hali yake ciki
Wani badakare ne ya yi ƙarfin halin fara ƙoƙarin saukar da kejin,sauran dakarun ma suka saka masa hannu,suna saukewa kuma shugaban nasu ya yi ƙarfin halin buɗe kejin
Yana buɗewa suka ja baya a ɗan tsorace,kafin ɗaya daga cikinsu ya yi ƙarfin halin matsowa yana kallon Kazuzi,da sai yanzu suka kula ashe duk abin da yake faruwa ma idanunshi a lumshe yake,babban dakaren ya saka hannu da nufin fito da shi, sauran dakarun ma suka saka hannu don fito da Kazuzi,amma duk ƙoƙarin su tamkar suna yunƙurin matsar da ƙaton dutse,ko motsi baya yi
Shiru suka yi,suka tsaya cirko-cirko suna kallon juna,kafin babban badakaren ya yi ta maza ya dubi Kazuzi ya ce
"Sadauki Kazuzi!
Kafin yau kai ɗin jarumi ne, mai gata da dama,mai sharafinshi a wannan nahiya,wanda ya gagari kowa,amma a yau kai ba komai bane face bawa,don haka sarki Iyaad yana umartarka da ka fito daga kejin nan don a kai ka inda aka warewa bayi irinka"
Maganar babban badakaren ta razana ƙananan,don da alamu sun manta wanene Kazuzi,sai dai abin da ya yi tsananin ba su mamaki bai wuce ganin Kazuzi ya yunƙura ba,cikin ɗan ƙanƙanin lokaci ya fito daga cikin kejin ya tsaya a gabansu,kuma har zuwa lokacin idanunshi a rufe suke
Da farko bin shi suka yi da kallo cikin tsananin mamaki da kaɗuwa,amma daga baya babban badakaren ya dake ya kama shi,kai tsaye suka wuce ɗakin da aka tanada don Kazuzi
Ba su kwance masa ko sarƙa ɗaya ba,daga ta hannu har zuwa ta ƙafa,suka tura shi zuwa ɗakin mai tsananin duhu,suka mayar da ƙofar da ta kasance ta wani nau'in ƙarfe mai nauyi suka rufe ta ruf
Kai tsaye wajen Sarkin yaƙi suka nufa, cikin girmamawa suka sanar da shi cewa sun kai Kazuzi zuwa ɗakin da aka tanada don shi,sarkin yaƙi Ra'uf ya kalle su yana murmushi ya ce"sannunku da ƙoƙari,yanzu sai a kai masa abinci"suka rissina, babban badakare ya ce"an gama ya shugaba na"
DAULAR KAIZUR
A hankali yake tafiya yana bin doguwar hanyar, dakaru uku da ke tsaron lafiyarshi suna take masa baya,yana zuwa daidai inda suke tsayawa suka tsaya ba tare da an umarce su ba, gami da juya baya,sarki Mu'iz ya cigaba da tafiya zuwa cikin duhuwar bayan ya ɗauki karan a ci bal-bal guda ɗaya da suke bakin ƙofar
Ƴar doguwar tafiya ya yi a cikin kogon kafin ya ƙarasa inda yake muradin zuwa, murmushi ya yi yana kallon dattijuwar matar da take durƙushe a kan gwiwowinta, ɗaure take da sarƙa mai matuƙar nauyi,tana sauke numfashi a wahale,kayan jikinta zuwa gashin kanta a hargitse
"MUNAYA!"ya ambata cikin wani irin amo mara daɗin ji, ɗagowa matar ta yi da kanta, cikin ƙarfin hali ta furta "Barka da zuwa ya shugaba na!"
Bai amsa ba,sai zama da ya yi a wajen da ya saba zama yana kallonta cike da tsana,bata damu ba,ta saba ganin irin wannan kallon daga wajenshi,har zuwa mutanen garin da suke kallonta a duk lokacin da aka fitar da ita daga inda take a kulle
"Munaya!
Tsawon shekaru ashirin kenan kina azabtar da zuciyarmu,akan abin da kika sani ba naki bane tun kafin wanzuwar shi a duniya, menene dalilin da ya sa ba za ki daina azabtar da zuciyoyinmu haka ba? menene dalilin da ya sa ba za ki huta ba mu ma mu huta?
Ki yiwa kanki adalci ki yi mana,ki bayyana inda kika kai ajiyar nan,daga nan za mu sallame ki kema ki huta"
A hankali Munaya ta ɗago kanta tana sauke numfashi, ba tare da ta kalle shi ba, cikin sanyin murya ta furta "a yi min afuwa ya shugaba na!
Amma abin da na saba faɗa dai shi zan maimaita,bani da masaniyar inda yake"
Shiru sarki Mu'iz ya yi yana kallonta zuciyarshi tana tafasa,da sauti irin na fushi ya ce"amma kin yarda da cewa da saka hannunki a ɓatan kadara mafi daraja a kaizur?"
Kai tsaye ta amsa da faɗin"tabbas haka ne ranka ya daɗe,ni na fito da shi,amma daga nan ban san komai ba,kuma ba zan iya komai don dawowarshi ba"
#Nusy_bee
08125952284
👑🗡️ MASARAUTAR KAIZUR 🗡️👑
https://chat.whatsapp.com/Is0HqhjNITL3VZIagV42u7?mode=gi_t
✍️Nusy bee
❤️ Young talented writers association YOTA ❤️
(Under YOTA'S AMAZING PENS)
Page 3
Sarki Mu'iz ya daka mata tsawa da cewa"ba ki da bakin yi min wani jawabi Munaya!
Ke kika ɓatar min da ɗa,ki yarda da hakan,amma ba ki da wasu kalamai da za ki kare kanki daga hakan,za ki cigaba da karɓar hukunci har zuwa lokacin da za ki bayyana ɗana,ko kuma ki bar duniyar,ke azzaluma ce tabbas,amma zaluncin zai rufto miki"ya miƙe a fusace ya fice daga wajen, Munaya ta bi shi da kallo ba tare da ta iya cewa komai ba
Masu tsaron lafiyarshi ba su yi mamakin ganinshi a haka ba saboda kusan duk lokacin da ya ziyarci Munaya hakan ce take kasancewa,suka rufa masa baya don komawa fada,kamar yadda suka saba har suka fice daga wajen babu wanda ya iya magana
*MASARAUTAR TAYAAR*
Da tsananin farin ciki take shiryawa,kuyanginta suna taya ta,a yau tana cike da tsananin farin ciki irin wanda bata taɓa tsintar kanta a ciki ba,ba komai bane ya faranta mata sai kame azzalumi Kazuzi da aka yi,wanda a yau ya dawo bawa a masarautarsu
Zata iya cewa a duniya babu wata halitta da ta tsana,tsana mai muni irin Kazuzi,shine ya kashe ɗan'uwanta ɗaya tilo da take tsananin so fiye da rayuwarta,wanda a dalilin rasuwar shi ne zuciyar mahaifiyarsu ta buga itama ta bar duniya,yanzu daga ita sai mahaifinta suka rage a raye,a dalilin Kazuzi Sarautar da suka gada zata bar gidansu suna ji suna gani
"Ya shugaba ta ga abin kama gashin"a cewar wata kuyangar ta,bata yi magana ba sai murmushin da ta yi,ta sanya hannu ta karɓa,ta kama gashin,sannan ta miƙe ta shiga gaba,su kuma suka biyo ta a baya,suka fice daga sashen nata
Sai da suka hau ƙawataccen keken doki wanda ya kai su har bakin ɗakin da aka ajiye Kazuzi,babban ɗaki ne wanda aka gina shi da zallar dutse da jan ƙarfe, ɗaki ne wanda ake kai duk wani taƙadarin gagararre a cikin Tayaar
Dakarun da suke gadin ƙofar suka bi su da kallon mamaki,saukowa ta yi daga keken dokin,kai tsaye ta tunkari ƙofar ba tare da ta yi magana ba,babban badakaren ya ƙaraso gabanta ya rissina yana faɗin "Barka da wannan lokaci ya shugaba ta"
Kallonshi ta yi fuska a tamke,kafin ta yi magana cikin izza
"Ina so na yi magana da dakaren da aka kamo a yaƙin Baruda"
Muryarshi har rawa take yi wajen furta "ranki ya daɗe su hamsin da uku ne ai,kuma....."
"Ina nufin Kazuzi,babban badakare a Baruda"
Cirko-cirko dakarun suka yi suna kallonta a matuƙar tsorace,ganin haka ta fusata ta ce"ko ba zan samu damar bane?
Ban isa a buɗe min shi ba?"
Murya na rawa badakaren ya ce cikin girmamawa "ranki ya daɗe akwai haɗari a cikin hakan ne,ki yi min aikin gafara shugaba ta"
Kai tsaye ta ce"ina son a buɗe min shi idan har ina da ikon faɗa a ji a cikin birnin Tayaar"
Ba tare da ya sake magana ba,ya miƙe cikin rawar jiki, suma sauran dakarun suka miƙe,aka buɗe mata ƙofar, ba tare da ta sake kallon ko da sashen da suke ba ta sanya kai a cikin tangamemen ɗakin, kuyanginta suka rufa mata baya,suma dakarun huɗu daga cikinsu suka rufa mata baya,ya rage saura biyu a cikin guda shidan da suke gadinta
A can ƙurya suka hango Kazuzi a zaune,tun daga yadda aka shigar da shi cikin wajen har zuwa yanzu yana nan a zaune kanshi a ƙasa, idanunshi a rufe, abinci da ruwan da aka kai masa ma ko bi ta kansu bai yi ba
Har yanzu damtsenshi,inda marigayi sadauki Waleed ya sare shi yana ɗan zubar da jini,duk da cewar an saka masa magani a raunin
Daga baya kuyangin da dakarun suka tsaya,ita kuma ta ƙarasa gabanshi tana jefa masa wani kallon tsana,kafin ta bushe da wata iriyar dariya,tana dariyar ta ƙarasa gabanshi, ta sanya hannu ta ɗago fuskarshi,ta sanya hannu ta yaye gashinshi fuskarshi ta bayyana
Ya subhanallahi!samun kyakkyawan namiji kamar kazuzi abu ne mai wahala,komai na fuskarshi mai kyau ne da tsaruwa,tamkar wanda ya shiga gasar zana kanshi, gashinshi da ya sauka har gadon baya ya sake ƙawata kyau da sura da Allah ya ba shi,gashi namiji ne mai cikar zati da mazantaka,muradin ƴan mata a wancan lokacin
"KAZUZI!haka sunan yake ko?
Barka da zuwa daular Tayaar,a wasu shekaru baya sunan Kazuzi kaɗai idan mayaƙa suka ji yana kaɗa musu hanjin cikinsu, ballantana karo da shi a filin yaƙi,sau da dama mayaƙa suna yi maka laƙabi da ka fi dodo illa, saboda yadda kake ragargazar maza kana gamawa da su
A haka karambaninka ya kai ka ka kashe min ɗan'uwa na ɗaya tilo da mahaifiyata ta haifa,wanda sanadin hakan ya sa baƙin ciki ya yi silar barinta duniya
A taƙaice dai,ina yi maka kallon makashin mutum biyu, Yarima Nashwaar,wato yayana,da sarauniya Shahida, wato mahaifiyata
Ba sai na cika ka da surutu ba, yadda ka zo masarautar nan a matsayin bawa,na yi maka alƙawarin sai ka amsa hakan,sai na tabbatar maka da lokacin wannan ba lokacin da kake tashe bane,ka san shi tashe lokaci gare shi,kamar yadda naka ya zo kuma ya shuɗe
Sai na tabbatar da ka yi rayuwar ƙasƙanci a cikin masarautar nan,sai na tabbatar da dabba ma ta fi ka ƴanci da gata a cikin Tayaar
Da gimbiyar Tayaar wato HAYAAT kake magana!!!"tana kai wa nan ta saki fuskar tashi ta miƙe cikin takunta na isa da izza ta fice daga ɗakin ranta fes, kuyanginta dakarun suka rufa mata baya
Har suka ƙarasa ficewa daga ɗakin kan Kazuzi yana ƙasa kamar yadda suka zo suka same shi,a karo na farko,tunda ya rasa muradin ranshi ya ji ya kamata ya buɗe idanunshi don sake ganin wannan duniyar da ta yi masa yankan baya a lokacin da bai yi zato ba
Shi dai jarumi,mayaƙi,kuma sadauki KAZUZI IBN MURAAD shine wai aka kawo shi a ɗaure a sarƙa a matsayin bawa,bawan ma na wani birni da ya raina,ya raina jarumansa,duk menene sila?MALLI!
tuna sunan kawai sai da ya ji zuciyarshi ta girgiza,a hankali ya mayar da kanshi ya jinginar yana sauke numfashi da sauri da sauri, menene amfanin rayuwarshi da babu Malli a ciki? meyasa aka kashe masa Malli a gaban idanunshi?shin ta cancanci irin wannan kisan? Wanene silar mutuwar tata?shine
To indai haka ne bai ga amfanin rayuwarshi a matsayin wani mai galihu ba muddin babu Malli a duniya,ya gwammace ya mutu a matsayin ƙasƙantaccen bawa da ya rayu cikin farin ciki amma babu Malli a gefenshi,zai yi fatan waɗannan mutanen su yanke masa hukuncin kisa mafi wuya,ko zai rage masa ciwo da raɗaɗin wannan gangancin da ya yi har ya rasa abun da ruhin shi yake marari a kowanne lokaci na rayuwarsa
Malli ita ce farin cikinshi, walwalar shi, ma'anar rayuwarshi,fitilar rayuwar shi,kuma mahaɗin rayuwarshi,ji yake yi a rayuwarshi zai iya bayar da fansar ranshi akan Malli ɗinshi ta ji rauni duk kanƙantarshi
A yanzu jin shi yake yi a duk duniya babu wanda ya kai shi baƙin ciki,babu wanda ya kai shi shiga tashin hankali,babu wanda ya kai shi asara a rayuwarshi
"Ruhi na!ruhi na kana ji?
Yaushe za mu je ka kamo min irin wannan barewar da ka taɓa kama min kwanakin baya?ina son namanta,yana yi min daɗi sosai, musamman ma idan kai ne ka gasa min da hannunka,sai na ji wani ɗanɗano na musamman ya ƙaru"
A hankali ya mayar da kanshi ya jinginar yana sake lumshe idanunshi, ire-iren shiriritar Malli kenan a duk lokacin da suke cikin nishaɗi
"Ruhi na!
Menene dalilin da ya sa ba ka bar babana ya jagoranci tawagar yaƙi ba?
Ba shine Sarkin yaƙi ba?ko so kake yi wani abu ya samar min kai?"
Murmushi Kazuzi ya yi ya dube ta ya ce"au haka ne?
Wato shi matarshi bata san soyayya ba da zata bar shi ya fara afkawa ba ni ba?"
Ɗan murmushi ta yi tana yatsina fuska,ta zauna a kusa da shi ta ce"ka ga Ni da kai mun kusa aure,ba zai kyautu a ce angon wani abu ya same shi ba,don dai na san ka fi ƙarfin wata runduna wadda ta wanzu a duniya ma, ballantana a wannan nahiyar tamu"
Ɗan murmushi ya yi ya dafa kafaɗarta,ya ce"hakanan Sarkin yaƙi shima,ya girmi dukkan wata runduna,kar ki manta rundunar Baruda shine ya ba mu horo,har zuwa yanzu an rasa wanda zai iya tunkarar mu ya farmake mu,kai ko da ya iya hakan ma ba zai sha ba"ƴar dariya Malli ta yi ta kwanto da kanta gefen kafaɗarshi,ta lumshe idanunta tana murmushi ta ce"Duniya ta,kaine komai na,kaine dukkan buri na da cikar burina,ina matuƙar alfahari da kai"Kazuzi ya yi murmushi ya ce"nima ke ce farin ciki na,abin alfahari na, duniya ta,dukkan wani buri na,hasken rayuwa ta,ke ce komai na,sannan alfahari na"ƴar dariya ta yi ya miƙe tsaye tana karkaɗe ƙasar da ta taɓa mata tufafinta,ya yi ɗan murmushi yana taya ta kaɗewa,ta kama hannunshi,ya miƙe suka wuce cikin gari
Doguwar ajiyar zuciya ya yi saboda tunawa da ya yi wadda yake yin wannan tunanin da ita yana murmushi babu ita a duniyar,a karo na farko tun bayan da ya rasa ta ya iya buɗe baki ya yi magana
"Abin bauta!!!
Wanne laifi na yi da girma?me na aikata ka raba ni da rabin rayuwa ta? meyasa?shin na cancanci hakan ne? menene dalilin hakan?
Na zaɓi zama a matsayin bawa ƙasƙantacce,ko nima a raba ni da numfashi na kamar yadda ka bari aka raba ni da ƙawar zuciya ta"ya ƙarashe maganar cikin wani irin rauni da bai taɓa jin shi ba a tsawon rayuwarsa
💫
"Barka da shigowa ya shugabana!"da kai ya amsawa kuyangar sannan ya ba su iznin ficewa daga sashen da hannunshi,babu musu suka duƙa da girmamawa sannan suka fice daga sashen,ya mayar da kallonshi ga Hayat da ke zaune a bakin gadonta tana bin shi da kallon mamaki ganin yadda ranshi ya yi matuƙar ɓaci
"Barka da shigowa abbana!"ta faɗa tana rissinawa
"Me ya kai ki ɗakin hukunci Hayat?"
A hankali ta ɗago kai tana kallonshi,zata iya cewa rabon da ta ganshi a cikin Irin wannan ɓacin ran ta manta, cikin sanyin murya ta sake rissinawa,ta ce"a yi min afuwa ya shugaba na,na yi wani alƙawari ne,shine na je na cika"
"Amma kin san cewa Kazuzi ya fi haɗari haɗari?kin san cewa Kazuzi ya fi shaiɗan?ya fi sharrin mayaƙan abokan hamayya dubu?
Kin san wanene Kazuzi da kika tunkari inda yake ke kaɗai ba tare da tsoro ba?
Yanzu da ace wani abu ya same ki fa?ko kin yi tunanin ya rissina ne saboda an kamo shi an kawo shi nan a matsayin bawa kawai?"
Hayat ya sauke numfashi, cikin girmamawa ta ce"ina neman afuwa abbana!
Amma tabbas na daukar wa kaina alƙawarin sai na ga ya durƙusa a gaba na,sai na bautar da shi na wulaƙanta rayuwarsa saboda a dalilin shi na rasa duniya ta, ɗan'uwa na magajin Sarautar Tayaar da mahaifiya ta, kana ganin na bar shi ya tafi a banza kenan?
Abby idan na yi haka bana jin na kyautawa ɗan'uwa na"ta ƙarashe hawaye suna zubo mata daga idanunta
Lokaci guda zuciyar sarki Iyaad ta buga sakamakon tuna wannan asarar da ya yi,amma sai ya dake,ya dube ta cikin tausasawa,da Muryar lallashi ya fara faɗin
"Ƴata!
Ki yi haƙuri da rayuwa,ki kasance mai yafiya da tausasawa
Mu masu jihadi ne, waɗanda suke yaƙi don ɗaukaka kalmar Allah,ashe idan haka ne mutuwa rahama ce a gare mu
Raki ne,ko na ce kai ƙarar Allah,ashe a matsayin mu na musulmai sai mun yarda da cewa shahada a wajen yaƙi ita ma nasara ce sannan za mu cim ma nasara?
Ba mu faɗi ba, kamar yadda Allah ya faɗa a Alkur'ani ba mu rasa shahidanmu ba,ciki kuwa har da ɗan'uwanki
Hayat!wannan ba lokacin ɗaukar fansa bane, lokaci ne na godiya ga Allah,zuwa gobe za'a laƙana wa ribatattun yaƙin mu kalmar shahada,muna fatan gaba ɗaya za su musulunta,daga wannan lokacin za muyi musu Barka da shiga musulunci ne,ba fansa za mu ɗauka kamar yadda kika ce ba,in sha Allah"
Sake rissinawa ta yi,cikin girmamawa ta ce "ka gafarce ni abbana!
Tabbas na yi kuskure, don ban san da wannan tsarin da kuka yi ba,nima kamar ku ina farin cikin samun ƙaruwar musulunci,sai dai Abba ina neman afuwarka
Idan bai karɓi addini ba ya kamata a ƙaddamar masa da hukuncin kisa kamar yadda aka yiwa sauran ƴan uwanshi "
Dan murmushi sarki Iyaad ya yi,ya ce"ina fatan ya karɓi addinin ma, ƙaruwar musulunci yana sama da komai"ɗan murmushi ta yi ta ce"haka ne, Allah ya ba ka nasara abbana"
Dafa kanta ya yi yana murmushi ya ce"na bar ki lafiya ƴata"daga haka ya juya ya fice daga ɗakin, kuyanginta da ke tsaye suna jiran fitowar shi suka rissina,sannan suka koma zuwa cikin ɗakin
TSIBIRIN GAYUR,FADAR SARKIN ALJANU
Ƙaton tsauni ne,mai tsawo na tsawon mil biyu, faɗi kuwa ya kai mil huɗu a tangamemen tsibirin na gayur,inda fadar sarkin aljanu yake mulki,wato SARKI LAIMUS
#Nusy_bee
08125952284
🗡️👑 MASARAUTAR KAIZUR 🗡️👑
✍️Nusy bee
❤️ Young talented writers association YOTA ❤️
(Under YOTA'S AMAZING PENS)
Page 4
A kaf nahiyar aljanu shine mai ƙarfin faɗa a ji, saboda tarin dukiya,da tarin mayaƙan aljanu da yake da su
Shine Sarkin musulman aljanu,kuma limaminsu,a duk duniya babu wata masarauta ko daular kafirai da bai yaƙa ya ga bayanta ba,banda ɗaya,wato Daular Baruda
A kowanne lokaci tsawon shekaru ashirin sarki Laimus ya kasa sukuni saboda baƙin ciki da ɗacin zuciyar da yake ciki na rashin nasara,ko cika alƙawarin da ya ɗauka sama da shekaru ɗari da goma baya, shiyasa ya yi duk iya yinshi,amma tasirin sarki Akaal a wancan lokacin ya shafe nashi,duk da kasancewar sarki Akaal mutum,amma manyan matsafan aljanun da yake tare da su daga wasu nahiyoyin na duniya sun shafe jarumtarshi
Wannan kenan!
💫
Shiru fadar ta ɗauka,ana sauraren saƙon da ɗan aiken sarki Laimus,wato Shabbir ya kawo, lokaci guda kuma fadar ta ruɗe da sowar murna da farin ciki,sarki Laimus da annuri ya cika fuskarshi ya dubi Shabbir da fara'a ya ce"Shabbir!
Yanzu kana nufin daular Baruda ta ruguje kenan?babu sarki Akaal a raye?"
Shabbir cikin girmamawa ya ce"haka ne ya shugaba na!"
Sarki Laimus ya ce"Allahu Akbar!to ya batun sarkin yaƙi Anudu da mafarauci Murad?"
Shabbir ya sake rissinawa ya ce"dukkansu sadaukin sarki Iyaad ya shafe labarin su ya shugaba na!"
Kabbara mai ƙarfi ta ratsa fadar,kowa fuskarshi ɗauke da murmushi,sarki ya ce"kuma da gaske ajiyarmu tana cikin garin aminci Daular Tayaar?"
Shabbir ya jinjina kai cike da girmamawa ya ce"haka ne ya shugaba na!
Sai dai akwai wani hanzari ba gudu ba"
Shiru fadar ta yi ana sauraren Shabbir,sarki Laimus ya ce"ina saurarenka amintacce na"
Shabbir ya gyara zama ya ce"a halin yanzu ajiyarmu baya addinin mu kamar yadda muka sani,kuma babu yiyuwar zai koma ɗin, saboda tsanar musulunci da musulmai sune abubuwa mafi girma da ake rainon duk wani ɗa a daular Baruda
Sannan Kamar yadda muka san jinin SUHAIF BIN YASSAR suna da kafiya da tsatstsauran ra'ayi,to shima ajiyarmu yana da wannan gadon"
Murmushi sarki Laimus ya yi,ya dubi Shabbir ya ce"duk wannan mai sauƙi ne,kuma mai wucewa ne
Na san sarki Iyaad sosai,sarki ne mai adalci,kuma a ko'ina aka samu adalci ana samun nasara,don haka mu zuba ido kawai,mu taya shi da addu'a,amma tabbas sarki Iyaad zai ƙarasa abin da ya fara, kamar yadda ya yi abin da ya gagare mu a baya"
"Ina fatan haka ya shugaba na"a cewar Shabbir yana murmushi
*DAULAR TAYAAR*
washe gari ta kama juma'a, Kamar yadda ya zama al'ada a daular Tayaar sarki Iyaad ne yake jagorantar sallar juma'a ta ƙarshen kowanne watan Musulunci idan ya kama,to yau ma haka ne, kasancewar yau ta kama ashirin da bakwai ga watan Safar ya zama shine zai jagoranci sallar juma'ar
Gashi kuma a yau ne za'a laƙanawa ribatattun yaƙin da aka kamo daga daular Baruda kalmar shahada,ga waɗanda suka yi turjiya kuma a ƙarar da rayuwarsu, kamar yadda yake doka a ƙasar ta Tayaar
Kuma a yau ne za'a yi liyafar murna ta wannan gagarumar nasarar da aka samu,irin wadda ba'a taɓa samu ba,asalima babu wata daula da ta taɓa karawa da Baruda ta samu nasara,sai dai ko Baruda ta yi nasara ko a yi kunnen doki
Daidai farkon mukhtarin sallar azahar Sarki Iyaad ya fito don ya jagoranci sallar juma'a,kuma ba tare da ɓata lokaci ba ya hau mumbari don fara huɗubar sallar juma'a
Dakaru ne suka gabato da ribatattun yaƙi zuwa gaban masallatan, waɗanda suka yi ƙasa da kai cikin jin ƙasƙanci
Ba'a ɗauki dogon lokaci ba aka idar da sallar juma'a,daga nan limamin Masallacin ya gudanar da jawabai masu ratsa zuciya,a ƙarshe ya tambayi ribatattun yaƙin shin sun amince da Allah shi ne abin bauta?
Kuma Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama bawanshi ne?
Ba tare da ɓata lokaci ba suka ce sun yarda,take liman ya laƙaba musu kalmar shahada,suka maimaita,take wajen ya ɗauki kabbara mai ƙarfi,bayan an nutsa liman ya cigaba da jawabi
"Kamar yadda na faɗa Allah ɗaya ake bautawa,rana da wata,da kogin Baruda da kuke bautawa dukkansu alama ce ta wanzuwar Ubangijin talikai, ayoyi ne daga ayoyinshi,ya yi su ne don mu ƙara iymani,ba don mu rasa shi ba
Muna yi muku Barka da shigowa Musulunci, Allah ya ƙara mana iymani baki ɗaya,ya ba mu rabo mai albarka"daga nan dakaru suka wuce da su don a koya musu al'amuran musulunci
Daga nan sai babban aiki,wato jin ra'ayin sadauki Kazuzi kan batun addinin Musulunci,wanda tunda aka kawo shi garin Tayaar har zuwa yanzu bai saka ko da ruwa a bakinshi ba,babu wanda zai iya cewa ya ga ko da ƙwayar idanunshi da suka kasance a rufe a kowanne lokaci aka ziyarce shi,mutane da yawa sun ayyana hakan a matsayin borin kunya,duba da cewa ba'a taɓa samun ko da kwatankwacin nasara akansa ba,kai tsaye yake ayyana dakarun da suka tunkare shi don yaƙar shi da sunan mata
Sarkin yaƙi da jama'ar shi ne suka fito da shi daga ɗakin hukunci,har lokacin babu wanda ya yiwa magana,babu wani yunƙuri da ya yi banda abin da aka saka shi ya yi
A gaban sarki Iyaad da limamin babban masallacin daular Tayaar aka gurfanar da shi,kamar koda yaushe kanshi a ƙasa,liman ya dube shi ba tare da wata shakka ko tsoro Ba ya ce
"Sadauki Kazuzi!
Muna yi maka Barka da zuwa daular Tayaar,ɗauka mai cike da adalci da girmama ɗan adam,muna yi maka fatan samun rabo mai girma,a don haka muke yi maka tayin shiga mafificin addini, addinin lumana,addinin zaman lafiya,wato addinin musulunci,menene ra'ayinka akan hakan?"
Shiru ya ziyarci wajen,gaba ɗaya jama'ar da ke wajen suka yi shiru suna jiran jin ra'ayin Kazuzi akan batun da liman ya zo masa da shi,sai dai har bayan shuɗewar wasu daƙiƙu babu alamun zai yi magana,wanda hakan ya kaɗa hanjin wasu daga cikin jama'ar, liman ya sake dubanshi cikin sarewa,amma ya dake ya ce"kai muke saurare Kazuzi!"
Nan ma dai shiru babu amsa, Sarkin yaƙi ya dubi Sarki Iyaad don jin ra'ayinshi,sarki Iyaad ya ɗan girgiza kai ya ce"a sake ba shi lokaci,duk da cewa ba mu san abin da ya saka shi yin shirun ba,amma nan gaba muna fatan ya magantu,kuma mu ji alkhairi daga gare shi
Da haka taron ya watse ran jama'a da yawa babu daɗi,don wasu sun so ya musulunta,wasu kuma sun so an ƙarar da rayuwarshi, cikinsu har da Hayat wadda ta koma cikin turakar ta a fusace,ta kori dukan kuyanginta ,ta fizge lulluɓinta ya jefar,sannan ta haye gadonta tana hargitsa dogon gashinta
Miƙewa ta yi a fusace, ba tare da tunanin komai ba ta fito daga ɗakin, kuyanginta suka rufa mata baya,kai tsaye ta nufi inda keken dokinta yake,ta shiga, kuyanginta suka bi ta,kai tsaye ta nufi ɗakin hukunci
A fusace ta ƙarasa inda dakarun suke,ganin yadda ta zo a fusace suka yi azamar buɗe mata ƙofa ba tare da ta yi magana ba,kai tsaye ta afka ɗakin a tsananin fusace
Yana zaune a inda ya saba zama,sai dai yau saɓanin koyaushe yana zaune a jikin bango Ya jinginar da kanshi, hannayenshi da ƙafafunshi ɗaure da manyan sarƙoƙin da har yanzu ba'a raba shi da su ba,tana zuwa ba tare da tunanin komai ba ta cafki gashin kanshi ta shiga jijjiga kan nashi da ƙarfin tsiya,tana haɗa kan nashi da bangon ɗakin da yake jingine,amma ko buɗe idanun nashi bai yi ba ballantana ya nuna ya san abin da take yi
Sai da ta yi mai isar ta sannan ta hankaɗa shi,kanshi ya sake dukan bango ya bayar da wani sauti,su kansu kuyangin nata da dakarun da suka biyo ta sun tsorata da wannan fusatar tata,ta fara magana a kausashe
"Baka jin magana?
Har yanzu kana jin