fatansu da burinsu shine na karanci aikin likita dan tun yanzu mafi yawan lokuta Abbaana da likita yake kirana, ni kuma domin farin cikin mahaifana nasa a raina cewar in sha Allahu zan yi duk iya ƙoƙarina na dage nayi karatu don wanzar da farin ciki bisa fuskar iyayena wanda kuma nasan ta hakanne zan biyasu da kaso babu cikin kaso ɗari na ɗawainiyar da suka yi da ni. Yanzu haka duk wata jarabawa da za'ai ni ke zuwa ta biyu bayan ƙawata Safiyya da ke ɗaukan ta ɗaya. Ina maida hankali sosai a karatuna matsalata ɗaya yaren turanci wato english bai zama akaina balle bakina, ƙila don Malamai ba da turancin suke mana karatu ba ne ko da zasu yi magana da mu, hakan na ɗaya daga dalilin da yasa turanci yay min ƙaranci, kuma shine kawai matsalata a karatun boko, iyayena duk ba su yi karatun boko ba balle na sami taimakonsu, Yayyuna ba zaman gidan suke ba, amma a hakan ma ina ɗan ƙoƙartawa wajen kwaɓawa. Ɓangaren islamifa kuwa nayi saukar ƙur'ani na makarantar allo tun ina shekara tara, yanzu haka kuma na kusa yin sabuwar sauka a islamiyarmu, banda tarin littafan addini da na sauke na haddace su, fagen larabci a bakina kuwa ba'a magana.
"Wallahi nayi mugun jin daɗin hutun nan".
Safiyya ɗaya daga cikin ƴan mata mu ukun ƙarshe da muka fito daga aji ta faɗa tana gyara goyon jakarta. Maimuna da ke daga gefen hannun hagunta ta ce,"ba ki kai ni jin daɗi ba, saboda dama duk na rasa yanda zanyi da bikin Anty Samira, Baba yace ba za'a je da mu Kaduna ba, kinga yanzu na sami dama tun da dai monday ba makaranta".
Tayi maganar cike da farin ciki.
Haka suka yi ta maganganunsu har sanda muka fito bakin gate. Maimuna na kallona tace,"Yau me zamu siya?".
Sanyayyan murmushi me faɗi nayi kafin na ce,"abin da aka saba mana".
"Mayyar rake, to ni kam yau siyan rake ba da kuɗina ba, sai dai kowa ya siya abin da ransa ke so". cewar Safiyya tana min harar wasa.
Na harareta da manyan fararen idanuwana, ban ce mata komai ba naja hannunta muka nufi titi muka tsallaka. Sai da muka je daidai wajen me rake tukunna muka tsaya, sallama muka masa ya amsa mana, daga yanayin yanda mu ke gaisawa da shi zaka fahimci mun saba da cinikayyar yau da gobe, yana zuba mana raken a leda Safiyya na ta zuba masa zance, shi kuma yana ta biyeta da yake yana da baki kamarta, irin hirar ta su ba zaka ce a wajen siyan raken suka saba ba, Ni da Maimuna dai sai um da um da ke itama irina ce wajen rashin son magana.
"Ka biyewa zancenta kana ta zuba raken da yafi ƙarfin na kuɗin da aka baka".
Maimuna tayi maganar tana ɗora hannunta a kafaɗata.
"Ƙila sai ya kwashe raken gaba ɗaya kafin ya ankare". cewata wadda nayi maganar da zolaya kuma lokacin ya ɗago ya kalle ni.
Dariyar da Safiyya ta saki yasa muka zuba mata ido, raken ne a hannunta tana kaiwa baki tana ce masa,"Yaya Nazifi kaga waɗannan ƙawayen nawa haushi su ke ji saboda ina sha su basa sha, kuma fa daga yau kafin na ƙara samun rake me kyau da zaƙinsa har sai nan da kwana huɗu. Don haka Yaya Nazifi rabu da su ka cika mana leda".
Na girgiza kai nace da ita,"ke dai ba ki da tausayi"..
Kallona tayi tana ɗaga gira irin eehh taji ɗin. Maimuna tace da me raken,"Yaya Nazifi to kaji mara ƙaunarka da rashin tausayinka".
Ba tare da ya ɗago ya kalle mu ba yaci gaba da zuba raken fuskarsa na washewa da murmushi. gaba ɗaya yaran jinsu yake tamkar ƙannensa, shiyasa sau tari idan sun zo siya baya basu da wuri sai yay ta laƙai-laƙai don yana jin daɗin hira da su, akwai tarbiya, kama kai da girmama manya. Sai bayan ya ɗaure ledar tukunna ya ɗago duk ya kalle mu kana yace,"ga shi ƙannena asha rake lafiya, yau na san har dalalar yawu za'ai saboda zaƙinsa na daban ne, ai dai sha a hankali kar zaƙin yaywa haƙori illa".
Yay maganar da ƙawataccen murmushi kuma cike da zolaya.
Ina kallonsa sosai na ɗan waro ido waje na ce,"Naira sittin fa muka baka, wannan kuma ai ya kusan na dubu ko ma yafi".
Maimuna ta ce,"wannan sudar ce ai duk taja, ka rage don Allah".
Annuri ya ƙara wadatuwa a saman fuskarsa sannan yace,"kar ku damu ƙannena, idan ban baku ba zai zama asara ne, saboda dama da makarantar taku na ke ciniki, ga shi kuma kunyi hutu, kuna ta murna abinku ni kam ina ta fargaba domin zan rasa kasuwa, ko cinikin kwana guda bana so na rasa".
Tausayinsa yay matuƙar kama mu, tun ma daga yanayin yanda maganar tasa da ke tattare da damuwa tsantsa. Safiyya tasa hannu ta karɓi ledar tana ta zuba masa godiya. Maimuna ta warce ledan daga hannunta tana faɗin,"ke ba ki da tausayi sam wallahi, hankalin ma ba shi ne da ke ba".
Sannan ta dubi me raken ta ƙara cewa,"gaskiya ba za'a yi haka ba, idan ka barsa za'a samu masu siya ko ba'a nan ba".
Haka muka yi ta fama da shi akan ko yane ya rage amma sam yaƙi, dole muka haƙura muna zuba masa adu'a da godiya. san da muka juya za mu tafi muka ce ya gaida Antin mu ya amsa mana da tabbacin zai isar da saƙonmu. Tare da ƙara cewa,"Mahaifiyata bata da lafiya don Allah ku sakata a adu'arku ta kullum".
"Subhanallah Allah ya bata lafiya yasa kaffara, Allah ya tashi kafaɗunta nan kusa, Allah yasa zakkar jiki ne".
Muka haɗa baki wajen faɗar hakan, yaji daɗin adu'ar na mu sosai, ni dai sarkin tausayi har da ƙwalla ta taru a idona, muka masa sallama muka wuce, yayin da shi kuma ya ɗaga bindi(jelar saniya da ake kore ƙuda) yana kore ƙudajen da ke neman kawowa raken hari, gefe guda kuma yana ƙara ɗaga murya da faɗin,"Asai rake, azo a siya rake me zaƙi, ga arha ga daɗi".
Cikin waƙa yake ta faɗin hakan domin janyo hankalin abokan ciniki.
Ai kuwa abin kamar almara, nan da nan sai ga sauran ƴan makaranta sun zo sun siye shi tas, a lokacin babu abin da ya tuna sai maganar Sa'ida da tace za'a siya insha'Allah, murya a hankali ya ce,"Na gode da adu'arki". Ya faɗa kamar a gabanta, bayan ya gama tattara kuɗin cinikinsa ya tura baron raken ya tafi.
*MANDAWARI ROAD, KANO.*
Daga cikin baƙar mota ƙirar Rolls-Royce, wata dattijuwar mata ce fara ƙal zaune a bayan kujera yayin da driver ke tuƙata, kallo ɗaya zaka yi mata ka gano tsantsar hutu, natsuwa, kwanciyar hankali da jin daɗi a jikinta, ka kuma san lallai naira ta samu wuri ta zauna. kunnenta zuwa wuyanta da tsintsiyar hannunta da ƙafarta sanye su ke da gwalagwalai na gasken gaske, ga walwalin adon stones na tsadadden less ɗin jikinta na matuƙar ɗaukar ido.
Waya ce kare a kunnenta ƙirar Iphone 6plus a lokacin ita ake ganiyar tashe, hankalinta ya tattara gaba ɗaya ga maganar da ake yi ta cikin wayar, da dukkan alama waya ce take yi da mutum me muhimmanci a rayuwarta, saboda yanayin tsantsar farin cikin da ya nuna a tare da ita, tun fara wayar bata furta komai ba, sauraren shi kawai take yi cike da annashuwa, a karo na barkatai fuskarta ta ƙara washewa da sanyayyan murmushi me faɗin gaske, take kuwa haƙoran makka guda huɗu dake a bakinta sama da ƙasa suka bayyana, inda asalin kyawun fuskarta ya ƙara fitowa.
"Tom shikenan, amma ka sani ina kewarka sosai ya kamata kaji tausayina ka dawo haka".
Shiru ya gimla na ƴan sakanni tana ci gaba da sauraron maganar cikin wayar kafin ta sake cewa,"ni dai ba na son wayo".
Siririyar dariya ta maye gurbin murmushin da take yi sannan ta ƙara cewa,"To ya zanyi da kai, yanda kaso haka zan so, fatana shi ne ka dinƙa kulawa kaji ko, a tsare mutunci ka kuma ji tsoron Allah a duk inda kake".
Ta numfasa tana lumshe idanuwanta tare da cewa,"Allah yay maka albarka, Allah ya kiyaye min kai. Ka kira Madam ku gaisa tana ta min sababi baka ganinta da gashin ido".
"Oak to bye bye, i love you so much my son".
Wayar ta yanke sa'ilin da take sauke gwauron numfashi tare da kwantar da kanta jikin kujera still idanunta a rufe, yanayinta kuma na canjawa, kamar dai tana ɗauke da wata ɓoyayyar damuwa da ke maƙale can ƙasan zuciyarta, yayinda a gefe ɗaya ta ɗan takure hannunta cikin mayafi kamar me jin sanyi. Kuma kamar a mafarki Mrs Abubakar Jadda taji tayar motar su ta bada sautin ƙara ƙuuuuuuu, ƙarar da ta shiga har can cikin dodon kunnenta, lumsassun idanuwanta suka buɗe a sanda Driver ke furta kalmar Innalillahi wa'inna ilihi raji'un.
"Me ya faru Muntaƙa?". tayi tambayar a ruɗe idanuwanta na firfitowa waje, tashin hankali na farat ɗaya na bijiro mata.
"Ranki ya daɗe mutum na buge...".
Bai ƙarasa maganar ba Mrs Jadda ta ƙwalla ƙara sakamakon tozalin da idanuwanta suka yi akan uban jinin da ya wanke rabin gilashin motar, bata san lokacin da ta fiddo da hannuwanta da ke ɓoye cikin mayafinta ba ta ɗora su aka tana biyo kalmar innalillahi wa'inna ilaihi raji'un. Tun driver bai ƙarasa bayaninsa ba ta buɗe murfin motar ta fita a sukwane, lokacin jama'a har sunyi cincirundo a wurin, cike da tsantsar tashin hankali ta raɓa ta tsakaninsu, ganin yarinya kwance cikin jini yasa ta ɗora hannu aka tana salati tare da zube gwiyoyinta a ƙasa.
"Wayyo Allah na, jama'a ku taimaka min mu shiga da ita cikin mota". maganar take cikin bala'in tashin hankali mara misaltuwa.
"Muntaƙa mu wuce asibiti". ta ƙara faɗa tana kamo yarinyar jikinta.
"You are under arrest". taji sautin muryar wani babban mutum a saman kanta, tana ɗaga ido taga ƴan sanda guda biyu suna ƙoƙarin sanyawa Driver ankwa. hankalinta ya kuma kaiwa ƙololuwar tashi, nan da nan ta shiga roƙonsu akan su yi haƙuri su bari tukunna a isa asibiti koma meke da akwai sai ayi. Kuma take anan hannu na rawa ta ɗauko waya ta kira mijinta ta sanar masa halin da ake ciki wanda ta mance da ya ba ya ƙasar ma, da kanta ta ɗauki Sa'ida da ke kwance cikin jini ta sanya a mota, har lokacin salati kawai take yi ganin kamar yarinyar ta rasa ranta, driver yaja motar a miliyan yayin da motar ƴan sanda ta mara musu baya.
Babu wanda ya lura da Safiyya da ke ta ruzgar kuka sai a yanzu, tsoro da fargaba da tashin hankalin da ya risketa yasa ta duƙe a wuri ɗaya ta ɓoye kanta a tsakanin cinyoyinta, jikinta gaba ɗaya rawa yake yi tana kiran sunan Sa'ida, ba ita kaɗai ba duk wani me zuciyar imani in yaga mummunan haɗarin sai hankalinsa ya nemi ya gushe. Wani dattijon mutum ya ƙaraso wajenta, yana taɓata ta ɗago a furgice, idanuwanta har sun yi luhu-luhu, bakinta na rawa tace masa,"Sa'ida tah kar ta mutu Baba don Allah kar ta tafi ta barni".
Sai kuma tayi shiru tana ƙara fashewa da sabon kuka. "Ya Allah? Ya Allah". iyakar abunda take faɗa kenan ta kasa yin aduar da take son yi.
"Kinga kwantar da hankalinki ina ne gidan ku?".
Sai ta miƙe a rikice tana girgiza kanta,"ba zani gida ba, ba zani ba hankalin Abbaa zai tashi Ummani zata yi kuka".
Kai da kaga yanda take maganar kasan ba'a hayyacinta take ba, tsohon ya riƙeta da kau aka tari me napep suka shiga don nufar gidansu ko na su Sa'ida
*YAKASAI B, LAYIN KWALE-KWALE.*
Ƙarfe takwas na dare a lokacin, unguwar ta ɗan yi tsit ba kamar da rana ba, gajiyayyen gida ne madaidaici daga ɓarin dama cikin tsakiyar gidaje biyar ɗin da ke jere, irin ginin gidan daga waje jar ƙasa ce sai ciki kuma aka yi ɗan gyare-gyare da bulo sai dai babu filasta, da zarar ka shigo dogon soron gidan guda biyu zaka ji warin daddawa na tashi, soron farkon duhu dunɗum baka iya ganin ko da yatsanka, a soro na biyu kuma zaka yi karo da manyan botikan da ake wanke kalwar yin daddawa, shima babu haske sai na farin wata da ya ratso ta ƙatuwar ɓular langa langar soron, duk da cewar dare ne a lokacin kuma babu hasken fitila amma kana iya ganin ƴan tsirarrun ƙudaje sun yi yaɗo a saman bokitan kalwar.
Daga cikin gidan kuwa tsakar gidan yay ƙal, ko'ina fes fes, duk kuwa da rabi da kwatan simin ƙasa ya farfashe. kai da ganin yanda komai yake a killace a tsabtace kasan ba gidan ƙazamai ba ne duk da cewar gidan talakawa ne sosai, ba zaka taɓa cewa gida ne da ya tara iyali da yawa ba saboda tsananin tsabtarsa, kuma da zarar ka zuƙi kyakykyawar iska zaka zuƙo ƙamshin turare ɗan tsinke sama-sama.
"Kambun-baka gaskiya ne domin yana faruwa kuma yana iya kai mutum ga mahallaka (mutuwa) saboda tsabar tasirinsa a jikin mutum, saboda haka ya zama wajibi mu nemi kariyar ALLAH Shi kaɗai, sai riƙo da hanyoyin samun waraka ko riga-kafi wadanda suka inganta a shari'ar Allah wajan kare kanmu da iyalanmu daga sharrin Kambun-baka da hassada. Kambun-baka ko Kambun-Ido, Nassi ya yi bayaninsa kamar yadda itama Hassada akayi bayaninta, kuma duk an bayyana mana irin illar da Kambun-baka yake yi ga lafiyar mutane domin yana iya hallakar da mutum ko kaga mutum yayita fama da rashin lafiya mai tsanani. Addini ya koyar da mu hanyoyin da za mu nemi ALLAH ya kare mu daga sharrin dukkanninsu da ma masu yin su gaba ɗaya, mu nemarwa kanmu, iyalanmu, dukiyarmu da duk wata ni'imar da mu kasan muna da ita kariya da tsarin ALLAH Ubangijin kowa da komai kuma mai iko akan kowa. yana da kyau muyi Riga-kafi akan kambun baka, wato (neman kariyar Allah kafin abin ya faru da mutum har yayi tasiri akansa), da kuma yin maganin da bai saɓawa Shari'ar Allah ba idan abin ya faru har yayi tasiri akan mutum. saboda haka mu yawaita karanta Ayatul Kursiyyu da Surorin Falaqi da Nasi musmaman a lokacin da za mu kwanta bacci saboda neman Allah ya kare mu daga sharrin Kambun-baka da na hassada, saboda tasirin sharrinsu a jikkunan mutane ya zarce wanda shafar jinnu ke haddasarwa, ga naci da ƙalata wajen son dauwama a jikin mutum da sanya cututtuka iri-iri, ubangiji ya kare mu da kariyarsa".
Maganar da ke fitowa kenan daga cikin ɗaya daga ƙananun ɗakuna biyar ɗin gidan, Kowa a cikin ɗakin zaune yake bisa ƙatuwar tabarmar da ke malale a tsakar ɗakin, kamar dai yanda suka saba kullum a gidan duk bayan sallar isha'i, sun kasa kunnuwa cikin natsuwa suna sauraron karatun da mahaifin su Malam ke musu.
Ummaa kishingiɗe a kusa da Malam, sai Iyam kwance gefen Malam ɓangaren damansa Gwaggoje mahaifiyarta na yi mata firfita, Amarya daga bakin ƙofa riƙe da tourchlight mara haske dalilin sanyin batir, sai yaran su a kusa da juna rabin hankalin su akan Malam sauran rabin akan Iyam da bata da lafiya tana fama da ciwon ƙafa da ko takawa bata yi, yayin da duk wani rai zuciyarsa kema Iyam adu'ar samun lafiya domin kusan ita ce garkuwar iyalan Malam Bala Mai Kalwa.
Jummai(Iyam) ita ce matar Malam ta farko wadda aka yi aure tun ƙuruciya, tana da bala'in kishin mijinta ga fafutukar sana'a don kusan ita ce jigon kasuwancin kalwar da Malam ke yi a ƙauyuka da birni, ita ce take dafawa tayi aikinta tas shi kuma ya fita da ita kasuwa a siyar. Ƴaƴanta goma banda waɗanda su ka rasu, Hashimu(Yaya Babba) Maijidda(Yaya), Najibu, Aisha(Anti), Rabilu(Yayan Shago), Nazifi(Yaya Ƙarami), Adamu, Lubabatu, Basira, sai auta Fati.
Asiya(Ummaa) ita ce ta biyu yaranta bakwai; Basiru, Sadiya, Zubaida, Habiba, Musa, Jabiru sai Garzali.
Fauziyya(Amarya) ita ce ta uku yaranta biyar; Radiya, Musbahu, Naziru, Sumayya, Sharifa.
"Salamu Alaikum". sallamar da akayi daga tsakar gida taja hankalin su, Amarya ta ɗaga labule ta leƙa bayan ta amsa sallamar.
"Nazifi". ta kira yi sunan nasa idonta a kansa.
"Na'am, ya naji ku a ɗaki kuma".
"ummm yau bamu zauna a tsakar gidan ba saboda sauro".
"kuma kinga na sha'afa ban taho da magani ba". yay maganar a sa'ilin da yake ɗiban ruwa a buta yana kaɓe sumar kansa da ƙasan wandonsa.
Ta sake cewa,"Ka kira wani a cikin su ya taho da shi, a haɗo da battery wannan yayi sanyi neman mutuwa ma yake gaba ɗaya".
"Ai na ma siyo sabuwar tocilayit ɗazu ta caji, na barta ne a gidan su Muntari anjima zan karɓo".
"Ciniki aka yi ne naji fa ana ta cajin da tsada".
"Wallahi yau kasuwar rake kam Alhamdulillah anyi ciniki dan duka wanda na fita da shi sai da ya ƙare, shine ina tahowa naga fitar na siya dubu ɗaya amma ƴar ƙarama ce".
"To masha'Allah, Allah ƙaro kasuwa me albarka, an gode".
Ya amsa da amin sannan ya bankaɗa labulen ɗakin ya shiga, ya nemi gefe ɗaya ya zauna yana gaishe da mahaifinsa tare da Gwaggoje da Ummaa, sannan yabi mahaifiyarsa da ido itama yana yi mata sannu da jiki, duk sai sanya masa albarka suke yi shi kuma yana amsawa cike da jin daɗi da farin cikin alfaharin da ahalinsa suke da shi. Kamar ba shine na ɗazu da yake tura baron rake cikin wasu jemammun kaya ba, yanzu yayi wanka ya sauya kaya zuwa blue jeans and white shirt me dogon hannu, ba sabbi ba ne kuma ba masu tsada ba ne amma yay masifar kyau sai zuba ƙamshi yake yi, lallai duk ranar da kuɗi suka zauna a jikinsa ba ƙaramin shege za'ai ba wajen kyau da iya ɗaukar wanka.
"Yaya Ƙarami zance kaje ne?". Zubaida tayi tambayar da tsokana. ya ɗago yay mata wani kallo ba tare da ya ce mata komai ba, fuskar nan tasa da bata rabo da murmushi na ta ƙyalli. Basira ta amshe da cewa,"ehh fa Yaya Ƙarami ka daɗe baka yi kyau ba irin na yau, ko dai ko dai".
Maficin da ke kusa da shi ya ɗauka ya jefa musu yana faɗin su kiyaye shi. kallon da mahaifinsa ke yi masa yasa shi miƙewa cike da kunya yana cewa da Amarya,"Abincina fa?".
"Ka duba kicin yana nan a wannan koriyar robar, ka ɗiba naka ka barwa sauran".
Bai fita a ɗakin ba ya zaro ɗari biyar a aljihunsa ya miƙawa Malam, mahaifin nasa bai karɓa ba ya girgiza masa kai alamar A'a, har ranso bai so ba, sam baya jin daɗin su bawa mahaifin su kuɗi yaƙi karɓa haka su ke fama ko da yaushe, ya ce shi ɗauke masa nauyin ci da gidan ma da suka yi kaɗai ya ishe shi, ban da ƙananun hidindimu da duk su ne suke yi. Manya samarin dama su huɗu ne, dukkansu bige bige suke yi babu me ƙwaƙwarar sana'a, amma a hakan su ke ƙoƙarin ganin su ciyar da gidansu da ɗaukewa mahaifinsu duk ɗawainiyar da ke kansa, kullum cikin ce masa suke ya huta ya daina fita Allah ya basa su za su masa amma yaƙi. shi yasa adu'ar Nazifi ta kullum Allah ya buɗa masa Malam ya huta yaji daɗi, sai dai a yanda ya ke ganin rayuwarsu abin da kamar wuya, duk da komai yin Allah ne, bai san abin da Allah ya aje musu ba anan gaba.
Ummaa ya miƙawa kuɗin ta karɓa tana faɗin Allah yay albarka. Ya fita a ɗakin ya shiga kicin ya buɗe koriyar roba babba wadda akayi kwaɗon kwaki ya ɗibi nasa sannan ya fice zuwa waje don su ci shi da abokinsa.
Yanayin yacca garin yake a lullume, sanyi na kaɗawa ta ko'ina yayinda iska ke busawa sosai, sai ya zamana yanayin ya zamto gwanin ban sha'awa a wurin duk wani rai mai motsi. cikin ƙanƙanin lokaci hadari ya haɗu yay gangami a gabas, garin yay baƙiƙƙirin sosai, sai walƙiya da ke haskawa, alamu na nuna daga kowanne irin lokaci ruwan sama zai iya sakkowa. dalilin hakan yasa kowacce halitta da ke waje ta shiga neman mafaka, yara na shigewa gidajensu da gudu, ƴan tebura na kasuwa na rurrufe kayansu wasu kuma na sakar musu lema, matafiya kan hanya kuwa duk hankali yayi gida saboda idan ruwan ya sauka Allah kaɗai yasan lokacin tsayawarsa, a wannan lokacin kuwa fargaba ta cika zuciyoyin talakawa bayin Allah, dalilin irin yanda suke jiyo gangamin hadari na ƙara haɗuwa yana buga tsawa wacca suke jin tamkar zata rusa ginin gidan na su ya zube, domin a irin ƙarfin iskar ruwa kanyi gyara sosai a gidajen ƙasa, zaka samu da yawa gidaje sun rufta har yay sanadin rayukan mutane da dama.
Yayyafin da aka fara, da kuma tashin iska da ke yin kaman zata ɗauke abubuwa, shi ya bawa masu mota damar ƙara gudun motocinsu, da yawa na zuge gilasan motar, waɗanda ke da matsalar ido kuma na neman wuri suyi fakin kasantuwar basa iya gani da kyau a cikin duhun hadarin. a daidai wannan lokacin ne wata arniyar mota ƴar ubanta baƙa ƙirar Lexus RZ da ke tafiya akan titin dawowa daga filin jirgin Aminu Kano, matuƙin cikinta ya gangara motar zuwa gefe ya faka, motar sabuwa ce karr ko ledar jikinta ba'a gama ɓarewa ba, sai uban ƙyalli take me ɗaukar hankali, ƙamshin da ke tashi a cikinta kana jiyo shi har waje, sai sautin waƙar Ve Maahi by Arjjit Singh ita ma da ke tashi cikin natsuwa. saurayin da ke tuƙin motar me kimanin shekaru ashirin da uku ya waiga kansa ga kujerar kusa da shi yana sauke idonsa kan Yayansa, wanda ya kai dogon hannunsa mai ɗauke da zarazaran yatsu ya ƙaro bolum na waƙar, idanunsa a lumshe ya kwantar da kansa a jikin kujera, wucewar minti ɗaya, biyu, uku, huɗu sannan ya buɗe su, a lokacin ƙwayar idonsa ta sauka akan yayyafin da ya ɗisa ɗis ɗis akan gilashin motar, cikin hukuncin ubangiji duk wannan hadarin da aka haɗa da tsawar da aka dinƙa bugawa ana zaton ruwa zai sauka tamkar da baƙin ƙwarya, sai ga shi cikin mintunan da ba su haura biyar ba anyi yayyafi an ɗauke, sararin samaniya har ya fara washewa, al'amarin ubangiji yafi gaban mamaki.
Dogon numfashi yaja ya sauke tare da ware idanuwansa akan titi yana bin tarin motoci da ke wucewa da kallo, kafin daga bisani ya ɗauke ƙwayar idonsa akai ya ɗauko wayarsa, wayar da kana gani ka san ba ƙaramin kuɗi aka zuba wajen siyanta ba, kuɗin da idan suka je hannun talaka tsab zai mallaki muhalli daidai zama da iyali. zamansa ya gyara a mazauninsa kuma daidai da gama laluben lambar da yake nema zai kira, ya danna kira ya tafi, kiran da ba'a ɗaga a farko ba sai ana biyu shi ma sai da ya kusa tsinkewa tukunna.
Daga can ɓangaren da aka ɗaga wayar murya mace mai zaƙi ta fito da faɗin,"Hello Bhai".
Ta san hali, ta san waye shi, ta san jini, shi ba ɗan sarki ba kuma ba jinin sarauta ba, amma yanda yake ji da girman izza da ƙasaita da uban miskilanci ko sarki da kansa albarka. a yanzu dai shi ya kirata, amma idan zata yi magana sama da sau dubu hamsin ba zai amsa ba tun da har ta san musababbin kiran nasa, in ace ma bata sani ba ne to zai iya ƙarfin hali ya ɗauki minti goma kafin ya faɗa mata abin da yasa ya kirata ɗin. Don haka daga can in da take tayi guntun tsaki a hankali gudun kar ya jiyota ta jazawa kanta masifa da bala'in duniya. kuma ita ma sai da ta ɗan ja lokaci sannan tace da shi,"Nan da ƙarfe bakwai suka ce".
Tun da ta faɗi hakan kuma tayi shiru, ta san dai abin da ya kira yaji kenan, ta kuma faɗa masa yaji, amma yanzu idan tayi gangancin kashe masa waya alhalin ba shi ya bata izini ba, to duk duniya babu wanda ba zai ji su ba a yau, gobe da jibi, shi ɗin kuma ba kashewar zai yi ba haka zai bar kuɗi suyi ta tafiya a iska sai lokacin da yaga dama. Sai dai a jiya tayi matuƙar mamakinsa lokacin da aka sanar da shi hatsarin da mahaifiyarsu tayi. Tana tuna lokacin tsaye take a bakin ward, duk jikinta kyarma yake yi, hannunta da ke riƙe da waya a kunne karkarwa kawai ya ke yana neman jefar da wayar a ƙasa, da ƙyar ta tattaro courage ta maƙale a jikin
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 21 Chapter of 23