dubansa ga ƙofa, Abban sa yagani, aikuwa da sauri yazo yatare shi haɗi da faɗin, "Abba barka da zuwa".
Sai da ya zauna kan kujera kana yace, "Ammar ya jikin Ummar taka?".
"Da sauki yace".
Dubansa yayi da kyau kana yace, "tun yaushe take bacci hala".
Yace "bayan fitar ka ba jimawa".
Tea ya haɗa yasha kana yace bari yaje gida yayi wanka idan ya dawo sai Ammar yaje.
Tunda taga Anwar yashiga ke-ke napep yabar ta tsaye takasa koda ɗaga ƙafa ta tafi bare ta mutsa, sose abin da Anwar yayi mata ya bata tsoro, to me Hafsat take dashi wanda ita bata da?, tunanin ne taga bashine mafita ba tayi kyafa kana ta tsayar da mai napep, sunan wata ungwa tafaɗa mishi tashiga ya kaita.
Abba na fita Umma ta farka haɗi da ƙiran sunan Allah, da sauri Ammar da ke kusa da ita ya ƙaraso gareta yana faɗin, "Umma ya jikin, mike miki ciyo?".
Buɗar baki tayi ahankali tace, "Ammar ba abinda kemin ciyo yanzu" sai da ta ɗan huta tace, "ina Abbanka yake ko har yanzu bai zomin da Hafsat ba?".
Ammar kasa magana yayi sai can yace, "kiyi haƙuri Umma nasan zai zo da ita".
Komai bata saki faɗa ba, amma tayi alwashin in har dai ta fita daga wannan hospital to ba shakka sai taje gida ganin iyayenta, dan tasan ko hakkinsu na kanta, amma ya ta iya tunda ba laifinta bane.
Bayan kwana biyu da faruwar haka jikin Umma yayi sauƙi sose dan har abinci tana iya ci da kanta, sai dai wasar ɓoyar da ake tsakanin Abba da Umma, dan yanzu baya son shigowa sai tayi bacci, dan baya son ta tambaye shi Hafsat.
Itako da ta lura da haka data ji alamun zai shigo sai tayi kamar bacci take har sai yafita kan ta buɗe idonta.
Yau Monday, Doctor nashigowa ya tambaye ta yatakeji gami da lafiyar ta, sai tace batajin komai, magani yarubuta mata haɗi da takardar sallama kana ya ƙara jamata kunne akan ta daina sa damuwa aranta.
Bayan Doctor yafita Ammar ya ƙira Abban sa ya sheida masa ansallamesu, ba jimawa kuwa sai ga Abba yazo sutafi, kayansu suka saka a mota kana suka shiga suka tafi gida, amma duk wannan abin Abba yakasa haɗa ido da Umma har suka ƙaraso gida.
Yana sauke su ya wuce wajan aikin sa, da yamma bayan ya dawo daga aiki har zai shiga gida sai suka haɗu da Baban Safiyya, bayan sun gaisa sai Baban Safiyya yace,
"Kunɓatar min da ɗiya hankalinku ya kwanta ko?".
Murmushi Abban Hafsat yayi kana yace, "ayi haƙuri Alhaji,fushin zuciya ne da sharin sheiɗan, amma dan Allah ayimana haƙuri wallahi yanzu haka ni kaɗai nasan halin da nake ciki, amma dan Allah kar ayi fushi damu a cigaba da sanyamu a addu'a".
Sai da Abban Safiyya yayi murmushi kana yace, "ba komai, kuma inaji ajikina ƴata tana hannun nagari, kuma insha Allahu lafiya zata dawo".....daga nan suka cigaba da firar su, daga baya sukayi ma juna sallama suka wuce.
Ƙarfi tara da rabi na dare, jirgin su Hafsat ya sauka a airplane ďin India, aikuwa tunda jirigin ya sauka taji gabanta ya fara dukan uku-uku, lokaci ɗaya wasu hawaye masu zafi suka fara antayu mata, abukin tafiyar sune Sulaiman yace, "Hafsat ki shafe hawayinki ki taso mu fita".....yana faɗa yana tashi domin su fita.
Bayan sa ta bi har suka zo matakalal jirgi, yana gaba tana biye dashi suma sauran na biye da su, aikuwa tana taka matakalar farko, sai wani iska mai haɗi da sanyin daɗi ya ziyarce ta, bashiri ta buɗa baki haɗi da ɗago harshin ta tafara yiwa Allah kirari.....
*#VOte*
*Comment*
*Share*
*°🔘°UMARNIN SAURAYI°🔘°*
*1441H/2020M.*
*NA MARUBUCIYA:-*
*SUMY M NA'IGGE✍🏼•*
~~WattpadSummy M Na'ige~
*SHAFI NA 21📑*
*__________*📖 A hankali taci gaba da ta kawa saman mattakalar jirgin har ta sauko, suna sauka gaba ki ɗaya, ba jimawa sai gashi anturu motar da zata kaisu makarantar.
Bayan angama duba jukkunan su kana suka shiga mota suka kama hanyar da zata sa dasu da makaranta, basu tsaya ko inaba sai bakin gate ɗin makarantar, kafin su shiga da ga ciki sai Hafsat ta dago da kanta, dan tun lokacin da suka shiga motar kanta na kasa taƙi ta ɗago bare taga jajayin fata .
Aikuwa tana ɗago kanta sai da tayi suman zaune, dan ganin wannan katafariyar makaranta da tayi sai da tayi tasbihi ga Allah, makarantar tabi da kallo, wadda aka rubuta sunanta da manya haruffa, wato (GALGOTIAS UNIVERSITY).
Bata ƙarasa kallon ba direban motar ya shiga cikin makarantar, bai tsaya dasu ko ina ba sai gyefin saukar baƙi da ke cikin makarantar, bayan sun shiga sun zauna aka kawo musu abin motsa baki, bayan sun kammala kowanin su yayi wanka ya ɗan huta kafin safe sai su fara shiga makarantar.
Sulaiman ne ya kalle abukain tafiyar sa kana yace, "wai ina Hafsat?, ayya taci wani abu kuwa?, dan nasan ƙila bataci komai ba tana can tana sana'ar ta ta kuka".
Sai ɗayan wanda akekira da Safuwan yace, "wata ƙila bata ciba, amma bari nayi mata knocking idan ta fito zamu gani ko taci".
Yana faɗa yana tashi dan ya ƙarasa ɗakin da akayi mata ma sauki.
Knocking da bai wuce uku ba ta ɓuɗe, wannda tagani bakin ƙofar ɗakin yasa ta ƙaƙalo murmushi haɗi da yin ƙasa da kanta, kafin ta ɓuɗa baki tayi magana yace,
"Idan kin kammala muna son magana dake".
Tace "tom gani zuwa".
Yana barin wajan itama ta koma ɗakin ta shirya jikinta tasaka hijba kana ta fito wajan su.
Sallama tayi musu, suka amsa haɗi da bata izini sannan ta shigo.
Bayan ta shigo ta gaishe su haɗi da musu ban gajiya kana ta zauna.
Dukan su suka amsa kana suka tambaye ta ko taci wani abu ba kuka taje tanayi ba?.
Sai da tayi murmushi kana tace, "wallahi naci kuma na koshi".
Suka ce to hakan yafi sannan suka ɗan taɓa fira gami da yadda karatun su zai kasance a wannan ƙasar, bayan sun ɗanyi shuru sai Sulaiman ya dube su kana yace,
" Gami da zaman Hafsat hostel ne, duk da hostel ɗin ƙasar yana da kyau amma ina ga kamar zaifi in kin yarda ko kun amice sai na kaita gidan Yaya ta dan itama karatu takeyi anan kuma tanada miji da yaro ɗaya, amma shi mai gidan nata sai wani lokaci ya kan shigo kuma ba zai wuce kwana biyu ba ya koma, dan wancan lokacin da nazo acan na zauna kuma naga zaki fi jin daɗin zama acan gaskiya, amma inkunga hakan yayi muku kuma yayi miki".
Gaba ki ɗayan su sukayi na'am da maganar sa kana ya dube Hafsat da tayi shuru ba tace komai ba yace, "Hafsat mikika ce akan maganata".
Ahankali ta ɓuɗa baki tace, "ba abinda zance tunda ni ban san kan ƙasar ba, amma tunda kai kasan kan ƙasar duk yadda kayi ba komai, sai dai kar mutakura ta".
Yace, "a'a kar ki damu dan Aunty Shemah ta wuce haka".
Sai da suka gama tattaunawa kana tafito ta koma ɗakin ta kafin safiya ta waye aba kowane class sai kuma ta wuce gidan da zata zauna.
*******
Wata unguwace mai napep ya sauke ta, bayan ta sallameshi tashiga wani longo tana shiga tafiya kaɗan sai tazo ƙofar wani ɗaki, da yake ɗakunane jere a unguwar kuma da gani ɗakunan hayane, na tsaka daga cikin su ta tura ƙofa tashiga.
Ƴan mata biyu ne aciki ɗayan na kwance ɗayan na shirin kayan sawar su, aikuwa suna ganin ta gabaki ɗaya suka buga shewa haɗi da faɗin,
" Matar Anwar ce tazo wurin mu?".
Sun faɗi haka ciki da tsokana.
Tsaki ta musu kana tace, "kubarni da ɗan iska, wai yau ni zaima walaƙanci akan wata banzar yarinya, wallahi naga har yanzu kansa bai daina rawa ba, amma dani yake zanci".
Tafaɗa haka ranta amatuƙar ɓace.
Ɗayan wadda ke kwance mai suna Zahara ita tace, "me ya haɗaki da Anwar ɗin naki hala?".
Kafin tayi magana sai ɗayan mai shirin kaya wato Hafiza tace, "ta tsoniyar gizo bata wuce ta ƙoƙi, ni dai wallahi Hajara da zaki bi tawa da kinbar Anwar da Hafsat, dan wallahi ko da zaki je wurin bokayin duniyar nan ba zai iya rabuwa da Hafsat ba, dan ni nasan son da yake ma Hafsat cikin jininsa yake, amma dan baki da imani kikabi kowace hanya kika lalata musu zama to gashi gaki ya aure ki .....aitun bata kai da rufe baki ba Hajara ta miƙi tsaye zata cikumo ta sai Zahara tayi saurin tashi tariƙi Hajara tana faɗin, "dan Allah Hajara ki kyaleta idan har ta isa tasa Anwar ya aure Hafsat, kuma bari kiji, wallahi Anwar koda mi yake taƙama sai ya aureki barin ni dashi, ai inyasan wata bai san wata ba".
Hafiza tace, "kanku akeji" tana faɗin haka ta buɗe ƙofar ɗakin ta fice batare da tasaki magana ba.
Tana fita sai Zahara ta dube Hajara da tacika tayi fam, abu kaɗan take jira ta fashe, Zahara irin yanayi da taga Hajara tashiga yasa ta ƙarasowa jikin ta sose, haƙuri ta fara bata kan ta ɗura hannunta saman dukiyar fulaninta, haɗi da kai bakinta kan na Hajara,kissing ɗinta cikin sigar rarrashi.
Sai da suka gama fanɗarewar su kana Zahara ta ƙara matse Hajara jikita tana faɗi, "ke daina sama ranki damuwa, indai Anwar ne kina zaune zaki gansa dan haka ki bar komai a hannu na nasan yadda zanyi da shi".
Dubanta Hajara tayi, taga da gaske take dan haka tace, "nagode masoyiya ta, haka dai suka cigaba da firar su daga baya kuma Hajara tayi mata sallama ta koma unguwar su.
Tunda Umma ta dawo daga hospital ta daina sakin jikinta da Abba dan yanzu ma haduwa wuya take musu, yau ma da dare bayan ya dawo daga masallaci ta kai masa abinci yaci har yayi shirin kwanciya sai gata ta turu ƙofar ɗakinsa haɗi da sallama.
Bayan ya amsa mata ya ɗago da kansa ya kalleta ciki da son matar tasa yaci, "ƙaraso daga ciki Fatima".
Ba muso ta ƙaraso ta samu waje ta zauna nesa kaɗan dashi.
Har ya buɗa baki yayi magana sai tayi saurin cewa, "Abban Hafsat, dama maganar da zan faɗa itace, ina son zanje gidan iyayena dan ina son naje na gansu, ko banza najima banje ba,kuma idan naje bazan dawo ba har sai ka nemumin ƴata".
Tana faɗar haka ta miƙi dan ta fita.
Da sauri ya ƙaraso gareta yana faɗin, "haba Fatima miyayi zafi haka, dan Allah karki barni wallahi ni kaɗai nasan halin da nake ciki, kuma zanci zuwa gida ki bari idan nasamu huta muje tare, dan koni ina son naje naga gashesu"......ai tun bai kai ƙarshin zanciba ta fice daga ɗakinsa yana kiranta amma tayi kamar batajiba ta shige ɗakinta haɗi da rufe ƙofa.
Tanda ta rufe ƙofa ta fara kuka mai cin zuciya da baƙin cikin rashin inda ƴar ta take, amma a gaskiya baza iya cigaba da zama ba Hafsat ba, inhar yana son taci gaba da zama dashi sai ya nemu mata ƴar ta, dan gobe tunda safe zata ta kama hayar garinsu ko da kuwa ba zata gane gidan ba, dan ita gani take bazata gane gida ba, dan rabunta da gida kusan shekara ashirin, aikuwa tana tuna haka ta fara kuka maicin zuciya.
Ko da yazo ga ƙofar yaga har ta rufe, ai basan sanda ya dafe kansa ba haɗi da faɗin "ya salam".....kansa ne yaji ya fara sarawa, dan haka ya koma ɗakinsa ya zauna haɗi da ɗauko magani yasha kana ya kwanta.
Koda gari ya waye bayan sun gamala komai sun shirya sunyi beark aka turu azo dasu cikin school ɗin.
Bayan sunje aka ba kowa nasa abinda za'a bashi kana akayi musu jagora zuwa class ɗinsu.
Bayan sun gama lecture ne sai Saulaiman shida abakan tafiyar su suka kai Hafsat gidan Aunty Shemah, kuma gidan ba nisa da school ɗin, shiyasa batayi wuyar ganewa ba.
Bayan sun shiga gida Aunty Shemah ta karɓe su hannu biyu² haɗi da kawu musu kayam mutsa baki, bayan su ɗan ci abinda ta kawo musu nan Sulauman ya ƙara yimata bayani akan Hafsat itama Hafsat ya ƙara yimata bayani akan Aunty Shemah.
Aunty Shemah sose tayi murna da samun abukir zama, dan zaman kaɗaice bayayi mata daɗi, dan mijinta bayar da taje ko inaba daga makaranta sai makaranta,wani ɗaki ta nunama Hafsat tace tazo ga ɗakin da zata zauna ,tashi tayi tabi bayan ta tanuna mata ɗakin, sose ɗakin yayi mata kyau, dan ɗakine mai haɗe toilet da ƙaramin gado da wadiruf, bayan komai ya kammala sai Sulaiman yayi musu sallama yayi tafiyar sa.
*Wanene Anwar*
*#Veto*
*Comment*
*Share*
*°🔘°UMARNIN SAURAYI°🔘°*
*1441H/2020M.*
*NA MARUBUCIYA:-*
*SUMY M NA'IGGE✍🏼•*
~~WattpadSummy M Na'ige~
*SHAFI NA 22📑*
*__________📖* Anwar hafafin ɗan garin kaduna ne, sunan mahaifin sa Alhaji Umar, fittacin ɗan kasuwa ne kuma babban ma'akacin gwamnati, yayi suna a cikin gari kaduna sose, dan kowa yasan Alhaji Umar dallah-dallah ,mahafiyar sa Hajiya Ruƙayya, suna da yara huɗu, Zainab, Hafsat, Sajida, sai autansu Anwar, iyayen su suna nuna musu so da ƙauna sosai, musamman Anwar da ya kasance auta, dukan su sunyi karatu mai zurfi sannan sukayi aure, yanzu Anwar ne ya yarage baiyi ba, kuma koshi iyayen sa na son yayi amma sai wani ƙaƙale² yake musu shi sai yayi karatu mai zurfi, bayan ya kammala karatun sa ne ya ƙaƙalo zuwa sokoto dan ya dubama mahaifin sa wani ƙamfanin shi, to acan ne ya haɗu da Hafsat har ya fara soyayya da ita, sosai yake son Hafsat kuma har cikin ransa aurin ta zaiyi sai daga baya sheiɗan ya shiga tsakanin.
*Cigaban labari*
Anwar dake airport sai kai da komowa ya keyi yarasa abinyi, ji yake kamar yayi tson-tso ya ganshi Indian, rasa abinyi yayi dan haka ya tsayar da ɗan aceɓa yace ya kaishi wata unguwa.
Dai-dai wani katafarin gida ya ajeshi, kud'i ya bashi bai ma tsaya karb'ar canjiba ya wuce cikin gidan, mai gadi na masa magana amma ga baki d'aya hankalin sa bai tare da shi shiya sa bai karb'a masa ba ya wuce cikin gidan.
Bai tsaya ko ina ba sai wani ƙayataccin falo wanda aka ƙawatashi da kayan ado na more rayuwa,iya haɗuwa wannan falon ya haɗu, ɗayan kujerun ya zauna haɗe da dafe kansa lokaci ɗaya yaji kansa ya fara sarawa, carpet ɗin dake shinfiɗe atsakar parlour ya kwata, bai jima da kwanciya ba bacci yayi awun gaba dashi.
Aunty Zainab ko da ta fito kwance ta ganshi a tsakiyar parlor, ba tama ganeshi ba sai data kara masa kallon kana tagane Anwar ne, da sauri ta ƙaraso gareshi tafara ta dashi tana faɗin, "Anwar lafiya katashi mike damunka?"....tafaɗi haka ciki da firgici.
A hankali ya fara ɓuɗa idonsa da sukayi masa jawur yace, "Aunty"..... girgizashi ta farayi ciki da tashin hankali tana faɗin, "mike damunka haka duk ka rame kayi baƙi, kafaɗamin dan Allah?".
Irin yadda yaga ta rikice duk tawani tada hankalinta yasa ya buɗa baki yace, "ba komai Aunty, lafiya ce ba nida kwana biyu amma yanzu nasamu sauƙi".
Bata yarda da abinda yace ba amma sai ta kyaleshi tace, "tau Allah ya ƙara lafiya, amma katashi kaci wani abu".
"A'a Aunty yanzu zan koma sokoto dan gobe nake son na koma gida dan har yanzu ban koma ba"......kafin ya rufe baki tace, "mi kazoyi abuja yanzu?".
Yace, "wani aiki ya kawuni nida abokina kuma koda nazo har ya wuce Indian "..... tace, "to duk da haka sai kaci wani abu kafin katafi.
Ba musu ya tashi ya ɗanci kaɗan kana yayi mata sallama ya wuce warsa.
filin jirgi ya isa, ciki ikon Allah ya samu jirgi ya shiga ya dawo da shi sokoto, gidansa ya isa koda yaje ga baki ɗaya garin yaji yayi masa zafi dan haka lokaci ɗaya ya fara haɗa kayansa kamar wani ma haukwaci, dan gaskiya bazai iya bacci a cikin garin ba, gara yabar garin ko yaji sauki abinda yake ji aransa.
Tunda aka nemi Hafsat ba a ganta ba Baban Safiyya ya daina kula kowa a gidansa, ba yadda Mamar Safiyya batayi ya haƙura ba amma yaƙi, sose suka shiga damuwa na rashin kulasu da Baban Safiyya ya daina.
Shiko Abbas Yayan Safiyya wani tashin hankali ya shiga wanda lokaci ɗaya har kwanci yayi kuma duk ba komai ya jawu haka ba sai rashi ganin Hafsat, dan yanzu shi kaɗai yasan ya yakeji na rashin Hafsat, dan ko ba afaɗa masa ba yasan ya kamu da son ta, kuma so bana wasa ba, dan ji yake a ransa duk inda take sai ya nemuta,dan a halin yanzu ji yake bazai iya rayuwa ba inba ita.
Safiyya ma duk tabi ta ƙare dan yanzu ko abinci da ƙyar take samun ci, ga school duk bata jin daɗin zuwa kuma gashi sun kusa fara jarabawa amma komai ta daina ganewa saboda rashi ƴar uwata.l
Tunda safe Umma ta fara shirin tafiya garinsu, ta haɗa duk wani abin buƙatar ta, tana cikin shirin tafiya sai ga Abban Hafsat ya shigo ɗakin ciki da tashin hankali, da sauri ya ƙaraso gareta yana faɗi, "haba Fatima miyayi zafi haka, dan Allah ki tausayamin wallahi ina cikin tashin hankali, kuma dan Allah ina son ki tsaya ki saurareni kona minti ɗaya ne Fatima".....yana faɗa amma kamar ya durƙusa mata sabida kaɗuwa.
Ba abinda tace dashi, kuma bata fasa haɗa kayanta ba dan ta tafi.
Daya ga ba alamun wasa acikin lamarin ta dan haka ya ƙarɓe jikar da take koƙarin fita da ita yana faɗin, "Fatima bari kiji duk son da kikewa Hafsat nafiki sonta nesa ba kusa, kuma bazan hanaki zuwa gida ba, amma kibari gobe insha Allah zan kai ki da kaina, kuma kisani fa Hafsat ba ko ina tajeba sai wajan karatu"....nan dai ya faɗa mata duk abinda ya sani game da Hafsat.
Sose Mama tayi kukan rashin ƴarta, amma duk da haka tace sai taje ganin iyayenta, ba yadda ya iya haka ya kaita tashir mota tashiga mota ta tafi garin su tabar Abba cike da kewarsu.
Awa ɗaya ta kaita tashar garin dange, napep ta hawa ya kaita cikin garin, tunda tashiga garin gabanta sai famar dukan uku-uku yake, bakin wata ƙofar gida mai napep ya ajeta, tunda ya ajita gabanta ya ƙara tsananta faɗuwa, sallamar mai napep tayi kana ta ɗau kayan ta dan ta ƙarasa cikin gidan, gab da zata shiga gida taga wani ɗan tsoho kwance da alamu ma bashi da lafiya, har zata wuce shi sai kuma ta ƙara kallonsa, gabanta ne ya bada dummmm ai basan lokacin da tasake kayanta ba ta ƙarasa gareshi tana faɗin Baba! Baba! lafiya kuwa na ganka haka?".....tafaɗi haka tana mai sanya kuka.
Kafin ya buɗa baki yayi magana sai ga wata mata ta kurnu kai dan taga wake kuka.
Ita kuma Umma mutsin da taje ne yasa ta ɗago kanta, ɗagowar da zatayi aikuwa sai ganin wata mata tayi tsaye tana kallon ta, suna haɗa ido ta zabura da ƙarfi ta tashi tana sun tayi magana amma takasa, bawani ɓata lokaci sai gashi ta faɗi ƙasa sume.
******
Sose Hafsat ke jin daɗin zama da Aunty Shemah, kuma tana jin daɗin karatu ba kamar da tana najeria ba, dan yanzu idan kaga Hafsat kamar ba ita ba, sose kyauta ya ƙara fita kamar wata balara ba.
Yau ma kamar kullum tana ɗaki kwance tana duba wusu books ɗinta sai jin wayar ta tayi tana ƙara, kamar baza ɗauka ba kuma sai ta ɗauka, suna Sulaiman taga ya bayyana, ba ɓata lokaci ta danna picking ,kafin ta ɓuɗa baki tayi magana yace, "ki samemu muna parlour muna jiranki".
Kafin tayi magana har ya datse kiran.
Cikin tsanaki ta tashi ta gyara jikinta kana ta sanya hijab ɗinta tafito falon gidan.
Ahankali take tafiya cikin natsuwa har ta kawo cikin parlour haɗi da sallama abakinta, izini sukayi mata da tashigo, tana buɗe labulen ɗaki sukayi ido huɗu da Sulaiman, murmushi yayi mata, itama ta mayar masa da martani haɗi gashe da su, amsawa sukayi da nuna faricikin ganinta afuskar su.
Bayan sun gaisa Sulaiman yace, "Aunty wai me kike ba ƙanwar taki ta koma kalar indian"......ya faɗa haka yana kallon Hafsat yana murmushi.
Sai Aunty Shemah tace, "kodai ka ƙyasa".
kafin yayi magana abukin tafiyar su Lukuman yace, "Hafsat shikenan kin bar mu tunda kin samu Aunty gashi ko a school baki neman mu".
Murmushi tayi tace, "a'a wallahi ba haka ba, lokaci ne babu amma naso na kai muku ziyara wannan satin".
Sai Sulaiman yace, "bawani nan ke dai kin samu Aunty kin manta damu"....haka dai suka sha firarsu, daga bisani kuma sukayi musu sallama suka tafiyar su, amma ako da yaushe Sulaiman na kirata yana tambayar ta koda tana buƙatar wani abu, watarana ko bata buƙata yakan yumata aiki, sose take jin daɗi yadda yake kula da ita, amma awani gyafe tsoro takeji.
Yau Monday tunda sassafe tashirya dumin taje makaranta, parlour ta fita ta same Aunty zaune tana jiran fitowar ta, Aunty Shemah na ganin ta fito murmushi ya bayyana afuskar ta kana tace, "Hafsat ki ƙaraso muyi breakfast muwuce school dan ƙarfe 8:00 zan shiga lecture kuma saura ƙan ɗan lokaci ya cika".
A gurguje sukayi beark suka fito suka wuce makaranta, koda suka isa saura kaɗan Aunty Shemah ta makara, dan haka suna shiga tayi parking ta fito batare ma da ta kashe mota ba ta bar ma Hafsat kye ta wuce warta.
Mota ta kashe haɗi da zare kye ɗin motar ta fito ta rufe, juyuwar da zatayi sai tayi arba da ƙawar ta Zeenatu, wadda suka haɗu da ita a nan kuma class ɗinsu ɗaya, kuma itama ƴar najeria ce, murmushi suka sakar ma junasu suka gaisa kana suka kama hanyar class ɗinsu, suna cikin tafiya sai jikin Hafsat ya bata kamar ana kallonta, juyuwar da zata yi sukayi ido huɗu da Sulaiman, murmushi tayi masa kana ta gaisheshi, magana yayi mata yace idan tagama lecture yana neman ta, tace tom sai ta fito.
Gaba ki ɗaya Anwar ya kasa zama ya kasa tsaye ba shiri ya kama hanyar kaduna cikin dare dan shi kam bazai iya zama garin sokoto ba Hafsat ba.
ƙarfe biyun dare ya isa garin kaduna, koda ya isa gida ko part ɗin iyayensa ba shigaba ya wuce part ɗinsa, ciki da damuwa .....
*Bani da bakin magana gareku, ku ƙara haƙuri pls, abubuwane sukayi min yawa, dan Allah ina baran addu'a gareku pls*🙏
*#Vote*
*°🔘°UMARNIN SAURAYI°🔘°*
*1441H/2020M.*
*NA MARUBUCIYA:-*
*SUMY M NA'IGGE✍🏼•*
~~WattpadSummy M Na'ige~
*SHAFI NA 23📑*
*__________*📖 da hanzari matar da ke ƙofar gidan tayi saurin ƙarasowa gareta tana faɗin, "Fati kitashi kinji"....tana faɗa ta ɗauku ruwa ta shafa mata a fuska.
Ba ɓata lokaci sai numfashin ta ya fara dawowa dai-dai, cikin hanzari Ummar Hafsat ta tashi tana riƙi Mama tana kuka mai cin zuciya tana faɗin, "Mama dan Allah kuyafemin".
Kafin tayi maga Baban ta dake kwance yana jin ance Fati ya tashi daga kwanciyar da yake, bakin sa na karkarwa yace, "wa na keji kamar muryar Fatina, koda gizo ne takemin ko mafarkin da na saba ne?".
Mama ta ɓuɗa baki cikin sanyi jiki tace, "eh Malam Fati itace"..tun bata rufe baki ba ya fara wa Allah hamdala kana yace, "Fati ƙaraso gareni kinji".
Ba musu ta ƙaraso gareshi tana faɗin, "dan Allah Baba kuyafemin nasan niyi kuskura amma dan Allah ina neman afuwarku".
Yace, "ba komai Fati, na yafemiki har a wajan Allah, kuma naji daɗin ganinki ina yaraye bam mutuba, sai dai dan Allah abinda nakeso dake shine Fati kuriƙa zumunci ko bayan raina kada kiyar da ki katse zumuncinki da ƴan uwanki,amma yanzu idan an kwana biyu ki shirya kije duk inda ɗan uwanki yake ki sada zumunci"....nasiha yayi mata sose akan tariƙa zumunci, daga baya suka tashi suka ƙarasa cikin gida.
Bayan kwana biyu da zuwan Ummar Hafsat gidan iyayenta ta kwashe duk abinda ke damun ta na ɓatan Hafsat har cikin da Hafsat tayi ta gaya musu, sose hankalin su ya tashi da suka ji wannan labarin, Malam da Mama faɗa sukayi mata sose kana suka nuna mata ba abinda yaje mata haka face katse zumuncin da tayi, bayan komai ya lafa suka bata magana mai sanyi kuma sukayi mata alƙawarin za su taya ta addu'a Allah ya bayyana ta duk inda take.
Mamar ta tace, 'ke Fati ke da mijinki bansa wanda yafi wani laifi ba, ace ka kwashe shekaru kana cikin garin sokoto amma kakasa leƙa ƴan uwanka, dan mi Allah bazai jarabe ku ba, ke kin
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 13