zan shawo kan ta
ta hakura ta aure ni". Mallam ya dube shi kawai domin ya san
zafin radadin irin wannan kaunar a zuciyar namiji, ya ce, "ba
komi, komi na Allah ne."
Ko da Yusuf ya koma Abuja bai da wani kuzari balle
tunanin kirki duk Hadiza ta gama rikirkitar masa da komi da ya
mallaka, ya yi ma Basiru kaninsa waya yace ya je maza
Malunfashi ya zo masa da Saminu yana son magana da shi. Nan
da nan Saminu ya zo ko babu komi Saminu cikin kudi ya ke
domin a ranar da Yusuf ya je dubu biyar cif ya danna masa.
Bayan sun gaisa ya ce, "Saminu ina ka ke jin Hadiza ta ke a halin
20
yanzu?" Saminu ya ce, "'Tana Kaduna yaya, ai ta koma aiki".
Yusuf ya ce, "Kana da wayar gidansu da ofis?" Ya ce 'E' ya
bashi har da ta Jos domin ya ce, Hadiza Jos ta haihu karshe za
ta je Jos. Ya yi mashi kwatancen gidansu na Kaduna.
Suna aje waya ya latsa wayar gidan Yaya Garba, wani
yaro ya dauka yana jin an ce Hadiza a ke son magana da ita sai
ya ce mata, "Anti Hadiza ga Baba Amiru". Ta je da saurí ta dauki
waya ta ce, "Na yi hushi angona, haka mu ka yi da kai saboda
Allah Amiru?" Yadda Hadiza ta rausayar da murya ta tsumar da
Yusuf amma a lokaci guda kishi ya dirar masa wai Haidizansa ke
ma Amiru magana mai dadi irin wannan? Kamar ya aje amma
kuma bai iyawa, ya ce, "Ba Amiru ba ne, Yusuf ne. Kina lafiya?"
Ta ja tsaki ta aje wayar.
Hadiza na sauraron aiken Amiru ne domin ya yi mata
alkawarin turo direba zai kai ta wajen taron sunan Hadizan Jos,
to amma shiru a zaton ta shi ne ya yo waya ta dauka da niyyar
ta yi masa tsiya sai ta ji Yusuf, to bayan ta dawo ta zauna sai
kuma Amirun ya yo wayar ya na bata hakuri akan ta yi hakuri
tafiya sai gobe, domin ya samu ya kammala `yan hidimomin
gabansa ne don haka shi ne zai kai ta ba direba ba.
Yusuf ya je ofis a washegari, ya rinka duba fayal-fayal
don ganin irin ayyukan da ke gabansu, a kalla akwai zuwa Legos
don shigar da wasu takardun kwangila da aka ba kanfaninsu na
sa wutar lantarki a garin Zariya, haka nan akwai zirga-zirgar
zuwa Kaduna kamar sau biyu a satin nan shi ma ana bukatar
kula da kwangilar hanyoyin da kanfanin su ke yi, akwai son akai
ma gwamnan jihar Kaduna wasu takardu don sa hannu suma na
sabon shigar aiki ne.
Yusuf ya ja birki daga nan ya ce, "Yauwa". Maganar zuwа Kadunan nan ita tafi damunsa domin wata dama ce da zai samu
ta kusantar Hadiza ba tare da aikinsa ya raunana ba, ya mike ya
nufi ofis din Shugaban kanfanin, ya gayas da shi bayan ya yi sallama. Yusuf ya shiga nuna mai mahimmancin kasancewarsa
a Kaduna na tsawon lokaci don ya samu ya gudanar da wa`annan
ayyukan da suka taso. Shugaba ya duba a tsanake sannan ya ce,
"A lalle kam, bayan wannan ma akwai wata takarda da ta iso a
21
daga Kaduna za` a zauna mitin da gidan gwamnatin da
kamfaninmu a sati mai zuwa don haka ina ganin kai ya dace ka
wakilci kamfaninmu, saboda haka duk sauran maganar shiryeshiryen maganar kudaden tafiya sai ka sami Yakubu
akawuntanmu sai in ce sai mun ji waya ko kuma ince sai Allah
ya dawo da kai lafiya". Yusuf ya ce, "zan yo wayar domin ta
yiwu wani abun ya taso daga baya."
Ya isa gida ya yi sallama da su Falanke ya kara jaddada
ma Falanke cewa kada a kara barin wata 'yar iska ta shigo mai
gida. Falanke ya ce, "Haba Yallabai tun yaushe wannan ta
kwaranye mu dai addu'ar mu Allah Ya bamu Hadiza a matsayin
matar sunna". Yusuf aka yi murrmushi aka сe "To Amin, mun
tafi farautar aure sai mun dawo."
A gidan Baba Garba babu kowa daga Hadiza sai mai aiki
sai ko mai gadi yana can bakin get. Hadiza ta ci kwalliya amma
a saukake kwalliyar matafiyi yadda ba zata wahala ba, jefi-jefi
ta kan dan dubi agogon hannunta ta na zargin Amiru da son ya ja
masu tafiyar dare.
Yusuf ya isa gidan Baba Garba ya rubuta ma Hadiza wasu
"yan maganganu na rokon arzikin son ya ganta, maigadi ya kai
mata wasika har gabanta ya fadi a zaton ta ko Amiru ne ya kara
aikowa yana bada hakuri, to sai tagaYusuf ya rubuto ta ja tsaki
ta tsaida maigadi ta rubuta masa amsa kamar haka
Yusuf
Ni Hadiza yanzu na manyanta a halin yanzu a gani na
kuma wannan zamani na da zan sarrafa al'amurana na zabin
aurena saboda haka ya dace na auri mutumin da bana so?
Maigadi ya mika ma Yusuf takarda wani daci ya daki
zuciyar sa, wai shi ko maye ne bai kyale yarinyar nan ne? Tabbbas
ya san ya yi nacin son Fa'iza to amma itå Fa'iza bata nuna masa
masifar kiyayya irin haka; nan da nan idanunsa suka yi jajur ya
rinka ganin duhu har shi maigadin, yayin da ita kuma Hadiza
tana can tsaye gindin taga tana kallon irin halin da Yusuf ya
shiga da ta ga ya shiga motarsa ta saki labulen ta dan rintse
22
idonta ta ja tsaki ta ce,`shit kawai'. Ta kwanta bisa gado ta
rinka tuno irin son da ta nuna masa a da anan ma ta kara tsanarsa.
Yusuf na kokarin fidda motarsa daga gidan Baba Garba
yayin da Amiru ke kokarin cinna tasa motar ciki, suka rinka huci
na jirı zafin dayansu yayin da shi Amiru na jin zafin me ke kawo
shi wajen Hadiza idan ba yana samun fuskar Hadizan ba ne?
Yayin da shi Yusuf yana jin zafin wai kan wannan Hadiza ke
muzanta shi? Tunda Hadiza ta shiga motar Amiru taga canjecanje da dama, ranta ya bata ganin da yai ma Yusuf ne, don
haka itama sai ta share shi ta daure ta ta fuskar.
Sun sami kimanin tafiyar awa daya da rabi, kafin Amiru
ya dan juyo ya dubi Hadiza ya ce, "yaya kina son wani abu mu
tsaya nan garin?" Hadiza kanta a sunkuye ta yi tagumi bata
tsinka masa ba sai akwai ta girgiza kanta nuna alamuna'a, ta
kara takurewa jikin taga, to anan ne kuma abinda rai ke so sai
Amiru ya dan rikice ya yi yakace dama bai bullo ma Hadiza da
hushi ba, ai fa sai ya shiga rarrashi, na tsawon lokaci amma bai
shawo kan Hadiza ba.
Amiru ya ce, "Amma a gaskiya Hadiza kin bani mamaki
ca nike idan duniya da gaskiya nine da hushi, ki duba tsakanina
da Yusuf? Amma kin hada mu kina gara mu kamar wasu 'yan
yara, ai ni a zato na bai kamata ki rinka sauraron kowa ba, bama
Yusuf kadai ba, haba Hadiza dlarajar da Allah ya yi wa mahaifinki
kin fi karfin haka ya kamata ace duk wata hulda da wani namiji
kin jingine ta."
Hadiza ta ce, "zaka iya rantsewa akan yau Yusuf ya gan
ni?" Amiru duk nauyin Hadiza ya lullube shi ta kara cewa "ka
tabbatas tunda na tsayar da zancenka na sake kula wani da
namiji? Duk shirmen Yusuf me ka ji ance nayi nuna alamun zubar
da mutuncina? Dan Allah Amiru idan za'a zarge mu a rinka jiran
ana kama mu dumu-dumu amma ban da zargi, domin ni dai
ma'aikaciya ce idan mun fara samun irin haka kaga ba karamar
matsala zargi zai haifar mana ba a rayiwar aurenmu.
Amiru ya ce, "To don Allah wannan ta shige haka nan,
23
wallahi sanin halin Yusuf na yi shegen mutum ne, duk abinda ya
kallafa rai yana so sai yaga bayan sa. Hadiza ta juyo ta dubi
Amiru ta ce, "Ba dai komi ba me ya hana shi auren wadda ya
mutu yana ciwon so Fa'iza?" Amiru ya ce, " ai lokacin da shirmen
kuriciya bai kai munzalin da dabararsa zata mallaka masa komi
ba". Hadiza ta ce, "gaskiya ban yadda da kai ba anan ai idan
mutum jarumin namiji ne ya dace ace da kuriciyarsa ya nuna
kwazo ya amshe ma wa'anda suka fi shi mata."
Amiru ya janye hannunsa daya daga kan sitiyarin mota ya
shafa kansa ya ce, "Ai shi kuma aure ba haka ba ne Hadiza na
Allah ne yadda duk ba ki tsammani haka yake faruwa, yanzu ba
gashi da can da Yusuf zaku yi aure amma Allah bai yi ba, a
wancan zamani babu irin lallashin da ban yi masa ba akan kada
ya kyale ki amma ya ki, cikin ikon Allah sai gashi Allah ya hada
mu zamu yi aure."
Hadiza ta shayar da Amiru mamaki ta ce, "tsakaninka da
Allah idan ka ganni a zamanin da Yusuf ya ki aure na zaka iya
aure na?" Amiru ya ce, "menene na wannan tambayar?" Ta ce,
"haka dai na tambaya don Allah fada mani?" Ya ce, "sanin gaibu
sai Allah! Suka yi shiru cikin motar kowanne da tunaninsa, tabbas
Amiru ya tuna hotunan Hadiza tana 'yar shekara shabiyar wanda
Yusuf ya taba nuna masa ko kusa bai taba tsammanin za`a sami
sambaleliyar mace ba kamar wannan.
Da yamma likis suka isa gidan Baba Rilwan gida kam ya
fara cika da`yan suna na murnar diyar da Hadizan Jos ta haifa
gobe ta ke suna.
Amiru ya ce, "To Hadiza ki gayas man da maijegon sai na
zo da yamma ni zani in nemi masaukin kwana. Ta ce, "To sannu
o, Allah huta gajiya". Ya dube ta su kai murmushi, abinda ya fi
damun Amiru shi ne Hadiza sai kodewa ta ke yi ta rame ta yi fari
fat abinda da ya dauka rasuwar mahaifinta ne, to amma ya
san matsalolin Hadiza sun fi karfin kidaya sai du'ae kawai.
Ranar suna aka radawa jaririya sunan Mama Binta wato
Fatima. To Hadiza ta sami kanta cikin rashin hutu ranar suna Ja
24
washegarin suna domin duk kawayensu ita ke kula da su haka
nan Dr Sani ya dora mata nauyin yawancin hidimomin sa da kula
da jama'arsa. Saboda haka ma ko da Amiru ya zo ranar suna a
tsaitsaye ya ga Hadiza da mai jego amma sun karrama shi ta
fannin abincin suna da kayan kwalan na suna, su kai sallama ya
ce zai tafi Lagos sai kuma bayan sati biyu su hadu a Kaduna.
Kashegarin suna Hadiza ta shiga kintsa ma mai jego
kayanta da ta samu suna kara tantancewa. Maijego ta roki
Hadiza don Allah ta kara kwana kafin ta wuce Kaduna, itama
Hadizan ta amince domin rudanin da ke kanta duk ya sukurkutar
da ita, tun tana daukar Yusuf wawa bata da lokacin sa shirme
ya ke, to yanzu ko al'amarin sa ya fara tayas da hankalinta, don
haka ne ma ta yanke shawarar idan ta koma Kaduna zata shirya
ta je Bakori ta yi ma Inna Tambai bayani don ta je ta yi ma Gwoggo Halima magana saboda a tsawata masa ya fita hanyarta.
Yusuf a Kaduna yana ci gaba da gudanar da ayyukan ofis din su, kullun ya sami sukunin tunanin Hadiza babu abinda ya fi bata masa rai irin wasikar da ta rubuta masa, anya Hadiza ta iya tabbataswa kanta cewa bata son shi? Ya nemo takardar ya kara
karantawa ya-yi mata kyakkyawar nazari sai ya ga ma ashe shirme ya ke yì, wannan takarda na bukatar a kara tattaunawa.
Da yamma ya shirya ya nufi gidan Baba Garba don ya ga Hadiza. Maigadi ya ce ai ta je Jos bata dawo ba, Yusuf ya nemi ganin matar gidan, aka shigar da shi falo ta tabbatas masa Hadiza
na can Jos suma yau suka dawo. Ya ce, "Ita fa sai yaushe?" Ta
ce, "Ba na iya cewa domin na je maijegon na cewa ta kwana biyu a can". Yusuf ya yi shiru sannan ya ce, "Don Allah a yi min kwatancen gidan Baba Rilwan".
Ta ce, "idan ka je Jos ka san dai jami'ar Jos ba boye take ba, kana isa get gidajen Malaman zaka iya hangen wani sabon gida zaboda ba su fi wata biyu a cikin sa ba, to nan ne gidan Baba Rilwan."
25
Karfe sha daya da `yan dakoki Yusuf ya sauka gidan
Rilwan shi da direban Kanfaninsu, su Hadiza sun koma daki
kanan sun raka Dr Sani zai koma Abuju, Mama Binta ta aiko wai
su je falon baki ga Yusuf can na san ganin su.
Hadizan Bakori ta dafe kirji ta dubi `yar Jos ta ce, “Ke da
gaske ne fa wasu mutanen suna da maita a cikin jikinsu, to na
yadda shi dai Yusuf yana da maitar, kin ga wasikar da na rubuta
masa kuwa ina nuna masa a shagube bana son sa amma wai
kin ji mayen ya biyo ni har Jos, to ba zai ganni ba, ya gaji da
zamansa ya tafi, Hadizan Jos ta ce, "Tafdijam! Ai wallahi sai
mun je Yusuf din da na ke ji kamar na je har gaban mahaifiyar sa
na ci mutuncinsa ace yau ga shi a gidanmu ba zan je na fada
mai maganganu ba wannan shi ne kuma karya!"
Murna da dadi suka kama Hadizan Bakori domin ta sami
mai yi mata maganin Yusuf yadda zai daina zuwa gareta. Suka
shirya don zuwa falo, abin mamaki har Mama Binta ta shirya
masa abinci an kai masa ya ma gama cì, shi ma direbansa yana
can waje an kai masa.
Hadizan Jos ce a gaba yayin da Hadiza ke bayan ta
rungume da Fatima an nade ta cikin tawul amma idonta biyu.
Ya amsa sallamar Hadizan Jos yana mai murmushi ya сe "Kar
dai ace min ke ce mai jegon, lalle godiya ta tabbata ga Sarkin
halitta da ya sauke ki lafiya ga ki tangaran-kamar ruwan sama,
wannan ina baki shawara kanwata idan kin tashi komawa gidan
Dr. Sani sai ya baki sabon sadaki domin na sabon amarci". Haba
nan da nan `yar Jos ta kyalkyale da dariya ta ce, “To na amince
kai ne mai amsar mani tunda kai ne yayana" Ya mike ya nufi
Hadizan Bakori ya cę, "Masha Allah bebin kenan? ya amsa cike
da murmushi ya koma ya zauna ya dade yana kallon Fatima ya
sha mur ya ce, "A duniya yauşhe rabon da na ga jariri ma
kyau irin wannan? Ya Allah! Ya Allah!! Ya Allah!!! Ka ba ni irin
wannan kyakkyawar jaririyar nan da wata tara!"`Yar jos ta
kyalkyale da dariya ta ce, "ka san ko abinda ka ke fadi, nan da
wata tara fa ka ce! Don Allah ka kara watanni". Ya kara zubaw
26
aririyar ido ya ce "Ai ni idan ma zata rayu ban ki ba a haifar
min ko nan da wata biyar ne kanwata". Ya kai fuskarsa daidai
kumatun Fatima yana sumbatarta ya dago ya dubi su Hadiza da
Hadiza ya ce, "Kin gama ma Dr. Sani komi Hadiza". Hadizan Jos
da Yusuf suka kyalkyale da dariya tace, "Ashe haka kake,
gaskiya ba ka da dama". Suka shiga yi ma juna bayanan
anguwarsu a can Abuja Yusuf ya fara kwatanta mata gidansa
ya ce ya san kanfanin Dr. Sani amma bai san gidansa ba.Yar
Jos ta ce "Ni ma na gane naka gidan inda teloli suke, wa` anda
sun fi yin'aikin hannu, na taba raka Dr. amma na zauna cikin
mota domin maza sun fi yawa a wajen". Yusuf ya yi dariya ya
ce,."Yes, kin gano gidana kenan." Tunda suka shigo falo Hadizan
Jos ta canzawa `yar Bakori yayin da`yar Bakori ta sha mur
tana ta hararar`yar Jos akan ta daina yi ma Yusuf dariya ta
shiga zaginsa kawai.
Fatima ta shiga rigima tana dan korafin kuka, Yusuf ya yi
galala yana dubar su Hadiza ya ce, "To kun ga fa inda za ai rikici
da ni ban san yadda ake rarrashin jariri ba, domin sai na ga
tamkar zan matse shi". Ya mike ya nufi Hadizan Bakori da
Fatima ya mika mata, ya ce, “Ga ta Gimbiya". Yana murmushi
yayin da ita ta sha bula, sai ta rungume Fatima a kirjin ta tana
riritata nan da nan ta yi shiru, sai Hadizan Jos ta mike ta ce, "ina
zuwa, bari na kawo mata ruwa na canzó mata hula kila wannan
ta yi mata nauyi."
Bayan tafiyarta an yi `yan mintoci Yusuf na kallon Hadiza
da Fatima babu abinda ya ke yi sai addu` a Allah ya bashi Dije ta
haifar masa kamar Fatima.
Ya yi ajiyar zuciya ya ce, "Ranki shi dade, ina gajiya? Ta dago kai ta galla masa harara ta ce, "Wai me ya kawo ka nan,
ba ka ga abinda na rubuta ma ba ne?" Ya yi dariya yace, "Oh
yes! Na ga ni mana, ai shi yasa na zo don muyi shawara, ina fa
zan yadda ina matsayin yayanki ki auri wanda ba kya so?"
Anan kuma ya saki layin wasa ya sha mur ya ce, "Don Allah
don Annabi Hadiza kin galabaitar da ni, kin wahalad da ni, na
27
azabtu na shiga halin da ban taba zatun diya mace zata sáka ni
ba, duk a dalilin dan kuskure kalilan, ki yi hakuri (anan sai ya
mike ya isa gabanta ya durkusa gwiwa bibbiyu) yana afi da
hannuwa yana hada ta da girman Allah, ga kwalla taf da idonsa
itama Hadiza anan taji jikinta ya yi sanyi karara, ta tuno irin
matsayin Yusuf a gidansu yadda mahaifiyarsa da kannansa ke ji
da shi, amma a yau gashi tsugunne gabanta yana kuka yana
mai rokonta.
Idonta ya kada ya yi jajur ta dubi Yusuf ta ce, "Wallahi
Yusuf ban rike ka da komi ba, domin ai ka so ni lokacin da na ke
shan wahala Allah ne bai yi aurenmu ba sai dai a gaskiya wallahi
ka ji na rantse bana iya fasa auren Amiru a wannan lokacin".
Har yanzu Yusuf na tsugunne ya ce "Hadiza don ba kya so na
kin fi son Amiru ko?" sai kawai Hadiza ta sami kan ta tana jin
tausayin Yusuf amma kuma tace mashi, “E to„ba wai bana son
ka ba ne, ai kai ma na so ka a lokacin da na so ka din, yanzu
kam gaskiya Amiru na ke so". Wasu kwalla suka sake taruwa a
idon Yusuf ya fiddo hankicinsa ya goge idonsa ya yin da kwayar
idon ta yi jajur, a daidai nan ne Hadizan Jos ta iso da niyyar kawo
ma diyarta ruwa amma ganin Yusuf na tsugunne a gaban
Hadiza vana kuka, sai ta ja da baya ta koma daki.
Yusuf ya koma ya zauna dirshan a gaban Hadiza sai gugar
kwalla ya ke mata, ya ce, "ina son na ga Mama ta nan gidan".
Hadiza ta mike da sauri ta fita, daman zaman ya gallabe ta,
yaya zai tasa ta ya rinka yi mata kuka ita lokacin da ta yi nata
kukan rashinsa yana ina? Ba yana can ya sami Fa`iza ba, to
itama yanzu ta sami Amiru don haka kada ya matsa mata.
Ta sanarwa da Mama sakon Yusuf sannan ta cimma Hadiza
a daki ta kwantar da Fatima ta koma inda Hadiza ke kwance ta
zauna, ta dubi`yar Jos tace, "A gaskiya kin ba ni kunya wai
duk bakinki da irin tsiwarki amma wai ki ka kasa ce wa Yusuf
komi sai ma wani gatanci da ya samu wanda ban ga Amiru na ya
samu ba". Hadiza ta tashi zaune 'ki vi hakuri, ni kai na nayi
mamakin yadda na yi ma Yusuf, saboda na tsane shi a bisa
28
labarin da ki ka bani, to amma ina shiga falo yadda na gan shi sai
na ji duk na sare domin kwarjininsa da barkwancinsa ya fi karfin
a yi mai wulakanci. Na san a da Yusuf ya yi laifi to amma yanzu
Hadiza ki tausaya masa, ki duba fa har tsugunnawa ya yi bisa
gwiwowinsa yana kuka? Haba! Hadiza ai namiii irin su Yusuf
komi su kai idan har $un gane kurensu sai a yafe masu haka nan,
wallahi yadda ya tsugunna a gabanki ba don kuka ya ke yi ba ni
kam yau da na dauke ku hoto da sauran fim din Fatima, kin ga
irin kyan da ku ka yi kuwa? Kai Hadiza ke da Yusuf Allah ya yi
ajiyarsa!"
Hadizan Bakori ta daga kai ta dube ta ta ce, "kina da
hankali kuwa? Kin manta an tsaida min miji Amiru?" Hadiza ta
ce, "Na fi kowa sani, amma in gaskiya ta zo a fade ta, haka nan
kuma sau nawa ake sa rana a warware wani lokacin ma ana
gobe za'a kai amarya gidan miji ake canza mijin" Hadiza ta cе,
"Tunda ba'a yi akan ki ba, insha Allah ba za`a yi akai na ba, su
Fatima ga su can gidan Amiru".
Suka dade suna kallon juna sannan suka kyalkyale da dariya.
Hadizan Jos ta ce, "Tafdijam! Ina ganin Bakatsine ba na auren
Bakano, sadda duk miji zai saka hulà sai dai kiga (birki kunne)
haka nan za su ranbadawa idanunsu kwalli bajau wa ya aike ni!"
Hadizan Bakori ta dingi dariya har tana kwantawa ta ce, "Wai ya
ake sa hula birki kunne kuma Hadiza?" Ta ce, "Idan Amiru ya zo
ki dube shi tsab za ki gani, amma kin hada da su Yusuf gogaggun
Katsina idan an saka hular nan a murza ta sai ta kusa danganewa
da gira, ke komi na Bakatsine fa daban ya ke, idan har an sami
tsantsar Bakatsine za ki same shi da daddadan lafazi mai tsima
jiki da kashe kwanya sannan ga kyan iya shirya lafazi yadda zai
shigi bil adam, sai kuma wata baiwa da Allah ya yi ma su na
kamun kai, wanda shi ne ya haifar da wata ilhama ta kwarjini na
musamman a gare su, to kin ji dalilin da yasa Katsinawa su ka yi
zarra, amma fa ba su danne `yan Bauchi ba domin suma sun
hada yawancin abinda Katsinawa suka tara, ko kin san duk
Nigeria ba wanda ya kai jama'ar Bauchi da Katsina mulki irin na
29
Kuma sun iya domin irirn jininsu kenan.
Hadizan Bakori ta ce, "kai Hadiza da dai Dr Sani ba dan
Katsina ba ne, sai na ce ya ba ni da bakin ki, to Allah ya taimakeshi
ya fito daga jiharku ta Katsinan. Ni kam ina kin Yusuf ne a
dalilin ina ganinsa a namiiin zara irin su ne a kullun suka hango
abun sha'awa jikin wata za su bar ka zuwa gare ta"..
Ina son kuma ki fahinci abu daya a wajen Kanawa kamar
yadda ki ka fahinci Katsinawa wato a duk kabilar arewa babu
masu ladabi da biyayya da sanin ilmin Islama kamar 'ya'yan Kano
daga nan sai`ya`yan Maiduguri, in da duk Bakano ya ke yana
girmama na gabansa, haka nan bai iya saba maganar iyayensa
ko yaya take, sannan za ki same su cikakkun mutane masu
sana`ar gado tun suna `yan kanana, amma kin hada da yaranmu
na jihar Katsina yawancinsu sun faye girman kai da nuna isar
ba a isa ba, da sauransu, to kin ji abinda ke ba ni sha' awa da
halayyar kanawa.
A can falo kuma Yusuf ya yi zaman dirshan bisa kafet
gaban Mama Binta ya fi awa daya yana kashe ta da lafazinsa
masu dadin sauraro, ya ce, "Wallahi Mama ina tausayin kaina
ina tausayin Hadiza domin yadda na ke sonta itama ni kadai take
so, to kin ga na kyale ta ta cutu akan wani jin kai da kunya?"
Mama ta ce, "E to sai na yadda da kai anan domin zurfin cikin
Hadiza yawa ne da shi, duk yadda ka ke da ita da wuya ka san
abinda take so ko wanda bata so, haka nan mu dai tunda muke
da ita a gidan nan ba mu san ko me ke bata ran Hadiza ba."
Yusuf ya gyara zama ya ce, “To kin san Allah daya ne
Mama, duk duniya daga ni sai Baba Kado wato mahaifinta muka
san cikin Hadiza da bai dinta, yanzu idan da yana da rai tabbas
ya san tafi so na fiye da Amiru babu tantama ba zai tsaya
sauraronta ba zai umurtai ni na ci gaba da shirye-shiryen biki,
yanzu haka idan zan aika na kira ta zata zo, illa dai zata rinka
fada min maganganun wulakanci amma idan na dubi kwayar
idonta wani zubin zan ga ba har cikin zuciyarta take min ba, sai
dai saboda jin dacin abinda na yi mata, na kuma tabbatas idan da
30
ni ne aka sa mana rana babu yadda za ai ta fito wajen wani idan
ya kira ta."
Mama ta ce, "Lalle Yusuf dole ne ka nace domin ba a san
rabo ba, ni dai shawarar da zan baka shi ne tunda ka fahinceta a
hakan, to sai ka koma can Bakorinku ka nemi daurin bakin su
Inna Tambai da aminan Babanta domin sanin kan ka ne, a duniya
Hadiza bata da uwa kuma aminiyar shawara bayan Inna Tambai,
sannan kuma tafi son Babanta fiye da komi na duniya, idan ka
sami amincewarsu ina gánin za su shawo maka kan Hadiza."
Yanzu a duniya Yusuf ji yake bai da masoya irin Saminu da
Hadizan Jos da Mama Binta. A ran nan ya koma Kaduna kashegari
ya yi ayyukan kanfaninsu da dama ya yi sa` a daya daga cikin
wa`anda ke da alhakin mallakar kanfanin ya na nan ya je Kaduna,
ya yaba da aikin da Yusuf ya gudanar har ya nemi Yusuf da ya zo
gidansa da yamma, gaban Yusuf ya fadi ras domin a niyyar Yusuf
so ya ke da yamma ya nufi Bakori ya kashe su Inna Tambai da
Baba lliya da dadin bakinsa, amma sai ya tuna aikinsa na gaba
da komi, idan babu aikin nan matar ma tsanarka ta ke. Ya cimma
uban gidansa da karfe tara daidai na dare sun yi rubúce-rubuce
har zuwa karfe biyun dare akan kanfaninsu. To a lokacin ne
Yallabai ya lura ba haka Yusuf ya ke ba akwai dai wani abu a
kalkashin ransa, yana tambayar Yusuf bai tsaya wani kawaici
ba ya warware mai irin damuwar da ke cin sa a rai, nan da nan
Yusuf ya fara kawo kwalla ya ce, "Yallabai ni na san na yi
kuskurena amma yarinyar nan ta ki hakura, ga shi abin haushi
wai abokina na kut