da ka yi, wanda yasa mahaifina ya rasu cikin
kwanciyar hankalin ya bar ni da miji na gari na gode da wannan
taimako a kodayaushe ba zan manta ba."
Yace, "Babu komi Hadiza aure nufin Allah ne, insha Allah
ba za ki yi dana sani ba da auren Yusuf". Ta daga mai hannu ta
ce, "Zancen Yusuf ba ya tare da ni don haka ka bar zancen kawai."
Yace, "To na bari, ina da hoton Salma a mota ko kina da bukatar
gani na kawo maki?"
Wannan shi ne lokaci na farko da ta taba tsanar Amiru
tace, "A'a bani da bukata". Ya dan cije lebe yace, "Ba dai kishina
ki ke ba ko Hadiza?" Ta dube shi da kyau ta ce, "idan ma har na
yi kishi a wannan lokacin ai daidai ne". Ya duba agogon hannunsa
yace, "Ai gara ki yi ma Yakumbo magana mu tafi kada dare ya yi
mana."
A cikin gida babu abinda ke fitowa daga bakinsu Inna da
Yakumbo sai ban hakuri ga junansu, bayan Inna Tambai ta fiddo
mata kaya akwati shidda ta dubi kaya babu ko kallabi da ya
salwanta, aka kira yara suka rinka fidda kaya zuwa motar Amiru.
Bayan sun tafi Hadiza ta shiga dakin Inna Tambai tana
43
wanisaboon kukan tana fadin "Ni dlai Inna na shiga uku anya ko
zan yi aune a duniya?"
Inna Tambai cikin nata bacin ran, ta danne ta ce, "Dori me
za kima kanki mummunan lafazi, lɔabu komi gara da hakanı ma
ta faru, daga wajensu ba wajenmu ba, ta shi ki wanke ido mu tafi Malunfashi."
Farar-farar ana gab da kirar mangariba suka isa gidan Yaya
Amina, a lokacin Yaya Aminar na kwashin tuwo ta rinka yi mıasu
sannu da zuwa, bata kawo komi a ranta ba sai tunanin shiryeshiryen biki ne ke tafe da su, ta kammala kwashin tuwo taa kai
ma Mallan Isa dakinsa, ta rufe na sauran jama'a a kicin yayin da
ta shiga da na su Inna Tambai daki, har Hadiza ta tayas da sallar
mangariba ita ma Innar ta shigo karnmale da alwala. Amina tace,
"To bari ni ma na je na yi sallar kafin mu gaisa ko?"
Hadiza dai na can gefe daya na jan casbi lokaci-lo kaci
tana share kwallan da ke zuwa mata yayin da Inna Tambai da
Yaya Amina ke cin tuwo a cikin kwano daya. Suna ci suna hira
can Yaya Amina tace, "Wai ita kuma waccan kukan me take
ne?" Inna tambai ta rinka side yan yatsunta daya bayan claya
itama kukan ya zo mata tace, "Wallahi al'amarin ne na Hadiza
Amina kamar almara, abubuwan da daure kai, dazun nan ne sai
ga su Amiru da Yakumbonsa sun zo amsar kayansu wai sun
hakura ta auri Maitama."
Amina ta yi shiru yayin da Hadiza da Inna suka ci gaba da
sharban kukansu.
Inna Tambai tace, "Ba ki ce komi ba?" Amina ta amsa da
cewa, "To me kike so nace Tambaya? Ta kore shi yadda ta saba
korar sauran jama'arta dole sai wannan mara kunyar yaron
wanda ya zo har gabanki yace bai son ta ita kuma shi take so, to
ai shikenan gata ga shi nan, sai ta zaba ko ni ko shi, idan har ta
auri Yusufa ba ni ba ta." Inna Tambai ta yi wal da ido tace, "Haba
Amina ke ko meyasa ba kya da tausayi ne? Idan ba a tausaya
ma Hadiza ba lalle ko ba a ga laifinta ba, me ta yi anan?" Amina
ta mike tsaye tace, "ke dama ai ba kya ganin laihinta, to duk
44
abinda za kuyi a fidda ni a ciki". Ta fice daga dakin ta nufi dakin
mijinta a can ta yi hirarta har sai lokacin bacci ta je ta baiwa sU
Inna Tambai kayan shinfida ta kara fita ta nufi dakin mijinta ta
kwana a can don ma kada a kara yi mata zancen Hadiza da
Yusuf.
Da safe sun kammala kalaci, Inna Tambai bata taba bacin
rai irin na wannan rana ba, me zai sa Amina ta yi masu haka, da
kyar ta samu Aminar ta zauna da ita ta saurareta inda Inna
Tambai tace, "Wai ke ko Amina kin taba sawa, an yi ma ki istahara
a bisa al` amuran auren Hadiza?" Amina ta girgiza kai, Tambai
tace, "To ni na sa an yi mani an kuma tabbatas mani aurensu da
Yusuf ba fashi domin akwai rabo". Amina tayi tsaki tace, "Nace
ke ce ke daure mata gindi kin yi mani musu, wane irin rabo! Ko
uban wa ta aura idan dai mai haihuwa ce zata haihu, ba, dolé sai
Yusufa ba, ni dai na gaya mata tabbas ta auri Yusuf ba ni ba ta."
Daya daga cikin kannan Hadiza ya shigo yace, "Yaya ga
su Yusuf sun zo suna son ganinku." Gaba daya falon aka yi tsit
can ita Yaya Aminar tace "kace su shigo."
Dalilin zuwansu Yusuf shi ne a daren jiya ya isa Bakori ya
isa gidan Inna Tambai aka shaida masa lalle sun tafi Malunfashi
ita da Hadizan, da safe ma ya koma aka ce acan suka kwana, to
abun ya basu tsoro shi da Falanke don haka suka yanke shawarar
zuwa Malunfashin.
Inna Tambai zuciyarta ta rinka raya mata koma menene
ba kiran arziki Amina ke ma su Yusuf ba, komi ya kara jagule
mata, ita dai Hadiza na zaune na jin su idonta duk sun yi firi-firi
har kukan ya fara janyewa don kan shi.
Yusuf da Falanke suka zauna a takure bayan sun gayas da
su Yaya da Inna a lokacin gaban Yusuf ya rinka bal, bal, bal
saboda yadda ya ga fuskar Yaya babu annuri. Bayan gaisuwa ba
a sake cewa komi ba a falon, daga can gefe Falanke ya kara
rusunawa ya dan goge fuskarsa da habar babbar rigarsa, yace,
"To Inna muna nan dai muna bada hakuri a kara baiwa Yaya
Amina hakuri mun.........." Amina ta dakatar da shi tace, "Duk
45
ku tsaya ni ba tsohuwar banza ba ce, ba'a magana biyu da ni,
idan har wannan yarinyar ta amince da ku, to ni ba ni ba ta
abinda nake son fada maku kenan." Maganar Yaya Amina ta
bugi kirjin Tambaya, bata san lokacin da tace "To Amina wacece
tsohuwar banzan mai magana biyu? Idan ni kike nufi da zargin
son su Maitama ga su nan me na taba ce masu aure ne na Hadiza
da Yusuf daga Allah ne, duk iyakar kokarinmu mun yi amma
komi ya gagara saboda haka ya dace mu hakura a bar wa Allah
ikonSa." Amina ta harzuka tace, "Daman na san abinda ke ranku
kenan, to ku je a yi aure amma tsakanina da ke Hadiza Allah Ya
isa! Allah Ya tsine maki!! Allah Ya wulakanta ki a duniya!!!"
Haba nan da nan Hadiza ta sa hannu a ka ta shiga ihu na
kururuwa tace "Ai ga Yusuf din nan idan na taba amince masa a
bisa bukatarsa nan da nan tsaffin cikin anguwa kamar su Hanne
mai kuli da Uwa mai kitso suka danno kai gidan su Yaya Amina
suna tambayar "lafiya ake ihu da kururwa ko mutuwa a kai?"
Bakaken maganganun da Amina da Tambaya suke fada ma
junansu ya baiwa su Hanne bayanin abinda ke faruwa rigimace
ta zancen auren Hadiza.
Daga Falanke har Yusuf sun firgice sun daina baiwa kowa
hakuri, sai su Hanne ne ke baiwa su Amina da Tambaya hakurin.
Hadiza ta mike ta dauko gyalenta da na Inna Tambai ta
mika mata cikin kuka ta lalubo hannun Inna Tambai ta nemi ta
tashi su tafi Bakori don ta ga rigimar ta fara tsanani. Suka baro
gidan Yaya Amina cikin rudani da yanayi na fitar hankali wanda
duk ya gan su a kan hanya sai ya tsaya ya dube su yana tunanin
ko rasuwa aka yi masu?
Sun kusa isa tasha Falanke da Yusuf suka sha gabansu,
daga Innar har Hadizan sun nuna kin amincewa su shiga motar
Yusuf, amma ganin jama'a an fara zuba masu ido, dole Tambaya
ta ruko hannun Hadiza ta bude masu motar Yusuf suka shiga.
Har suka isa kofar gidan Inna Tambai Hadiza kuka take yi.
Haka nan babu wanda ya tsinka balle ya sami bakin baiwa Hadiza
magana. Inna Tambai ta fara shiga gida yayin da Hadiza ta bi
46
bayanta Yusuf ya yi sauri ya bi ta zaure yace, "Hadiza". Ta tsaya
ta dube shi yace, "Ji nan mana." Tace, "Me kake so na ji duk
jawabin da yaya ta yi bai gamsar da kai ba, koko tsinar da ka ja
mani ce bata ishe ka ba?"
Yasa halshe ya lashe busasshen labbansa yace, "Wallahi
Hadiza ko daya bani da niyya baile ra ayin son na hada ki da
yaya, ki kwantar da hankalinki in dai irin wannan zagin ne bai yi
ma auren sunna komi sai albarka, tsinuwa bisa auren da aka
shinfida akan gaskiya bata tabbata sai dai ta zama albarka".
Hadiza ta tsinka mai harara tace, "Makaryacin banza, dan
yaudara, kai yanzu nan har wata albarka zan tsinta gare ka,
wawa wanda bai san ciwon kanshi ba, wallahi randa duk ka
kara zuwa gare ni Allah ya isa tsakanina da kai, wawa kawai."
Ta juya ta shiga gida shi ma ya juya ya ja motarsa ya nufi
sabon gidansa, ya kulle kansa a dakinsa ya yi kuka. Ya yi irin
wannan kukan akan Fa'iza, daga lokacin ya daina son Fa'izar,
don haka a yau ma yana tabbatarwa zuciyarsa zai kyale Hadiza,
tsiya da wulakancin sun isa. Ya mike yayi alwaia ya zo ya gabatar
da nafila yana rokon sauki akan jarabawar da Allah ya dora masa
akan Hadiza.
Sai bayan sallar la'asar ya fito falo ya dubi kwanonin abinci
ya kawad da kan shi ya koma gefe guda ya zauna har yanzu
abinda ke mai kuna a zuci shine tsinewar Yaya Amina, wai shin
me ya yi haka da har Yaya ba za ta iya gafarta mai ba? Ko dai
dama can Yaya bata kaunarsa ne, ya mike ya shuri takalman sa,
jikinsa jallabiyace 'yar madina koriya ya nufi gidan Gwoggo Halima
a kasa ba cikin motarsa ba.
Ya samu tana sallar la'asar, ya nemi kujera ya zauna sharaf
babu kuzari a tare da shi duniya ta hadu ta cakude masa, fatarsa
a lokacin da ma ya san gidan da mutuwa take da ya kai kan sa.
Gwoggo ta sallame ta tsaya tana kallonsa, yana can wata
duniyar bai san a inda ya ke ba tunanin bacin ran da ke tattare
da shi kawai ya dame shi. Ta ce, "Wai kai ko lafiya ka ke? Kaman
kan ka faro komen neman aure da ka ke neman ka lalata kan
47
ka?"
Yusuf ya rausayar da kai gefe guda, gwanin ban tausayi
kwalla suka cika taf a idonsa yace "Ai dai shikenan gwoggo, na
hakura da Hadiza ta yi min kashedi da ita'
Gwoggo ta yi shiru tana kallon dardumar sallarta, sannan
tace, "Ba zai yiwu ba ka kyale ta in ba dai aure aka daura mata
ba. Yanzu nan dawowata daga Danja wajen Malan abokin Babana,
ya yi istahara har kwana uku ya ce lalle insha Allah za'a yi aurenku
da Hadiza domin akwai rabo." Yusuf ya zaro ido komi na shi ya
saki yace, "Gwoggo rabo fa kika ce? Rabon aurenmu!" Kanta a
sunkuye tace "Har ma rabon haihuwa. Malan yace, idan muna
shakka mu jaraba da kanmu mu gani, wato istaharar yace idan
mun kammala dukkan hidimominmu za mu kwanta sai ayi alwala
mai kyau kada a sake magana a karanci sabbi raka'a daya rak
da niyyar abinda kake so to insha Allah Ubangiji zai nuna ma
wani abu cikin baccinka haka nan Malan ya yi mani wani alkawari
yace, idan har na samo mai sawun kafar Dije zai hada wani sirri
in Allah ya yarda da kansu za su aiko mana." Yusuf ya ji wani irin
dadi yace "To Gwoggo a ina zamu samo?" Tace, "zan san yadda
na yi a daren yau na samo gobe a kai mashi domin lokaci na
kurewa." Yusuf yace, "Ina zuwa Gwoggo bari na yi ma Falanke
maganar kila zai iya samowa domin dabara gare shi."
Yusuf na tuntubar Falanke da maganar Falanke ya yi dariya
yace, "Ai ina da sawun Hadiza." Yusuf ya tambayi yadda akai,
Falanke ya bashi bayani ya dauko masa ya kai ma Gwoggo
Halima.
Gwoggo Halima tace, "Oni Halima to kaga Shu aibu har
ya fi ka kokari kai ka zauna sai sukurkucewa kake yi, ka kasa
tabuka komi." Yace, "To ai ni gwoggo ina ganin kaunata da Hadiza
kamar ba sai na yi mata asiri ba addu`ar da na ke yi ma ta isa."
Tace "E haka ne amma ance ko kana da kyau ka kara da wanka
sannan ina tsoron bakano wa ya san irin yasin din da suke aiko
wa Dijen da mahaifiyarta suke mana wannan tsiyar?" Yusuf ya
dube ta ya ce, "Wace irin yasin gwoggo?" Tace "Ai ka san shi
48
bakano akwai shi da aiki da yasin don cin galabar al amuransa а
dan kankanin lokaci.
Yayi shiru yana tunani shi kam yana ganin kamar Amiru
ba zai iya yi mai wani mugun abu ba kila dai sai ko iyayensa idan
sun ji zafin abinda yayi.
A cikin daren nan gwoggo ta sa Basiru ya kai ta gidan
Malan a Danja a motar Yusuf. Mallan yace, "Madallah ku kwantar
da hankalinku in dai matarsa ce to babu fashi zasu aiko maku
har gida."
Kwana daya da yini daya Inna Tambai ta shiga yi ma Hadiza
nasiha akan ta janye akidarta na kin auren Yusuf ta hakura
su yi aurensu domin wannan sako ne daga Allah. Hadiza
tace, "Inna ki yi hakuri idan de ina da rabon aure a duniya
zan sami wani mijin ne amma duk wulakancin da Yusuf ya
yi min sannan kuma ace daga bisani na zo na aure shi a
bisa tsinuwar mahaifiyata?" Inna Tambai ta hasala
zuciyarta, ta kara turnuka tace, "sai ki ta zama har duniya
ta nade, tunda ke da uwarki Amina kun fi kowa zuciya a
duniya ba a yi maku laifi ku yafe, daga yau insha Allah babu ruwana bisa zancen aurenki ran da duk akace an
daura maki aure da wanda kike so, idan ina duniyar ban
mutu ba kamar ubanki na zo na shiga cikin 'yan rakiya". Hadiza ta yi raurau da idanu tace, "Don Allah Inna me yayi zafi haka?" Tace "Don ba ni na haife ki ba haka nan kin nuna
min Allah bai ba ni haihuwa ba." Nan da nan Inna tasa kuka ita
ma Hadizan kukan ne dai wiwi.
Sun wuni zungur cikin mummunan yanayi babu mai cewa
wani abu, ko wanne zuciya kamar ta fashe don daci. Bayan sallar
issha'e Hadiza ta yanke shawarar zuwa ta ga Mallan lliyasu sun jima da Mallan din a dakinsa suna hira.
Zuwa can Hadiza tace "Don Allah Baba na zo da wata
muhimmiyar matsala ina so kada ka rufe mın komi ka sanarshe
ni komi dacin amsar babu komi ka gaya min." Ya dube ta da kyau
49
ya tausaya mata yace, "ina jin ki Dije, ki sawa ranki tamkar kina
magana da mahaifinki ne." Tace, "Wai Baba bayan rigimar
aurenmu da Yusuf sau nawa Yusuf ya kara zuwa wajen Babana?"
Malan Ilyasu ya dan daga kai sama nuna alamun tunani yace, "A
gaskiya Dije babu adadi ba zai kirgu ba." Tace, "Zaka iya tuna kalaman da mahaifina ya rinka yi akan Yusuf bayan rabuwarmu
kafin ya rasu?" Mallan lliya ya girgiza kai ya ce "Ai daidai da
rana daya ban taba jin marigayi Alhaji Kado ya yi mummunan
lafazi ba akan Yusufa bayan na yabonsa da yi mai kyakkyawar
addu`a kamar yadda na san yana yi maki a kodayaushe domin
lokacin da muka sami labarin an fasa aurensa da Faiza babu abinda
ya fito bakin bawan Allah nan mahaifinki sai cewa ya yi`kila dai
rabon yaron nan sai ya auri Dije ne ka ji wai an fasa aurensa,
itama kuma Dijen ka ga bata sami miji ba a can Malunfashin',sai
na ce don Allah Mallan Kado kada na sake jin zancen yaron nan
Yusuf daga bakin ka,y a yi murmushi ya ce Mallan Iliya ba
dama."
Hadiza ta yi jigum a ranta ta rinka tunanin wai wannan
wane irin so ne Baba ke yi ma Yusuf? Tayi ajiyar zuciya tace "To
Baba tunda ake zuwa neman aurena tun daga kan Yallabai Mamud
har zuwa Amiru ya taba nuna maka gara su da Yusuf?" Malan
lliya ya yi shiru sannan yasa habar riga ya goge kwalla ya ce, "Ai
akwai wata maganar da marigayi ya taba yi mani a lokacin yana
kwance asibiti ba lafiya farkon tafiyarki Malunfashi kenan, ya
nace da zancen Yusuf sai na rika yi mai fada nace ka san wanda
Allah zai ba Hadiza kila ma yafi Yusuf? Wallahi Allah ya jikan
bawan Allah nan yana kuka ya rinka ce mani shi kowa za ki aura
bai kai Yusuf ba, ko da kuwa shugaban kasa ne domin shi yana
ganin Yusuf tamkar yayanki Tasi'u inda kuma na ji dadín Yusuf
shi ne, har Alhaji Kado ya bar gidan duniya bai yada shi ba ya
nuna masa gatanci kamar Tasi`u ne domin lokutta da yawa zai
zo nan gidana ya ba ni kudi sabbi masu yawa yace ga wannan ni
ma na taba idan nace ina ka sami kudi har ka ke rabo ya kan yi
dariya yace, "Dana Yusufa ya zo ko yayi min aike."
50
Hadiza na share hawaye tace "Baba!" Ya amsa, "Na'am
Hajiya Dije?" Tace, "Wannan rana da aka sa za`a yi arenmu da
Amiru kada a canza a daura da su Yusuf din amma fa Baba Yaya
Amina sau takwas tana tsine min jiya akan Yusuf." Yace,
"Wannan duk ba komi ba ne idan kin bi Allah kin kuma yi biyayyar
aure babu abinda zaki gani sai albarka, ki ci gaba da kyautatawa
mahaifiyarki tare da neman gafararta." Wanshekare lokacin da
Mallan Iliyasu ya je wajen Inna Tambai suna daidaita yadda zasu
sawa su Yusuf kudin sadaki sai ga Hadiza ta kawo mai wasika
tace ya kai ma Yaya Amina ta neman gafara.
Malan Iliyasu ya isa gidan su Yaya Amina ya yi sa'a ya
cimma mijinta Malan Isa, bayan sun gaisa da Isa, ya shigar da
shi zaure ya kawo mai tabarma sannan suka fito shi da Amina.
Duk hanyar da Malan lliyasu ya bullo mata sai ta bulke haka dai
suka hadu shi da mijinta ana lallasinta ana bata hakuri, daga
karshe tace aje ayi aure ba za ace ta hana 'yar ta aure ba,
domin ta san in ba Yusuf ba Dije ba za ta yi aure ba amma fa babu sauran wata hulda tsakaninsu.
Mallan Isa yace, "Zancen wofi kenan idan kince babu hulda babu ruwanki da ita kenan" Ta ce, "Shikenan Mallan tunda dai
kun tilasta min na yafe a yi aure amma kowacce irin matsala ta sami kanta kar ta neme ni haka nan dukkan walakacin da zata
sami kanta gidan Yusuf babu ni babu zuri`ata."
Mallan Iliyasu ya mike ya shuri takalmansa yace, "Aure kam za'a daura domin wannan shine burin mahaifinta a zahiri
insha Allah kuma kowa sai yace gwamma da aka yi kuma albarka
na tare da Hajiya Dije duniya da lahira saboda tabi iyaye yadda duk Ubangiji ke son dan kwarai ya bi. # * *
Bayan Mallan Tukur ya dawo sallar azuhur ya shiga dakin gwoggo
Halima fuskar nan cike da annuri, bayan ya zauna ne, Halima
ke cewa, "Kai Mallan wannan irin fara'a haka kamar an
aiko mana an mana gafara?" Yayi murmushi ya ce, "Halima
kail Ai dole ne na yi murna da na ya sami aure?" Halima ta
51
danne murnarta ta nuna kamar bata gane ba tace, "Wane
dan kuma?" Mallan ya dube ta da kyau ya yi dariya yace,
Mata sarakan gulma kamar wadda ke iya bacci, wadda
bata da wani sukuni duk kin fita kamanninki a dalilin wannan
auren shi ne yanzu na zo da albishir har za` a a rinka nokewa
a nuna min ba'a san abinda na ke nufi ba, to da na Yusuf da
Dije alkawarin Allah ya cika, Mallan Iliyasu ya zo min da
zancen sadaki da komi da komi na aure yau sauran kwana
goma sha daya a daura aure ayi biki, na aiki yaro a kira min
Basiru ya zo ya je ya yi ma Yusuf din waya a Funtua.
Halima ta kasa danne murnarta, ta ce "Allah Yasa alhairi".
Anan ne Basiru ya yi sallama ya shigo ya durkusa yace "Ga ni
Baba an ce kana nemana?" Malan yace, "E ka je ka yi ma Yusuf
waya ka sanar da shi an bashi Dije." Sai Basiru ya rike baki yace,
"Ikon Allah! Baba wannan albishir din ai gara na je Abujan ta fi
karfin waya." Gwoggo Halima ta yi dariya tace "Don ka tatse
shi ko, ya fiddo kudin sabon mashin din da ka ke nacin ya sai
maka", aka kyalkyale da dariya. Malan yace, "Amma ina ji maka
tafiyar dare". Yace "Babu komi Baba, ku yi min dai addu`a Allah
Ya kiyaye hanya."
Basiru bai isa gidan Yusuf ba na Abuja sai misalin karfe
goma saura na dare, ya iske su Falanke amma Yusuf na tare da
shugabansa suna gudanar da wasu ayyukansu don haka bai zo
ye işke bakonsa ba sai karfe goma sha biyu da minti arbain da
tara ya shiga gida, ya sami Basiru ya langabe a falo yana
avengyadi.
Abinda Yusuf ya fara kawo ma zuciyarsa shine cikin daya
biyu ko zancensa da Hadiza ko kuma wani babu lafiya a gida
"Kai me ya faru Basiru, waye babu lafiya, don me baka yo min
waya?" Basiru ya yi dariya yace, "Babu komi sai alhairi yaya,
kwantar da hankalinka zancen aurenku ne ya tashi kai da Hajiya
Hadiza, har sun sa sadaki Baba Tukur ma ya biya,"
Yusuf a tsaye yake sai ya nemi kujera ya zube yana
washe baki yana shafar kai yace, "Godiya ta tabbata ga Sarki
Allah, Ubangiji Allah Ka ba ni ikon rike amana, wai ka fadawa
Falanke kuwa, ya ban iske shi nan ba?" Basiru ya ce, "Gaskiya
kin gaya mai na yi domin ina ganin wannan albishir din kai ya fi
cancanta na fara sanar mawa."
Yusuf ya kwallawa yaronsa Jerry kira yace, "Kira Falanke
a baskwata." Falanke ya iso ido cike da bacci, Yusuf yace "To.
shugaban mayaka, aure fa ya tabbata akan mu, ni da Hadita
Faianke yace, "Ranka shi dade idan na yi guda ban yì laifi ba?
Yusuf yace, "Don Allah kada kayi domin ko wajen matan ma
ance babu kyau balle kuma namiji." Ai sai Falanke ya shiga rawa.
yana juyawa dama abu ga mai kiba Yusuf da Basiru dariya suke
suna tintsirawa har dai Yusuf ya mike ya fiddo kudi a aljihunsa
ya rinka likawa Falanke suna ta tintsirar dariya Yusuf yace, "To
ya isa Falanke sai kuma ran biki rannan za kayi rawa da `yan
koroso." Falanke yace, "Ana magana ran ka shi dade? Amma
don Allah ina rokon shaddar nan wadda ka zuba a ranar da muka
je gaisuwar Baba Kado, ita zan zuba ran daurin aure." Yusuf
yace "baka son a dunka maka sabbi?" Yace, "Wa`ancan nake so
ranka shi dade." Basiru yace, "Ni ma yaya ina tunin mashin dina."
Yusuf ya ce, “Kai sakarai ne wata mota nake son saya maka ko
don saboda kai su Gwoggo anguwa, kila ma gobe za` ai cinikin motar.". Basiru ya rasa kalmar da zai yi godiya anan ya kara amincewa lalle ba karamin so yaya ke ma Hadiza ba.
Yusuf kwana yayi bai runtsa ba, bayan ya gabatar da nafila
ya yi ma Baba Kado addu'a domin ya san darajarsa ya sami
Hadiza sannan ya yi ma Jallah godiya sai ya zauna ya fiddo biro
da takarda ya shiga rubuta abubuwan da zai shirya a lehen Hadiza.
Da safe bai nufi ofis ba sai gidan shugabansa ya yi masa albishir. Anan ne Shugaba yace "zancen tafiyar mu Legos aiki
babu kenan. Sai ka fara hutu daga gobe don ka ji dadin gudanar
da hidimar bikin tunda lokaci ya kure." Yusuf yace, "A'a ranka shi dade za mu iya zuwa aikin Legos domin zan yi anfani da
wannan damar na hado lehe daga can."
Yusuf ya sallami Falanke da Basiru yace su tafi da motarsa
53
su jirasa a Kaduna za su aiki Legos na kwana biyu.
A Legos Yusuf ya dauki yarinyar kanfaninsu Bimbo suka
shiga kasuwa ya zabo lesisika na shiga tsara da atanpopi na fita
kunya, da duk wani abu da ya dace da rayiwar diya mace 'yar
bimi. Bimbo ta sa Yusuf ya sayi akwati hudu da kit na biyar. A
gaskiya ya ci mutuncin naira, naira kuma ta mutunta kaunarsa
ga masoyiyarsa Hadiza.
Da suka yi sallama da Shugaba ya kawo cek na dubu dari
biyu da hamsin ya bashi yace, "Ga wannan a sai ma amarya dan
kunne sai mun zo daurin aure." Yusuf ya ce, "Ranka shi dade
wannan ai kace a sai ma `yan Bakori dan kunne ba amarya
kadai ba, Allah ya saka da alhairi." Jirgi ya sauke Yusuf a Kaduna
su Felanke na jiransa ya zuba akwatunan lehe sai gida Bakori.
Wanshekare dangin Gwoggo Halima suka shirya zuwa kai
lehe. Yusuf ya kashe ya tsare yana fadin don Allah Gwoggo idan
an je ace ma Inna Tambai ta ba Hadiza wannan dan karamin
akwatin ta adana domin duk zinari ne a ciki, idan ba zata iya
adanawa ba a dawo min da shi zan kai banki saboda taron
jama'a." Gwoggo Halima ta danna mai harara tace, "Wai kai
mevasa ba ka da kunya ne, lehen ma sai ka fadi yadda za`a yi?"
Bayan masu kai lehe sun nufi gidan Inna Tambai su Ankudi
da Sabura sune 'yan taryar baki. Duk da su Ankudi suke kauyawa
amma sun san darajar zinari don haka suka fara rade-radin ko ba
komi lehen Yusuf ya fi na Amiru tsada idan akai la'akari da
tsadaddun zinaran da ya zuba.
A daidai lokacin da ake shagalin amsar lehe, shi kuma
Yusuf da Falanke na can takure zauren Mallan lliya suna godiya
waien Mallan din, anan ne Mallan lliya yace, "To Yusufa aure
abu ne mai wuya ga wanda bai fahinci dokokin Allah ba amma
kuma abu ne mai sauki idan aka bi tsarin Sarki Allah, haka nan
wanda duk ya