sanyin jiki falmata ta kalato murmushi ta ɗora bisa fuskar ta, zuciyar ta na bata cewa Rahima ce wannan take hangowa A hankali tace
"Rahima ni ce fa, ni ce Falmata ƙanwar Yakaka baki gane ni bane ?
Kwarashin hannun Khaalty Rahima ya faɗi ƙasa bata kula ba ta miƙe tsaye ta nufi inda Falmata take , zuciyarta na bata tabbacin cewa mafarki take , wataƙila kuma gizo take yi mata ,
Tana zuwa ta miƙa tafukanta biyu ta dafa kafaɗun Falmata idanunta suna jiran ɓacewar ta daga ganinsu ,
Ƴar dariya Falmata tayi , kafin tace ,
"Rahima kina mamakin gani na ko ? Yakaka ma ai tana zuwa wataƙila gobe zata iso ba tare muka zo ba Rahima....
Hannun Rahima da taji yana tattaɓa mata fuska , yasa ta haɗiye sauran kalmomin ta , ta riƙe hannuwan tana ƙoƙarin sauƙe su daga fuskarta , da wani irin sauti ƙasa-ƙasa , Khaalty Rahima tace
"Falmatana ke ce ? Ke ce wannan Falmata ? Ke ce ? Ina Yakakana ?
Rungumo ta tayi gaba ɗaya zuwa cikin jikinta tana fashewa da kuka mai sauti ...
Assalamu Alaikum masu karatu .
Da fatan duk kuna lafiya ??
Ina mai baku haƙurin ji na shiru da kuka yi wasu hidindumu ne suka sha kaina , da fatan kun min uzuri ? ❤
Nagode .
[12/16/2019, 6:36 AM] +234 706 503 6187: MAFARI
( Hargitsin Rayuwa )
Umm'muaz
45
Da rashin yadda a fuskar Falmata , ta ɓanɓare jikinta daga na khaalty Rahima , Muryar ta na ɗan ƙyarma tace ,
"wacece ? Rahima kece ?
Zuwa lokacin Murmushi Khaalty Rahima take , murmushin da har ya bayyana haƙoranta , sake riƙe hannun Falmata tayi , da sautin muryar ta mai ɗan ƙarfi tace , "Falmatana ni ce Mamar ku , ni ce , ashe kuna raye Falmata , ina Yakaka ?
Da wani irin yanayi Falmata take sake wara idanunta tana ganin dusu-dusun fuskar matar da take gabanta , tana jin wani irin bugu da zuciyarta ta sauya a take da ziyarta ruɗani a tare da ita tace, "Mama na ? Ke ce Maman mu ?
Sai tayi baya da sauri kamar zata gudu , ta waiga dama da hagunta , da wani sauti tace , "Yakaka ina kike ? Kina ina ? Ki zo ki ganta wai wannan Maman mu ce ? Wai da gaske ita ce ?
Murmushin fuskar Khaalty Rahima bai ɗauke ba lokacin da hawayen fuskarta suke cigaba da sauƙa ta matsa tana sake kusantar ta , sai ta miƙa hannu ta jaa hancin Falmata da bai wani ciƙa tsayi ba , ta zarce da riƙe kumatunta duk biyu da hannuwanta , sannan ta haɗa goshin su guri guda , tana sake cewa ,"Ni ce Mamanku Faɗimah-Zahra ni ce Ina Amina ?
Wani irin yanayi ne na zallar Farin-ciki mai tafe da sanyi mai samar da nutsuwa , taji yana bin duk wata jijiyar jikinta , a sanyaye ta karkata kanta , muryarta da rangwamen sauti tace ," Maman mu ke ce ? Ke ce Mama da gaske ba mafarki ko gizo ba ? Mama daman kina Raye ? Mamana .
Bata jira ta amsa mata ba ta zarce da rungumeta ,tana sakin kuka da ƙaramin sauti , irin kukan da Ɗa yake irin sa a lokacin da ya tsinci kansa a gaban Mahaifiyar sa bayan tsawon lokacin da ya ɗauka yana haɗiyar baƙin-ciki cikin kewar ta .
Khaalty Rahima ta sa hannu biyu ta rumgumeta , tana jin wani irin tarin farin-ciki marar misaltuwa , ashe daman rayuwa zata sake iya yi mata sauyi mai tattare da farin-ciki irin wanda ta fidda rai da samun sa , ashe watarana zata zo da zata sake ganin ƴa'ƴan ta ? Allah abin godiya .
Sauƙowar Amnee daga Sama ita ta jaa hankalinta, da mamaki ta ƙaraso tana kallon su , da har zuwa lokaci , Falmata take kwakume da Mamanta bata bar kuka ba , da alamar tambaya a muryarta tace
"Ukhtee Rahima me ya faru ? wacece wannan ?
, jin sautin muryarta yasa Falmata ɗago kanta , kafin ta bi bayan Khaalty Rahima da take riƙe da hannunta , suka ƙarasa gaban Amnee , da murmushi Khaalty Rahima ta haɗa hannun Falmata da na Amnee , tana cewa
" wannan ita ce 'Ya ta Falmata da na baku labarin su ina zaton sun mutu ita da yayar ta mai sunanki Amina da ake mata laƙabi da Yakaka , ikon Allah da girma sai ga shi ya kawo min ita har gabana .
Sai ta waiga ga Falmata , tare da cigaba da cewa , "Fatima ya akayi kika san ina nan ?
Da bayyanuwar murna Amnee ta zarce da rungume Falmata , kafin ta ɗora da cewa , Alhamdulillah , Alhamdulillah , ashe ba haka nan ba na so yaran nan tun a rana ta farko da na fara ganin su , ace 'ya'ya nane , jini na , 'ya'yan 'yar'uwa ta , Ukhtee Rahima ai nasan Fatima da Yakaka tun shekarun baya suke rayuwa tare da 'yan uwansu a gidan nan ba tare da sun san dangantakar su da juna ba , kai Alhamdulillah .
Saman kujerun wajen suka zauna ,suna sanya Falmata a tsakiyar su , khaalty Rahima ta ce ,
"Ikon Allah Ukhtee ashe ma kun san su ? Ashe suna hannun ku ?
" ƙwarai na san su , ai yayan Zainab ( Doctor Hamza ) shine ya kawo su gidan nan a matsayin ƴan gudun Hijira , a gidan nan suke tsawon shekaru kusan biyar zuwa shidda , ikon Allah kenan ai kuwa ko zuwan Yakaka na kwanan nan taje har wajena ta gaishe ni , ai itace wacce kika ji na tambayi Rahima shekaranjiya kan ina take ta shaida min ta tafi Niger wajen Ƙanwar ta da 'yar ta , Allah ya saɓa haɗuwar ku ai da gidan nan zaki tarar da ita .
"Ikon Allah , to Alhamdulillah , Alhamdulillah , sune kalmomin da Khaalty Rahima take faɗi farin-ciki na sake gauraya ta , ji da tayi ashe ma 'ya'yan ta gida suka dawo , ashe ma tare suke da yayun su , ƙarƙashin kulawar mutumin da yake mazaunin Uba a wajenta , Babu shakka tare da dukkanin tsanani akwai sauƙi , kuma ba'a fidda rai daga Rahamar Ubangiji .
A kusan tare suka jefawa Falmata tambaya ,
"Fatima ina Amina da 'yar ta ?
Shiru Falmata tayi da famin raunin cikin ranta , a hankali ta ce da su ,
"Allah ya yiwa Mama rasuwa kwanaki huɗu da suka wuce ,
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'oon, Innalillahi wa inna ilaihi raji'oon," suka haɗa baki wajen cewa , shiru kuma ya gifta tsakanin su cike da jimamin rashin jikar su da basu kai ga samun damar ko da ganin fuskarta ba a zahiri , babu shakka Allah baya barin wani domin wani ya ji daɗi .
" Ina Maisunan Ukhtee ita kuma ? Ba wajen ki ta tafi ba ?
Ƙhaalty Rahima ta sake tambayar Falmata ,
Shiru Falmata tayi tana sunkuyar da kanta ,
Wani busasshen yawu Khaalty Rahima ta haɗiye tana jin tashin hankalin da yake farmata , kada dai ace wani mummunan lamari ne ya afku ga ɗiyar ta mafi soyuwa gareta ?
Matsa hannun Falmata dake cikin nata tayi da ɗan ƙarfi , ta ɗan ɗaga sauti tana sake maimaita tambayar " Falmata ina kika baro Yakaka ??
***
A Niamey tunda Yakaka ta dawo daga tasha , bayan samun tabbacin Falmata ta riga ta tafi Nigeria ta wannan mummunar hanyar mai cike da hatsarin ƴan kungiyar Boko Haram ,
bayan kuka babu abunda take yi , gabadaya ta ɗora laifin gudun Falmata akanta , tayi danasanin zuwanta ƙasar baki ɗaya yafi a ƙirga , ganinta da ace bata zo ba da Falmata bata gudu ba , sai ta ji inama da ta zauna akan batun Youssouf da yace su rufa asirin tsakanin su kada Falmata ta sani a tun farko , ƙila da suna da damar da zasu haɗu ita da Youssouf su wanke kansu a wajen Falmata bayan sun ƙaryata ƴan uwansa a gabanta , da kuma lamarin bai kwaɓe ya haka ba ,
Ganin kuka ba zai mata magani ba yasa ta miƙe tsaye ɗauke da jakar kayanta , Hajja wacce take zaune zugum ta dube ta tare da cewa ,
"Babba uwar Mama ke kuma ina za ki ? Kadda kice min kema gudun fanfalaƙin za kiyi ? Kiyi wa Allah ƴar nan ki tsaya mu ji da damuwa ɗaya kadda ki ɓaro mana wata sabuwa , guje-gujen nan ba kana bane , 'ya'yan nan ai ƙwarya ta gari tana ragaya , kamar yadda darajar ɗiya mace ɗakin Mijinta kar ki tafi ko'ina Dan Allah ,
Ba tare da Yakaka ta dubi Hajja ba tana share hawayenta da gefen hijabinta tace ,
"Hajja gara na tafi saboda Falmata fa ko da taje Maiduguri lafiya , bata fa san hanyar gidan Baa prof ba, kuma bata san kowa ba a garin bayan shi , dole zanyi hanzarin tafiya nima ko Allah zai sa na haɗu da ita a tasha , na tarye ta Hajja ina ƙaunar Falmata ita ce kaɗai jinina a duniya ina tsoron rasa ta Hajja , zan tafi bazan iya zama ba nima .
Guntuwar ƙwallar da ta tarawa Hajja a ido ta sa hannu biyu ta shafe fuskarta ta muttsuƙe ,
" To Shikenan Yakaka tunda kin ce haka bari nima na haɗa ƴan kananun kayan buƙatu na mu tafi tare , ai nima zama bai ganni ba , to na zauna nayi me ƴar nan ? Ai tunda ganga ta fashe sai ƴan rawa su watse ,
Da hanzari Hajja ta shiga harhaɗa kayanta, tana cewa ,
"bari na tafi da waɗanda dole zan iya buƙatar su , sauran kuma idan Allah ya min dawowa na cigaba da Amfani da abuna idan kuwa ma tafiyar kenan , to a biyo ni da tsunmokara na , wannan lamari dai da ɗaure kai yake babu shakka da walakin wai goro a miya .
Yakaka da har lokacin a tsaye take akan ƙafafunta bata ce da ita ƙala ba ,
Cikin ƴan mintoci kaɗan ta haɗe kayanta a cikin wata babbar jakar matafiya da Youssouf ya taɓa saya mata , tana shirin yafa mayafinta suka tsinkayo sallamar Youssouf daga ƙofar falon , Hajja ta amsa tana nufar falon
A tsaye ta tarar da shi shirye tsaf cikin riga da wondo na kaftani da ya sha aiki irin na saraki , ba tare da ya yadda Hajja ta ga ƙwarar idanunsa ba fuskarsa babu walwala ko kaɗan sai tarin damuwa da tashin hankali da suka bayyana kansu ɓaro-ɓaro , cikin Amonsa da a yau ya sake kaurara da buɗuwa yace
"Hajja ni zan tai Maraɗi yanzou Hajiya Umma tai ƙirana , don Allah ku zauna a gida har na kai ga dawowa nan da kwanaki biyu , lamarin Fatima kouwa zan yi dukkanin ƙoƙarina da Yardar Allah babu abunda zai samu Matata da abinda ke cikin ta .
Ɗan karkata kai Hajja tayi da sigar tausayawa tace ,
" Babban soja Allah ya tsare hanya , sai dai kuma yanzu na gama fama da ita yayar Falmata kan cewa da tayi a yanzu itama za ɗau hanyar Nigeria saboda ko Allah zai sa su gamu da ƴar uwarta a tasha idan sun isa Maidugurin dan ita Maiɗakin naka ai kasan bata san ko'ina ba a can ko gidan shi mariƙin nasu bata sani ba , ana gudun kar ta ɓata ko ta shiga wani mawuyacin hali kuma a can , da naji haka sai nace to fa nima zama bai kamani ba tare zamu tafi , to kaga shirin nan da nayi ma na tafiyar ne ga kayana ma can na haɗa su gu ɗaya .
Bayan ya gama sauraron Hajja da tayi shiru tana tsumayen iznin sa , sai yace ,
" hakka ma shawarace mai kyaou Hajja , to idan hakka ne ku taho na sauƙe ku ga tasha na sanya kou a mota , nima sai na tai gida ,
"Amma Hajja doumin Allah dagga kun cimma gida kun tadda Fatima ki sanar min ta téléphone , sabadda na san halin da kuke ciki a can , duk da nima ba da jimmawa ba zan tai can Nigeria ɗin , kuma a nan sojin mu zasu yi bakin ƙoƙari wajen duba hanyar da ita Fatima zasu bi , sai dai kouma idan har ta ɓarauniyar hanya ta daban zasu ɓulla yanzou fatan mu dai yana ga Fatima ta cimma gida lahia .
" to babu laifi Babban soja ai sai mu tafi ɗin , Allah dai ya sassauta wannan lamari , bari na ƙira ita Yakaka ,
Mota ɗaya suka tarar wacce zata tafi Kano kai tsaye daga Niamey dan haka Youssouf ya biya musu gidan baya na motar su biyu rak da daman mutum ɗaya suka tarar a gaban motar dan haka nan take aka shiga neman direba ya zo kuɗin kujerun mota sun kammala ,
Laluba aljihunsa yayi ya fiddo kuɗaɗen ciki da baki ɗaya CFA ne , mayar da su aljihunsa yayi saboda sanin da yayi daga sun bar shiyar ƙasar su ba zasu musu wani amfani na sosai ba , ya zaro wallet ɗin sa da dalolin Amurka ke ciki a miƙe , ya matsa kusa da gilashin motar da yake sauƙe ta sashin da Yakaka take ,
Ba tare da ya dubi fuskar ta ba yake miƙa mata kuɗin da bai riga ya ƙirga ya san adadinsu ba ,
Yakaka wacce tunda ta shiga motar ta ɗauke kai daga barin kallon sashin da yake tsaye , amma tana ankare da shi ta kuma ga tsayuwar sa akanta yana miƙa mata ƙudi , bata son sake kallon fuskarsa ne dan haka taƙi ɗago kanta ,
Hajja wacce take raba ganinta a tsakanin su biyun , ta ɗan zunguri Yakaka ,
"Babba uwar Mama , Babban soja yana baki saƙo ,
Da wani irin yanayi na gargaɗi a fuskarta ta kafe Hajja da idanunta da suke da kaifin kallo masu kamar gilashi ,
Galala Hajja tayi tana mayar mata da martanin kallonta , sai kuma ta muskuɗa ,tana cewa
"Ajabba inji kanurai, o ni hauwa'u ,
sai kawai ta maida ganinta can gefe tana kyeɓe baki .
A hankali Youssouf ya zura hannunsa kaɗan ta cikin motar ya sauƙe mata kuɗaɗen akan cinyarta yana cewa "Hajja Allah shi kiyaye muku hanya don Allah Hajja duk yadda lamari ya kassance muku ki jisheni ,
" Amin Amin Babban soja , da yardar Allah zan sanar da kai duk yadda ake ciki , kaima kuma Allah ya tsare maka hanya , mungode , mungode sosai Allah shi yiwa rayuwa Albarka .
"Amin Hajja nima nagoude , yace yana kama hanyar barin wajen ,
Yakaka wacce tunda ya ajiye mata ƙuɗin ta runtse idanunta tana tuno da lokaci na farko a haɗuwarsu , yadda ya ajiye mata kuɗin da ya sayi martabarta da su akan cinyarta ya haka ,
Hannunta ta kai tana ture kuɗin da ya ajiye mata a yau zuciyarta cike take da rauni mai tarin yawa , sanin da tayi a yanzu Youssouf ya haramta a gareta , ta kuma Haramtawa kanta shi koda kuwa babu ran Falmata .
Tashin ƙugin motar su yazo dai-dai da sauƙar hawaye a idanunta , haƙiƙa so gaskiya ne , so halitta ce da Allah yake sarƙawa a tsakanin zuciyoyin bayin sa domin ya samar da Salama a tsakanin ƴan Adam , yafiya , haƙuri tare da tsusayawa tafe suke a cikin so na domin Allah ,
Babu shakka Youssouf shine mutum ɗaya da Allah ya ɗarsa mata son shi tun bata san menene so da kansa ba , ta kuma so shi ba domin kome da ya mallaka ko ya taɓa mallaka mata ba , cikin rashin sanin ta jarrabawa ce Allah yayi mata kan soyayyar sa ,
Tun ranar da ta san laifin da Youssouf yayi mata kan Yaudarar ta da yayi ya ɓata mata rayuwa bata taɓa jin tsanar sa tsana irin ta ƙiyayayya ba , sai dai ta ji tsanar shi bisa ga laifin da tasan ya aikata mata, take kuma neman yadda zata yi ta hukunta shi domin ta goge wannan tsanar da tayi masa a dalilin laifin sa ,
Dawowa da tayi ta tarar ya auri Falmata , ya rugurguza mata zuciya , lamarin ya girgiza ta fiye da duk wani abu da ta taɓa cin karo da shi cikin rayuwarta ,
Tashin hankalin da ta hango tare da Youssouf lokacin da tayi tattaki ta same shi take masa togaciyar ya saki Falmata , tare da tirjiyar da yayi mata sun shaida tare da bata tabbacin cewa Youssouf yana son Falmata , so kuma mai tarin yawa , abunda ya kassara mata duk wani karsashin ta , ya kuma ƙara mata hau-hawar ɓacin rai ,zuciyar ta ta shiga tuhumar ta kan yaya zai yi mata haka ?
Rana ta farko da ta san da tabbatuwar cikin jikin Falmata sai ta ji ta tsani kanta tana kuma tir da zuciyarta da ta gagara yakice shi baki ɗaya daga cikinta , alhalin tuntuni ya zama mallakin ƙanwar ta ,
A yau saƙo-da-lungu take bi tana zaƙulo duk wani ɓurɓushi na son sa tana zarewa daga cikin ranta , duk wani gurgun tunani ko hasashen da ta dunga yi a baya na zasu dawo suyi rayuwa tare da ita da shi da ɗiyar su har ma su haifi wasu ƴa'ƴan , yana zagwanyewa tare da gogewa daga cikin ƙwaƙwalwarta , ta rabu da Youssouf da sunan so kamar yadda Allah ya rabata da Mama ,
Youssouf ba nata bane , ya taɓa zama nata ne kaɗai akan shimfiɗar da shaitan ya shimfiɗa musu .
Youssouf na Falmata ne tare da ƴa'ƴan da zasu haifa nan gaba da kuma sauran matansa ,
Takurewa tayi a jikin ƙofar motar tamkar zata tsaga ta koma ciki saboda wani irin zogi da zuciyarta ke yi , babu shakka cikin sadauƙarwar soyayya ta gaskiya akwai ciwo mai tsanani .
***
Ya juya tare da tarin tausayinta cikin ransa , yaso ko da sau ɗaya ta bashi dama ya nemi yafiyar ta bisa ga laifin da shi yasan ya aikata mata , har abada ita ai uwa ce ga ɗiyar sa mafi soyuwa a gare shi , bai so ba suka sake yin rabuwa makamanciyar ta farko ,
A shekaru da girma gami da hankali nashi irin na cikakken Namiji , ba sai ita ko wani ya taɓa faɗa masa cewa tana son shi ba so kuwa mai tarin yawa da shi yake iya hango shi a kwance cikin idanunta ɓaro-ɓaro koyaushe ta dube shi ,
Sai dai shi da ita dukkanin su sun faɗa ne ga jarabawar rayuwa , kuma shi bai mata so irin na auratayya ko kaɗan , sai dai yana tausayawa mata sanin yadda ciwon so yake ,ga wanda duk Allah ya jarabta .
gefe guda kuma yana jinjina Yakanah irin tata da bata taɓa furta masa kalmar so a gaban sa ba ko sau ɗaya , ta kuma yi ƙoƙarin dannewa ta ɓoye hatta ga shi kansa bata yadda cikin saninta ta nuna abunda ke binne cikin ranta ba , bare kuma ga ƙaunarta da yasan abadan baza ta taɓa bari ta fahimata , daga ƙasan ransa ya furta "Madallah da ƙarƙƙarfar kyakkyawar zuciyar da take iya danne tasirin So , ƙwarai ita ɗin ai jaruma ce . "
Ƙarfe uku na ranar ta yi masa a cikin Masarautar su inda ya tafi kai tsaye ga fada ya kai gaisuwa gurin Maimartaba wanda ya amsa masa fuskarsa ba yabo babu fallasa , sai dai saɓanin baya da idan har ya shigo fada ƙirarin da manyan fadawa da kansu ke yi masa har ya tashi , yau dai shiru babu wanda ya kambama shi da ƙirarin sai fa dogarai da suke tsaye daga bakin-fada .
Shiru yayi kansa a sunkui yana jiran Maimartaba yayi masa umarnin dawowa daga gefensa kusa kamar yadda ya saba a koyaushe , sai dai har ya kusan mintoci ishirin a zaune maimartaba bai sake duban sa ba , dan haka ya miƙe yana mai sallama da Maimartaba da sauran jama'a da suka amsa a sama-sama ,
Idanunsa suka kai inda yake mazauninsa ada kusa da ƙafafun Maimartaba , karaf suka haɗa ido da Mammadou da yake zaune a gurbin sa , wanda yake jifan sa da wani ɗan guntun murmushin ƙeta , ɗauke kansa yana ƙarasa barin Fadar .
A sanyaye ya taka yana yana nufar ciki sashin Hajiya Umma , a hanya babu abunda ya sauya na yadda bayu ke zubewa gaishe sa , sai dai yana lure da wani irin kallo da wasun su ke binsa da shi wasu kuma yana iya jiyo ƙus-ƙus ɗin su daga ya gota .
Ita ɗaya ya tarar da ita a falonta na ƙurya da yawanci sai zata yi ganawa ta sirri take shigarsa ,
Zama yayi a gabanta yana mai sunkui da kai cike da ladabin da yake halayyar sa ya gaishe ta , muryarta babu amo sosai ta amsa gaisuwar sa ,
Shiru ya ɗan gitta kafin da murya mai kaushi tace da shi ,
" Ina kouma itta ɗiyar da kake amren ?
Shiru yayi kaɗan kafin ya ce
" sun tai ga ƙasar su baki ɗaya ,
Sake tsare shi da ido tayi , duk kuwa da ta ɗan yi farin-ciki da cewa da yayi "sun koma ƙasar su , sai ta ɗora da cewa " ka sau amren ta ko kuwa ?
Shiru yayi cikin fargaba , yana tsoron kadda ta tilasta shi ya saki Fatima , wani sashi na zuciyar sa ya ji yana gargaɗin sa daga sake yin ƙarya ,
wani busasshen yawu ya haɗiye , ya ɗago da kansa ya dube ta , a hankali ya mayar da kansa ƙasa kafin yace ,
"Ban sau amrenta ba sun tai gida ne kafin al'amura su dai-daita anan ,
"Youssouf ,
Hajiya Umma ta ƙira sunan sa , a tsorace ya amsa "Na'am Umma , zuciyarsa tana mai tsananta bugu yauce rana ta farko a iyakacin sanin sa da ta taɓa ƙiran sunan sa kai tsaye .
" na maka oumarni ka sau amren ɗiyar nan ka aika mata da shikan ta can zouwa ga ƙasar su , muddin kana ƙamnar da na yafe ma kouma Mahaifinka shi maka afouwa , idan kouwa ka ƙi bin umarni na Youssoufa , shiru tayi bata ƙarasa ba ,
sai dai ya fahimcin munin abunda ka iya biyo baya ganin yadda ɓacin rai ya ƙara hauhawa a kan fuskar ta bayan ta kawar da kai daga barin duban sa ,
Gumi ne ya shiga keto masa kota'ina cikin jikin sa , ya sanya hannun sa yana share zufar goshinsa ,
Muryarsa can ciki yace , " Na amshi oumarnin ki Umma, ki yafe min bissa ga kuskuren da na aikata .
Muryar ta da ɗan sassauci tace , " Laifin ka ga Allah kayi ka nemi Yafiyar sa , doumin shi mai yawan afouwa ne ga bayinsa , sannan ka kyautata tuban ka , ni kam abou ɗai nake so kayi shine sakin auren ɗiyar nan idan kayi hakka shikenan .
Shiru yayi baice kome ba , saboda zallar tashin hankalin da yake ciki , duk wata ƙafa ta isar da saƙo a jikinsa jinya take da amsar umarnin Hajiya Umma .
Ganin yadda ya zamto tamkar wanda aka zarewa lakka a gabanta yasa tayi gyaran murya tana mai ƙarfafa zuciyarta daga tausayi irin na tsakanin ɗa da mahaifiya daya soma mamayarta , musamman kasancewarsa mafi soyuwa a gareta cikin 'ya'ya ,
" ka tashi ka tai ga matanka bayan ka tanadi kyawawan kalmomin da za ka yi amfani da su wajen tausasa zuciyar su doumin laifin ka mai nawi ne a wajen su .
Kamar jira yake tace ya
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 81 Chapter of 111