abota Frist?" Ta sake miƙa masa hannun a karo na uku. Gefenta ya bi ya shige yana rufe ƙofar gidan ya bar ta tsaye da hannu a ƙaƙe takaici ya ishe ta shi wannan yana ɗan ta'adda yana jin kansa kamar ɗan gidan ƙaruna saboda faɗin rai ga miskilancin masifa the manager ita Safiyyerh take magana ake sharewa bai san cewa akan dole take yin maganar ba? Ta lumshe idanunta hawaye na cika cikinsu da ƙyar ta yi alwala ta fara jero salloli. Goje ne ya shigo da sauri ya ce
"Ke kina ina fito maza taso" ta miƙe za ta yi masa gaddama kawar Moh ya shigo ya damƙi hannunta ta kalli baƙin hannunsa da ɗan mitsitsin nata farin hannun ya jata sukai waje mota ta gani bai tsaya jiran komai ba ya dannata a gaba Goje ya shiga baya Mangal dake tsaye ya ce
"Waye zai ja motar yanzu? Ni ban iya ba kuma haka?"
Moh dake shirin shiga mazaunin driver ko me ya tuna ya kalli Safiyyerh a karo na farko ta ji muryarsa a sake ya ce "Dawo nan" tsoran shi take ji ta fito ta koma wajan driver ya dawo ita ta tashi, ya cilla mata key ɗin motar "Muje" bisimillah ta yi ta fara driving ta juya ta kalle shi ta ce "Ina?" Ya bata wayar hannunsa wacce yanzu ya shigo da ita ta duba location da ya fara driving cikin sauri har suka bar wajan.
Mintuna kaɗan da barin su motoci suka tsaya a ƙofar gidan Captain ya fito jikinsa danye da uniform na sojoji da suka amshe shi sosai ga ƙatuwar bindiga sauran yaransa suka fito a hankali ya dinga bin wajan da kallo har ya shiga cikin gidan abin da ya fara cin karo da shi ya sanya zuciyarsa bugawa ganin rigar baccin Fiyya yashe a ƙasa ya ɗuka ya ɗauki rigar idanunsa ya sauka akan wani busasshen jini ya dinga kallon gidan a nan ya kalli ƙwayoyi kala-kala da wuƙaƙe da gorori ya lumshe idanunsa "Where are you Wife? Ina suka kai mini mata?"
"Captain kuma ka tabbatar tracking ɗin nan ya nuna?" Ya jinjina kai don baya jin zai iya magana. "Sun gudu, amma ya akai sukai san an yi tracking location nasu har suka gudu da wuri haka?"
Captain ya girgiza kai irin bai sani ba "Ka kwantar da hankalinka matarka zata kuɓuta ko kana tunanin sun yi mata wani abu ne?" Captain ya nuna masa rigar baccin Safiyyerh da jinin dake wajan mutumin ya dafe kai ya ce
"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un, in sha Allah ba abin da muke zato bane muje" fita sukai Captain ya ji a ransa ba zai bar abin haka nan ba.
Mutallab wani gida ya kai su madaidaici mai kyau da tsari da yake can bayan gari duk suna zaune Safiyyerh kanta na ƙasa tana mamakin yawan shiriun bawan Allan nan, idan ya yi shiru shi kaɗai sai ya saki ajjiyar zuciya ko ya ƙurawa waje guda ido.
***Wajan sati guda babu labari akan batun sace Safiyyerh ba kiran waya babu komai Daddy ya hana a faɗi maganar ko a social media ko a gidan rediyo ya ce a bar ta tsakaninsu. Yana ƙwace hannunsa maƙale da ruwa muryarsa a hankali ya ce "Aliyu waye ya saka?"
"She is my wife daddy"
"And? Ɗan sanda ne kai ko soja?"
"Zan iya amfani da uniform ɗina ko babu haka ai she is my responsibilities yanzu na kula da haƙƙina zan ji na zama lusari idan ban nemo Safii ba, kar ka dakatar dani daddy police su yi nasu aikin ni na yi nawa"
"Ka cire hannunka a ciki Aliyu"
"Ok zan jire akan wanne dalili?"
"Aliyu yanzu baka tunanin dalilin hakan su yi mata wani abu ne? Baka san su waye mutanen nan ba, duk abin da zaka ji a bayan nawa dana Zahiyerh yake kar ka yi kuskuren da za su salwantar da rayuwar Maama na roƙe ka, mutanen ba mutunci ne da su ba kamar komai hannun Sp Ghali" Aliyu ya miƙe ya nufi ƙofa "I am sorry daddy idan kaga na tsaya to na mutu ne, idan da numfashi a ƙirjina ba zan gusa ba sai na dawo da Safiyyerh cikin rayuwata i am sorry" yana cewa haka ya bar ɗakin.
Daddy ya rufe idanunsa daya cika da ƙwalla ya wani irin ramewa ko abinci baya ci Ummi ta ce "Ka san halin Aliyu da baka fito masa ta haka ba, gwara ka saka Ummimi yi masa magana" daddy yaƙi cewa komai. Wayarsa ta fara ƙara number ya gani sai ya yi sauri ya ɗaga yana kaiwa kunne aka ce.
"Barka, ina magana da Professor Abdu Marafa na sani ko baka amsa, zan fara da yi maka ya jiki don ina da yaƙinin kana nan zuciyarka na ciwo bari na ɗora maka da wata maganar ban sani ba ko zaka iya jure jin abin da zan faɗa. Yarinyar da kake ji da ita ni na saka a sato mini ita Safiyyerh kenan ina son ka lashe aman da ka yi da kanka. Professor ni ɗan siyasa ne lissafin ɗan siyasa daban yake dana Malami, bana barin kota kwana daman mun saba saka jama'a a uku, wallahi ka shiga komata yanzu nine da wasan ka fara lissafa ranakun mutuwar yarinyarka daga yanzu" da sauri Daddy ya ce
"Waye kai?"
"Sarai ka ɗauki ne muryarta professor, kana magana da Eng Ali wali mai neman takarar ɗan majalisa, ka hanani bacci yanzu lokaci ne da zaka ji abin da nake ji". "Ali wali me kake buƙata me Safiyyerh ta yi maka karka cutar mini da yarinyar don girman Allah kar ka taɓa ta"
"E, ba zan taɓa ta ba muddin ka yi abin da nake so"
"Me kake so?"
"Ka dawo jam'iyyata kuma tsagina ka lashe aman da ka yi ka kuma gyara ɓarnar da ka mini na rusa mini dukkan shirina, yadda ka ɓata sunana a wajan matasa da al'umma a gidan rediyo da kai da ɗan jaridar da yake mara maka baya ku sake sabon lale wajan wanke ni inma kana buƙatar kuɗi zan bayar hakan ba laifi bane ba"
"Uhm Ali wali kenan tun yanzu har ya yi sauri haka? Ni kake cewa idan ina buƙatar kuɗi kaga na yi maka kala da mabuƙaci? Kamar dai ka manta waye Professor kana buƙatar tuni na, laaa la la dama sauran lokaci ai. And da kake batun Safiyyerh tunaninka ita ce raunina ko?" Daddy ya tsige ruwan hannunsa da ake ƙara masa ya sakko daga saman gadonsa daman tuni ya nunawa Ummi ƙofar fita tun kafin ma ya ɗaga kiran.
"Ka yi kuskure sosai, Safiyyerh is nothing to me kuma she never be my headache idan ka so ka saka wuƙa ka yankata a yanzu is doesn't matter for me, idan akan Safiyyerh ka kira ka mini warning ka makara Ali wali tunda Safiyyerh ta bar gidan nan ko da dai da rana ban taɓa tunaninta ba siyasa ce kai kuma yaro ne mu zuba mu gani"
A ɓangaren Ali wali dariya shima ya yi ya ce "Lallai prof ka cika ɗan siyasa, to wallahi ka shirya ganin gawar Safiyyerh a wannan daren ku tara ƴan jana'izarta". "Idan ka haifo kuma kai cikakken ɗan iska ne idan har ba zina akai ka haifeka ba na roƙeƙa Ali wali don Allah ka kashe Safiyyerh nima fa wani aikin ka rage mini..," ƙit Ali wali ya kashe wayar daddy ya saki dariya yana wani irin murmushi wata number ya kira ana ɗagawa ya shige toilet yana saka key, ya jima ciki kafin ya fito ya zauna saman gado Dr Hash ya shigo da Yaya J ganin daddy zaune ya saka dr cewa "Daddy ya jikin naka?" Hawaye ya cika idanun daddy ya ce "ba abin da zai tafi daidai babu Safiyyerh zuciyata zafi take my innocent Fiyya, Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un ina tsoran halin da Ummimi zata shiga" ganin hawaye a idon mahaifin nasu ya saka Junaid ficewa dr ya zauna ya dinga lallaɓa daddy da bashi bakin za a ga Safiyyerh in sha Allah.
Aliyu yana zaune a ɗakinsa aka buɗe ƙofa tare da shigowa ya ɗaga kai ya kalleta ya miƙe da sauri duk da babu fara'a a fuskarsa amma sai da ya saki ajjiyar zuciya. Ta juya idanunta "Nan ka ɓoye?" Ya girgiza mata kai
"Ka cigaba da binciken inda Safiyyerh take Aliyu kar ka saurari mahaifinka ka ji ko?" "in sha Allah Ummimi" ta zuba masa ido sai ta juya ya ce "Tafiya za ki yi?"
"Me zan maka?"
"Love, ganin ki nake son yi" ta haɗe rai tana cewa "To ɗakko zani na goyaka" ya buɗe idanunsa ya yi wajanta yana rungume ta ya saki ajjiyar zuciya "I love you Ummimi, and I love Safii too"
Kan shi ta shafa ta ce "Kawai ka zaɓa ni ko ita" ya lumshe idanunsa ya yi mata shiru, rungume shi ta yi a jikinta ta yi shiru tunani daban daban a ranta sai kuma ta sake shi ta ce "Fito waje" saƙo Aliyu ya samu cikin gaggawa sunansa ya fito a jerin sojojin da za a yi posting nasu wajan aiki ya dinga kallon saƙon yaushe ma ya dawo da za a sake tura shi wani wajan bayan babu shi a sojojin da aka yi list? Sai kawai ya fita da nufin zuwa kiran da ya samu domin bata uzurin yana da wani muhimmin aiki akan nasa iyalin ya manta da batun a tsarin aikin sojoji babu sauyi idan har a zaɓe ka.
****Mafarki ta yi mai ban tsoro ta farka a gigice tana kiran sunan TAHHB sai haki take yi fitila taga an kunna an hasko ta ya zuba mata idanu a ransa yana ƙara mamakin wannan hasken nata gefensa zabtareriyar addace saboda tsaro ya miƙe a hankali ya kunna hasken parlon sai a lokacin Fiyya ta lura da Goje dake cikin kwance cikin jini haka Mangal ga wuƙaƙe a gefen su sai numfarfashi suke yi. Ya taka ya je gabanta ya tsaya can ya duƙa dab da ita baki ta buɗe za ta yi ihu ya saka yatsarsa a bakinsa "Shhhh" ta yi tsit ya cake addar
"Mene?"
"Ban kira ka ba wallahi" ya zuba mata idanunsa masu kaifi ta janye nata "sunan wa kika kira to?"
"Tahhb"
"Sunanki ne? Ko na Abdu Marafa?" Ta girgiza kai "Mafarki na yi a mafarkin na ji sunan, amma ban sani ba ni na manta komai na mafarkin ma kai na ciwo yake i have a headache"
Ya ɗaga addar ya cake ta tsakanin ƙafafuwanta sai sheƙi take yi ya ce "Ko dai ki faɗa mini waye Tahhb ɗin da kika dame ni da kiran sunansa yanzu ki na ɓula miki cinya"
"Don Allah ka yi haƙuri wallahi ban san shi ba"
"Ke wace?" Moh ya tambaya "Safiyyerh sunana" ya cije bakinsa sosai ya ce "Matar soja ko?" Ta jinjina masa kai
"To ni waye? Kuma ya nake a wajanki?"
"Wallahi ban san ka ba, kai ba kuwa bane a wajane" idanunsa har ruwa yake ya daka mata tsawa a gigice ya ce "Waye ni? Waye ni waye tell me....
❤🔥🔥💃1 page remain ba zan taɓa buɗe komai ba shafi 15 is nothing nothing ku biya you'll never regret sai mun yi nutsu za ku fahimci labarin MUTALLAB bai haɗa hanya da kowanne kalar labari ba, idan za ka yi kuka ka fara tun yanzu 😭😂ba kuma zan taɓa sauya labarina a yadda nake ba, you better shut up...
MUTALLAB.
Book 1, 2 &3
500 Naira
0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S a tura shaidar biya ta nan 08164069385
'Yan Nijar ku turo carte airtel ta 300fcfa saman wannan layin 84506476
[1/7, 9:33 PM] Sis Fauzy: *The story of a thug husband MUTALLAB, as a good parents za ku bada auren yarinyarki ga ɗan daba ɗan ta'adda? Ban ce ku fara kuka tun yanzu ba,ban ce ku ji soyayyar ciki kamar a ƙirjinku ake wanzar da ita ba.* *The story of TIGER and MOH The destiny of CAPTAIN and FIYYA. Finally the eternal love* *between..The love that separate them and back them together❤🔥😭*
*❤🔥 MUTALLAB ❤🔥*
Page 15 last free episode
*Bright pens.. 2nd batch*
For more updates follow Mutallab on Arewabooks in sha Allah ❤🔥🥰
Page 15 shine last free pages na labarin, kar ka yi tunanin ganin wani page ɗin a waje ka yi payment a yi naka into paid group akan 500 kacal, love ɗin da kuke showing yanzu ne zai yi aiki🫠MUTALLAB.
Book 1, 2 &3
500 Naira
0116886423 Union Bank Na'ima Sulaiman S a tura shaidar biya ta nan 08164069385 'Yan Nijar tsarin biyan zai kasance ta *Stock na airtel*. Ku yi wa wannan layin 84506476 magana sai ta ba ku lambar da za ku turo mata stock ɗin. Kafin ɗorawa da inda muka tsaya zamu ɗauki hutun zango na sati ɗaya tal😂 maybe har a yi albashi ko masu mining ta fashe musu.
Godiya ga Hajja Aisha Abubakar Khadhfsum data biyawa mutane 8 🥰 ga masu business zaku iya badawa a tallata muku idan kun ɗauki nauyin page in sha Allah.
Ba zan manta da BESTIE ba🥰I so much love her wish you all the best Aunty Nazeefah Sabo Nashe ta ce HADARIN GABAS yana hanya. Ina son ta sosai😮😮
Gaisuwa ga haƙarƙarina😂🥰uwar gidan Viper tunda mun amince Nabila ce amarya Ayushercool masoyiya. My beb Zee kumurya sai tallafe ƙirji muke muna sata a addu'a gashi zata fara yi mana ZAYTOON a watan Nuwamba i love them sosai🥰
Conversation bana ce kuci kanku ba, saboda ina ƙaunarku Sarautar's library Mutallab fans, Nimcy paid group my ArewaBooks people. Mikiya writers Association Mikiya fans AUTAR MANYA❤🔥 Ubangiji Ya bar ƙauna.
Page 15
Last free pages
*What if I tell you, I love you?*
"kar ki ce ba ki sanni ba, kar ki ce haka dole ma tarihin rayuwarki ba zai taɓa cika ba sai da sunana, dole a same ni a cikin rayuwarki sai dai idan za ki cire wani sashi na cikin tarihin" ya furta yana huci da gwame numfashi Safiyyerh was shocked and speechless at the same time ta kasa kallon shi wani irin tsoro shi take ji mai girma ya ratsa zuciyarta. A hankali ta ɗago kanta zuwa gare shi hawaye na taruwa cikinsu yana sauka akan fuskarta
Ta ƙura masa ido da sauri kuma ta girgiza kai ta ce "Wallahi da gaske ban san ka ba, ban taɓa ganin ka ba sai kwanakin nan, i don't even know your name balle kai,me ya sa zan sanka to?" za ta sakar masa kuka ya ɗora yatsarsa a baki ya ce
"Shhhh" ba shiri ta yi shiru tana sauke ajjiyar zuciya shi dai har lokacin fuskarta yake kallo yana murza tsinin wuƙar a ƙasa. "To kai ka sanni ne? Ni ka cire mini wuƙar nan ka ji ɗan baƙi" ta furta tana juya idanu ta langwaɓar da kanta gefe guda.
"Ki daina kiran sunana daga yau"
"Sai na dinga ce maka me to? Ka faɗa mini ban ma san sunan ba ai" ƙoƙarin biye mata yake wajan ganin ya samu abin da yake buƙata amma a duk kalma ɗaya daya furta ko kafin ya furta sai ya fama hautsina kan shi kafin ya san me zai furta mata. Wuƙar ya ɗauke ya cilar gefe guda ya juya ya kalli Goje jira ya ke yi safiya ta yi ya fara tunanin yadda zai samu likita ya ji ta ce
"Kai ne ka yanke su ko? Ba kyau wallahi ka mutu a haka wuta zaka tafi babu fashi kana kallo za mu shige aljanna muna jiyo ihunka a cikin lazza ko saƙara tunda baka da wani aiki a rayuwarka sai daba da bushe-bushe cikinka ba komai sai ƙwaya da hayaƙi, gabaɗaya gudanawa kake daka zaɓi wannan rayuwar ne ɗan baƙi? Bayan rayuwa akwai mutuwa fa karka bari ka mutu cikin wannan halin ba zaka ji da kyau wajan Mala'iku ba"
"Kina da ɗan'uwa mala'ika ne?"
"Subuhanallahi, kai ko wa'azin baka so kamar jinin fir'auna ni tausayinka kawai nake ji tunda baka gani shikenan" ta haɗe fuska irin ta ji haushin nan har ƙasan zuciyarta ita ƙyamar shi take yi rayuwarsa a gurɓace take babu wani abu na birgewa ko ban sha'awa a ciki deep down kuma tausayin rayuwar tasu take ji tana jin da tana da iko tabbas ba zata taɓa gazawa ba wajan ganin ta taimaka musu. Ya rufe idanunsa yana daga zaunen saman kujera ya ɗauki ƙafa ɗaya ya ɗora akan ɗaya ya fara yin fito wanda ya cika ɗakin a hankali kuma ya zaro sigari zai kunna ta yi saurin cewa.
"Matsalar daƙiƙi kenan a rayuwa, shi da kansa bature ya ce tana lalata lafiya dake babu arabi ba boko ba'a gane komai ai shikenan, goodness Safiyyerh what exactly wrong with you, that's not your business" ta faɗa lokaci guda kuma tana miƙewa tsaye sai dai bata kai ga zuwa inda ta yi niyya ba ta gan shi tsaye a gabanta hannunsa riƙe da sigarin yana zuƙa da fesarwa, ta saka zata rufe hancinta ya sa hannu ya tukare jikin bango ya sata a tsakiya sigarin a bakinsa yana binta da jajayen idanu bakinta na rawa ta girgiza kai ta ce "Mene haka wai?" Ya yi shiru yana duƙawa fuskarsa dab da nata har lokacin ita ɗin da yake kallo
"Iskanci ne wannan matar aure ce ni fa, saboda ƙwaƙwalwarka bata faɗa maka daidai ko? Idan ka sato ni a gidan mijina shine yake nufin me? Zan barka ka yi yadda ka so ko ƙazamin jikinka ya taɓa fatar Safiyyerh ba zan taɓa yafewa kai na ba, da babbar murya ina faɗa maka ni Safiyyerh matar aure ce ka ji ko? Kana jin Hausa ai?"
Ya zare sigari hayaƙin daya zuƙa ta cikin bakinsa ya dinga fesa mata a fuska ta fara tari tana ɗauke kai, ya ƙara zuƙar sigarin a baki ya matsa dab da fuskar tata ya sake fesa mata lokacin ta buɗe baki za ta yi magana gabaɗaya ta haɗiye hayaƙin, a gigice ta fara tari tare da kakarin amai ganin da gaske aman za ta yi,ya matsa a wajan tare da shigewa wani ɗakin. Safiyyerh ta durƙusa tana riƙe ciki saboda wani irin ciwo da yake yi mata ga amai dake ƙara hautsina mata kayan ciki ta rasa yadda za ta yi ta kwanta tana riƙe cikin da dinga rusa kuka. Duk abin da ya fara Goje na jinsu kawai yana cikin wani hali ne tsautsayi ya saka su fita a daren sukai karo da ƴan daban cikin gari sun shigo ɗaukar fansar wani faɗa da aka yi can kwanaki shine suka rufar musu, a cikin ƴan daban cikin garin wanda yake jagorantar su me suna Bakin wuta shine ya sare su shi kuma Moh sai da ya sari wajan mutum goma a yaran Bakin wuta wanda kuma shine faɗan su na farko a rayuwa ba wanda ya san wani, a cikin yaran ba sai da aka buɗewa wani ciki kuma duka aikin Moh ne yana da tabbacin kuma Bakin wuta ba zai bari haka nan a ci bulus akan shi ba.
Goje ya juya kaɗan ya kalli Safiyyerh dake kuka sosai kamar ranta zai fita itama yarinyar naci gare ta ga bakin tsiwa da Moh na taɓa mace da tuni Safiyyerh bata duniya ya san ba zai iya kashe ta ba amma zuwa gaba zata gane bata da wayo idan ta cigaba da kai shi bango. Tana kukan a haka bacci ya ɗauke ta bata ji kiran sallah ba amma tunda ta motsa bakinta ɗauke da addu'a ta san asuba ta yi ta miƙe da ƙyar ta nufi banɗaki ta yi alwala ta jima tana azkar kafin ta yi raka'atul fijr kana ta yi sallar asuba. A hankali ta dinga leƙa shi abin da ya bata mamaki bai shige ganinsa durƙushe a kan qwiwinsa ba yana kallon gabas ba kuma sallah ya yi ba, kan shi a ƙasa ya yi shiru kamar zata shiga sai kuma ta fasa ta tsaya cak ta samu kanta da yi masa addu'a samun sauƙi da mafita a rayuwarsa da shiriya idan yana da rabo.
"Allah Ya shiryarka idan kana da rabo"
Ya ɗago kan shi ya juya kaɗan suka haɗa ido, ba ƙaramin gigita ta yi da ganin idanunsa a haka ba, ya ƙura mata ido a ransa girman nacinta yake ƙara jinjinawa duk da bai yi mamaki bai kuma zama sabon abu ba, bai fiya son takura ba wani lokacin. Safiyyerh ta harɗe hannayenta a ƙirji ta ce "Ko yunwa kake ji na daba maka abinci? Ko shayi?"
"To na zo na yi maka shira? Ko waƙa?"
"Get out..."
Ya ce a hankali muryarsa ƙasa ta buɗe ido jin ya yi turanci ta ce "Wow ashe a ɗan san wani abu, nifa ba zan fita ba bakina ciwo yake na rashin magana gaskiya" kafin ya yi magana ta shiga cikin ɗakin ya yi saurin tashi da ƙyar ya nufi kujera ya kwanta ƙafarsa ɗaya a armchair ɗaya a can saman kujera hannayensa ya harɗe a ƙirji idanunsa rufe. Safiyyerh ta zauna a ƙasa ita kanta bata san me ya sa take son yin magana da shi ba, ta ji kuma tana barin wajansu zata haɗa Kinal da shi ita take son auren ɗan daba a hankali muryarta a nutse ta ce "Sunana Safiyyerh Abdu Marafa, ni ce auta a gidanmu..." Ta ɗan yi shiru bata ga alamar yana ma jinta ba kamar bacci yake yi haka yanayinsa ya nuna bata karaya ba ta sake matsawa ta ɗora da faɗin.
"Mahaifina professor ne ya koyar a jami'o'i da yawa a wannan ƙasar cikakken lakcara ne matasa na son shi sosai saboda yana taimaka musu da shawarwari. Ina da yayyi huɗu babban yayenmu sunansa Aliyu muna ce masa Captain shi soja ne, bashi da kirki gabaɗaya baya dariya kamar kai ɗin nan amma shi ba baƙi bane fari tas, yana da ilimi he is educated, sai mai bi masa Dr Hash likita shi a ɓangaren kwakwalwa Neurologist, shi rayuwarsa ba sawa ba hanawa sai my favourite Yaya J sunansa Junaid shi aiki biyu yake yi aikin banki da business, ina son shi sosai kamar yadda yake so na, rayuwarsa abar sha'awa ce wallahi. The last one Awais Shi kuma ɓangaren siyasa yake so amma daddy baya so yanzu dai ya ce yana son zama shahararren ɗan kasuwa ne, sai kuma ni Safiyyerh nima na yi karatu ina aiki yanzu matsayin Manager a FS WORLD INVESTMENT COMPANY, ina da saurayina da nake so kuma yake so na Ashraf sunansa ɗan mai kamfanin da nake aiki ne, akwai wasu abubuwa da bana ganewa a kamfanin..." Shiru ta yi da sauri kuma ta kalle shi taga har yanzu idanunsa rufe yake bai motsa ba
"Kodayake shikenan, saura kwana ɗaya auren mu da Ashraf ya rasu, Ashraf died ya mutu ya bar ni cikin tsoro da fargaba, a ranar daya rasu a ranar ne aka aura mini yayana Aliyu, da dai bana jituwa da shi sam amma ƙaddara ta haɗa kuma Ubangiji kaɗai ya san dalilin hakan, wannan shine labarin Safiyyerh Abdu Marafa"
Ta leƙa fuskarsa taga idonsa still a rufe ta tura bakinta gaba "Nima sai ka bani labarinka ai muna zaune waje guda bai kamata bamu san juna ba" miƙewa taga ya yi ya nufi ƙofa kafin ta bi bayansa har ya fice daga cikin gidan.
****Eng Ali wali ya dinga kallon Moh da yake tsaye kafin ya ce "Ina wayar daka amsa wajena? Mene amfaninta ina kira baka ɗauka wai?"
"Ba gani gabanka ba?" Moh ya ce yana kame fuskarsa kamar kodayaushe.
"Yarinyar nan tana wajanka ko Mutallab?" Moh ya yi tsaki a fili da ƙarfi kuma ya ce "Ni a tarihina sau ɗaya ake faɗa mini magana na haddace ka yi batu kawai" ya ƙarasa maganar yana jawo flask ɗin shayi ya tsiyayi ruwan zafi ya saka madara da su milo ya nemi waje ya zauna ya janyo biredi da plate ɗin ƙwai ya fara ci duk zafinsa da taurin kan shi a nutse yake cin abinci sai dai baya laumar wasa
"Daman kai aka kawowa abincin karin Mutallab? Ai shikenan magana nake so mu yi very important akan yarinyar nan daka ɗakko" ya yi shiru can ya ce "magana nake maka fa ka yi shiru"
"Kunne ke ji"
"Professor ya raina mini hankali wai ko kashe yarinyar nan zan yi ko a jikinsa yana nufin bai damu da ita bane ko mene? To wallahi ni Ali wali zan bashi mamaki,
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 15 Chapter of 17