wanda ba domin kan titin shal yake babu kowa ba a sakamakon gudun da kowa yayi , da tabbas babu abunda zai hana ya samu tukuicin zagi daga wurin sauran direbobi saboda sam ya gaza yin sauri , zuciyar sa taƙi aminta da ya tafi ya bar ta cikin halin da take ciki , wani sashi na zuciyar na son sanin me ma ya kai ta wannan unguwar wacce take cike da hatsari .?
Gangarawa yayi gefen titin ya tsaya dai-dai lokacin da tunanin abun da zai iya samun ta marar kyau idan har dare yayi mata a wannan unguwar ya gitta masa , da hakan ya sa ba shiri ya karya kan motar ya juya batare da la'akarin ba akan hannun da yakamata ya juya bane .
Wannan shine karo na biyar da take safaa-da-marwaa a bakin babban titin tana mai kwalla kiran sunan falmata , wanda zuwa yanzu da ta kawo tsakiyar hanyar ta ji juya ya fara kwasar ta a sakamakon muguwar yunwa da kishirwa gami da tsantsar sanyin da yake ratsa bargo da kasusuwan ta ta jikin jiƙaƙkun kayan ta da iska ta fara busar da su ,
Ba shiri ta dira guwowin ta duk biyu a ƙasa tare da sake fashewa da wani matsanancin kukan da baya fitowa sosai a sakamakon kwalla kiran da take ya fara dusar da karfin muryar ta .
Kuka take bilhakki tana kiran sunan falmatan a hankali cikin ƙaramar murya ,"
Falmata nyi dan3? ( falmata kina ina ?)
Falmata nyi dan3? ( falmata kina ina ?)
Allahgammama falmata are3 nyi baa maa range3 kindaa dikkin3 baa ," (Dan Allah falmata ki dawo idan babu ke bazan iya rayuwa ba )
Ƙarasa bajewa tayi daɓas a cikin guntun ruwan da yake wajen idanun ta na fara ganin bibbiyu ,
Daf da ita ta bayan ta ya zo yayi birki , kallon ta yayi ya ɗauke kai gami da matsa mata hon ,
Taji ƙarar motar sarai a daf da ita amma bata yi wani alamu na motsawa ba hasalima wani ɗan guntun tunani ne ya gifta mata na ina ma da motar nan zata take ta ta mutu ita ma kamar yadda mahaifin su ya mutu take kuma hasashen mahaifiyar su da sauran kannen ta ciki har da mafi soyuwa a gareta "falmata" duk sun riga sun mutu sun bar ta ," tunanin hakan da tayi ya sa ta sake muskuɗawa ta matsa kan titi sosai yadda zata bawa motar da ta taho damar bi ta kan ta ,"
Wani dogon tsaki ya saki ganin yadda ta rarrafo ta hau kan titi a maimakon ta taso ta zo su tafi kamar yadda yake nufi ,
Balle murfin motar yayi ya fito laɓɓan bakin sa suna furta kalmar "sokuwar banza ƴar kauye ",
Tsayuwa yayi a kan ta ya zuba mata ido yana nazarin ta cikin tantamar samuwar cikakken hankali a gareta , gefe guda na zuciyar sa na yaba kyaun dogayen fararen yatsun kafafu da na hannayen ta da suke zara-zara kuma fasalin yatsun hannayen nata kamar an feƙe fansiri haka suke da ɗan tsini ta saman su , gwanin ɗaukar hankali duk da ɗauɗa da maikon miya da suka bata su .
Tsayuwar sa akan ta bai sa ta ɗago kan ta da ta ɗora bisa hannayen ta dake kan guwaowin ta ba wanda hakan ya bata ɗamar dunkulewa guri guda tana jiran motar tayi awon gaba da ita ,"
Ganin taƙi ɗago kan nata ya sanya ransa sake ɗugunzuma ganin sa tana neman ɓata masa lokaci alhalin shi taimakon ta kawai yake son yi wanda har zuwa yanzu ya rasa dalilin da ya sa yake son taimaka mata ,"
Ke duba bana son wawanci ki taso na mayar da ke sansanin ku tun kafin dare yayi miki anan karnuka su yagalgala ki ,
Hamza ke furta hakan yana yi yana yamutsa fuska tamkar an sanya shi yin maganar a dole ,"
Har illa yau dai yakaka taƙi ɗago kan ta taƙi cewa koh uffan duk da cewa ta gane shi ,a ranta kuwa ta gama yankewa kan ta shawara a dalilin zancen karnai da ta ji ya ambata wanda take taji hanyar mutuwar ta mafi sauki shine kawai ta kwana a nan wurin domin tana da tabbacin idan har tayi ido biyu da karnuka a sulusin dare babu abun da zai hana jijiyoyin da ke kai jini cikin zuciyar ta su tsinke ta mutu nan take ," tunanin hakan ya sa ta sake gyara kwanciyar kan ta ta maida fuskar ta zuwa ɗayan bangaren cikin sallamawa.
Wanda hakan ya bawa hamza damar ganin fuskar ta da jijiyoyin kan ta daga goshin ta da na gefe-gefen idanun ta suka taso raɗa-raɗa koraye shar "kasancewar ta fara sol "
Firgita yayi da ganin ta a haka wanda a take ya fahimci rangwamen lafiya a gare ta kasancewar sa cikakken likita kuma kwararre wanda gwamnatin jaha ta amince da shi har ya zama ɗaya daga cikin likitocin da ke kula da marasa lafiyan dake sansanin ƴan gudun hijira .
Sunkuyawa yayi a gaban ta gami da kai hannu ya taɓa goshin ta ," a ɗan tsorace ta ɗago da idanun ta da suka ƙanƙance gami da sake zurmawa ciki ainahin launin su na zaiba-zaiba kamar gilashi suka bayyana tar ,"
Da sauri ya janye idanun sa daga cikin nata sakamakon ji da yayi kamar akwai wani ɗigo dake sashi cikin wani yanayi tun daga ƙasan ruhin sa a tare da idanun yarinyar .
Ya janye hannun sa tare da miƙewa ya tsaya ,"
Baki da lafiya , ki taso mu tafi na mayar da ke sansanin ku a duba ki a baki magani zaman ki anan hatsari ne ,"
Kin ji koh ?
Jin ta sake yin shiru a karo na biyu ya sa shi shafa sumar kan sa cikin gundura da halin ta ,"gefe guda na ran shi yana mamakin kan sa ta yadda ya damu har yake rarrashin ƴar gudun hijirar da bai san ma daga wanne ƙauye take ba.
Ke idan baza ki tashi ba zan cicciɓe ki koh da bakya so na kai ki saboda hakki na ne na kula da lafiyar ku , ( haka kou ? naga alama 😂 )
Ji da tayi yace zai ɗauke ta ya sa ta miƙewa tsaye batare da ta bari sun sake haɗa ido ba , ta nufi cigaba da tafiya ,
Idan kika sake kika sake taku biyu da waɗannan ramammun siraran kafafun naki zan ɗaga ki sama na jefa ki cikin mota ,"idan ya so ki karye ma ke kika sani doluwa kawai , "dan ma kin samu ina sauke hakki na na taimakon ki da Allah ya ɗora min shine zaki dunga min iskanci da reni ,???
Tare da rashin jin dadi danganta ta da yayi da mai reni ta koma da baya ta tsaya a jikin motar ,' tana mai riƙe kan ta da hannu bibbiyu wanda yake masifar yi mata ciwo tamkar zai faɗo ,"
Da sauri ya buɗe mata murfin motar
Shiga muje ! ?
Tafiyar kurame ita ta biyo bayan gudun da hamza yake shararawa akan titunan da babu wani wadatar motoci , cikin mintuna goma sha biyu ya karaso bakin sansanin nasu ,"
Sauke gilashin motar yayi gami da gaisawa da sojojin da suke gadin sansanin da hakan ya sanya yakaka ɗago kan ta da tun da ta shiga cikin motar yake sunkuye ,"
Karaf ta sauke kwarar idanun ta akan ta tana tsugunne a tsakiya tana fuskantar duk wanda zai shigo sansanin ,"daga inda take tana hango yadda take rawar sanyi da jikakkun kayan jikin ta ,"
Wani irin numfashi ta sauke mai tafe da nishin jin daɗi bata yi wani jinkiri ba ta fara tura murfin kofar da kokarin ɓalla ta ta fita ,'cikin sautin da yake bayyana tsantsar murna da farin cikin ta take jera kiran sunan ƙanwar ta ta ,"
Falmata nah !
Falmata nah !
Mayar da duban sa yayi inda yaga idanun ta suna kallo ,' yamutsa fuska yayi tamakar ya ga kashi ,"domin haushin yakaka da yake ji kaɗan ne akan irin tsanar da yayi wa falmata.
Ke dallah ki nutsu kar ki ballamin murfin mota ," ke da baki da lafiya ina zaki fita da gudu ki je ??
Tun kafin ya rufe baki ta amsa masa cikin siririyar muryar ta da take gauraye da sautin farin cikin da ya gaza boyuwa har akan siririyar fuskar ta da siraran laɓɓan ta suke ɗauke da dariyar da har ya bayyana gajejjerun hakoran ta irin na ƴar uwar ta ,"
Na warke wallahi na warke falmata na ashe ta dawo bata mutu ba ,"bata ɓata ba dan Allah ka buɗe min kofa naje wajen ta wallahi na daina jin kowwane ciwo a jikina .
Shagala yayi wurin sauraran sassanyar muryar ta da koh kaɗan bata tare da hayaniya uwa uba ɗan bakin ta da yake bayyana baki sidik ɗin dasashin ta da ya kawatu kwarai akan farar fuskar ta ,"
Jijjiga kofar tayi da ɗan karfi cikin nuna alamun ƙosawa
Dan Allah ka buɗe min !
Cikin sanyi jiki da sabon yanayin da yake ji yana ratsa kowanne sashi na zuciyar sa ya miƙa hannu a kasalance ya matsa ɗan mubuɗin kofar ta bude , fit ta fita a guje har tana koƙarin faɗuwa ,"
Takun gudun kafafun ta shi ya fara isowa ga kunnuwan ta kafin taji sautin muryar ta ,"
Zuruf ta miƙe tsaye ita ma tana ambaton sunan ta ," tare da nufar inda take jiyo tahowar ta ,"
Kyakyawar runguma suka yi wa juna zuciyoyin su suna masu cika da farin cikin ganin junan su cikin koshin lafiya bayan taraddadi tare da zullumin da kowaccen su ta shiga na tunanin rasa ƴar uwar ta ,"
Hannu bibbiyu yakaka ta tallafo fuskar falmata ," da take dariya
Falmata ya akayi kika dawo ? Waye ya dawo da ke ? Meyasa baki jira ni ba a wurin kamar yadda muka yi yarjejeniya? falmata kin tayar min da hankali dan Allah nan gaba kar ki sake tafiya wani waje mai nisa ki barni ,"
Yakaka nima ba'a son raina na matsa daga gurin da kuka ajiyeni ba , bom ne ya tashi yakaka , duk mutane suka dunga gudu ," kowa yana neman wajen tsira ," na rasa yadda zan yi , inaso naje inda kuke ban san wajen ba kuma bani da ido bare nima na gudu , Allah ne ya taimaka min , wannan mutumin da kuka ajiye ni a gefen rumfar sa shi ya kama hannu na ya kawo ni tasha , da nufin mu nemi ƴan uwa na tun da na gaya masa kuna kurkusa da wajen ya san za ku zo tasha ," sai dai wajen minti talatin babu wanda ya zo daga cikin ku ga gaf ake da fara ruwa , har ya yanke shawarar zai tafi da ni gidan sa , sai naji muryar "Kolo" tana kiran suna na , nayi murna sosai domin a tsorace nake ina ta kuka ,"
Na tambayi kolo ina kuke ke da yagana ta tabbatar min da kuna tare kuma zaku dawo ," sai dai hankali na bai kwanta ba tun da muka dawo na kasa zama ina tsoron kar ku ɓata yakaka ku kasa gane sansanin mu ,"zuciya ta baza ta jure rashin ki ba yakaka ", domin bani da kowa bayan Alllah sai ke yakaka ,"
ta ƙarashe zancen ta tana mai kai hannunwan ta ta ɗaura akan na yakakan da take tallafe da kumatun ta ta zubawa ƴar kewayayyiyar fuskar kanwar ta ta idanu," kamar yadda fararen idanun kanwar ta ta ma suke fes akan fuskar ta tamkar dai tana kallon ta ,"
Murmushi tayi tana mai sake jin yadda zuciyar ta take narkewa da ƙaunar ƙanwar ta ,gefe guda tana sake jin zuciyar ta tana ƙarfi da ɗaukar ƙudirin zamantowa GARKUWA ga falmata ..!!
********
Kai kawo yake yi a gaban gungun zaratan sojojin cikin matsancin bacin rai yake magana da maɗaukakiyar murya ,"
Matsayin mu na jami'an tsaro ba shi ne zai bamu damar cin zarafin Al'umma tare da mayar da rayukan su ba a bakin kome ba ," ba'a bamu kaki da makamai domin naɗa mu jagorancin zalinci ga fararen hula ba ," sai domin mu basu kariya da tsaro tare da kwato musu hakkokin su ," sai dai yadda kuka tafiyar da mutanen ƙaramin ƙauyen da yake tsakanin yankin difa da birnin maiduguri ya sha banban da rantsuwar kare martabar jama'ah da muka yi ," labari ya zo min na yadda kuka ci zarafin mutanen ƙauyen ta hanyar yi musu kisan kiyashi ƙona dukiyoyin su da yi wa matan su fyaɗe dan kawai an sanar da mu akwai ƴan tawayen boko haram daga cikin su , ni a matsayina na shugaban rundunar ku ba haka na tura ku kuyi ba ,"gwamnati ba mutanen ƙasa ta turo mu mu yaka ba face ƴan tawayen boko haram ,
ɗan tsagaitawa yayi yana mayar da numfashi ,"
Wannan ya zama karo na farko kuma na karshe da zaku hau kan mutanen gari da kisa a zuwan kuna yakar ƴan tawayen boko haram .
Jaan kafafu suka yi suka buɗa gami da ƙamewa su sara masa da hakan yake nuni da sun karbi umarnin sa ,"
Shigewa yayi cikin ɗaya daga cikin manyan tantunan da suke kakkafe a sararin faffaɗan filin da yake cikin daji sosai daga gefen birnin na maiduguri .
Zama yayi a bakin ƙatuwar katifar da take yashe cikin tantin gami da kama kan sa da hannu biyu , wani iri yake jin kan nasa yayi masa matuƙar nawi kamar ba nasa ba , ga zuciyar sa da tayi wani irin cunkushewa sam sam ba ya jin sa dai-dai da ya riga ya danganta abubuwan da yake ji da rashin shan abar sa "Burkutu" har na tsawon kwanaki biyu yau ana yinin na uku ,
Miƙewa yayi ya nufi wurin da jakankunan sa ke jibge ya jawo ɗaya daga cikin su gami da buɗe ta sai ga tarin kwalaben giya sumfuri daban daban da yayi guzurin su, ɗaukar ɗaya daga cikin kwalbaben yayi ya riƙe a hannun sa yana jujjuya ta ,"
Kwarai yana da bukatar son ya sha giya sai dai shi sam ba giyar ba turawa yake sha ba , hasalima idan ya shs giyar turawa bikita masa jiki take yayi ta haraswa tare da matsanancin ciwon kai ," giyar gargajiya ta burkutu ita ce abar shan sa .
Mayar da kwalbar giyar yayi cikin sauran ƴan uwan ta gami da rufe jakar yana me miƙewa cikin ransa yana jin ya zama dole ya nemo burkutu duk inda take idan har yana so ya iya cigaba da rayuwa cikin kwanciyar hankali ya kuma gabatar da aikin da ya zo yi cikin nasara , tabbas burkutu ta zama mahaɗin rayuwar sa domin ji yake kamar zai iya rasa ran sa idan ya ƙara wasu awanni bai zubawa cikin sa ruwan zafin burkutun ba ,"
Da sauri ya fita daga tantin yana jin yadda kan sa yake jujjuyawa ," a take sojojin dake da alhakin kula da shi , kama daga tuƙa shi idan zai fita da masu rakiyar sa ,zuwa masu yi masa wanki da girki da sauran aikace aikace duk suka taso ,"
dakatar da su yayi ya kira direban sa kawai tare da yi masa umarnin ya tuƙa sa zuwa cikin birnin maiduguri ," .
Lol 😂😂
Anya ma na kai 3k words ???
Aradu ban kai ba 😂
Well amma ai nayi koƙari koh ??
Alright naga ra'ayoyin ku kuma naji daɗin su sai dai kun sani fah akwai tarin aiyuka akan mu koh ??
Ok zaku cigaba da ji na akai-akai kamar yadda na Alƙwaranta muku insha Allah ,"
Kar ku manta da danna ɗan tauraron nuna yabawa , tare kuma da faɗin ra'ayoyin ku domin bani karfin guiwar cigaba da rubuto muku .
#fikrh
#umm'muaz
[6/24, 10:57 AM] +234 701 013 7848: MAFARI ......
( Hargitsin Rayuwa )
14
umm'muaz
Babban Barikin soja dake tsakiyar birnin maiduguri nan direban youssouf ya dakata ,
Karo na uku biyamuradi youssouf yana yunkurin faɗawa takwaran aikin sa kuma sabon aboki agare shi wanda ya kasance babban sojan nigeria mai matsayi irin na biyamuradi ( colonel ) amma sai ya ji ya kasa , saboda shi da kan sa yana jin kunyar mummunar ɗabi'ar sa duk da cewa kusan hakan ba bakon abu bane wurin su soji , amma yadda yake da kamala da nutsuwa a zahiri ,uwa uba kasantuwar sa ɗan nasaba da akan san su da kyaun tarbiyyah , tashin farko zai yi wuya ayi hasashen yana kurɓar burkutu ,"
Sake ƙutawa yayi a karo na barkatai yana me jin duk ya gundura da hirarrakin da abokin nasa mai suna "colonel nuhu " yake yi masa , ya kai ɗan yatsan sa ɗaya gami da sosa ƙeyar sa .
Taɓo sa nuhu yayi lokacin da ya lura baki ɗaya youssouf ɗin bai bashi amsar hirar da yake yi masa tamkar ma hankalin sa bai tare da shi yayi zurfi cikin tunani .
Abokina yaya dai ?
Meye yake damun ka haka da har ka zurfafa cikin tunani ?
Ɗan ƙaramin tsaki youssouf ɗin yayi kafin ya ce
Bari kawai abokina akwai abun da nake bukata ne ,
Wani shu'umin murmushi nuhu yayi domin shi tun tuni ya harbo jirgin youssouf ɗin duba da yadda duk yake a birkice ga fuskar sa da take bayyana matsanancin halin da yake ciki ," amma dan ya sake tabbatarwa tare da son ya tsokani youssouf ɗin ganin kamar yana son boye masa cikin sa , ba tare da ya san shi da shi dukkanin su ƙwaryar sama da ta ƙasa ne ( duk kanwar jaa ce )
Me kake bukata haka abokina ??
Ɗago kan sa yayi da yake a sunkuye ya wara idanun sa da suka sauya launi zuwa jaa yana jin yadda nawin da ya tokare shi a kirji akan rashin samun kurbar burkutun yana sake ƙaruwa ta yadda yake jin tamkar matse masa jikin sa ake da dukkanin hanyoƴin jinin sa ," cikin wata irin sarƙaƙƙiyar murya yace ,"
Burkutu ," Burkutu zan sha nuhu ,' dan Allah ka taimaka ka kaini inda zan samu burkut da farko , zan yi maka bayani daga baya ,"
Wata shu'umar dariya nuhu ya kwashe da ita ,'
haba abokina ai ba ma sai ka min wani bayani daga baya ba duk su biyun za'a tanadar maka a lokaci guda , kaga daga ka gama kora ruwa sai kuma a faɗa harka ,"
Shi dai biyamuradi youssouf bai ce kome ba hasalima bai kai gano ba cikin kalaman nuhu illah kawai ya ji ya fara samun nutsuwa tun da nuhu ya ce zai samar masa da abun da yake muradi ,"
Direban sa yayi niyyar kira amma sai youssouf ɗin ya dakatar da shi tare da faɗa masa shi yana bukatar sirri ne dan haka so yake su tafi su biyu kawai ', a cikin ran sa yana ƙudurtawa zai sanya ido sosai ya gane hanyar domin duk lokacin da ya bukata kawai ya tafi shi ɗaya ya shaa abar sa ba tare da rakiyar kowa ba , ba kuma tare da kowa ya sani ba. ( mai kowa me kome ya sani kuma yana ganin ka youssouf amm )
Haka suka kama hanya tare nuhu shi ke jaan motar suka keto titi tare da bullowa ta bayan kasuwa suka gangara zuwa cikin unguwar BULABURIN wacce kaf cikin garin anan kaɗai ake iya samun giyar gargajiya gangariya ƴar asali ,"
Suna yin fakin a harabar wurin da ya cika ya tumbatsa da mutane zuwa ababen hawan su sakamakon yamma da tayi ," kiɗa yana tashi ta cikin manyan sifikokin da suke a kusurwa huɗu na zagayen filin ,ga matan banza da shigar fitsara burjik suna kai kawo cikin sigar tafiyar tallata baiwar jikin su , kowacce taci bilicin tare da izgar doki a tume a kan ta yayi tozo kamar na tsohon rakumi ,"
Juyowa nuhu yayi tare da kallon youssouf da ya lura yana ƙarewa matan wurin kallo , cikin yanayin da shi nuhu bai kai ga fahimta ba ,"amma sai ya fassara kallon da na tsantsar zalama da nuna muradi ,"
Abokina duba waɗannan ba irin naka bane waɗannan duk ajawos ne na kananan yara ," daina ma kallon su irin naka suna daga ciki a adane ba kowa ke hayar su ba sai ire-iren mu manyan yara ,"
Yana kammala faɗin hakan bai jira cewar youssouf ɗin ba ya balle murfin motar gami da fita ,
Kutsa nan bulla ta chan suka bullo ainahin wurin da ake sayar da burkutun da mashayan ta suka tabbatar da tafi ta ko'ina inganci a cikin da'irar wajen watau ( burkutun madam saly )
Suna doso wurin youssouf ya shaƙi ƙaƙƙarfan warin burkutun ya lumshe idanu yana sake jin nutsuwa tare da matsuwar ya ji ya kwankwaɗa , dan haka ya sake sauri ,inda suka tadda mutane akan kujeru gaban tebura ,
Ɗaya daga cikin ƴan matan wajen da suke da alhakin rabawar ga masu saya wacce take raƙube a gefe ita ce ta zaburo ta nufo wurin su ,'
Tun da ta nufo su nuhu yake mata kallon sheƙeƙe , saboda sam ba ita yayi zato ba , ba kuma ita ya so gani ba ," budurwar sa ko kuwa ace farkar sa samy baby , yarinyar da take tashe a da'irar ta su ita yake son ganin kamar yadda ta saba taryar sa kaf ƴan matan wurin sun san shi kwastoman samy baby ne ,
saɓanin ta sai yaga wata yagwalgwalalliyar ƴar yarinya tana tahowa gare su hasalima shi tun da yake zuwa rumfar madam saly bai taɓa ganin wannan ƴar ƙwailar ba ,"
Da zuwan yakaka wurin ta ɗan rage tsawo tare da tambayar su kofi nawa zata kawo musu ," ɗauke kai nuhu yayi yana wani hura hanci domin shi gaba ɗaya ma ransa ya gama baci ,"
Biyamuradi youssouf da yayi baya da jikin sa akan kujera tare da yin ƙasa-ƙasa da idon sa tamkar dai yana gudun wani ya gan shi a wurin ",alhalin nan kuwa shauƙin burkutun ne ke kwasar sa da kamshin ta suka haɗu suka samar mishi da mutuwar jiki ," shine ya amsa mata cikin hausar shi ta bamarɗe ,"
" Ki ɓido min mai auki kawai "
Kasaƙe yayaka tayi a tsaye cikin rashin fahimtar abun da ya faɗi ," hasalima hausar da ake yi cikin maiduguri ma da bata da nisa ba gane ta take yi sosai ba bare fa wannan gangariyar hausar sam bata tsinci koh kalma guda ba ,"
Sake rusunawa tayi tana me sake maimaita tambayar da tayi masu cikin gurbatatciyar hausar ta ,"
Wannan karon nuhu ne ya amsa mata a fusace ,'ke dallah cewa aka yi ki kawo dayawa ,"
Sum-sum yakaka ta juya da nufin zuwa ta kawo musu,
'conole youssouf ya bi takun kafafun ta da kallo yana saƙe ƙagauta,"
" dai-dai tahowar samy baby wacce shigowar ta kenan wurin aka yi dace idanun ta suka sauka kan yakaka tana abun da ta ayyana shi a taɗi da gwarzon ta na wannnan wattanni "conole nuhu" wanda a yanzu kaf samarin ta babu kamar shi a kuɗi da shi take tinƙaho ,"
A take wutar kishi ta ruru a ƙarƙashin ran ta ," wata irin bangaza tayi wa kafaɗun yakaka tare da sanya tsinin dogon takalmin kafar ta , ta take mata kan yatsun ta biyu tare da tsayuwa akan yatsun kafar sannan cikin raɗa bayan ta kawo bakin ta kusa da kunnuwan yakakan wacce ta ɗimauce cikin jin azabar takun da samy baby tayi mata tace
," yarinya ki kiyaye wannan ɗan itacen marmari nane zan iya kashe wacce ta shiga gona ta har tayi gigin taɓa ɗan itaciya ta ,'
Duk tsayuwar samy baby akan ƙafar yakaka biyamuradi youssouf yana ankare da hakan saboda idanun sa da suke wurin daman ," ji yayi tausayin wacce aka takewa kafar ya ɗan kama shi wanda tun daga kan kafafun nasu ya fahimci banbancin da ke tsakanin su ,ganin kafar yakakan
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 14 Chapter of 111