suna zaune a tebir na musamman. A
lokacin ne Yusuf ya danno cike da kwarjininsa da haskensa na
amarci da annurinsa na zama kamilallen mutun, wato na zama
mai auren sunna.
Ako ina Yusuf ya ke ya kan fita daban domin halin sa
daban ne da na sauran jama'a yana shiga fili bai nemi wajen
zama ba sai ya zarce kai tsaye wajen mawakan Sudan ya shiga
manna masu 'yar wa-zo-bia har sai da daya daga cikin yaran
maiwaka ya nemo sunan Yusuf, nan take lasifika ta dauka gaba
daya da Y-U-S-U-F amanar K UBRY.
Salma ta dan rusuna zuwa kunnen Amiru tace "Yaya
wannan kuma fa?" Amiru ya kai bakinsa zuwa kunnenta yace,
"Shine babban aminina wanda na bar wa Hadiza!" Suka yi
murmushi Salma da Amiru sannan daya daga cikin kannan Amiru
ya mike ya je inda Amiru ya kirasa, ya dan rusuna, Amiru yace,
"Babangida ina son ka baiwa Yusuf kujerarka." Babangida yace
"An gama Yaya." Babangida ya nufi inda Yusuf ya ke ya taho da
shi zuwa tebir na musamman.
Kafin Yusuf ya zauna sai da ya kai gaisuwa wajen ango da
99
amarya da sauran jama'ar dake tebir na musamman. An yi tandetande da ciye-ciye haka nan an cashe da makada na zamani
yadda rayika ke so, na tsawon lokací mai yawa. A karshe Yusuf
ya rinka tunanin tashi galleliyar amaryar Kubra na can zaman
zuru zai fi kyau ya yi ma Amiru bankwana don ya koma wajen
ta.
Sun kebe gefe daya Amiru da Yusuf suna sallama, inda
Yusuf ke zolayar, Amiru da cewa "Irin wannan jajayen mutane
Amiru kamar muna a Saudiya?" Amiru ya dan doki kafadar Yusuf
yana dariya yace, "Ka san mahaifiyar Salma halarabiya ce, to
kuma Salma itace diya mace ta farko a gareta don haka ta yi
anfani da wannan damar na gayyato zuri'arta. Amma fa ina
gadiya Yusuf da ka nuna min karanci ka halacci bıkinmu." Yusuf
yayi murmushi yace, "Ni ya dace na yi ma godiya da ka kai min
katin gayya har gida ina fatan kuma abotarmu da zumuntarmu
zata ci gaba kamar da, haka nan kaman kullun kofar gidana a
bude take a gareka ina maraba da kai da iyalinka ni da kubra, har
abada ba zan taba zarginka da Kubra ba."
Amiru ya yi murmushi ya ce, "Na yi murna da jin haka
daga wajenka in Allah ya yadda babu abinda zai shiga tsakaninmu
sai zumuncin da muka kullo tun muna samari amma fa Yusuf
kana daya daga cikin al'umman Annabi masu rabo a duniya wai
na tambaye ka mana kai ko me ka ke ma Sarki Allah?"
Yusuf ya dan yi shiru sailin da ya zuba idonsa a kasa, nuna
alamun tunani zuwa can ya dubi Amiru ya ce, "Ka yi min tambayar
da ban yi zato ba amma kuma sanin kana daya daga cikin aminina
na hakika illa kawai wani rabon auren mu da ya gitta a lokaci daya kuma a wani rudadden yanayi sai dai kawai na san daga ni
har kai muna da kyakkyawan tunani wanda za mu iya cewa
aurena da kubra da neman ta da ka yi wani mukaddari ne daga
Allah. Lalle Amiru ka yi min tambaya mai kyau domin sanin kan
mu ne mun sabi Allah ta hanyar zinace-zinace wanda babu
tantama laihi ne tsakanin mu da Sarki Allah, sai dai kuma a
wancan zamanin da shaidan ya rudı zuciyarmu ban taba nemar
67
matar aure ba, saboda shiga hakkin wani, saboda ka ga laihi biyu
kenan dole ka nemi gafarar mijinta haka nan ka nemi gafarar
Allah wannan ken ina tabbatar maka tun zamanin da
mahaifina ya rasu ban taba yarda mahaifiyata ba ta tonawa kan
ta asiri inde duk zan shiga zan bi don inga na kare hakkinta da na
kannena, haka nan babu abinda nake iya rutewa Gwoggo wanda
na san tana alfahari da hakan, bana iva cin abinda na san ba zan
iya mallakawa Gwoogo ba sannan na roki Ubangiji kada ya ba ni
hatsabibiyar macan da zata zama sanadiyar raba ni da Gwoggo.
A kullun na yi sallah da asubah bana tashi sai na gabatar da
salatin Manzo cikin casbi hailalah cikin casbi sannan istingifari
cikin casbi komi saurin da na ke yı haka nan idan na yi sallar
isha'i yayin da na kammala da komi na yi shirin bacci, na kan yi
kokari na ga cewa kalmata ta karshe ita se (Astangafirillah lazi
taila ha illallah Huwal Hayyul kavyum wa atubi ilaihi) sau uku,
haka nan na kan gabatar da wannan istingifarin a dukkan sallolina
na farillah."
"To kuma ka san halina Amiru ban iya cin naman mutun
ba, kowaya taba ni nan take zan sanar da shi, ka dai san matsayin
cin naman mutun wajen Allah, ina ganin dai duk namijin da ya
tsare tsakaninsa da Ubangijinsa da mahaifiyarsa da kame bakinsa
daga giba to lalle zai rinka samun saukin al amuransa. Zan kara
maka haske daya Amiru a tun ranar da aka aiko min an ba ni
Kubrə na yi nafila na yi godiya zuwa ga Sarki Allah na daga
hannayena bayan ra gabatar da shugaban istingifari nace, Ya
Arrahamin Rahim sau uku, Kai ka halicceni kai ne ka azurtani da
mata saliha ka tsirar da ni daga zaluntar ta, kar ka karkatar da ni
zuwa-ga aikata zina."
"Sai kuma na sami ingantattar addu'a wajen Babana Malan
Tukur na rinka sha da zuma na tsawon kwana uku, itama ta
neman tsari daga zina."
"Sai kuma na samí wata ingantattar addu a wajen Babana
Malan Tukur na rinka sha da zuma na tsawon kwana uku, itama
na neman tsari daga zina."
68
Amiru ya yi galala yasa hankici ya goge fuska yace, "Don
Allah ya addu'ar take Yusuf?" Yusuf yace (Walata karabu zina
innahu kanafahi shatan wasa'a sabila) kafa goma sha daya.
Amiru yace, "Na yi murna da zuwanka wajen bikin nan
fiye da kowa Yusuf.Ubangiji Allah ya gafarcemu gaba daya, Allah
ya ba mu ikon rike matanmu da gaskiya da amana."
Yusuf da Falanke suka mike hanyar Bakori ya sai banza ya
sai wofi na ciye-ciye wanda zai kai ma Hadiza. Ba su iso kofar
gidansa ba sai goma na dare. A falo ya cimma su Larba sun yi dai
dai bacci na dibar su, haka nan kuma sun kunna kandir, ya ca
"Ina Kubran?" Suka ce "Ai tana daki tana bacci." Ya ca, "Don mi
ba ai ma maigadi magana ba ya tayas da injin da aka dauke wana sai ku zauna a haka?" Munari ta ce, "Ai antin ce bata fito be
tunda aka dauke wutar ko sallah ma bata yi ba, saboda bata lafiya amma Basiru ya kawo mai yi mata allura shi ne Gwoggo ta
ce kada mu tashe ta." Munari na kai karshen maganarta, Yusuf ba zai iya cewa ya tantace da komi ba ya watsar da abin da ke hannunsa ya waiwaya ya dubi Falanke, sai yasa kai zuwa dakin da Hadizan ke kwance, wani abun al ajabi ya cimmata ta yi laga-laga ta galabaita cikin amai a bisa kafet duk amaine Allah dai ya rufa asiri aman ya tsaya na ruwa, domin ruwa da shayi ne kawai a cikinta. Nan da nan kwalla ta kawo ma idon Yusuf a
yanayin da ya riske Kubra, ya zauna a firgice cikę da zullumi ko zai rasa Kubra ne? Ya ciccibo kirjinta gaba daya va rungumeta bisa cinyoyinsa muryarsa ta kasa tsayawa daidai, ya daure cikin rudanin murya yace "Kubra me ke faruwa da ke?" Tayi layau da hannunta ya yin da ya cafe hannun ya dora kan kirjinsa sai ya ji hannuwan sanyi karara, cikin murya ta rashin lafiya tace "Wayyo Allah D kai na, tun bayan tafiyarka na fara ciwon kai sai zazzabi,
to shine nace ma Basiru ya samo min fanadol mai kyau amma sai
ya zo da abokinsa su kai mani allura. Da farko na ji dadin allurar
domin na sami bacci amman tunda na farka ban yi zaton zan vi kwanan duniya ba."
Yusuf ya kara shiga wanin rudanin har bai san kome kuma
69
zai yi ba yace "Kubra shirya mu je asibitin Funtua." Tace "D bana
iya zama ka jure ka hakura har zuwa gobe mu koma Abuja a
duba ni a can."
Ya kwantar da ita yace "Ina zuwa". Ya cimma Falanke
yace, "ya ba ku tayas da injin ba?" Falanke ya ce, "Mun duba
ashe babu mai ne a ciki, ya jikin Hadiza?" Yusuf yace "To ni kam
sai kuma abinda Allah ya yi domin idan ma da ciwon da jahilcin
wannan bakauyen yaron Basiru, wai dubi sokonci daga ta nemi
fanadol ya debo wani wawan abokinsa ya zuba mata allura, babu
nazari balle bincike." Falanke ya bude baki yace "Me ya sami
Basiru da inin wannan kankanbar?" Yusuf ya ce "Oho! Raini mana,
don Allah ga kudi aje a sawo man injin. Falanke daga nan ka biya
ka zo min da Basiru." Ko da falanke ya dawo sai da su ka yi
kiciniyar tayas da injin haske ya sawwaka a gidan sannan Yusuf
ya zarewa Basiru jan ido yace, "Basiru a bisa wacce hujja za ka
debo wani wawan abokinka ayi ma Kubra allura?" Basiru ya shiga
yarfar da hannuwa yana yan kame kame ya ce, "Haba yaya ka
ko ga yanayin jikin Hajiya Hadiza a lokacin, ya zame min dole na
nemo taimakon gaggawa ganin ba ka nan." Yusúf ya galla mai
harara ya ja tsaki yace "To ga ta can kwance rai hannun Allah
idan har ta mutu kai ne sanadi kuma kada ka yi zaton zan taba
yafe ma, tabbas ka ja an yi mata alluran da suka gama aiki."
Basiru ya yi rau-rau alamun kuka, ya yi kokari ya baiwa
Yusuf hakuri amma kalaman su ka ki fita hankalinsa gaba daya
ya jagule. Sai su Falanke da Yusuf ke kai da kamowa akan Hadiza.
Hadiza ta sami bacci amma Yusuf zaune ya kwana yana
rungume da Hadiza, in ta motsa ya juya ta yana yi mata 'sannu
har karfe shidda na safe ya sa ruwa da tawul ya goge mata jiki
tsab kamar ta yi wanka. Yusuf da kan shi ya fiddo kwalayen da
suka yo ma kannan Hadiza saye-sayen komawa makaranta ya
mika masu tare da makuden kudade yace su biya kudin
makaranta. Sannan yace idan gari ya yi haske su koma gida
amma su shaidawa Inna Tambai Kubra ce babu lafiya shiyasa ba
za su tsaya ba sun koma Abuja don ta ga likita.
70
Karfe shidda da minti goma sha shidda na safen ya tsaya
da mota kofar gidan Gwoggo Halima ya yi mata sallama yace
sun shige Abuja domin kwana ya yi akanı Kubra jiki dai ya ki dadi.
Ta yi masu kyakkyawar addua.
Suna isowa Zariaya sai idon Yusuf ya kyallo wani
shahararran asibiti mai suna Mayfair Cliniic. Ya juya ya ce "Falanke
yi ribas mu shiga asibitin nan, a zamanin da na ke karatu anan na
san labarin asibitin akwai wata mata jair fata mai suna Dr Banu
kamar aljana tai ke don sani, bari mu shiga ta duba min Kubra."
Bayan nas ta amshe su an bude masu kati an auna nauyin
Kubra an auna yadda B.P din ta yake sannan ta rubuta dukkan
rufotonta a katin. Nas ta shaida masu ga likitan da za su gani.
Yusuf yace, shi Dr Banu ya ke son gani, tace yau lahadi tana
gida. Yusuf ya nemi kwatancen gida akia yi masu.
Cikin sa' a Dr Banu ta duba Hadiza a gidanta, a kalla sai da
su Yusuf suka kwashe awa biyu a gidan [Dr Banu tana diba Hadiza
da yi mata abunda ya dace, cikin ikon Allah ciwon kai ya sauka,
sai rashin jin dadin jikinta da kwabewar ibaki, bakinta ya yi takab
kamar wadda ta yi watanni tana ciwo. Daga karshe Dr Banu ta
shaidawa Yusuf kada a kara yi ma Hadiza allura ko shan magani
sai da izinin likita domin tana da shigar ciki na sati uku.
Yusuf yayi jagwale ya rinka jin kamar ya koma Bakori ya
shake Basiru, wai cikin da ya ke addu'a tun kafin ya mallaki
Kubra shi ne a lokaci guda Basiru ya nemi halakawa don tsabar
kauyanci da sokonci. Amma dai abu daya ya karfafawa Yusuf
zuciya har ya manta da tsanar Basiru shi ne bayan sun fito daga
gidan likita Falanke ya mike hanya santal sai Hadiza ta rausayar
da sanbala sanbalan hannayenta a bisa Yusuf yayin da shi kuma
duk ya tattaro hankalinsa ya dora akanta yana hanzarin son ya ji
abin da zata fada. Tace a hankali "D bakina babu dadi amma da
zan samu sakwara miyan ganye da na ci." Nan da nan murna da
zumudi suka kama Yusuf tabbas sauki ya samu, ya umurci Falanke
da su biya Shagalinku. Anan ma an yi sa'a domin sai da gidan cin
abinci na Shagalinku suka lissafa masu suna da miyar ganye kala
71
uku, Yusuf ya dubi Hadiza sai ta yi mai murmushi tace, "Na fi son
miyan shuwaka."
Yusuf bai yi odar na shi abincin ba sai da ya ga
majinyaciyarsa ta dan ci abin kirki sannan ya yi odar dankali da
koda da kwai da shayi ya dan kakkafe ido yana zolayar Kubra
yace "Kubra a zo a taya ni mana kada ki manta ni ma fa na sa
ma naki abincin albarka." Hadiza ta rausaya kai tace, "Haba D,
so kake na yi amai ko?" Yace "Sai na tara maki hula ta ki yi a
ciki." Tace "Baka jiye min wahala kenan?" Yace, To me kike so
na sai maki yanzu?" Ta dube shi ido cikin ido tace "lemo tanjirin
da goro." Ya yi dariya yace, "Oh ni dan Yusufulle Allah Yasa dai
cin goron ba mai dorewa ba ne domin bana son wa'annan
kyawawan hakoran su yi ja."
Ciki dai sai da ya shiga wata hudu sannan Hadiza ta koma
hayyacinta har ta fara jin dadin amarci. Sau biyu Inna Tambai da
Gwoggo Halima Basiru na kawo su har Abuja suna gayas da
Hadiza. Ba wai gidan Yusuf ba kadai hatta 'yan aikin gidan
Gwoggo Halima kamar ta hade su don so da kauna. Albarkacin
Yusuf, babu jin dadinta irin yau ga ta a gidan Yusuf na Abuja tare
da matar da suke so kuma har da juna biyu; ko tari Hadiza ta yi
sai Gwoggo Halima ta ji har cikin ranta, wannan irin son ya rinka
dawo ma da Hadiza tunanin mahaifinta, ina ma yana da rai ta
auri Yusuf? Amma anya ko Yaya Amina na son ta domin ko da ta
ji labarin rashin lafiyar Hadiza na juna biyu ne babu abinda ta yi
illa tsaki da kin yadda ayi maganar.
To wajen aikin Hadiza ma dai har yanzu tana bisa aikinta
tun tarewanta Abuja takardan taransufa dinta ta iso a daidai
lokacin da ta sami wata biyu gidan Yusuf haka dai ta rinka zuwa
aikin cikin ciwo ga wani masifan kyau da tayi saboda haka sai ta
rinka ganin kamar duk mazan da ke shiga bankinsu ita kadai
suke kallo, wannan abu ya dami Hadiza don haka sai ta yanko
yadi kala-kala ta baiwa Falanke ya dinka mata manya-manya
72
hijabai ta rinka zubawa idan zata aiki amma duk wannan bai
janye wasu kwazababbun mazan ba da yawaita kallonsu a
fuskarta ko kuma kyawawan yatsunta.
Yauı wata bakwai kenan da auırensu kuma watannin cikinta.
da yamma tana kwance bisa cinyar Yusuf hannun Yusuf na bisa
kan Hadiza yana warware mata kitso, yayin da idanun Hadizan
ke lumshe tunani ya rinka karakain a a zuciyarta, ita dai kawai ta
san ta yi sa'ar miji domin irin dawainiyar da yake yi akan ta itta ta
san bata tba shi wadatattar kulawa saboda yanayin aikinta, sau
tari bata dawowa daga aiki saigab da mangariba kullun shi Yusuf
aka fi samu a gida yana aiwatar da abinda ita ya dace ace tana
yi sannan kuma bai nuna damuwarsa haka nan ita gaba da ya a
tsarin rayıuwarta sai take ganin aikin banki bai dace da ita ba in
dai tana son gyara lahirarta. Waya ta yi kara ta katse tunanin
Hadiza, Yusuf ne ya mikar da hannunsa ya dauki wayar, Hadizan
Jos ce bisa layi tace, "kwana hudu Yusuf ba zuwa babu waya,
ka san dai don ta Hadiza ba za a yi zumunci ba daman kai ne mai
kwaranniyar gidan na ku." Yusuf ya yi dariya yace "Gaskiya ne
Hadiza kwarai ko na kwna biyu ban kira ki ba abubuwan ne sun
mani yawa, ga kula da Kubra sannan ga lura da shi ainihin bebin
domin yana matsawa Kubra da rigima sai idan ina kusa ina taya
ta hidima da shi." Hadizan Jos ta kyalkyale da dariya tace "Da
alama za' a haifo mai rigima inn ka."
Hadiza ta mike zaune ta ams he wayar daga hannun Yusuf
tace "To ina jin irin sharrin da ake man har jaririn da ke ciki ba ku
raga masa ba ko?"
Sun jima ana wasanni irin na aminan junan daga bisani
Yusuf ya roki arziki da cewa 'yar JJos ta shirya ta raka su sayesayen jariri gobe. Aka aje wayar da wannan alkawarin.
A vvata alhamis rannan Hadiza ta yi sa'a ta dawo aiki da
wuri kamar kowanne ma'aikaci, bayan ta idas da sallar la'asar
sai ta fiddo akwatuna har uku na kayan jariri tana gyarawa tare
da kiyasta kudinsu a zuci yanzu dai cikinta wata takwas hatta
kayan da zata saka ran suna D din ta ya kammala ko hankicin da
73
zata yi anfani da shi ba wai bebin ba sai da ya tabbata ya saya.
Hadiza ta yi jigun tana tunani to wai ita ina anfanin aikin
da take yi? Na farko dai bata baiwa Yusuf kyakkyawar kulawa
sannan ga shiga fitinar maza kullun, kuma ko sisi baya bari ta
kashe cikin albashinta ya dauke mata nauyin komi, shin wai me
zai sa baza ta hakura da wannan aikin bankin ba ta rungume
Yusuf da kyautar da Allah ke shirin ba su?
'Salamu Alaikum' Yusuf ne ya turo kofar dakin Kubra ya
shiga ya cimmata zaune dirshan bisa kafet ta yi daidai da kayan
jaririnsu ta waiwaya ta amsa masa yace, "Na kwalla kira Kubra
kamar sau uku amma na ji ki shiru, duk shirye - shiryen haihuwar
ne, ai ni ba ki sani ba Shugabana zai takura min kwarai ainin, wai
London za mu ni da shi nan da sati biyu." Ta dube shi tace, "Shi
ne me D, kai za kai min haihuwar? Don Allah kada ka damu kuyi
tafiyarku, inda duk ka ke addu` a ce taka, ni ba ka san ma abinda
ke damuna ba wallahi ni fa so na ke na aje aikin nan." Yusuf ya
fiddə ido yace "Me ke damun ki ne Kubra? Ki aje aiki fa ki ka
ce!" Ta yi dariya tace, "To menene na zaro idon aiki kala nawa ne
ya halatta ga diya mace?" Yusuf ya aje hularsa a jikin gado ya je
ya zauna kusa da ita ya ce "Don Allah Kubra idan har da gaske ki
ke to ki fasa ki rufa min asiri da bacin ran Yaya Amina don ba za
ta so aje aikin ki ba." Hadiza tace "Bacin ran ta za mu duba koko
haduwa ta da Ubangiji? Ka ma daina wannan maganar, ilmi dai
na yi don tspron lalura amma aiki na hakura da dai na zabi fannin
da ya dace ne to." Yusuf yasa hannú ya dafe kai ya dago ya dube
ta yace, "Kubra ban amince ba, ki tuna fa duk wahalad ilmin ki
babu wanda ya sani sai Yaya Amina da `yan uwan mijinta, dama
- dama idan da Baba Kado da ni mu ka sha dawainiyar ilminki sai
na amince, amma yanzu kullun ina kokarin na ga mun shirya da
Yaya Amina sai kuma ta ji ance kin aje aiki dole zata kara tsanata."
Hadiza ta sha mur tace "Kana nufin ta nemar min ilmi ne don na
nemar mata kudi koko?" Ya dube ta nan da nan ya razana don ya
ga irin kallon da baya so idan ranta ya baci ya gyara zama yace
"Look Kubra ki fahince ni mana wane irin zance kuma ki ke......
74
" Tace, "To na fahinta kai ma ka fahince ni. Zan bar aiki don
tsakanina da Mahaliccinmu ka gane?" Ya dan dube ta har yanzu
bata daina irin kallon da bai so ba sai ya ce "To na ji amma don
Allah ki ban lokací zan yi tunani ko mi kenan zan sanar da ke." Ya
yi haka ne domin baí son abinda zai kawo rudani tsakaninsa da
Kubra saboda ya lura ta fusata, shi kuma ba wai yana son aikin
nata bane dole sai dai yana tsoron Yaya Amina.
Bayan sallar isha'e da Yusuf ya dawo masallaci ya tsaya
jikin wata itaciya a harabar gídansa yana tunanin matakin dauka
yadda ba zai batawa Yaya Amina ba kuma ba zai cutar da Hadiza
ba. A karshe ya yanke shawarar da ya ke ganin ta dace. Ya iske
Kubra kwance bisa gado ya isa gare ta ya zauna a bakin godo,
ya yi tagumi da hannaye bibbiyu ya kira sunanta 'Kubra' ta amsa
'Na'am' yace "Zai yi kyau ki shirya ki je gida can Malunfashi
wajen Yaya Amina ki nemi shawararta kaman yadda ki ka nemi
tawa ko?" Ta dan runtse ido tabbas itama tana shakkan tunkarar
Yaya da wannan magana, sai tace, "Amma tare za mu ko?" Shi
ma gabansa ya fadi ras domin irin yadda Yayar ke nuna masa
abun ya fara baci, a kwanan baya za su Katsina daurin aure sun
biya gayas da ita shi da abokinsa da kyar ta amsa, da zai tashi ya
aje mata dubu biyar, amma abin mamaki yana shiga mota ta
aiko karamin danta ya aje mai kudin a cikin motarsa, wannan
abu ya yi ma Yusuf ciwo domin ko darajar abokinsa bai sa Yaya
ta raga mai ba.
Ya ja dogon ajiyar zuciya yace, "To Kubra idan dai kina na
raka ki zan raka ki, amma zan ba ku hili ku yi shawara wallahi
tsoron Yaya nake." Tace, "menene abun tsoro game da maganar
lahira, ni dai idan ba ka zuwa ni ma ba za ni ba." Ya jingina jikinsa
zuwa jikin Hadiza ya lumshe ido ya shiga tunanin yadda za su
wanye da Yaya Amina.
Ranar asabat da azuhur suka isa gidan Yaya Amina, sun yi
sa'a Yayan na daki tare da wata tsohuwa Gwoggon Yayarce,
don haka sun sami kyakkyawar marba wajen Gwoggon da ta
zan kaka ce ga Hadiza, ta rinka yi ma Yusuf wasa na maigida.
75
a
Bayan sun jima cikin barkwanci Yusuf ya dubi Hadiza yacе,
"Zan koma dakin Saminu na jira ki." Sai Yaya Amina tace "Tafiyar
me za ka yi, itama ta tashi ku tafi mana." Gwoggo ta juya
fusace tace. "ke Amina ya kamata ki sakar ma yaran nan mara,
ina dalilin irun wannan riko? Ko wannan rabon ai ya dace ace kin
janye hushin ki." Amina ta kawad da fuska gefe daya cikin nuna
jin zafi tace "Ni ban ce ina hushi da su ba Gwaggo, harkarsu се
dai babu ruwa na." Yusuf dai ya mike ya yi waje.
Hadiza ta karkace kai ta ce, "Yanzu ma matsawa ya yi
wai sai na kawo ma Yayan shawara don na ce masa ni, fa zan aje
aiki." Yaya Amina ta galla mata harara tace, "zancen wofi ina
kuma ruwa na da aje aikinki? Ke daman yanzu kina da wani aiki
ko sha'awa wanda ya zarce nashi? Ai bukatarki ta biya kin fake
da karatu sannan aiki kina zaman jiransa to kin same shi me
kuma zaki ci da aiki?" Nan da nan hawaye tar daga idanun Hadiza
tace, "Wallahi Yaya ba haka ba ne, matsalar aikin namu ne, ba ta
matar aure ba ne---". Gwoggo tace, "Ke Dije kuna dai zaman
lafiya da mijinki ko?" Hadiza tana share hawaye tace, "E
gwoggo. Tace "To ki aje aikinki ki bi mijinki sau da kafa, Amina
ko ki bar ni da ita kada ki kara kawo mata irin wannan shawarar."
Da suka tashi tafiya Yusuf'ya kawo kudi kamar yadda ya
saba ya baiwa Yaya Amina itama Gwoggo aka bata na ta rabon
mai tsoka.
Kamar Gwoggo Halima ta san da zuwansu dan lokaci
kankani ta shirya masu abinci iri iri, Hadiza ta yi rashe-rashe a
dakin Gwoggon tana ta zuba shagwaba, kai ka ce Gwoggo tà
kawo ta duniya, ita ko Gwoggo Halima sai kara rawan jiki take
yı ganin ciki dai ya bayyana fili jikin Hadiza.
Yusuf vace, "Gwoggo ina son ku je Abuja ku zauna ke da
Inna Tambai nan da sati biyu saboda zan yi tafiya London." Gwoggo
tace, "To Allah Ya nuna mana; a dai dai nan Malan Tukur ya
shigo, bayan an jima da gaisawa Halima ta sanar da shi bukatar
Yusuf, Mallam yace "ban yadda ba, abu duk taron mata?" Nan
da nan Yusuf va rude yace, "Baba wai saboda asibiti kuma ga
76
Falanke." Mallam Tukur yace, "Wani abu ne Falanke? Me zai iya yi, haihuwar farko ce fa, sam ka maido mana ita nan Bakori a
gabanmu, kai ko ka tafi wajen aikinka." Yusuf ya yi jagwale yana son ya hada ido da Hadiza amma ta ki yadda.
Yadda Mallam yace hakan aka yi domin baya da ubar da
ya fishi, yace, "Ni abin da yafi damuna shi fa Baba saboda wankan
ganye ya ke son a maido ki Bakori ni ko ba don sun yi min ta
karfin tisya ba ban yi niyyar su yi ma ki wankan gargajiyar nan ba." Hadiza ta yi dariya tace, "kai D wallahi ka daina irin wannan
rudewan akan al` amurana, kada ace ka faye zakewa akan mace,
menene idan ma na yi wankan, ina ce suma su Gwoggon sun yi ga su nan sumul ina ma laifinisu, ita Yaya ko kallo cikin ma ya ishe ta?" Yusuf ya shafa kai yace, "Ai itama Yayan da dalili
take yi mana haka babu komi mu ci gaba da addu'a insha Allah
sai ta yi ma wannan jaririn rawa tana juya shi."
Hadiza dai ta rubuta takardar aje aiki ta kuma kai masu kayansu, yanzu ta mike kafa a gidan Yusuf. Ana sauran kwana
biyu tafiyar su Yusuf ya hada kayan Hadiza da