Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 9
rungume sunnar Manzo bil hakki da gaskıya yana tare da dukkan nasara duniya zuwa lahira. Ina so na gargade ka anen Yusuf wato a yadda al amuran aurenku suka kasance kai da Dije vanzu dole ne kai ka zama mata: ita zata zama mijin, 54 abun nufi anan a dalilinka ta shiga hali iri-iri wanda ya ja batawarta da mahaifiyarta bayan tsegunguman jama'a, to kaga anan yanzu tana cikin radadin kunar zuci, dole ta tsinci kanta cikin tsanar ka wanda zai jawo ta kasa kyautata maka, amma idan duk akai hakuri za ka amshi mulkinka a hankali." Maganar Mallan Iliya ta shigi Yusuf sosai ya kuma amincema ransa zai bi shawarar Mallan din. Bayan sun baro gidan Mallan lliya Falanke yace, "Ya dace anjima mu je ka gayas da Inna Tambai Malunfashi dai mallan lliya ya gargade mu kada mu je yanzu sai can gaba in kura ta lafa." Yusuf ya shafa kansa yace, "Wallahi Falanke ban ki ba na koma da zama gidan Inna Tambai amma ni tsoron idon Hadiza nake don baka san yadda muka yi da ita ba ne a karshe." Falanke yace, "Ka san Allah lafiya lau domin jiya da naje mun sha hira nace ango na gaisuwa ta ce, nima ina gaida shi dazun kuma da safe kafin ka tashi mun je ni da Basiru, wallahi abun da ta fara ce min `yaya Sha`aibu ya aiko ka ne?' Na ce "E cewa yayi in zo in ga tashin lafiyarki." Yusuf ya yi murmushi yace, "Ku take nuna ma fara'a amma yanzu da żata ganni sai tsana zan je dai amma ba yau ba ina tsoron bacin ran Hadiza." Sai da Yusuf ya sami kwana hudu a Bakori amma bai leka Hadiza ba sai dai dan kwarako Falanke na nan bisa hanya kullun. Inna Tambai na dai lura da Hadiza irin nasihohin da take mata suna shigarta don haka da alama tana kaunar ganin mijin nata. Shi kan shi Yusuf duk ya kagara a kawo masa Hadiza kila a gidansa ba za ta rinka yi mai kallon nan da bai so ba wanda ya ke firgita shi amma kuma yadda Falanke ke cewa ta canza yana kwadayin ganin nata, don haka sai ya shirya shawara ya baiwa kaninsa Basiru kudin cefane ya ce ya je ya sawo kayan ciki da wake ya kai ma Hadiza yace, tayi mai farfesun kayan ciki da alale. Hadiza ta amshi kayan girki tace ma Basiru 'ka je ka tambayo shi kamar na mutun nawa za'a girka kuma da karfe nawa ya ke so?' Haba murna da dadi suka lullube Yusuf da ya ji aiken Hadiza 55 ya ce "Kа ce mata kamar na mutun hudu da karfe biyu da rabi na rana za'a zo a karba." Abinda ya kara birge Yusuf shine a irin kwanonin da Hadiza ta zubo abincin sannan kuma irin alalan da ta taba yi masa tun zamanin suna samartaka a wani zaman jinyarasa da ta yi. Karfe takwas na dare Yusuf ya fesa wanka ya zuba wanda da riga na shakwara da janfa na kirim din boyel ya mulke jikinsa da wani turare mai dadin kanshi da ake kira (hold the heart of your love). Ya fito yana tayas da mota Falanke ya iso da sauri yace, "Yallabai ba zan yi rakiya ba?" Yusuf yace, "Bisimillah, za ni ban gajiyar aikin abinci ne." Falanke yace, "Ai yau kam amarya ta biya mu." Inna Tambai na zaune tsakar gida tana shan iska ita ko gimbiyar na cikin daki tana sauraron wa'azin Mallan, hasken musulunci. Su Yusuf su kai sallama suka shiga, bayan sun jima suna hira da Inna, sai Innar ta ce "Ku shiga daki mana ai Dijen na ciki." Suka shiga tana zaune ta mike kafafuwa, sanye da jallabiya mai ruwan zuma, ta amsa sallamarsu kan ta na sunkuye, Falanke ya gaisheta sannan ya dubi Yusuf ya ce "Ranka shi dade zan je cikin mota na jira fitowarka." Yusuf yace, "Babu laifi ga makullan, sai na fito." Yusuf ya zauna bisa tabarma shi ma ya mike na shi kafafun ya dubi Hadiza a sunkuye ya ce, "Amarya wa`azi ake saurare ne?" Bata iya dago kai ba ta amsa`E' yace "Allah yasa wanda zai anfanemu ne." Tace "Amin" Ya sake cewa "Ya gajiyar aiki?" Tace, "Babu gajiya." Sun yi shiru kowanne na sake-sake cikin ransa, har yanzu dai Hadiza bata iya dubar Yusuf ba, shi din ma a kasa-kasa ya ke kallonta duk maganar da zai furta mata yana zullumi don yana tsoron kar ta birkice masa, don haka a dosáne yake, haka nan itama Hadizan ta lura da cewa a firgicen ya ke, amma babu abinda zata iya ce masa, illa dai kawai ta yi alkawari ba za ta sake yi mai tsiya ba a dalilin maganganun da su ka yi da Mallan 56 Iliyasu ta tabbatas wa ranta duk duniya babu mai son mahaifinta Baba Kado sai ita da Yusuf haka nan ta na alfaharin har ya mutu yana kaunar Yusuf, don haka ya dace ta auri Yusuf a ko wane mataki na fannin farantawa mahaifinta rai, kamar yadda Inna Tambai kejaddada mata cewa 'Dije kin gamawa marigayi komi tunda ki ka auri Yusuf a dalilin son da ke tsakanin mahaifinki da shi Yusuf.' Hadiza na son Amiru tana kaunar halayansa, taso kuma kwarai ya zama mijin aurenta amma kuma soyayyarta da Yusuf wata irin kaunace wadda ke cikin jininsu illa kawai bacin rai ya haddasa tsana da kiyayya mai tsanani a tsakaninsu, wadda kuma yanzu gatancin da Yusuf ya nuna wa marigayi Alhaji Kado yasa Dije na jin nauyi da tausayin Yusuf, don haka ta yi alkawarin shanye duk wani batanci da yayi mata, ko a da bai son ta tunda yana son mahaifinta ya gama mata komi. a Yusuf ya katse zaman shiru yace, "Bari na tashi na tafi kila na takura ki, kin sadda kai kin kasa sakewa." Sai Hadiza ta daure ta dago kai a hankali ta dan dube shi kadan tace, "Na ce ba, ko zai yiwu gobe ka ba Basiru mota ya kai ni Kaduna akwai wasu kaya da nake son daukowa, kuma akwai zancen bayas da katunan da ka aiko min." Yusuf har ya so ya karyata kunnuwansa, shin da gaske ne Hadiza ke mai wannan lafazin a hankali mai ratsa jiki, ko dai zolayarsa take? Yusuf cikin murmushi na rudani yace "Me zai hana ya yiwu sai dai zan fi so ni na kai ki domin akwai bukatar zuwanmu Kaduna ni da ke a dalilin taransufa na aikinki komawa Abuja, haka nan akwai wani dinki da nake so mu je wajen telolinki na Kaduna za mu kai na wani boyel les wanda za mu sa a daren dina." Ta dube shi tace "Me zai sa ba za ka ba Shuaibu ba?" Yace "Ai na bashi aikin hannu na wani farin boyel na ga ma har yanzu bai gama mana ba." Hadiza tace, "Amma ina ganin zai fi kyau mu tafi da zinaran nan Kaduna mu aje a banki ko?" Yusuf ya kara matsawa kusa da Hadiza ya tabbatas Hadiza ra'ayinsu daya sha'awarsu daya tunaninsu daya yace, "Wallahi 57 abinda nace ma Gwoggo kenan a ranar da za'a kawo kayan amma ta hau ni da fada kin dai san halin Gwoggo komi tace an yi rashin kunya." Hadiza ta mike ta dauko kit suna kara dubawa, yana gaya mata wanda ya saya a London tun wani zuwansu da Shugaba, da wanda ya taba sawowa a umarar shekara biyu da ta wuce da wa'anda ya saya farkon zuwansa aikin hajji, da wa'anda ya saya a Indiya. Hadiza tace, lo Gwoggo kake ba ajiya?" Yace, "Wallahi banki na ke aje abuna kin san mutanenmu ba su faye sanin daraiar wa annan abubuwan ba". Tun Inna Tambai na jin maganar Hadiza da Yusuf samasama har bacci ya kwasheta, yayin da Yusuf sai da yasa Dije ta gwada duk sarkokin nan da zabba da abun hannu an yi sa'a abun hannun mai sukuro ne, ana iya ragewa ko kara girmansu, a Madina wata balarabiya 'yar kasai Jordan ta sa Yusuf ya saye su domin yace bai san size din matar da zai aura ba. Bai bar dakin Inna Tambai ba sai misalin karfe goma sha biyu na dare. Falanke ya dade da bacci a mota ba don tausayin Inna Tambai na kwance a waje ba kila Yusuf da sai an kira asuba zai bar gidan, duk ilahirin kayan lehen nan kuwa babu wanda basu yi daidai da shi ba. Shi da Hadiza suna dubawa, yana fada mata yadda ya sayi kowanne. Ta dube shi tace, "Akwai irin wannan turaren da ka shafa cikin kayan nan?" Ya dan lunshe ido ya ce, "Kina son shi ne?" Tai mai murmushin da ya shekara bakwai bai gani ba, ta ce, "Irin turaren da na fi so kenan domin bai yamutsa hankali." Suka dubi juna suka yi dariya, yace, "Ba irin sa anan amma na yi alkawarin aje maki nawa". Ta ce, "Lah ka bar shi ka rinka shafa abinka". Ya ce "A'a idan kin zo mun rinka shafawa tare." Wanshekare karfe goma da rabi na safe ya iso shi da Falanke don daukar Hadiza tafiya Kaduna. Ta fito ta cimma masa yana tsaye gindin motarsa rike da wata 'yar karamar rediyo mai kama tashoshin kasashen waje. Kwalliyarta irin ta kamamnun musulmai ta kayatar da Yusut ainin ya kuma yi alfahari da ita 58 har zuci, ta dafa gefen mota ta dan rusuna ta gayas da shi. Ya bude mata kofar gaba ta dube shi tace, "Ba da Sha aibu za'a ba?" Yace, "Da shi za mu mana." Tace, "To ai shi ya fi dacewa ya zauna a gaba ni na zauna a gidan baya." Suka dubi juna su kai dariya shi da Falanke." Ta koma gidan baya ta zauna Yusuf ya shiga, amma kafin ya tayas da motar sai da ya dauki lokaci yana yin saitin madubin gaba a daidai fuskar Hadiza, ta dago ta duba suka yi ido hudu ita da Yusuf ta madubi, nan da nan su kai ma juna murmushi, Yusuf ya saukar da wata sansanyar ajiyar zuciya. Sun kwana sun yini ana zirga-zirga a Kaduna kafin su gama abubuwan da suka kai su, don haka sai cikin dare suka isa Bakori. KASHI NA GOMA SHA BIYAR Da karfe biyu na rana Baba lliyasu ya daura auren Yusuf da Hadiza, an gabatar da addu'a ta musamman ga marigayi Alhaji Kado daurin aure da 'yar kwarya-kwaryar walima ta kayatar, duk dawainiyan abinci na gidansu da na gidan Inna Tambai Yusuf ya yi komi domin ya san dai karshe Hadizan ce za ta yi. Baba Rilwan, Baba Garba da Baba Malan Isa zuwa kannen Hadiza su Saminu sun halarci daurin auren, haka nan matar Baba Garba da Mama Binta da Hadizan Jos su kadai za mu iya cewa sun halarci bikin a bangaren dangin yaya Amina mata. A ranar da biki zai tashi tun da safe Yusuf ya sa Falanke ya sawo mai zabbi guda biyu yace ya a adana su can a gidansa wato Falanken. A can ma Kano an daura auren Amiru da Salma a daidai lokacin da ake daura na su Yusuf. Karfe goma sha daya na dare Yusuf ya dubi Falanke kowannensu a gajiye likis, yace "Falanke na gode, Allah va bar mu tare, amma kafin ka tafi gida ka kwanta, nima ba zan shiga wajen amarya ba sai ka yi min wani aiki daya." Falanke da kyar yake daga ido don tsabar gajiya yace, 59 "Me ya kuma rage Yallabai?" Yusuf yace, "Ina son ka je ka dauki zabuwa daya ka kai ma Talle mai tsire ya gashe min ita yanzu ka kawo min, ita kuma daya zabuwar ka mikawa Gwoggo kace ta soyo ta gobe da safe ta aiko min." Falanke yace "Tirkasahi! Wannan aikin amarya ne ko? To amma ka san kila su Gwoggo yanzu gajiyar biki tasa sun kwanta ba ka bari da safe na kai mata?" Yusuf yace, "To yi sauri ka cimma Talle mai tsire ya gaso dayar." Falanke ya dawo karfe daya saura 'yan mintoci na dare yana magana a gajiye yace, "Yallabai ga zabuwa an yi sa'a yarinya ce zabuwar mai maiko, a sha amarci lafiya. Ubangiji ya bada raboa daren yau, amma fa a sa mai suna Shu'aibu." Yusuf ya yi dariya yace, "Kai ka yarda a fara sa sunanka, bayan ga sunan Baba Kado." Falanke yace, "Tuba na ke Yallabai kai na bisa wuya, Allah ya kawo mana takwaran Baba Abdulkadir, mu kwana lafiya." Yusuf ya shigar da mota garejin gidansa, sannan ya yi wata addu'a wadda Mallan Tukur ya ba shi. Ya shiga falonsa kamar ya doshi dakin Hadiza amma ya kanne ya nufi na shi dakin, ya sunce kaya ya fada kewaya ya yi wanka tare da alwala sannan ya fito ya dauko maganinsa na ciwon jiki ya kora ya saka kayan baci ya dauki turaren da Hadiza tace, tana so ya nufi dakinta. Abin mamaki karfe biyu ta yi amma sai ya rinka jin karatun Alqurani na fitowa daga rediyon dakin Hadiza yace a ransa kada dai ace Hadiza ba ai bacci ba? Ya murda kofar a hankali ya shiga, ta yi dai dai bisa gado a bisa dukkan alamu bacci mai nauyi ya dauke ta, ya nufi inda rediyonta yake ya kashe ta yi firgigi ta tashi nan sai ta tsuke mai fuska tace, "Don me zaka kashe min? Ni na riga na saba, kwana na ke da karatun Ahmad Sulaiman domin rediyon mai juya kanta ce." Yusuf ya dan firgita da yanayin fuskar ta yace, "Na yi zaton ba ki sani bane." Ya tsaya shi bai zauna ba haka nan shi bai kunna rediyon ba, amma Hadiza ta kara tsuke fuska fiye da 60 shigowarsa, ya cije yace, "Hadiza akwai bukatar mu gabatar da nafila tashi ki yo alwala?" Sai da ta bata lokaci sannan ta je ta yo alwalar, bayan sun idas da nafilar ya dade yana masu addu'a a fili tana amsawa da "Amin". Sai ya juyo da sauri ya kamo hannuwanta ya rike zai kai bisa kirginsa ta fisge ta mike ta koma can gefen gado ta tsaya yace, "Me kuma ya faru?" Ta juyo ta dan harare shi ta kawad da kai ya dauki turaren da ya shigo da shi ya je zai fesa mata tace "ba na so" cikin tsiwa. Baya son rigimar ta yi tsami sai ya fita da niyyar ya je falo ya yi tunani ko zai iya tunano abinda zai shawo kanta, amma sai ya ci karo da gasassar zabuwar sa ya dauka ya juya ya koma dakin Hadiza don ya cika alkawarin da ya daukar mata. Yanzu tana zaunè bakin gado ta yi tagumi, ya tsaya a gabanta ya langabe kai ya ce, "Ki dubi girman Allah ki saurareni na gabatar da nauyin alkawari daga bisani kina iya ci gaba da musguna mani, zan iya jurewa har Allah yasa ki daina." Ta daga kai tace, `Wai menene?' Ya tsugunna a gabanta da `yar leda à hannu yace, "Akwai wani zamani idan ba za ki manta ba na yi alkawarin cewa ran da duk na gan ki a dakina, a rannan zan kawo maki zabuwa wadda zan yi maki lakabin sunan da nake so wato KUBRA, to Allah Ya yarda yau ga ki a gidana kuma kin ci ma'anar sunan wato BABBA da larabci shine Kubra, a yau kin zama babba a gidana, a zuciya ta, a cikin gidanmu ma keсе babba tunda kece matar babban yaya. Hadiza ta yi wata irin`yar siririyar dariya `yan kananan hakoranta masu daukar hankali suka bayyana a idon ango Yusuf tace, "Allah da gaske ka ke, idan da gaske ne bude ledar na gani idan zabuwar ce!" Yusuf bai san yadda zai bayyana farincikinsa ba a wannan lokacin, sai ya dube ta ya ce, "Ina zuwa ki jira ni." Ya mike ya nufi kicin don ya kawo faranti ya dora zabuwar a kai, amma sai ya tsaya cak yana alajabin yadda Hadiza ta cika masu kicin da na'urori na girke girke, ya rinka mamakin a ina Hadiza ta sawo wa` annan na` urori masu tsadar tsiya? Ya yi murmushi ya 61 ce lalle Hadiza na shirin sangartashi, ya dauko faranti ya koma dakin Hadiza, ya zauna a gabanta dirshan ya fid do zabuwa ta yi narai-narai da maiko, an kuma shafe ta da magi mai tauraro da atarugu da albasa. Yusuf ya yago cinya ya ce, `Kubra'. Ta dago kai a hankali ta yi mai wani irin kallo wanda ya zarce wanda ta taba yi masa a wancan zamanin da suka yi irin wannan magana, tsigar jikinsa ta tashi yar, ya lumshe ido sannan ya dan bude ya ce "Kubra, Allah! Allah!! Yasa ki haifa min`yan mata shidda masu irin idonki su rika kallona kamar yadda kike kallo na." Ta tumshe ido. Ya mika mata cinya ta kai bakinta tana ci, ya ce, "Amma kin ba ni mamaki yanzu nan kin nuna min bacin ranki tamkar nayi laihi yanzu kuma na ga kin huce." Ta ce, "Haba Yaya ai dole ne na yi ma haka, a zatona ka manta da wannan alkawarin wanda yana daya daga cikin abinda ya gina kaunata da kai haka nan yana daya daga cikin abinda ya sa na tsane ka, domin ina mamakin wanda zai fada wa diya mace wa`annan kalamai sannan ya dawo ya ce bai son ta." Ya yi ajiyar zuciya ya ce, "Har yanzu inan nan a yaya? Ni ma ai an yi min alkawarin raba ni da suna Yaya ko?" Ta dan rusunar da kwayan idanunta ta ce, "Idan na kira ka da D ya isa?" Ya ji wani irin dadi ya rastsa shi ya ce, "Me ke nan kike nufi?" Ta ce, "Ina nufin Darlin ko?" Ya sake tsinkewa don dadi yace, "Me zai hana ki ce Darling din gaba daya?" Tace, "Yanzu a gabansu Gwoggo da su Basiru da irin su Sha'aibu ba zan ji nauyi ba? Amma ko idan na ce D kamar su Gwoggo ba za su gane ko me nake nufi ba." Yace, "Na gamsu, na gode, ni ba za ki samman zabuwar taki ba?" Sai ta dan zolaye shi tace "Ta Kubra ce fa mara fasali". Haba nan da nan ta jagula masa lissafi, amma sai ya dake ya maida shegantaka yace, "Haba ba dai Kubra dina ba, kine zancen wata yarinya ce Dije" Sai ta dan yi murmushi tace "Oho dai ai yan karin magana sunce kowa ya raina tsayiwar wata ya hau ya gyara idan zai iya." Yace, "Haka ne, ko da can rashin wayau ne ya hanani gyarawa, amma yanzu zan kara mikar 62 da komi ba ki ji abinda Inna Tambai tace ba ne? Cewa ta yi namiji shi ke mikar da mace......." Yusuf ya kammala shirnsa tsab Hadiza na tsaye rike da agogansa, fuskarsa a murtuke tana nuna alamun bacin rai da damuwa Hadiza ta ce, "D kawo hannunka na daura maka agogonka, wai me kuma aka yi ma ne sai huci kake? Ya mika mata hannu yayin da ya zuba ma fuskarta ido, yace "Na yi maki tambaya, saboda Allah Kubra yau kwana nawa da bikinmu?" Ta ce, "Yau kwana shidda wani abu?" Ya ce "Abunda ke bata min rai shi ne wa'annan matan masu isar mu da zuwa wai ganin daki, sun hana mu sakat mu kwanta mu huta wannan wacce irin aladace! Da sassafe karfe takwas zasu tayas da mu har mu kwanta bacci gidan nan ba a kara barin mu sakat haba ina dalili, mutun ba za a bar shi ya huta ba?" Hadiza ta yi dariya tace "Ga wasu mattan ma can falo suna zaman jiranka tun kana wanka suka zo, ina zaton a bayaninsu daga kauyensu Gwoggo su ke." Yusuf ya girgiza kai yace, "Bana iya zama har hutun wata daya a garinnan ki shirya abinda kike so wa'anda za ki yi anfani da su gobe insha Allah za mu koma Abuja." Da yamma Yusuf na gaba Hadiza na bayansa suka shiga gidan Gwoggo Halima, kai ka ce Gwogo Halima bata taba ganin danta Yusuf ba da Hadiza sai a wannan rana, sun birgeta sun bata sha'awa haka nan sun tsuma mata zuciya domin sun yi matukar dacewa da junansa ko wanne sai kwarjini da kuriciya ke bayyana daga gare shi. Murna da jin dadi suka hana Gwoggo Halima kulle bakinta. Bayan an kammala gaishe gaishe da ban gajiyar biki Yusuf yace, "Gwoggo gobe da sassafe Falanke zai tafi Abuja da motar kayanmu, yayin da ni da Kubra za mu tafi da azuhur." Gwoggo Halima ta sha bula tace, "Ni fa ba na son sokonci ca na ke hutun naku wata daya ne shi ne za ku gudu tun jama'a ba su gama ganin daki ba." Yusuf yace "Ai kin ji matsalata wa'annan mutanen da ke hana mu kwanciya mu huta, su za su kore mu." Gwoggo Halima ta dubi Hadiza tace, "Ke Hajiya Hadiza 60 kin amince da hakan?" Hadiza ta yi dariya tace, "To Gwoggo yadda yace yana so ai haka za'a yi ko?" Gwoggo Halima ta dan harare su tace, "A to ke ke daure masa gindi Hadiza." Hadiza ta kyalkyale da dariva ta ce, "Allah Gwoggo babu ruwana." Gwoggo ta ce "idan haka ne, shi ya tafi ke ya bar ki anan jama'a su gama ganin dakin amarya." Yusuf ya yi zanbur yace, "Haba Gwoggo ai itace shugaban tafiyar". Gwoggo ta dalla mai harara ta ce "To shugaban yan rashin kunya ban yi da kai ba." Da suka gama hira sun tashi tafiya Gwoggo Halima tace "Babu abinda za'ai maku wanda za ku tafi da shi?" Hadiza tace, "A yi mana hura Gwoggo." Sai Gwoggo tace, "Insha Allah za'ayi idan kun je wajen Tambaya ku ce ina gaishe ta ina sauraronta jibin don mu je Malunfashin." Yusuf da Hadiza sun sami yadda su ke mafarkin son rayuwar ta kasance komi ya yi masu acan acan, yau kwanansu ashirin da shidda da aure, Yusuf ya dauko katin bikin Amiru da Salma yana dubawa ya ce, "Amma Kubra ban yi zaton da Amiru zai sake wata hulda da ni ba balle har ya gayyace ni liyafar bikinsa." Tana daga can kwance bisa doguwar kujera a falonsu na Abuja ta dubi Yusuf tace, "Ni kam ban yi mamaki ba domin irin wannan ta sha faruwa daga bisani kuma ai ta zumunta tamkar wani abu bai taba faruwa ba. Don Allah idan ka je wajen bikin nan ka nunawa yawancin abokan nan na,ku tsakaninka da Amiru babu wata damuwa sai zumunci, domin na fuskanci akwai masu son su ga batawarku." Ya dube ta ya yi dariya ya ce'"Har kin amince min na je kenan?" Ta lumshe ido tace, "Me zai hana ka zuwa D? Ai tunda har ya aiko maka, ya dace ace ka yanke duk wasu al`amuranka ka je." Yace, "Amma da ke za mu ko?" Ta ce, "Haba D kamar ba mu da wayo! Kai kadai za ka idan ka je da ni, dole `yan tsegumi su yi halin nasu babu ma kamar abokanku da `yan uwan Amiru." A ranar da Yusuf za shi Kano wajen liyafar Amiru tare da 64 Hadiza suka taho ya aje ta gidansu na Bakori domin zata sallami kannanta komawa makaranta. Tun mahaifinsu na da rai ta yi kokarin ganin sun je babbar makaranta, wato Kuluwa da Larba suna kwalejin 'yan mata da ke Katsina sai Juma da Munari sun je makarantar 'yan mata da ke Kabomo. Tunda Hadiza ta sauka Bakori sai ta tsinci kanta da canzawar yanayin jikinta da farko abinda ta dauka rashin isasshen bacci ne da bata samu ba a daren jiya, sannan kuma a yau sun yi sammakon tafiya, to amma sai ta ji ciwon kai na neman kwantar da ita haka nan bayan ta kwanta wai ko ta ji sauki sai kuma zazzabi ya dirar mata, tana cikin wannan halin ne har kimanin awa daya da rabi sai ga Hassi kanwar Yusuf ta je. Bayan sun gaisa ta ce "Ai ina gida na ji an ce kina nan gida shi zai wuce Kano." Hadiza ta daga kai a hankali ta dubi Hassi tace, "Kin gan ni na iso Bakori da ciwon kai ya su Gwoggon? Da maigidanki?" Hassi tace, "Kowa lafiya lau, Gwaggon ma tana cewa na gaisheki tana can tana shirya maku abinci tace ko akwai ani abu da ki ke sha'awa?" Hadiza tace, "Anya zan iya ma cin abincin nan? Sai dai a dafa saboda su Yaya da wanda ya shigo ni kam ruwan zafi za ki dafa min ki zuba min a flas, na fi son shayi." Nan da nan Hassi ta nufi kicin ta jona butar ruwan zafi `yan mintoci ruwa sun tafasa ta shiryo ma Hadiza kayan shayi ta kai mata. Bayan Hassi ta mike don ta koma gida ta yi ma Gwoggo bayani sai Hadiza tace, "Don Allah Hassi a sami wani yaro a tura shi can gidanmu a yi min kiran su Larba da Munari." Har misalin karfe biyar na yamma Hadiza na dakin baccinsu a kudundune ciwo na cinta, sai kannanta su Larba ke kai da komowa a cikin gidan. A lokacin ne Basiru ya kawo Gwoggo Halima don ta duba jikin Hadizan, to ganin yadda Hadian take ya dan tsorata Gwoggo tace, "Hajiya Hadiza ko za ki yi karfin hali ki je asibiti? Tunda ba'a san lokacin da su Maitaman za su dawo ba?" Hadiza tace, "A'a Gwoggo a yi hakuri sai sun dawo domin ba za su kwana a Kano ba, in dai akwai fanadol mai kyau Basiru ya samo mani." Gwoggo tace "To shi kenan Basiru je ka ka samo 65 mata fanadol din." Basiru sai ya davvo da wani malamin asibiti abokinsa ya zankadawa Hadiza allura biyu har da ta bacci, ya danna mata wasu kwayoyi guda shid da ta hadiye. Bacci mai nauyi ya dauke ta, sannan Gwoggo ta gargadi su Larba akan su rik.a duba Hadiza kuma kada su tsananta hayaniya don kada su danme ta, ta koma gidanta. A Kano inda Amiru ya kama ya cika makil da bakin larabawa zuri'arsu Salma. Kami kam ya kayatu acan acan, abin sai in ka gani da idonka. Masu kidan Sudan ke cashewa a hankali cikin nishadi suna fidda sunan Amiru da Salma a tsanake kai kace akan su aka fara kirkirar vvannan wakar. Amiru da amarya Salma zuwa manyan abokan su

Chapter 6 of 9