tara da rabi na safe dalilin bacci da wuri da ban samu nayi ba, sai dai Alhamdulillahi isassan baccin da na samu yau ɗin da ya kaini har wannan lokacin sai ya zamana ban tashi da ciwon kai da zazzaɓi kamar yanda na saba tashi da su ba a ƴan kwanakin nan. Sai da na gyara ɗakinsa tukunna na fita na wuce ɗakina, kafin na haura saman kuma sai da na tsaya na buɗe ƙofa saboda zuwan mai yi min wanke wanke da share share.
Ko da nayi wanka na ke shiryawa zuciyata cike take fal da matuƙar mamaki gami da saƙe-saƙe daban daban akan al'ammarin nan mai girman gaske, yo mai girman gaske mana tunda miji bai kwana a gida ba bayan ba tafiya yayi ba, kuma abin da bai taɓa faruwa ba tsawon shekaru. Har yanzu ƙarfe goma sha ɗaya da na ke muku wannan maganar banga alamun Hubbi ya dawo gidan ba, na leƙa farfajiyar gidan babu motar da ya fita da ita. Nauyayyan numfashi na sauke, tarin tambayoyin da ke kaina a game da inda ya kwana da rashin dawowarsa da abin da ya tsaresa suna da yawan da har suke neman fasa min kai.
Wayata da ke ajiye kan madubi na ɗauka zan kira wayarsa, ina buɗeta kuwa na fara cin karo da saƙonsa na jiya da yake faɗa min ba ya son damu. Da sauri kuwa na dire wayar ina kulle idona kafin na buɗe bayan wucewar daƙiƙa ɗaya. zuciyata cike da ƙunci na fita a ɗaki na sauka ƙasa, a falo na tarar da mai aiki tana goge gogen gilasai, wanda tuni ta gama shara, ko'ina ya ɗau ƙamshi, dama ni ɗin gwanar ƙamshi baka taɓa zuwa ka riski gidana ba ya tashin ƙamashi tun daga harabar waje.
Muka gaisa da ita na wuce kitchen, ruwan shayi na dafa na soya ƙwai, na zubo nawa na barwa mai aiki nata, falon na dawo na zauna na kunna tv, ina shan shayin ina kallo hankali da tunanina kuma na can wani wajen.
Motsin buɗe ƙofa yasa na juya kaina wurin, Hubbi na gani ya shigo yanayinsa kamar tashin bom, ko inda na ke zaune bai kalla ba yay wucewarsa sama fuuuu kai kace tashin iska, ni kuwa nabi bayansa da kallo zuciyata na zullo, kamar in share shi amma sai naji ba zan iya ba, lokaci ɗaya naji abin da nake ci ya fita akaina, hakan yasa na dire na miƙe nabi bayansa da sassarfa. Ina shiga ɗakin na tarar har ya shiga banɗaki, nayi tsaye bakin wadrobe kamar munafuka ƙirjina sai bugawa yake saboda bala'in tsoron da ban san ta ina ya zo ba, wucewar wasu mintuna na dawo hayyacina na buɗe wadrobe ɗin na kwaso masa kayan da zai saka na zaman gida, na ajiye anan gefen gado, duk wani abu da na san zai buƙata na ɗauko na ajiye masa.
Mutumin da ba ya jimawa a banɗaki shi ne yau sai da na fara fidda tsammanin zai fito tukunna sai ga shi ya fito, ƙugunsa ɗaure da towel sai wani ƙarami kuma a hannunsa yana goge ruwan kansa da jikinsa. Ta gabana ya wuce ya isa wajen mudubi, yaja stool ya zauna ya shiga shafa mai, ni dai kallonsa kawai nake yi, wallahi kamar sabon mutum ba mijina ba, maganar da na ke ta so nayi ta gagara fitowa, na rasa tantance abin da nake ji a ƙirjina, tsoro ne ko kuwa shakka. haka ya gama shafa mai da oil perfumes na oud ya taso, yana niyyar buɗe wadrobe idonsa ya kai kan kayan da na ajiye, idonsa ya ɗauke akansu ya ɗago yana kallona, kamar me shirin faɗar wani abun amma sai bai ce komai ba. Kayan ya ɗauka ya saka, jallabiya ce milk ƙirar dubai.
Gado ya haye ya jingina bayansa da filo, sai a sannan na sami zarafin yin magana nace,"Hubbi wai lafiya?".
Shiru bai amsa min ba kamar ma ba da shi nayi maganar ba. Na danne abin da na ke ji a zuciyata cikin raunin murya na ƙara cewa,"Hubbi wai me yake faruwa?, in da akwai wata matsalar ka faɗa min don Allah, jiya fa baka kwana a gidan nan ba, kuma yanzu ka dawo ka ƙi ce min komai, gaba ɗaya fa ka sani cikin damuwa da tashin hankali, idan laifi na maka bisa rashin sani ka faɗa min na gyara in kuma nemi afuwarka, kai ɗin fa shugabana ne".
Nan ma banza yay min tamkar da dutse na ke magana. Na hasala, duk yanda naso in taushi kaina abin ya faskara, kun san an ce mai haƙuri bai iya fushi ba, muryata a sama nace,"magana fa na ke yi maka kana jina kayi min banza, nace aina ka kwana?".
Idanunsa ya ɗago ya waresu tas akaina, kallona yake da irin mamakin ɗaga masa muryar da nayi a karon farko tun aurenmu da shi, da kausashshiyar muryarsa mai kaifi yace,"ni kike ɗagawa murya?".
"Ya ba zan ɗaga maka murya ba alhalin kayi abin da yake ba daidai ba, kuma baka gyara kuskuren hakan ba kake ci gaba da yi, me ka mayar da ni da zan ke magana kana bawa banza ajiyata".
Idonsa kamar zai faɗo wajen kallona ya ƙara cewa,"ok in dawo gida ba ki iya min sannu da zuwa ba, ba ki tambayi matsalar da ta sameni ba, sai tsare ni da banzan tambaya, to matsayinki na wa kike tuhumata?".
Yanayin yanda yay maganar cikin ɗagawar murya ya kamata inji tsoro, to amma ko kaɗan sai banji hakan a raina ba, bayan ba ƙara ɓata min rai da yay, kuma tambayar da yay tasa na buɗe kallona da kyau akansa nace,"ohhh ka manta nauyin da ya rataya a wuyanka kenan, to matsayina na matarka ta sunnah, wadda ka auro ni saboda kana so ba saboda an cusa maka ba...yau ko ba aurena kake yi ba tun da har da kanka ka kawoni cikin gidan nan ka je ai ina da hakki kuma ina da hurumin tuhumarka inda kaje ka kwana da abin da ya hanaka dawowa gida".
Ina faɗar hakan na juya zan bar ɗakin saboda marayan kukan da ke neman ƙwace min, wanda ni kuma ko kusa bana so yaga rauni na tun da a yau nayi jarumta. Ina gab da fita ya kira sunana.
"Sa'ida". Yanayin yacca ya ambaci sunan kaɗai zai baka tabbacin gargaɗi yake so yayi haka kuma ransa a ɓace yake.
Na juyo nayi masa kallo ɗaya na watsar nace,"ina jinka". Tasowa yay daga kan gadon yazo gabana ya tsaya, ba don komai ba sai don ya nuna min ainihin tsayinsa, gabana ba ƙaramin faɗuwa yay ba da hakan musamman yanda nake jin tururin zuciyarsa a saman fuskata.
"Ki buɗe kunnuwa da kyau ki jini, daga rana mai irin ta jiya, ko ƙarfe nawa zan kai a waje, kar ki kuskura ki ƙara gigin rufe min ƙofa, idan kuma ba haka ba wallahi tallahi ranki sai yayi mummunan ɓaci, hukuncin da zan ɗauka akan hakan ba zai yi miki kyau ba. Gidana ne ba gidanki ba, ruwana in fita lokacin da na ke so in kuma dawo a lokacin da naga dama, ni ke aurenki ba ke kike aurena ba, saboda haka ina rabaki da tuhuma makamancin haka...don haka Sa'ida, Sa'ida kika ƙara rufe min ƙofa...".
Sai kuma ya ƙyasta yatsu yana jijjiga kai alamu na shi ya barwa kansa sanin abin da zai aikata. Ni kuwa hakan raina fes, ban damu da kalaman gargaɗinsa ba ko kaɗan, ashe ma cikin gidan ya kwana, kuma rufe ƙofan yay masa zafi, don haka na saki gajeran murmushi na jin daɗi na juya zan bar masa wajen aiko a zafafe ya fizgoni na dawo gabansa.
"Me kike nufi?".
Na ɗaga gira nace,"ina nufin sai in har ba ka ƙara kaiwa irin lokacin jiya a waje ba, amma sai na rufe ƙofofina, don ba zan bari in kwana a wangale ba saboda a cikin gida na ke ba'a kango ba".
Kallona ya tsaya yi kamar wani mutum mutumi, wani irin kallon mamaki yake bina da shi da har ya hanasa magana, sai da yaga dama ya sake min hannu yana sauke dogon numfashi tare da cewa,"ki kawo min kayan karin kumallo".
Kai tsaye nace,"rasawa kayi a in da ka kwana?".
Kallonsa da nayi kawai sai naji tausayinsa ya tsarga min, amma hakan na da ke na ƙara ɓata rai nace,"sai dai ka jira na rana".
Ficewa nayi da sauri na wuce ɗakina, a can na sha kuka na ƙoshi, ban ƙara fitowa ba sai da akayi sallar ƙarfe ɗaya tukunna na sauko. Ina shiga kitchen na sameshi gaban cooker gas yana ƙoƙarin ɗora tukunya. Yanda bai kalle ni ba haka nima ban kalle shi ba, na wuce na shiga hidindimuna, yana ta aikin girka ruwan shanyinsa nima ina aikin ɗora shinkafa da miya, har ya kammala ya fice bai min magana ba haka nima ban masa ba, dan ko da nazo ɗora tukunya ma na ɗan buge shi ban sani ba ruwan zafin ya zubar masa a hannu sannu ban ce masa ba, haka shima ɗin kallo kawai ya bini da shi.
Bayan na kammala girki na kwashi kwanukan abincinsa na kai ɗakinsa, lokacin yana zaune bisa darduma yana jan carbi, na ajiye na zauna ina faɗin,"ga abincinka".
Sai kuma na kalli hannunsa nace,"kayi haƙuri bana sane ruwan zafin ya zubar maka".
Ina jin yanda ya kalle ni, ban san tunanin me yayi ba sai kuma yaja jallabiyarsa ya lanƙwasa ƙafafu, na dire plate ɗin da na zuba masa shinkafa da miya a gabansa tare da zuba lemo a kofi shima na ajiye. Fuskata a haɗe kamar hadari, tun da ya ɗau cokalin yake ta kallona, ni kuma hannun nasa da ruwan zafin ya zuba kawai nake kallo, sai naga kamar shi ya hana shi cin abincin, a hankali nace da shi,"ba zaka iya cin abinci da hannun ba ne?".
Ya haɗiye yawun da ke maƙoshinsa yace,"abinci babu nama ba kifi?".
Nace,"ka ci abin da ya samu mana".
"Ban gane me kike nufi ba".
Na miƙe ina kwashe kayan da ya cire nace,"babu ɗaya daga cikin abin da ka tambaya a gidan".
"Kuma shi ne ba za ki iya shaida min sun ƙare ɗin ba, ban hana abu ya ɗauko ƙarewa ba aƙi sanar min".
Baki na taɓe nace,"ban ganka a gidan ba ne".
Bai ce da ni komai ba naji ya ɗauki waya, Labaran ya kira wanda yake bawa yayo cefanen gida, ya karanta masa abubuwan da zai siyo, ina jinsa yana tambayana bayan nama da kifi sai mene babu, ni kuwa na bawa iska ajiyarsa, sai da ya ɗaga murya sannan nace,"ina jin su kaɗai ne babu, sai maltina wadda ta rage iya shan yau ce".
Wankinsa da ke cikin kwando na tattara na ɗaure na ajiye a gefe, na ce masa,"ga wannan wankin".
Ta gefen ido ya kalle su yace,"Shehun bai zo ya ɗauka jiya ba?".
Nace,"ban sani ba ko ya zo ɗin".
A ƙufule yace da ni,"saboda kin je ina?".
"Saboda ina ɗakina".
Na faɗi hakan ina tsugunawa zan ɗauke plate ɗin abincin gabansa da ya gagara taɓawa har yanzu, ya barsa sai shan iska yake daga ba ya yace ba zai ci mai sanyi ba, dakatar da ni yay da cewa,"me kika taka ne wai?".
Shiru nayi ban ce masa komai ba. Ya ƙara cewa,"ba magana na ke miki ba".
Kamar ba zan tanka ba sai nace,"me kuwa na taka Hubbi wanda ya wuci abin da ka taka".
Yanayinsa naga ya sauya haka kuma muryarsa tayi sanyi wajen cewa,"asibiti na tsaya jiya, na bige wani yaro, amma da sauƙi".
Gabana naji ya faɗi, har zan yi ƙorafi kan cewa shi ne ya gagara ya sanar da ni, sai kuma kawai na bagarar nace,"Allah ya ƙara sauƙi".
Yace,"amin, ya zubar da jini da yawa yau zanje a ɗibi nawa a saka masa".
Kallonsa nayi ta ƙasan ido nace,"Allah ya taimaka".
Ina faɗar hakan na bar masa ɗakinsa na fita. Samu nayi ana ƙwanƙwasa ƙofan falo, na ƙarasa na buɗe, ganin wadda ke tsaye a gabana nace,"Hassana Tijjani".
Na faɗi sunan nata da muryar bayyana murna da jin daɗin ganinta. hanya na bata ta ƙaraso ciki tana ta nishi alamun ta gaji da yawa, jakar hannunta ta wancakalar kan kujera tare da kwance goyon bayanta, sannan tace da ni,"me gidan yana nan?"
Nace,"Yana ciki". sai ta fasa cire mayafinta tana sake cewa,"ke ƙaro gudun Acn nan, jina nake kamar a garwashi".
Na wuce wajen makunnin AC na ƙaro ina cewa da ita,"daga ina kike haka ne?, Naga sai zufa kike haɗawa...bari na kawo miki ruwa".
Kitchen na wuce ina jiyota tana faɗin,"ke dai bari tafiyayya nayi tun daga Shanono, naje gidan wan Mamarmu gaisuwar ɗansa, muna shigowa kano kuma muka wuce gidan ƙanwata Saratu anyi mata tiyata an ciro yaro babu rai, nace dai to yau tun da Allah yasa nayi kusa da unguwar su Sa'ida in sha Allahu sai na zo mun gaisa".
Ina ta murmushi na ajiye babban farantin hannuna da na sako ruwan sanyi da lemun ɓawo da ayaba,"sannu da hanya, to ya aka yi kika gane gidan?".
Tana goge zufa tace,"na kira wayanki ban samu ba sai kawai na kira Ummani ta min kwatance".
Nace,"kar ki ce min sai da kika je gidanmu".
"Wallahi sai da naje, ai ba zan iya zuwa kano dai in yawace yawace ban je na gaida Ummani ba, tace ma in gaida ke".
Na kuwa ji daɗi matuka da cewarta, fuskata ta washe da annuri ina cewa,"Maimuna ina godiya da yanda kike girmama mahaifiyata, Allah ya bar zumunci". Ta amsa da amin, ni kuma na ƙara cewa,"ya ƙarin haƙuri?".
"haƙuri mun gode Allah, kwanakin nan anata rasuwa wallahi, rasuwar ma ta matasa".
Nima cikin jajantawa nace,"wallahi kuwa sai fatan Allah yasa muyi kyakykyawan ƙarshe. Dama Saratu lokacin haihuwarta yayi?".
"Ina fa bakwaini ne, to ɗan ma sai yazo babu rai".
Nace,"Allah sarki Allah ya bada rayayya".
Naje na ɗauki yaronta da ke bacci na kwantar da shi kan wata ƙaramar katifa da na ɗauko gudun kar yay fitsari akan kujerar. Ni dai har raina naji daɗin ganinta, rabona da ita tun kafin mu dawo gidan nan, ƴar ajinmu ce tare muka yi sakandire, tana cikin abokan arziƙin da aka yi zaman mutunci da su, ƴan gidanmu kaf babu wanda bai san Hassana Tijjani ba, kafin muyi aure yawan lokuta ta kan zo gidanmu, bini bini ta kira Ummani su gaisa, saboda tana sonta sosai, ko ina ta shiga ta yabi mahaifiyata taita bada labarin mutuncinta. duk da ni ina ɗan shashshareta saboda ban cika son ƙawaye ba, amma hakan bai sa ta ja baya da ni ba, ko da bikina tun daga Zariya ta zo sai da ta kwana uku, haka da su ka dawo zama kano ta jajje gidana ba zai ƙirgu ba, amma ni kuwa tsabar kirkina zuwana gidanta bai fi sau uku ba.
"Sa'ida ban fa yi sallah ba. In fara yi kafin mu zauna wannan hirar tamu ta yaushe gamo". Ta ce bayan ta ajiye jarkar ruwan da tun da ta kafa kai bata sauke ba sai da ta kusa shanyewa.
Na kalleta murmushin fuskata bai ɗauke ba na ce,"to ko sama zamu hau, kyama yi wanka kiji daɗin jikinki".
Tana dariya tace,"wanka Sa'ida kamar wacca ta zo kwana, raba ni, na dai yi sallar kawai. Sallar ce in baka yita ba babu natsuwa kwata kwata".
Tashi nayi na ɗauki yaron nata da na ke ta jin kunyar in tambayeta sunansa, lokacin da ta haihu har hotonsa ta turo min da sunansa, haihuwanta biyu duk babu wacca naje mata barka, amma hakan baisa ko kaɗan Hassana ta nuna min rashin jin daɗinta ba ko ƙorafi, ita ce ma mai yawan nemana a waya taji ya nake.
Ina nufar sama ta ce da ni,"Sa'ida ku fa gidan nan na ku na ƴan gayu ba a rasa ku da banɗakuna a ƙasa, saboda haka ki taimaka ki rabani da hawa dogon benen da idanuwana ke gani, ba za ki gane yanda ƙafafuna su ke a gajiye ba".
Gajeriyar dariya nayi na maida yaron na kwantar, bedroom ɗina na ƙasa na rakata, sai da na takurata akan tayi wanka. Na fito na barta a ciki na wuce kitchen na haɗo mata kayan abinci, lokacin yaronta ya tashi na ɗauke shi ina ta masa wasa, yaron tubarkallah ɗan kuɓulɓul da shi ga shi tsab tsab, babu ko irin ƙarnin tumbuɗi a jikinsa sai ƙamshi yake yi, daɗina da Hassana kenan tsabta gaba ta bata ba baya ba.
Dawowarta tana murmushin jin daɗin da ya kasa ɓoyuwa a fuskarta take cewa,"au Jamil tashi ya yi?".
Aiko nan naji daɗin faɗar sunan da tayi, ina murmushin nima nace,"ai yanzu na ke cewa Jamil har haka yayi wayo sai dariya yake yi abinsa, ga shi babu ruwansa da rigima".
Haka ta zauna ta shiga cin abinci, tana ci muna ta hira abinmu, sai zuba santin gidana take yi, faɗi take wannan ai shi ake kira da aljannar duniya, dama gata ƴar barkwanci duk in da na zagaya da ita sai tace wannan kuma ni Hassy menene shi, haka fitilun falo ma wai ai ita ba zata iya kwana ba gani zata yi kamar zasu faɗo kanta taga haka ake yi a film ɗin indiya...cikin hirarmu take bani labarin mutuwar mijin Firdausi itama ƴar group ɗinmu ce a makaranta, na ke ce mata wallahi ban sani ba amma zan samu in shiga a satin nan in mata ta'aziyya. Hirar tamu kuma ta juya kan kasuwancin da uwar bari tasa mata su ka durfafa, har take neman shawarata akan sana'ar da take so ta fara na kiwon kifi, ai kuwa nan na ƙarfafa mata gwiwa akan tayi ɗin na kuma daɗa nuna mata muhimmancin sana'a a wajen mace. Taji daɗin shawarwarina sosai, mu ne har la'asar anata zuba ana shewa, sai lokacin ne tayi ɗan jim ta kalle ni tace,"don Allah kiyi haƙuri da tambayar da zan yi miki".
Nace mata,"tambayan me Hassana?".
Ta numfasa tace,"kiyi haƙuri ba sa ido ba ne, damuwa da ke ne wallahi, ke dai kin san yanda Allah ya jarabce ni da sonki, domin ni ba matsayin ƙawa kike garen ba, ganinki na ke tamkar Hussaina da na saki Nono ta kama".
Na murmusa kuncina na ce,"na sani Hassana kar ki damu faɗi abin da yake cikinki".
"Me yake damunki naga kinyi uwar rama haka?".
"Wai da gaske ramewa nayi?, Sai aita na rame ni kuwa banga ramar da nayi ba, Hubbi ma ce yay nayi ƙiba".
Galla min harara tayi tana faɗin,"ban sani ba ƴar rainin hankali, ga fa ƙashin da ke wuyanki Sa'ida abin da babu a da".
Dariyar da ta bayyanar da haƙorana na yi nace mata,"kar ki damu ba wata damuwa ba ce, jinya na sha kwana biyun nan, watana biyu a kwance".
Aikuwa ranta ya ɓaci ta nuna min rashin jin daɗin hakan. ta fara mita akan me yasa ban taɓa faɗa mata ba, ta ya za'ai ace har na sha jinya irin haka bata sani ba, ko bata zo duba ni ba adu'a da sannu ai suna da daɗi. Ni dai haka nayi ta bata haƙuri, ta gama mitar sai kuma can ta doka tsalle ta rungumoni tana murmushi cikin fara'a tace,"kinga ki bani wanga albishir kawai kar ki ja min rai".
Nayi lakato ina kallonta domin na san in da zancen nata ya dosa, ta zame a jikina tana daɗa cewa,"wata nawa?".
Na waro ido na ce,"keee mene wata nawa?".
Tayi min wani kallo na kar ki raina min hankali. Na ce,"Allah kuwa, idan shi ne ai tun a waya zan sanar miki, wallahi bani da komai Hassana har yanzu shiru, sai dai a ci gaba da samu cikin adu'a".
Jikinta a sanyaye tace,"to Allah yasa jinkirin Alkhairi ne. Amma dai ai ba kya fuskantar wata matsala ko, kin san sha'ani na dangin miji".
Murmushi nayi na ce,"ko ɗaya fa, ai kin fi kowa sanin surukai na. Ita Iyam ma da kanta take nema mana magani".
Tace,"Allah sarki. To Allah yasa a dace, ke kam Sa'ida ai kinyi dacen suruka wallahi, ga dangi miji kamar kece ƴar tasu".
Ni dai murmushi kawai nayi na kuma san yanda nayi na katse maganar haka. ta miƙe tana faɗin,"bari nayo fitsari in zo in ɗauki hanya yanzu za kiga magriba tayi".
Tashinta ba daɗewa naji Maganar Hubbi akaina yana cewa,"ina jiranki".
Bayansa na bi da kallo wanda tuni ya wuce yay komawarsa ɗaki, nayi godiya ga Allah da yasa Hassana bata nan, da haka zai fallasa lamarin da na ke ɓoyewa. Kaina na girgiza cike da takaici da baƙin ciki na tashi, na ɗauki Jamil na tafi da shi. A ɗakin na same shi yana kaiwa da komowa, na tsaya daga gefe na ce,"gani".
Tsaye yayi yana ƙarewa Jamil kallo, ban sani ba burge shi yaron yay kome masa ne oho, yana dai ta kallonsa kamar ma zai miƙo hannu ya karɓe shi. shirunsa yay min yawa na ɗago kaina na kalle shi naga bai ɗauke ido daga kallon Jamil ɗin ba, muryata a hankali na ce masa,"ɗan gidan Hassana ne".
Sai sannan ya ɗauke idonsa akan yaron yana cewa,"wace hakan?".
Na kalle shi nayi guntun murmushi na ce,"Hassana Tijjani dai ƴar ajinmu".
"Ohhh, haihuwa ta ƙara yi?".
"Ehhh shi ne wanda aka haifa ranar da zaka tafi Hajji ban samu zuwa barka ba".
Ya sake cewa,"ohh Allah ya raya". Na amsa da,"amin". jimm na ƴan sakanni kuma sai ya sake cewa,"ashe Yaya ta zo jiya".
Furucin nasa yasa gabana ya faɗi ras, duk sai na nemi na daburce da yay maganar wacca ta fama ciwon jiya na cin mutunci da Yaya ta yi min. Idona na rumtse gam nace,"ehh na manta ne ma ban faɗa maka ba".
Cikin fusata ya ce,"wai ke mene matsalarki ne, iskanci ko kuma rashin mutunci?, Yayan ta zo jiya, jiyan ma da daddare amma saboda rainin wayo za ki buɗi baki kice kin manta da zuwanta. dama har haka kika fara raina min ƴan uwa?, Ashe maganar da na ke ji na cewan kina wulaƙanta su gaskiya ne ba ƙarya ba, to bari kiji na faɗa miki, zan iya ɗaukan komai amma ban da cin zarafin ƴan uwana, ba zan ɗauki hakan ba Sa'ida ke kin san waye ni, akan ƴan uwana ina iya rabuwa da kowa ko da ace ɗan cikina ne...".
Furucinsa na ƙarshe yasa na kalle shi babu shiri, ɓoye raunina nayi na tari numfashinsa ina basa haƙuri, saboda yacca yake ɗaga murya tsab Hassana da ke falo zata iya juyo komai.
Daka min tsawa yay wacca har ta firgita Jamil, nan kuwa ya tsanyare da kuka, na furta na shiga uku ina jijjiga yaron a kafaɗata, na kalli Hubbi da idanuwansa ke a warwaje nace,"don Allah kayi haƙuri".
Ya watsa min banzan kallo da ya saka yanayina sanyi, na sadda kai ƙasa ina mayar da ruwan hawayen da ke shirin sakkowa. A hankali nace da shi,"don Allah kayi haƙuri kayi ƙasa da muryarka kaga bamu kaɗai ba ne a gidan...".
Ni dai ban iya ƙarasa maganar ba kuka ya ƙwace min, ƙafafuna na rawa na nemi kujera na zauna don sam bana so in fita a haka Hassana ta fuskanci matsalar da ke tsakanina da mijina. Ganin na zauna takaici ya kama shi ya kuma doka min tsawa da cewa,"dukanki nayi ko zaginki nayi da za ki sakar min kuka?". Sai kuma yaja tsaki yace,"ki wuce kije ki sallameta ta bar min gida, minti biyar na ba ki ki shirya zamu fita".
Saboda yanayin yanda na ga ya rikiɗe nayi saurin miƙewa jiki na ɓari, Allah yasa ta cikin ɗakinsa akwai ƙofar da zata sadaka da saman bene, don haka nabi ta nan gudun kar in fito in haɗu da Hassana. Har na shiga ɗakina Jamil na ta kuka ina aikin jijjiga shi, wanka na yiwa yaron na saka masa wasu sabbin kaya da na siya nacl ce zan kaiwa Maman Amatu kayan barka. ai kuwa kamar jiran wankan yake ina gama shirya shi yay bacci, nima shiga nayi na ɗaurayo jikina na zo na ƙara shiryawa cikin dogowar riga coffee colour, na ɗauko hijab ɗina yadi uku da rabi na saka sannan na ɗauki liƙab na zura a jakata.
Ko da na sakko na sami Hassana tana jirana, galala tana kallona ta ce,"wai bacci yaron nan yayi?".
Ina murmushi na ce,"bawan Allah shima ya gaji, kuka ya saka ina masa wanka kuma sai bacci".
Ta karɓe shi fuskarta sai ƙara fidda annuri take yi tana ta godiya da yaba kayan da na saka masa. Tana ce mun za ta tafi nayi shahadar ce mata,"a'a ai ki tsaya kawai mu fita tare sai mu rage miki hanya, kema ai sauƙin ki ne".
Bata ƙi
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 3 Chapter of 23