da kut zata aura."
Yallabai ya yi shiru tausayin Yusuf ya kama shi balle ma
da yaron ya nuna mai shi maraya ne, duk zuri`arsu a kan shi aka
rataya, sai ya ce ma Yusuf "To kai ba ka dan sakarma iyayenta
31
kudi ne ko kamar abokin na ka?" Yusuf yace, "Inal Yallabai ai
wa'annan sun fi karfin a rude su da ku". Yallabai ya yi dariya
yace "kai wawa ne ba ka san halin kanawa ba kenan. Bari na
baka wani guntun labari: akwai wani bakano za shi England neman auren baturiya fara kal, sai abokansa suka ce masa 'wai wai Alhaji ka rufa mana asiri, kai da ba ka jin turanci ita kuma bata jin hausa? Ka dai ci gaba da auro filanin mata kyawawa', sai Alhaji ya yi dariya ya sa hannu aljihu ya fid do takardar 'yar wazobia wata naira hamsin ya daga masu ita yace, 'kun ga wannan, to babu yaren da ba ta ji a duniya, sai dai idan baka da ita'. Yusuf da Alhaji suka bushe da dariya.
Yallabai yace, "Gobe zani gida Katsina sai ka shiriya zan tsaya Bakori na ga iyayen ita yarinyar wa anda su ke da karfi
akan maganar, sai ka shirya da wuri karfe takwas na safe." Yusuf ji yake kamar an ce an bashi Hadiza dan murnar
Yallabai zai sa baki a al'amarin. Karfe goma sha daya na safe suka isa gidan Inna Tambai. Yusuf ne ya fara shiga ya firgita
Inna da cewa ta yi manya-manyan shinfidu ga shugabansu nan gaba daya ya zo ganinta, ai ko Inna ta rude har wata darduma ta shinfida bisa tabarma.
Sun jima ana gaisawa yawancin gaisuwar a bisa matuwar
Baba Kado. Sannan Yallabai ya gangaro bisa zancen Hadiza shi
dai Yusuf na gefe ya takure, (manya na magana).
Yace, "To Inna Tambai ai ina ganin da kai da kaya duk mallakar
wuya ne, ki tuna fa ke mai nemarwa Yusuf aure ce, bayan
kuskuren da yayi domin ko ita takun Ubangiji na iya jarabar ta da
irin hakan, shin ashe idan da ta yi wani aure sannan ta fito ta zo
tace a duniya kuma babu wanada take so sai Yusuf ashe
mahaifiyarsa bata isa ta tursasa Yusuf ba akan ya yi hakuri ya
auro Hadiza, domin kamar kanwa ce a gare shi? Dole ne kuma
ya aureta ba zai ki ba domin kuskuren aure ba inda ba a yin sa.
Amma yanzu inna kuna kallon Hadiza kun kyale ta zata bar
dan uwanta akan wani kuskure kalilan na kuriciya?" Inna Tambai
nan da nan ta ga gaskiyarsu anan, domin ta sha ganin yarinya ta
32
ki mijin sai daga baya, a dawo a neme shl bayan ta yi aure ta hayayyafa, kuma a rnatsawa namijin dole ya aura hakanan bayan
a da can babu irin wulakancin da bata yi mai ba. Yallabai ya katse tunaninta yace "Wannan Amiru ba fa halin sa kuka sani ba, bayan Yusuf tun yana cikin ciki kun san halinsa. Don Allah ki natsu ki sami lokaci ki yi ma Hadiza nasiha irin taku ta manya".
Inna Tambai tace, "Ranka shi dade wannan zance na ka fa
abun dubawa ne, na yi ma alkawari zan yi iyakar kokarina, sai
dai kuma idan haka Allah Ya kaddaro, to sai Yusuf yasa hakuri"
Yallabai ya ji vwani irin sanyi domin babu wanda bai son ya
nemi alfarma a ki yi masa, to anyi mai alkawari yace Yusuf ya
dauko mai jaka cikin mota. Yusuf ya fita da sauri ya kawo jaka
ya tsugunn yaba shi, ya bude ya fiddo bandir din 'yan wazobia
sabbi fil na dubu as hirin ya baiwa Yusuf yace ya mikawa Inna Tambai.
Inna ta bude hannaye tace, "kai Yusuf ina zan kai
wa annan kudi ku bar su kawai". Ya yi dariya yace, "Haba Inna
ku amsa, karamin aikin Yallabai kenan idan ki ka ji babban sai ki rike baki."
Sun isa gidan Malan Iliya motar Yusuf ce gaba ta Yallabai
na biye, sun kuma ci sa'a Malam din na gida. Bayan an gama
gaisawa Yusuf ya gabatar da Yallabai kamar yadda ya gabatar
da shi wajen Inna Tambai, shi kuma Yallabai ya shiga kurunta
matsayin Malam Iliya a wajen Baba Kado, ya nuna masa shi kadai zai iya lankwasa Hadiza har ta saurari Yusuf.
Malam lliyasu yace, "Ba haka ba ne, shi sha anin aure ba
ai mai shishigi, haka nan ba za mu iya ja da ikon Allah ba, sannan
ni yanzu Hajiya Hadliza tausayinta na ke ji, sanin tsakaninsu da
mahaifinta, ba zan so na kara mata wani zafi ba a zuciyarta idan
na yi haka ban taimake ta ba, na zalunce ta. Yallabai yace, "A'a
ba wai muna son ka tursasata ba ne, a`a cikin nasiha dai". Yace,
"Na yi maku alkawari in dai har ta nemi shawarata zan nuna
mata gaskiya abinda ya dace".
Anan ma aka danna mai dubu goma, suka kidima mai
33
kwanva.
Yusuf basu yi sallama da Yallabai ba sai da ya kara
gargadarsa da cewa lalle ya makalewa wa'annan 'yan tsaffin
guda bıyu yana ganin akwai nasara a wajensu.
Y isa gida wajen mahafiyarsa. A gaskiya ran gwoggo
Halima ya fra jaqulewa a yadda ta lura da sigar dan ta Yusuf ta
fara canzawa, ya zauna ya yi jagwale bai son yin ko wacce irin
magana domin va san ba abinda gwoggo Halima zata yi masa, ta
shiga kawo mai labarai amma bai kula ta ba domin bai san ma
abin da take cewa ba, itama sai ta sa masa ido ta yi shiru zuwa
can tace, “To wai kai yanzu haka za kai ta jerangiya bisa hanya
akan neman auren da bashi da tabbas, ni fa ina jiye ma aikinka?"
Yusuf ya yi kasake yace, "Ba haka ba ne gwoggo, yau ma tare
mu ke da shugaban nawa har gidan Inna Tambai na kai shi, a bisa
dukkan alamu mun fara samun kan Inna Tambai."
Abin ya yi ma Halima dadi, sai ta ce “Ni ma zan shiriya na
je anjima da yamma".
KASHI NA GOMA SHA HUDU
lyakan tika-tika tik komi ya yi farko zai yi harshe, masu
tatsuniya kan ce tsakani-tsakani tsakanin gizo da koki in a gizon
ba koki, to mu kuma anan mun ce in ba Yusuf ba Amiru, yau dai
sauran kwana goma sha takwas kacal ayi sadakat arba'in din
Baba Kado haka nan a bisa alkwari sauran wa'annan kwanaki a
aurad da diyar Baba Kadon Hadiza ga mai tsananin rabo.
Zamu iya cewa zamani rikicewar rayuwar zuri'ar gidansu
Hadiza da Yusuf da Amiru, yayin da kowa ya ke fadar albarkacin
bakinsa. Duniya ta yi wa Hadiza kunci, komi daci ya ke mata na
cikin duniya babu abinda ke birgeta babu wanda ya ke bata
sha'awa, maganar soyayya kwata-kwata wannan baya cikin ranta
illa daga Amiru har Yusuf tana ganinsu bakirkirin, domin ta ga ita
iyakar gwargwado tana nunawa Yusuf wulakanci, to amma shi
Aniru a 'yan kwanakin nan ya fitittike mata sai a zaba akan wai
34
laifin ta ne Yusuf ke zuwa gidan iyayenta, tace "kana nufin tare
da shi na ke yawo koko?" To ire-iren wannan maganganun ya fara haddasa masu matsala har to fara tsanar Amiru, yayin da
shi ko Yusuf tana ganinsa akan mara tausayi wanda bai damu da
kowa ba sai kansa, domin duk shi ya haddasa mata wannan bala'in maimakon ya bar ta taji da dacin mutuwar mahaifinta.
A Abuja su Yusuf da Falanke sun lura da yawancin
abokansu, yanzu an rabu gida biyu, akwai masu zuga Yusuf akan
lalle shi ya dace ya auro Hadiza yayin da wasu suka zabi Amiru
suna ganin Yusuf bai yi adalci ba. To a wannan 'yan kwanakin ne
da suka rage kowanne ke nuna tashi bajintar don dai aga wanda
zai nasara. Su Yusuf suka zuba kamar mutun uku wa'anda ke
bin Amiru a gindi a gindi don a san abinda ya ke ciki, rufoton
farko an kawo mai labarin cewa ga cikakken adureshin kanfanin
da ya kai ayi mai aikin katin biki wato (invitation cards) kenan.
Yusuf ya yi shiru, sai ya mike ya jawo waya ya latsa lamber
Jos gidan Baba Rilwan kenan, yasa aka nemo masa Hadizan Jos
bisa layi, bayan sun dan yi bakwanci yace, "Don Allah kanwata
taimako daya na ke son ki mani" Tace "menene?" Yace, "Na san
dai ba kya rasa haton mutuniyar mai kyau ita kadai don Allah ki
taimaken ki ba ni yau din nan za aiko a karba". Hadiza ta dan yi
shiru sannan tace, "kai Yusuf wai kai har yanzu baka hakura ba?
Don Allah ka kyale yarinyar nan kada ka sa mata ciwon zuciya".
Ya yi murmushi yace, "Haba kanwata Ubangiji ya baka abu, ka yi
wasa da shi, kada ki damu wannan damuwar ta Hadiza duk ta
dan lokaci ce, da mun kasance tare sai kun yi mamaki". Hadizan
Jos tace, "To Allah dai ya zaba mafi alhairi sai ka aiko din".
Karfé goma da 'yan mintoci Falanke ya dawo Abuja daga
Jos da wasu hotunan Hadiza guda biyu kamar wadda aka kera
da luu-luu don sheki.
Wanshekare da safe Yusuf da Falanke suka je inda Amiru
ya kai aikin buga katin gayya, sai da suka sa babban ma'aikacin
a kwana suka ji ko nawa Amiru ya biya kudin aiki, sannaa suka
bada na su da hoton Hadiza da na Yusuf ya linka masa kudin
Amiru sau uku amma yawan katunan daya, mai aiki ya yi mamaki.
Vusuf ya ce, "Ina son kayi min abu daya". Yace, "Ranka shi dade
fadi ko minene za'a yi". Yusuf ya gyara tsayiwa yace, "Wa'annan kudin na ba ka su kyauta, kada ka buga min wani kati illa kawai
idan Amiru ya zo ka fiddo hotuna na da na amaryata ka nuna
masa ka ce masa, 'yaya a kai bikinmu ya zo rana daya, kuma
sunan yarinya daya sannan a gari daya?' Sai ka ja bakinka ka yi shiru kada ka kuskura ka nuna mai cewa na san ya kawo aiki anan."
To a wannan 'yan tsakanin Yusuf da Falanke ba sa iya cewa ga iyakar zuwansu Bakori, domin wani lokacin tsakar dare suke shirya tafiyar sai dai jama'ar Bakori su wayi gari su gan su. Ba tare da sanin Yusuf ba Falanke ya shirya ya je Tsiga wajen wani tsohon Malami aminin kakansa, ya fede masa bire har bindi na halin da Yusuf yake ciki. Tsoho ya yi shiru sannan ya ce, "Ina son ka yi kokari ka kawo min abu daya daga cikin wa'annan ko dai ka yanko min gefen kallabinta ko kuma sawun kafarta insha Allah idan na hada wani abu in dai har nan da
kwana biyar babu magana mai karfi to ya hakura ba matarsa ba ce
Falanke ya koma ya yi sa'a Hadiza na gidan Inna Tambai
ya tsaya a kofargida gindin wata itaciya ya aika a kira mai Hadiza
aka ce ya shiga, ya kafe ba zai shiga ba, ya matsa mata da aike
sai da ta fito, ya shiga kuranta ta yana wasa Yusuf, zúwa can ta
ce, "Abinda ya kawo ka kenan Falanke?" Yace, "Don Allah ki
auri dan'uwanki Hadiza mai kaunarki". Tace, "Falanke kuna son
ku zama sanadiyar batawa ta da mahaifiyata ne?" Yace, "Me zai
sa ki zarge mu da wannan? Ai shi aure tunda aka halicci duniya
aka san shi da rikici insha Allah mahaifiyarki sai ta yi alfahari da
aurenmu". Ta yi dariya tace, "a cikin satin nan zan fara raba kati
insha Allah ba zan manta da na ku ba Falanke, ni ka ga tafiyata,
sai anjima".
Ta juya ta rinka tafiya a tsanake, shi ko Falanke tafin
kafarta kawai yake kallo, yana kallon in da take takawa sawunta
36
na bayas da shaida.
Ya duba ko ina bai hangi kowa ba, ya fiddo wata leda ya
durkusa ya debi sawun kafar Hadiza na hagu da dama, ya kulle a
leda sai Tsiga wajen Baba Tsoho.
Baba tsoho ya dan danki kadan ya ce ta isa. Falanke ya
mayas da sauran cikin aljihu, Baba tsoho yace, "In dai na yi
wannan aikin nan da kwana biyar babu bayani to ya kyale ta".
Falanke ya fiddo kudi dubu biyu ya bashi, Baba ya girgiza kai ya
ce, "Na gode mai da kudinka ai wannan kulla sunnan Manzo ne
Allah ya ba mu lada, ya fi min wa'annan kudin."
Wannan kenan a gidar Gwoggo Halima kuma, kullun a
rikice take, gani take yi tamkar zata rasa dan da ta ke ji da shi a
dalilin Hadiza, ya bi ya sukurkuce ya rame ya tsangwame kan sa
kamar ba wata mace a duniya sai Hadiza, to har sai ta rinka
raina taimakon da Malan Tukur ke masu. A wani marece ta shiriya
ta je kauyensu Danja wajen wani tsohon Malami aminin
mahaifinta, rabonta da shi tun zamanin tana goyon Yusuf da
suka rinka samun matsala da Babansu Yusuf shi ne ta kai kukan
ta wajensa, ya yi mata istihara yace, ta yi hakuri domin shi ne
uban 'ya'yanta, haka nan akwai daukaka a cikin 'ya'yan da
zasu haifa, ya kawo taimako ya bata suka zauna lafiya lau da
Babansu Yusuf har sai da mutuwa ta raba su.
Ta isa Danja ta je wajen Malam ya rinka yi mata fada
domin bata kula shi, "Ya dace ace ko su Yusufa kina turowa
suna gaishe ni". Ta ba shi hakuri tace, "ko yanzu ma zancen shi
wannan din na zo maka da ita". Yace, "Lafiya ko?" Ta kwashe
tun farkon lamarin Dije da Yusuf ta gaya ma Malam. Malam ya
yi shiru yace, "Aure kenan! Yau sauran sati biyu da` yan kwani
bikinsu da shi wancan abokin nasa?" Tace, "E Baba, ni kam idan
wannan aure ba mai yiwuwa ba ne, na fi son ka yi mai asirin da
zai ji ta fita ransa kwata-kwata, wallahi ba ka ga yadda yaron
nan ya lalace ba". Mallam yace, "Ba komi, zan yi istahara kwana
uku ki dawo. Idan fa matarsa ce ai ba mu da yadda za mu yi, in
kuma ba matar ba ce dole ne ya hakura".
37
Gwoggo Halima duk ta kosa taji abinda kwana ukun za ta
haifar domin cudewar lamuran ta isa.
A can kuma Abuja bom din su Yusuf ya fara tashi domin
Amiru ya isa Abuja ya je ofis din wani abokinsu Ashiru bayan
sun gaisa, Ashiru ke cewa "To kai Amiru mu fa ba mu gane ba
wai daurin auren wa za mu cikinku kai koYusuf?" Amiru yacе,
"Wanda kuka zaba". Ashiru ya yi murmushi yace, "ni fa ina
tsoron yarinyar nan Hadiza a cikinku na rasa wanda take yaudara,
yanzu ran nan suna waya da Yusuf lokacin ta je Jos har ya ba ni
mu ka gaisa kai ka ce sun riga ma sun yi auren, yanzu haka cikin
satin nan Yusuf ya zo da hotunan ta, to amma duk ace wai kai
zata aura ni fa ina tsoron yanmatan zamanin nan wa'anda
idonsu ya bude, kada kana takamar ka yi aure ashe Yufuf ka
auro mawa, abinda fa mutun ke yi shi ke samunsa Amiru". Anan
zufa ta rinka karyo ma Amiru, duk wani son Hadiza sai ya ji ta
fita ransa fit, amma ya cije bai nunawa Ashiru ba, ya mike yace,
"Kai ni wannan bata damuna an ce matar mutun kabarinsa sai
kun zo daurin aure".
A mota ya rinka sake-saken ba zai yadda Hadiza ta yi aiki
ba, ko alama, domin a ganinsa itace barakar da zai bar wa Yusuf
da Hadiza har su rinka saduwa.
Ya isa wajen buga katuna anan ma ya cimma sakon Yusuf
kamar yadda ya umurci ma aiki ya aiwatar, ganin wani matsiyacin
hotan Hadiza da na Yusuf, sai kawai Amiru ya amincewa ransa,
wannan aure ko ya auri Hadiza shi da Yusuf ke da ita domin idan
ya hana ta zuwa aiki zai hana ta ziyarar 'yan'uwanta ne a Bakori?
Komi zai iya faruwa idan taje ganin gida wannan tunanin ya rikitar
da komi na Amiru.
Da ya bar wajen buga kati sai ya fasa komi na al'amurar
kasuwancinsu ya koma Kano.
Da aka yi sallar isha'i ya kintsa ya nufi falon manifinsa ya
cimmasa tare da Alhaji Kabir. Bayan ya gayas da su, ya koma
gefe daya ya takure, Alhaji Kabir yace, "Yaya ne Amiru wani
abu ke tafe da kai?" Alhajinsa yace, "Ai shi ne, shi da muka yi
sallama jiya akan ya tafi Abuja sai jibi zai dawo kuma ga shi na gan shi yanzu."
Amiru yace, "E Baba daga Abujan na dawo, dole ce ta ja min dawowar, a gaskiya lamarin auren nawa yana ba ni tsoro, shi dai wannan abokin nawa Yusuf kusan yanzu ince ya fara juyarwa da Hadiza hankali, to ni abinda nake zullumi daya ne, kada mu yi aure da ita, daga baya ta rinta munafunta ta suna hulda ta can garinsu idan na yi magana tana iya cewa ya zata yi kamar wa ne a gare ta, To wannan shi ne üzuri na yanzu haka inda na bayar da aikin kati na iske shi ma ya kai na shi aikin katin shi da ita."
Alhaji Kabir yace, "Kai Amiru kada ka zama wawa mana ka san Katsinawa fa shakiyay ne. Yanzu haka ya kai na shi katin
ne, ganin ka kai don ya ruda ka, ka zargi yarinyar." Alhajin yace, "E da wannan amma ka san halin Katsinawa shegen hadin kai ne da su, ni kam tun kwanan baya na shawarce shi ya kyale auren nan, duk a yi a gama hade mai kai za su yi. To bai hakura ya
dawo gida ya auri kirinmu? Ni kam idan za ka bi shawarata ka
kyale su, domin har auren ya fita kai na, wannan irin fitina! Bana
son fitina ni ka gan ni nan."
Alhaji Kabir ya gyara zama yace,"'Ya'yan yanzu ne ba a
sha ma ku alwashi, amma mene ne abun zuwa neman aure har
Bakori Amiru, ga ya ya nan a gidana? Yanzu haka za`a sami
yan mata shidda wanda suka kammala karatu, sun kuma isa
aure. Da za ku amince sai kaje gidana ka fidda wadda ka ke so,
Insha Allah ranar da aka sa maka ba a fasawa za`a kawo maka
mata."
Amiru ya koma dakinsa ya kwanta ya yi lamo tunanin
rayiwar da yaso ya shirya da Hadiza ya rinka rushe ta a hankali,
yasan zai so 'ya'yan Baba Kabir domin su Maryam da su Salma
da sauransu duk babu ta yardawa kodayake babu mamaki matan
Alhaji Kabir biyu amma fa larabawa ne, ya yi kuma sa'a gaba
daya 'ya'yan sun debo kalar iyayensu mata.
Kashegari da azuhur ya daidaici lokacin da Alhaji Kabir
39
bai gida Amiru ya kai ma gidan ziyara,ya cimma 'yan matannan
shidda cif har da 'yan gutsatsi suna zaune a falo malaninsu na yi
masu karin karatu, abun ya burge shi domin kowacce ta sauke
alkurani tilawa take yi. Amiru ya zauna yana kallonsu daya bayan
daya ya rasa wadda zai zaba don kyau (daman Bakano da farar
mace?).
Bayan an yi addu'a an shafa kowacce ta juyo tana cewa
"sannu da zuwa Yaya". Ya amsa masu sannan yace, "Ashe Baba
Malamai ya tara mana a gida haka?" Suka yi dariya, yace "zan
sami lokaci na zo daya daga cikinku ta rinka koyar da ni". Suka
yi dariya. Salma ce sarkin wayonsu da surutun tsiya itace tafi
zakewa wajen zance da shi har tana cewa, "Yaya mune dai 'yan
gaba gaba wajen liyafar bikinka ko?" Yace, "Babu ma kamar ke,
ga kujerata ga taki". Ta ce, "Wai Yaya an ce 'yar Katsina ce
kuma wani dan Katsina na son ta?" Ya yi dariya kawai tace, "To
Yaya a ina za ku zauna ba dai can Katsinan ba kada fa ta raba
mu da kai.”
Maryam ta daka mata tsawa ta ce, "wai ke me yasa kike
da shegen surutu ne Salma?" Amiru ya yi murmushi yace, "Kyale
ta mana, ai ni ina son mace mai fadar abinda ke ranta, bana son
kumbiya kunbiya. Gobe ma ki shirya. Salma zan zo ki raka ni
kasuwa, amaryata ta ba ni sako ni kuma ban iya sayayyar mata
ba."
To a gaskiya Amiru ya kwana tunanin yadda Salma ke
surutu ko babu komi ta debe mai kewar damuwan rashin Hadiza,
haka wanshekare ya dauketa suka yini tare yana yi mata sayesaye, ya kawo kayan dakin sa ya aje da niyyar'su zai bata а
ranar sayen bakinta mai surutu, amma a yinin rannan ya mallake
zuciyar Salma kaf.
A kwana daya, kwana biyu zuwa kwana uku Amiru ya
gama shiryama zuciyarsa cewa Salma ta dace ta zama
uwargidansa ta kowanne irin mataki, haka nan ya san shi mutun
ne ba mai son yawan magana ba, amma yawan surutun Salma
sai ya zamar masa abin yabawa, domin sai ya rinka jin wasu
40
maganganun nata suna da ma'anar sauraro. A kullun ya kan kira
ta a waya amma sai karfe goma sha dava na dare, yayin da zasu
kai har asuba suna bayyanawa junansu irin rayiwar da su ke
sha'awar shiryawa.
Bayan komi ya daidaita tsakanin gidan.su Aminu da na
Salma abin nufi sun amince za'a daura auren Amiru da Salma
kaman yadda a kai niyyar yi a da da Hadiza amman mahaifiyar
Salma ta nemi alfarmar a bar shagalin biki sai bayan sati hudu
domin 'yan'uwanta na birnin Misira su sami halarta.
Sati biyu kacal yanzu ya rage a daura auren Amiru da
Salma, Hadiza fa, Allah ga wa? Amiru ya yi waya Kaduna aka
ce ai Hadizan na Bakori.Ya yi murna da jin haka sai kawai ya
dauki yukunbonsa suka nufi Bakori.
Hadiza da Inna Tambai suna tsakargida suna sallamar wasu
samari da suka sa aikin shirya masu kaya a dakin zaure wato
kabet ne da gado da madubi da waduruf Hadiza ta yo oda daga
wani kanfani a Kaduna na gogaggen katako sai walkiya da sheki
su ke, Inna Tambai, ta rinka yabawa tace, "Kai Hadiza amma fa
kin yi kaya da kyau sai dai tsada". Hadiza ta yi murmushi tace,
"Amma Inna rai da rai ne fa! Idan ka gaji da wannan fantin za ka
iya canzawa, kuma katakon bai komi."
Yakunbon Amiru ta yi sallama ta shigo, nan da nan Hadiza
ta fara sunkuye- sunkuye nuna alamun jin kunya, Inna Tambai ta
kai ta daki ta debo mata ruwa suka shiga gaisawa sannan Hadiza
ta leko daga can bakin kofa a tsugunne ta gaida Yakunbo, sai
Yakunbon tace, "Ke Hadiza tare muke fa da Amiru yana can
kofargida."
Hadiza ta mike a cikin jin kunya ta surutuka, ta ce, "To".
Ta nemi tabarma ta nufi zaure, yana tsaye a zaure rike da wata
yar karamar casbaha, ya daga kai ya dubi Hadiza ya amsa mata
sallama yana mai 'yar siririyar dariya yace, Hajiya Hadiza!' Tayi
murmushi tace, "Yallabai barka da zuwa, zauna mana". Ya cе,
"Na gode". Ta zauna itama a gefe guda na tabarma tace "Menene
na godiya kuma?" Ya ce "Ai dole ne wanda aka karrama da
41
gurin zama?"
Sun jima yana yi mata dan barkwanci, sai ya rasa ta fuskar
da zai iya bullowa Hadiza da cewa ya fasa aurensa da ita, domin
mutuncinta da kamun kan ta zuwa kwarjinin da Allah ya yi mata
sun cika masa fuska, zuwa can Hadiza ta ce, "Ina fatan ka zo
mana da katin gayya domin ina son aikawa da na jama`ar nesa".
Amiru ya tsurawa Hadiza ido sannan ya sunkaya yace, "Anya ko
Hadiza zan kawo katunan nan kenan?" Gaban Hadiza ya fadi ras
"Me kuma ya faru, Amiru?" Wannan itace tambayar da ta fito
daga bakin Dije cikin murya mai fargaba.
Amiru yace "E to ya zama dole na yi nazari a bisa al'amuran
aurenmu da ke daga bisani na nemi shawarar magabata na, to
sun nuna min yin hakuri zai fi alhairi a gare mu"
Hawaye wasu na bin wasu daga idanun Hadiza har ta kai
Amiru bai iya hada fuska da fuska da ita don tsabar tausayi
saboda ya tsani mace na kuka balle macen da ya ke da tabbacin
ransa na so ya dai hakura da ita ne akan tilas.
Cikin murya mai sheshekar kuka ta ce, "Amma Amiru
idan ka bar ni ka ci amana ta, me aka fasa cikin shirye-shiryen
aurenmu?" Ya kara kawad da kan shi gefe daya yace, "Hadiza
ban ci amanarki ba domin na dawo maki da wanda ki ke so ya ke
son ki, kuma dan uwanki kamar yadda ki ka gaya min tun farko".
Ta kara share hawayenta da gyalenta yayin da wasu suka tararo
tace, "Wannan zance kana yi ne a bisa son zuciyarka babu wani
son da ke tsakanina da Yusuf wanda har zai sa kace ka fasa
aurena."
Ya dan yi shiru yana tunani shin ko dai kishi ya ja masa ya
yi wawanci! Lalle Hadiza na son shi, to yanzu ya zai yi, ya ce ma
Yakunbo ta bar kaya kar ta amsa a ci gaba da aurensu shi da
Hadiza har da ita Salmar, nan ne ma zai gane wadda tafi son shi
idan suna rayiwar aure?
Yace "To Hadiza yanzu kam zancena ya koma hannun
manya!" Tace "me ka ke nufi?" Yace, "Baba Kabir ya ba ni mata
42
Gaba daya tun daga zuciyar Hadiza har cikin idonta sai ta
rinka ganin duhu lunfashi ya rinka kokarin dauke mata, ta sa
hannu ta danne kirjinta, ta rinka kuka a bayyane, Amiru ya juyo
a firgice yace, "Shi kenan Hadiza zan iya hada ku ku biyu idan su
Alhaji a can Kano sun amince min."
Hadiza ta girgiza kai tace, "Babu komi Amiru ban ce ka
roki kowa ba wai don ka aure ni insha Allahu Allah zai ba ni miji
lokacin da ya dace na yi aure". Ta rinka addu` a a ranta wadda
zata sami natsuwar ranta don hakalinta ya dawo jikinta, yayin
da shi kuma Amiru ya rinka lallashinta yana yi mata nasiha, ta yi
shiru sai dai goge hawaye akai akai.
Amiru yace, "To Hadiza na gode kwarai da irin kaunar da
ki ka nuna min Ubangiji Allah Ya sa yadda mu kai din nan ta
zamar mana alhairi baki daya".
Hadiza ta yi juriya tace "Amin Amiru, ni ma ina godiya ga
niyyarka ta aurena