, kafin ta kalle ni cikin zafin rai tace,"wallahil azim idan ba ki bar min magana ba zan zabga miki maruka a wannan damammiyar fuskar taki da ta zame mana musiba cikin ahali, kuma ki kwashe kayanki tun da ban ce miki a yunwace nake ba".
Ni dai ban ko motsa ba kaina na ƙasa ina ta biya kalmar innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Yayin da ita kuma na ke jinta tana ci gaba da faɗin,"haba wannan wacce kalar annoba ce, yarinya sa'annin aurenku duk sun haihu daga masu ƴaƴa biyu sai uku, amma ke kina zaune sai dai a ciyar da ke ki cikawa mutane masai da kashi, aure shekara takwas babu wani labari, ai wallahi da sake a wannan lamarin, dole a duba".
Furucin nata yasa na ɗago da sauri na kalleta, ta ƙara jefa min wani matsiyacin kallon tace,"ƙarya na miki?, ko sharri na miki?. to ki kira min mijinki duk inda yake ya dawo ina son magana da shi, yazo ayiwa tufkar hanci, ba zai yiwu yayta ɗawainiya da ke yana faman hidimta miki amma kin kasa biyansa da ƙyanƙyasar ƙwai ko guda, gida har gida kamar wannan ace babu ƴaƴa, wa zai gaji uban dukiyar da aka tara?, to idan shi baida hankalin tunani da lura mu ƴan uwansa da muka san ciwonsa zamu nemi mafita. Yazo ya ɗauke ki a daren nan kuje asibiti ayi miki gwajin haihuwa, idan haihuwar ce ba kya yi muji, idan kuma irinku ne masu dogon jinkiri shima muji, ke idan ma da gayya kika hana haihuwar zamu ji ai, don ni nafi tunanin mugunta ce irin ta ɗiyar talakawa, bai wuci zuwa kika yi aka sa miki tsarin iyali ba. Yo me ma ake da ƙarin aure da ba zai yi ba ya ke ta zama da baƙar aniya, ai wallahi muddin ɗaya cikin abin da na lissafa ba za'a shafe wata guda curr ba sai ya ƙara aure tunda ke ba abar mora ba ce, gwara auren wadda ahali za suyi alfahari da ita, waye ba ya so yaga zuri'arsa?, yo wannan ma ai cutarwa ce ace yana zaune da macen da bata haihuwa, me amfanin auren?, Ai ko ma'aiki cewa yay kuyi aure ku hayayyafa domin in alfahari da ku ranar gobe ƙiyama...don haka Maza maza tashi kira min shi a waya, kuskurena ne ma da ban zo da tawa ba, ki kirasa yazo kuje asibiti yanzu yanzu, wallahi ko haihuwa ko ƙarin aure, ba za'a ci gaba da zama a yanda ake ba".
Maganganunta duk sun saka jikina ɓari, cikin kaina babu abin da ke nanatuwa sai kalmar rashin haihuwa da ƙarin aure, wato duk a baya basu san da matsalar rashin haihuwar ba sai a yanzu. Kuma har tana da bakin kirana ƴar talaka, ehh lallai ciki mai manta kyautar jiya, saurin share hawayena nayi ina ƙoƙarin daidaita yanayina, domin kuwa tun da har na gano manufarsu ta tsangwamata to ba zan taɓa bari suga raunina ba, ballatana su ƙara samun damar cin zarafina yanda suke so.
"Ba kiji me nace miki ba ne, ki tashi ki kira min shi a waya, ni ba wajenki na zo ba balle ki sani a gaba da kirsa".
Hmmm ɗan Adam kenan mai wuyar gane hali, dama ai shi gwano ba ya jin warin jikinsa, ban da haka mancewa tayi ƴarta ta fari har yanzu bata haihu ba, shekararta goma sha shida da aure shiru babu labari, kuma babu wanda ya tsangwameta ƙarshe ma ɗa aka samu a dangi aka bata, sai ni da ban ko rufe shekara goma ba zata ƙwazzafe ni, ta ɗaga min hankali, ita ba ɗanta nake aure ba, yo ko ɗanta na ke aure irin rayuwar da na yi da shi ai ta shafa min lafiya.
Ji nayi ba zan iya yin shiru ba da zage zagen da take ta yarfo min, hakan yasa murya a hankali nace,"Yaya dama wannan shi ne kuskuren nawa wanda yasa duk ku ka juya min baya?, soyayya ta koma ƙiyayya?, akan abin da bani na ɗorawa kaina ba, akan lamarin da yake na ubangiji shi ne ake tsangwamata haka. Yaya haihuwa fa ta Allah ce na san kin sani, haka duk wanda ya haihu ba shi ya bawa kansa ba, kuma duk wanda aka haifa ba shi ya haifi kansa ba. in har ace ina da iko da haihuwa ai da tuni wani labarin ake, domin nima ina so na ganni da zuri'ata, na ga yau na kafa nawa ahalin".
Muryata ce ta raunana a daidai wannan gaɓar, sai dai ban bari ko kusa ta fahimci cewa kuka nake so nayi ba, tabbas ba zan juri wulaƙanci ba matsawar akan wannan matsalar ce, ai bani kaɗai zan haihun ba, dole sai da ɗan uwan nasu, don haka muddin za'a duba lafiyata akan rashin haihuwata to shima sai an duba tasa. Maganarta naji a tsakiyar kaina tana faɗin,"kin gama min wankin babban bargon?, Nace kin gama zagin nawa?".
Na kasa danne abin da nake ji a ƙirjina na ɗago kaina ina kallonta, lokacin ta miƙe tsaye tana gyara yafen mayafinta, na rumtse ido nace.
"Ki haƙuri ban faɗa miki komai da rashin kunya ba, iya gaskiyata na faɗa, haihuwa ba ni zan bawa kaina ita ba Allah ne mai bayarwa, kuma mafi aksarin jinkiri alkhairi ne, bamu san mai Allah ya shirya mana ba, da haihuwar yuyuyu gwara haihuwar babu, rayuwar nan ba'a ƙareta ba duk da bamu san gawar fari ba, amma ni ina da yaƙinin ba zamu kai ga kushewa ba sai Allah ya azurtamu da haihuwa, sai Allah ya bamu mai jin ƙanmu da alfaharinmu. Kar ki tafi zan kirasa a waya muje asibitin yanzu a duba ni, amma don darajar Allah kar ku yanke hukuncin ƙarin aure, don Allah kar ku saka ya ƙara aure, ba don bana sonsa naƙi haihuwa ba, Allah ne bai kawo lokacinta ba ki duba min Yaya, nayi ƙaranta ace za'a min kishiya yanzu".
"Mtswwww". Taja wani dogon tsaki mai muni wanda yay duka har tsakiyar ƙwaƙwalwata. tasa ƙafa tayi fatali da teburin gabanta, lemu da ruwan da suke kai suka zube akan carpet.
"Sa'ida kici min mutunci ki tsammaci za ki ci gaba da rayuwa ke ɗaya a wannan tamfatsetsen gidan, kice ke ɗaya za ki mori dukiyar Nazifi?, Bayan kin tauye masa hakki kin hana shi ƴaƴa kice ba zai auro mace mai lafiya ba, ai ƙarya kike wallahi...ni bani hanya na wuce ko in bi ta kanki, banza juya kawai marar amfani".
Juya! Kalmar tayi wani tsallen maimaituwa a ƙoƙon kaina, na ɗaga idanuwana nabi ta da kallo har ta fice ta bar parlon. Juya! Juya! Juya!, kalma mafi ciwo da raɗaɗi a duk cikin kalaman da ta gaggaya min, wannan hanyar da suka ɓullo da ita tabbas zata zama hanyar karayata, bana jin zan jurewa gorin haihuwa, duk haƙurina ba zan ɗauki wannan ɓangaren ba.
Idanuwana naji su na zugi, duk da ban kallesu ba na san sunyi jajur, sai dai ko kusa ko alama hawaye sun kasa zuba daga cikinsu. Plate da kofunan da ta kifar na tattara na kai kitchen, na dawo ɗauke da tsumma na goge lemun da ya zube kan carpet, ac na ƙaro saboda wurin yay saurin bushewa gudun kar yay ɗoyi.
Cikin ƙarfafawa kaina gwiwa na wuce ɗakin barcin Hubbi, ina shiga na gyara ɗakin kaman ko da yaushe da na saba. na hau sama na kwaso kayan abincinsa na sakko da su, akan tebir na ajiye, haka kuma ban canjawa warm coolers ɗin da na tarar ba waje. Ayyuka na daban na tsira duk dan in mance da cin zarafin Yaya, ina ji aka fara kirayen sallar isha'i, ban tsaya da aikina ba naci gaba kasancewar ina cikin jinin al'ada, gyara na musamman na yiwa bedroom ɗin nasa a wannan daren, duk wani kai komo da nake maganganun Yaya ba su bar haska min a cikin kaina ba, sai dai ina ta ƙoƙarin kawar da komai ɗin domin bana son hakan ya tsaya min a rai, don ko Hubbi ba zai san da wannan labarin ba, shiru shiru har ƙarfe tara Hubbi bai dawo ba, kuma bai kirani ba bai tura min saƙo ba.
Ɗakina na koma na sake wanka don idan ina cikin jini sam bana sakewa, sai in ta jin kaman jikina duk ya ɓaci, haka kuma kaman ina ta ƙarni.
Murmushin takaici nayi da na kalli kaina a madubi, me yasa nayi wannan saken?, ta ya zan bari jikina yay wannan lalacewar?, dududu shekarata nawa?, ni akaran kaina ƙirjina ya daina burgeni balle kuma miji da kansa, ba komai ya lalata ni ba irin saka damuwa a rai, ni da ban taɓa shayarwa ba ai bai kamata ace na bar nonuwana sun zube ba yaraf, bayan na san Hubbi na matuƙar son su, to dole na miƙe tsaye, zan dawo asalina mai cikakkiyar sura ta ko'ina, in kuma fita daga cikin sahun mata masu dugun kai a gidajen aurensu ta ɓangaren shimfiɗa soyayyar aure. Sai da na gama kimtsa jikina tsab tukunna na fito ɗakin na kulle duk ɗakunan sama da kitchen, na sakko ƙasa na kashe fitilun falo tare da kunna karatun ƙur'ani wanda dama da shi muke kwana kullu yaumin. Agogo na kalla naga har ƙarfe goma daidai, tsammanina zuwa lokacin Hubbi ya dawo tun da na jima a ɗakina, sai dai ina shiga ɗakinsa naga babu alamarsa, kenan har yanzu bai dawo ba, take zuciyata tayi zullo na fara jin tsoro, ban san me yake faruwa ba, fatana ɗaya Allah yasa lafiya.
Kasa tsaye nayi na kasa zaune, in kai mari in kai gauro saboda kiran lambarsa da nake yi bata ko tafiya. Tunanin in kira office ɗinsa yazo min, sai dai ko da na kira aka tabbatar min da cewa ai tun biyar ya bar office. nan fa hankalina ya tashi, na rasa wa zan kira tun da shi ba wasu abokai gare shi ba, haka yake kamar mace mara son ƙawaye.
laluben lambar ƙaninsa na shiga yi, ko da ya ɗaga bamu wani tsaya gaisawa ba na tambayi ko Hubbi yaje gida, yace ba ya gidan tun da rana da yazo gaida Iyam. muna gama wayar na ƙara gwada kiransa, wani sanyi naji a raina da ta fara ringing, sai da nayi kira har sau goma bai ɗaga ba sai daga ba ya message ɗinsa ya shigo.
"Ba na son damu akwai abin da nake yi".
abin da ya rubuto min kenan, kuma ina gama karantawa na aje wayar jiki a sanyaye, ko ba komai naji dama-dama tun da lafiya yake, sai dai naji babu daɗi sosai, domin kamata yay ace in akwai adalci ya ɗaga wayan ya faɗa min uzurinsa, ko kuma ya rubuta min idan babu daman ɗaga wayar, amma saboda rashin sanin hakkina da girmama aure yana can lafiya ya barni anan cikin damuwa da tashin hankalin halin da yake ciki, ko abinci na kasa ci haka cikina yake fayau tun ruwan safe da na sha.
gudun tunanin da ka iya rufe ni na miƙe na kwanta akan gadon. Sai dai me? daga kwanciyar tawa na saki marayan kukan da nayi ta dauriyar riƙewa tun tafiyar Yaya, sautin kukan ya cika ɗakin, kuka nake kamar wadda aka yowa aiken mutuwa don kawai in samu in fitar da baƙin cikin da ke raina. na janyo filo na toshe bakina da shi amma duk da haka sautin kukana bai ɓuya ba. Lokaci ɗaya jikina ya ɗauki zafi na kama kyarma dama ni ban iya zazzaɓi ba. A wannan lokacin duk wani mai imani ya ganni sai zuciyarsa ta motsa da tausayina. Haka na ke ta faman zubar da hawaye, ban isa na goge su ba don ina gogewa wasu na sakkowa.
Na daɗe ina kuka don har wajen sha ɗaya da rabi, zuwa wannan lokacin kam na fidda ran dawowar Hubbi, banga alamun yau zai kwana a gidan ba. saboda haka na miƙe na shiga banɗaki na wanko fuskata ina hana kaina ci gaba da kukan da baida amfani gare ni, adu'a maganin annoba ita ya kamata in riƙe ba wai damuwa da kuka ba. Ina fitowa na wuce nasa key na kulle ƙofa duk da zuciyata na faɗa min komin dare zai dawo, bai da wani wajen kwana a daren nan sama da nan ɗin dai da yake ƙauracewa, tsakin ƙasan maƙoshi nayi, to ina ruwana da dawowarsa, raina ɓace na fita falo na bi duk ƙofofi shigowa na saka musu maƙulli, zanga ta in da zai shigo, ai sai dai yay kwanan ɗakin mai gadi, ba abar banza ba ce ni, auroni yay don yana so ba cusa masa aka yi ba, kuma a gidan iyayena ya ɗauko ni ba gidan marayu ba. kamar ma in koma ɗakina amma sai na dawo ɗakin nasa, na murza key na kashe fitila me haske na bar mara hasken wacce ke kan durowar gefen gado.
Bacci nake ta so nayi amma gaba ɗaya na kasa, sai juyi da nake ta faman yi, zuciyata kuma cike da saƙe saƙe, kaina kuwa ya cika fal da tunani daban daban. Ni dai lafiya ƙalau muke da mijina, sai dai tun bayan dawowarmu nan gidan da wata bai fi biyar ba komai ya canja na daga yanda muka saba rayuwa, ni da shi kamar abokai haka muke, amma yanzu ya zamar min wani horo har tsoronsa nake yi, magana ma shakkar masa na ke, komai nayi ban iya ba, saɓanin a baya duk abin da nayi ko da bai masa ba zai yaba min kuma yace nafi kowacce mace iyawa, yanzu abu kaɗan zan yi ya zama laifi, zama da shi ban isa ba in ba haka ba ya dinƙa ƙunci kenan ni kuma bana son ƙuncinsa, hatta makarantar tahfeez ɗin da nake zuwa yanzu nema yake ya kashe zuwanta, don duk san da zan tafi sai yayi ƙorafi akai, sai yace ai tunda na iya karatun sallah na san wankan tsarki na kuma san zaman aure ya ishe ni, da nayi magana sai yace ai shi ke biyan kuɗin ba wani ba saboda haka yana da ikon ya hana zuwan.
Na kau da tunanin matsalata da mijina, na koma tunanin furucin Yaya na za su sa ya ƙara aure, tabbas na sani ƙarin aurensa tozarcin da nake sha sai ya ninku, don sai na ƙwammaci ina ma ban auresa ba, Allah ɗaya ya san irin wulaƙancin da matarsa zata dinga min, balle ta san don manufar da aka aurota, zata goranta min fiye da yanda dangin miji za su min, kuma daga zarar ance ta sami ciki ta haihu shikenan tawa ta ƙare, zaman auren sai ya ishe ni, takaicin da zan sha ba daga wurinta ba kaɗai har da shi uban gayyar. ni kaina na sani Hubbi yayi ƙoƙari, ba kowanne namiji ne za'a kai wannan lokacin ace bai yi ƙorafi ba, kamar yanda Yaya ta faɗa shekara takwas ban taɓa ɓatan wata ba balle azo ga maganar ɓari, kuma ko da wasa Hubbi bai taɓa min magana ba, balle ya nuna min damuwarsa ko ƙorafi, ni ce ɗin ma na ke damuwa, don sau tari har kuka na kan yi, sai yay ta min nasiha yana ƙara faɗa min lokaci da rabo ne, idan na ɓata masa rai akan nuna masa kar a fara cewa bana haihuwa ya dinƙi faɗa kenan, yace min duk wanda ya fasa faɗar hakan ba ya ƙaunar Allah, kai duk wanda ma yay min gorin haihuwa in sanar masa hukuma ce zata raba su, watarana kuwa da nace masa muje asibiti a duba ni bai ci abincina ba. yanzu kuwa yanda muke zaman babu daɗi da shi ai nayi kaɗan in kai masa ƙarar Yaya akan cin mutuncin da tazo ta min, kuma ko da ace shima wannan ne dalilin samun matsalarmu ba zanga laifinsa ba, a yanzu kam yana da buƙatar magajinsa, wanda zai ɗora akan kasuwancinsa ya kuma mallakawa kadarorinsa. sai dai fa ya tuna ana barin halak don kunya, ko mai zai yi min banda wulaƙanci, don ni na sha gaban ya wulaƙanta ni a rayuwa, domin na masa abin da ko ƴan uwansa basu masa ba, ya kuma san hakan, sai dai in ya butulce, kuma shi butulci dama ai ba sabon abu ba ne a wajen ɗan adam musamman wanda ka yiwa rana.
Haka dai a wannan dare nayi ta tunane tunane, in raya wancan in saƙa wancan, in lissafa wancan, sai dai na kasa warware komai, haka duk na ƙosa gari ya waye, ni ba sallah ba balle in yi nafilfili, a haka dai har ɓarawon bacci ya ɗauke ni a lokacin da ban san ko ƙarfe nawa ba.
Washegari ban farka ba sai wajen ƙarfe
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 2 Chapter of 23